Ticker

6/recent/ticker-posts

Barazanar Dabi’un Zamani Ga Al’umma: Nazari Kan Jigon Wakar Dabi’un Zamani Ta Imamu Sani Gaya

Citation: Ɗangambo, H.A. and  Mainasara, A. (2024). Barazanar Ɗabi’un Zamani ga Al’umma: Nazari Kan Jigon Waƙar Ɗabi’un Zamani Ta Imamu Sani Gaya. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 233-241. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.028.

BARAZANAR ƊABI’UN ZAMANI GA AL’UMMA: NAZARI KAN JIGON WAƘAR ƊABI’UN ZAMANI TA IMAMU SANI GAYA

Halima Abdulƙadir Ɗangambo
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Bayero, Kano

Adamu Mainasara
Sashen Koyar da Harsunan Afirka
Jami’ar Al
ƙalam, Katsina

Tsakure:

Yadda barazana da ɗabi'un zamani suka dabaibaye rayuwar al’ummar Hausawa a yau, babban ƙalubale ne da ya daɗe ana tattaunawa a kai, wanda marubuta waƙoƙin Hausa ba a bar su a baya ba wajen bayar da gudummawa a wannan vangare, a ƙoƙarinsu na isar da saƙon don kwalliya ta biya kuɗin sabulu. Hakan ce ta sa aka tsara wannan takarda ta hanyar nazartar waƙar “Ɗabi’un Zamani”, ta Malam Imamu Sani Gaya, don fito da wannan barazana da ɗabi’un zamani ke tattare da su don kamo bakin zaren; wanda wannan ita ce babbar manufar takardar. Hanyoyin da wannan takarda ta bi wajen cim ma manufarta sun haɗa da karantawa tare da nazarin baitocin waƙar wadda aka samo daga wani littafi mai suna Waƙoƙin Malam Imamu Sani Gaya (2018). Sai kuma tattaunawa da wasu jama’a don ƙara fahimtar ire-iren ɗabi’u waɗanda zamani ne ya kawo su. Dangane da ra’in bincike, wannan takarda, an yi amfani da ra’in Gudummawar Adabi ga Al’umma da kuma ra’in Ɗangambo (2007) don cim ma manufarta. A sakamakon gudanar da wannan bincike an fahimci cewa, marubuta waƙoƙi sun taka rawa wajen kakkave ire-iren waɗannan munanan ɗabi'u, da zamani ya kawo a cikin waƙoƙinsu. Sannan an gano cewa munanan ɗabi’u sun yi kaka-gida a zukatan jama’a waɗanda idan aka yi ƙoƙari wajen magance su, to za a samu tsaftatacciyar al’umma.

Fitilun Kalmomi: Barazana, Ɗabi’un Zamani, Al’umma, Waƙar Ɗabi’un Zamani, Imamu Sani Gaya

Gabatarwa

Kamar yadda aka fara nunawa tun a tsakure, manufar rubuta wannan takarda ita ce, yin nazari a kan wannan waƙa mai suna “Ɗabi’un zamani”, da niyyar jan hankali ga al’umma wajen kiyayewa tare da kauce wa waɗannan ɗabi’u waɗanda idan an lura zamani ne da ya yi tasiri a kan al’umma Hausawa ya haifar da su. A daidai wannan wuri, bari mu gabatar da abubuwan da wannan takarda ta ƙunsa a taƙaic.

Da farko, akwai bayanai a kan dalilin da ya sa aka rubuta waƙar. Sannan sai bita a kan ayyukan magabata da kawo bayanai a kan ma’amar kalmar “barazana” da ma’anar “ɗabi’a/ɗabi’u” da kuma me ake nufi da ɗabi’un zamani. Daga nan sai bayanin da ya shafi ra’in bincike. Sai kuma gundarin nazarin wanda ya haɗa da abubuwa kamar su tarihin marubucin waƙar da kuma cikakken nazari a kan jigon waƙar da kuma sharhin jigon waƙar bisa ra’in gudummawar adabi ga al’umma.

Bita

Dangane da bitar ayyukan da aka gudanar a ƙarƙashin inuwar rubutattun waƙoƙi, a kan abin da ya shafi jigoginsu, za a ga cewa ba baƙon abu ba ne; domin an sha gudanar da aikace-aikace masu tarin yawa. Sai dai abin da za a lura da shi a nan shi ne, kowane jigo yana da nasa irin tasirin da muhimmanin matsayi a tsakanin al’umma. Sannan marubuta suna tsara shi ne gwargwadon bukatar al’umma ga wani muhimmin al’amari da ya dangance shi.

Wasu aikace-aikace an gudanar da su a matsayin kundayen neman digiri na ɗaya zuwa na uku. Sannan akwai wasu aikace-aikacen da aka rubuta a matsayin littattafai. Da takardu na ilimi da sauransu da suka shafi nazarin jigo a rubutattun waƙoƙin Hausa.

Waɗannan aikace-aikace sun haɗa da: Ɗangambo (1990) da Mukhtar (2005) da Ɗangambo (2007) da Yahya (2016) da Birnin-Tudu (2009) da (2011) da Dunfawa (1990) da Auta (2017) da Bunza (2014) da Halima A. Ɗangambo (2021) da (2014) da (2011) da (2002) da (Sa’id 2002) da dai makamantansu da yawa.

Manufar Rubuta Waƙar

Babbar manufa da rubuta wannan waƙa, wadda ta kasance ɗaya ce daga cikin waƙoƙin da Malam Imamu Sani Gaya ya rubuta, a cikin littafin nan mai suna Waƙoƙin Malam Imam Sani Gaya (2018) wanda Dakta Abdulbasid Imam Sani ya tattara tare da rubutawa, ita ce saboda koyar da al’umma wa’azi da kuma nusar da su al’amuran rayuwarsu. Wannan kuwa ya yi daidai da tunanin cewa shi wannan marubuci yana ɗaya daga cikin malaman da suka rubuta waƙoƙi a fannoni daban-daban, kamar fiƙihu da tauhidi da wa’azi da faɗakarwa da siyasa da sauransu[1].

Ma’anar Kalmar Barazana

Wannan kalma idan an yi mata kallon tsanaki, za a ga cewa Bahaushiyar kalma ce, ma’ana kalma ce ta asali ta Hausawa, ba aro ta aka yi daga wani harshe ba. A nan za a iya bayyana wannan kalma da cewa tana nufin haɗari ko ban-tsoro ko kuma wani abu da zai iya haifar da ko kawo wani naƙasu ko wata matsala ga rayuwa.

Ma’anar Ɗabi’a/Ɗabi’u

Kalmar “ɗabi’a”, tana nufin halayya. Ɗabi’a tilo ke nan, yayin da kuma “ɗabi’u” jami’i ne na ɗabi’a. Ɗabi’a/halayya iri biyu ce: akwai mai kyau, akwai kuma marar kyau (mummunar ɗabi’a). A al’adance, al’ummar Hausawa tana horon ‘ya’yanta da su gudanar da kyawawan ɗabi’u, su kuma guje wa munanan, ba don komai ba, sai don samun ingantacciyar al’umma. Babu ala’da[2] ta mutum ɗaya, sai dai akwai ɗabi’a/halayya ta mutum ɗaya. Haka kuma ɗabi’a tana da wuyar sauyawa, a wasu lokutan kuma takan sauya cikin ɗan ƙaramin lokaci saboda wasu dalilai da kan taso[3].

Ɗabi’un Zamani

Ɗabi’un zamani nau’i ne na ɗabi’u wanda kan wanzu a tsakanin al’umma sakamakon cuɗanyarsu da baƙi. Ire-iren waɗannan ɗabi’u suna kawo sauyi tare da yin tasiri a tsakanin al’umma musamman matasa. Waɗannan ɗabi’u har ila yau, ɗabi’u ne baƙi mabambanta da ake samu. Dalili a nan shi ne ɗabi’un kan kasance daban-daban gwargwadon ire-iren al’ummomin da suka maƙwabci wata al’umma. Sannan gwargwadon yadda al’umma ta karvi waɗannan ɗabi’u, to iya gwargwadon yadda waɗannan ɗabi’u kan samu gurbin zama ke nan, su yi kaka-gida. Ma’ana idan al’umma ta gamu da wannan barazana, to hakan kna yi sanadiyyar sauyawarta ta fuskoki daban-daban, musamman dai vangaren munanan ɗabi’un irin su kwaikwayon sanya sutura na wasu al’ummu da tarbiyyarsu da sha’anin zamantakewarsu da sauransu.

A taƙaice, ɗabi’un zamani suna nufin, ko mu ce suna nuni ne da ɗabi’u, waɗanda sauyawa da jujjuyawar lokacin rayuwa kan haifar su kuma zama jini da tsoka a lokaci guda. A irin haka ne al’umma kan faɗakar da ‘ya’yanta da su riƙi ɗabi’u na gari, da kuma yin watsi da na banza; da dai sauran abubuwa makamantan waɗannan.

Ra’in[4] Bincike

Wannan takarda ta zavi ra’o’i guda biyu don gudanar da wannan aiki. Sannan kowane ra’i daga cikin waɗannan ra’o’in da aka zava, akwai dalilin zavensa. Ma’ana, an lura cewa ra’o’in sun dace da manufar takardar. Misali ra’in “Gudummawar Adabi ga Al’umma”, an zave shi ne saboda dacewarsa ta fuskar kallon yadda ya kasance cewa, ya yi tanadi a kan nazarin adabi game da tsarin zamantakewar al’umma, da kuma yadda adabi yake tafiya da al’adu da kuma gudumamwarsa ko tasirinsa ko amfaninsa. Za a fahimci haka idan aka dubi jigon waƙar da ke magana a kan ɗabi’u/halaye na al’umma don kawo gyara a cikin al’umma. Haka kuma an zavi ra’in Ɗangambo (2007) saboda dacewarsa da manufar takardar dangane da abin da ya shafi matakan nazarin rubutacciyar waƙa. Idan kuma an duba za a ga cewa wannan waƙa da aka nazarci jigonta ta kasance rubutacciya ce.

Barazanar Ɗabi’un Zamani Daga Alƙalamin Malam Imamu Sani Gaya

Da farko, bari mu fara kawo taƙaitaccen tarihin rayuwar marubucin waƙar kafin mu shiga nazari da sharhi, dangane da yadda ɗabi’un zamani suka zama barazana a tsakanin al’umma, kamar yadda alƙalamin rubutu na wannan marubuci ya nuna mana daga wannan waƙa, mai suna “Ɗabi’un Zamani”; kamar yadda aka fara nunawa a can baya.

Tarihin Marubuci[5]

An haifi Malam Imamu Sani Gabaya a shekara ta 1943 a garin Gaya da ke cikin Jihar Kano, mahaifinsa Malam Sani Gaya, wanda aka fi sani da Malam Maidarasu, Alamarma ne kuma shahararren malamin addinin Musulunci ne da ke zaune a garin Gaya. Malam Imam ya tashi wajen mahaifinsa inda ya fara karatu a gabansa tare da taimakon ‘yan’uwansa ya haddace Alƙur’ani tun yana ƙarami a lokacin da bai wuce shekara 15 ba. Sannan ya yi saukoki na satu da dama. Bayan haka, ya rubuta Alƙur’ani har sau bakwai.

Daga baya Malam ya duƙufa wajen neman ilimin addinin Musulunci a wajen mahaifinsa, ya karanta littattafai da ake karantawa a karatun zaure tun daga Ahlari har Mukhtasar. Haka a vangaren lugga ya karanta littattafan nahawu da waƙoƙin Larabci, kamar su Alburda da Hamziyya da Ishiriniyya har Muƙama da Sha’ara’ul Jahiliyya. Haka zalika, ya karanta littafin Kifaya a vangaren Tafsir.

Wannan malami bai tsaya a nan ba, domin kuwa ya dage wajen zurfafa a vangarori daban-daban musamman ilimin Tajwid inda ya halarci wato Daura da Larabawa suka gabatar a birnin Kano domin ba da horo a kan ilimin Tajwid a ilimance da aikace.

Malamin ya tashi a gidan makaranta, wannan ta sa ba abin da yasa a gaba illa harkar koyo da koyarwa. Saboda haka ya duƙufa wajen havaka makarantarsu da taimaka wa mahaifinsa, inda ya dage wajen havaka wannan makaranta har sai da ta zama shahararriyar makaranta a Kano.

Malam Imamu ya rasu, Allah ya yi masa rahama a garin Gaya cikin shekarar 1993, ya bar tarin waƙoƙi a vangarori da fannonin ilimi da dama. Wasu ya rubuta su da Hausar boko, wasu kuma da Hausar Ajami”.

Jigon Waƙar

Abubuwan da wannan vangare ya ƙunsa sun haɗa da furucin ƙwayar jigo na waƙar da taƙaita jigon waƙar da kuma warƙarar da shimfiɗa na jigon waƙar.

Wannan waƙa kuma tana yin magana ne a kan yadda sababbin ɗabi’u na zamani suka mamayi al’ummar Hausawa.

Furucin Gundarin Jigo

Dangane da furucin gundarin jigo, wato ƙwayar jigon wannan waƙa shi ne faɗakarwa ne a kan illar da ɗabi'un zamani suka yi ga al’ummar Hausawa, musamman yanayin sanya suturu wanda ake alaƙantawa da cigaba, amma a zahiri lalataccen cigaba ne, ko ma mu ce cigaban mai haƙan rijiya ne.

Dubia abin da marubucin waƙar ya ce:

“Kan abin da ya zo wa zamani,

 Wai ana cewa ma cigaba”.

“Sai ka hangi mutum ya kai mutum,

 Suttura tasa ba suturarsa ba”

(baiti na 8-9).

A cikin waɗannan baitoci guda biyu, ƙwayar jigon wannan waƙa ya fito, inda marubucin ya nuna cewa waƙar ta ƙunshi faɗakarwa ne a kan abin da ya zo wa wannan zamani na yadda ake kauce wa kyawawan ɗabi’u na gargajiya, ana biye wa ɗabi’u da ma al’adun baƙi, musamman munanan. Misali yadda aka riƙi suturu musamman na Turawan yamma da kuma yadda mata kamar mazan ba a bar su a baya ba wajen yin koyi da waɗannan ɗabi’u na zamani ta vangarorin rayuwa iri daban-daban.

Jigo a Gajarce

Wannan waƙa idan mun dube ta za mu ga cewa tana da yawan adadin baitoci guda 101 a cikin zubin ƙwar biyu. Waɗannan adadin baitoci su ne marubucin ya sarrafa ya zuba manufofin har ya gina jigonta. A nan za a ga yadda marubucin ya karkasa manufofin a cikin waɗannan baitoci.

Ga waƙar a gajarce:

Bt. na 1-7: Addu’ar buɗewa baitocin suka ƙunsa, inda Malam Imamu ya yi godiya ga Allah da kirari da kuma salati ga shugabanmu Annabi Muhammadu (S.A.W.) da sahabbansa da dai sauransu.

Bt. na 8-9: Furucin gundarin jigo na waƙar.

Bt. na 10-17: Bayanai ne da suka shafi irin yadda mutane suke sanya suturu da suka kauce wa al’adar Hausawa. Ya kuma kawo bayanai na yadda maza da mata suka raja’a ga waɗannan ɗabi’un zamani musamman yanayin sanya sutura.

Bt. na 18-20 :Magana ya yi a kan yadda ire-iren waɗannan ɗabi’u na zamani suka bayyana ƙiri-ƙiri a nan ƙasar Hausa birni da ƙauye.

Bt. na 21-29 :Ya danganci bayanai ne a kan ƙoƙarin marubucin wajen nusar da jama’a cewa su daina kwaikwayo wasu a kan abubuwan da ba su dace ba

Bt. na 30-40 :Waɗannan baitocin sun ƙunshi bayani ne a kan shawarwarin da marubucin ya yi ƙoƙarin bayarwa ga mutane a kan wannan matsala.

Bt. na 41-52: Baitocin sun shafi magana ne a kan cigaba ko bayanan jigo na shawarwari a kan yadda iyaye za su kiyaye tarbiyyar ‘ya’yansu don samun tsira duniya da lahira.

Bt. na 53-69 :Bayani ne tare da yin kira ga jama’a da cewa su guje wa bin ƙawace-ƙawacen da rayuwar ƙarya da Turawan yamma suka zo wa Hausawa da su.

Bt. na 70-86 :Ya shafi bayanai a kan mu’ujizozin halittu na Allah da yadda duniya take dangane da yanayin yadda Allah ya ƙage ta don ya zama izini a kan komawa ga Allah don buwayarsa. Sai bayani a kan yadda jama’a suke koyi a kan wasu munanan ɗabi’u da suka shafi ƙayyade iyali da tsara su.

Bt. na 87-90 :Ya ƙunshi bayani a kan yadda ni’imomin Ubangiji da kyautarsa take ga bayinsa.

Bt. na 91-97 :Ya ƙunshi bayani a kanyadda za a koma ga Allah ta hanyar yin addu’o’i da tuba da neman taimakon Allah.

Bt. na 98: Addu’ar rufewa

Bt. na 99-100 : Waɗannan baitoci sun ƙunshi Ramzi, inda ya nuna cewa ya yi waƙar ne a shekara ta 1970.

Bt. na 101: Bayyana sunan wanda ya yi waƙar, wato Malam Imam Sani Gaya.

Warwara da Shimfiɗar Jigon Waƙar

Jigon wannan waƙa kamar yadda aka fara nunawa a baya shi ne faɗakarwa a kan yadda aka rungumi al’adu da ɗabi’un zamani. Haka kuma kira ne da babbar murya ga iyaye a kan waɗannan ɗabi’u na zamani da matasa maza da mata suka ara suka yafa, kamar yadda marubucin ya yi ƙoƙarin nunawa a ƙoƙarinsa na isar da jigon waƙar.

Misali dubi wannan baiti na farko inda furucin gurdarin jigo na waƙar ya bayyana:

 “Kan abin da ya zo wa zamani,

 Wai ana cewa ma cigaba”.

(baiti na 8).

Lallai kuwa idan aka dubi wannan baiti za a ga yadda ɗabi’un zamani suka zama barazana a tsakanin al’ummar Hausawa duba da yadda abin ya zama ruwan-dare game duniya. Wannan kuwa barazana ce kuma babban ƙalubale ne duba da yadda al’umma take yawan kokawa da matsalar, wanda hakan kan haifar da illoli a rayuwa ta fuskoki iri daban-daban; musamman ma ga matasa maza da mata.

Baiti na 9, wanda shi ma ya daɗa fito da gundarin jigon waƙar, ya bayyana yadda mutane suke sanya suturu da suka kauce wa al’adar Hausawa, suke kuma aikata ɗabi’u marasa kyau da sunan cigaba.

Dubi abin da baitin yake cewa:

“Sai ka hangi mutum ya kai mutum,

 Suttura tasa ba suturarsa ba”

(bt. na 9).

A nan wajen za a ga yadda Malam Imamu ya bayyana yadda mutane a yau suke kwaikwayon ɗabi’u musamman wajen yanayin sanya tufafi ta yadda da ka ga mutum ba za ka ce Bahaushe ba ne, sai idan ya yi magana, dalili shi ne yanayin shigarsa bai dace da suturu irin na al'ummar Hausawa ba.

Haka kuma dubi waɗannan baitocin da suke ƙasa:

Kyan Musulmi dai a ga suttura,

 Tai ba za a ga alarassa ba.

“Wadda za ta suturce ko’ina,

 Ba ka gan shi ka kau da idonka ba”.

Inda ma munin ya ta’azzara,

 Ka ga mata ba da shigarsu ba”.

Sai su sa wando na matsar jiki,

 Taguwar ba za ta zarce cibi ba.

Ko su ɗaura sikel ɗan tofi ne,

 Wanda bai kai inci goma ba”.

Ba zama ba tsuguno da shi,

 Sunkuyo ma ba zai samu ba” 

(Bt. na 12-17)

A cigaba da warware jigon wannan waƙa da ke nuni da faɗakarwa a kan barazanar da ke tattare da yadda ɗabi’u na mutane suka lalace a wannan zamani musamman a sakamakon zuwan Turawa, waɗannan baitoci guda shida (6) da ke sama sun bayyana cigaban warware wannan jigo.

Misali, idan aka duba baiti na 12 da na 13, za a ga yadda marubucin ya nuna yadda ya kamata suturar Musulmi da ya amsa sunansa na Musulmi ta kasance sutura ce yalwatacciya wadda za ta rufe masa tsiraicinsa ba wadda za ta bayyana ba. Haka kuma suturar ta kasance mai ma’ana ba wadda da an kalli mutum a kawar da ido ba, saboda rashin dacewa; musamman kan abin da ya danganci suturta al’aura.

Mawaƙin bai gushe ba, sai da ya tavo vangaren mata, musamman ‘yammata masu sanya suturun banza don kwaikwayon al’adun baƙi, musamman ma Turawa. Idan aka duba baiti na 14 da na 15 da na 16 da kuma na 17; za a ga yadda marubucin ya tattauna a kan ɗabi’un banza na zamani da suka zama barazana ga ‘ya’yan Hausawa, inda a daidai nan ya buga misali da yara ‘yammata saboda ta’azzara da matsalar ta yi. Misali a cikin bayanan jigo na waƙar da ke ƙarƙashin waɗannan baitoci an ji inda ya nuna cewa mata suna sanya wando mai matse jiki, wanda wannan ba ɗabi’a ce mai kyau ba, hasali ma ba suturar Hausawa ba ce. Sannan marubucin ya cigaba da nuna yadda mata suke sanya taguwa[6]. Har ila yau, ya ce ita wannan taguwar ma da suke sanyawa ‘yar mitsil ce, ma’ana ‘yar ƙarama ce wadda ko cibiya ba ta rufewa idan an sanya ta.

Haka kuma waɗannan baitoci sun ƙara fito da yanayin yadda mata suke sanya sikel wanda shi ma ba a sanya wadatacce, maimakon zani da Hausawa suka saba amfani da shi. A nan sai da marubucin ya ma bayyana kwatankwacin girman sikel ɗin da matan yanzu (Hausawa) suke sanyawa, inda ya ce bai kai inci goma (10) ba. Da an dubi wannan bayani na sigar wannan nau’i na sikel, za a ga cewa lallai ƙanƙani ne wanda ba zai suturce jiki ba.

Dubi kuma wasu misalan:

Kyan Musulmi ko’ina yake,

 Ko ƙasa tasu ko ba tasu ba.

Suturar muslinci suttura,

 Ce da arne ma bai ƙi ba.

Gun maza na faɗa haka ba gurin,

 Mace wadda ta kai girmanta”.

(bt. na 20, 23, 25)

Waɗannan baitoci sun bayyana yadda mawaƙin ya nuna yadda ya kamata mutane su dinga suturce jikinsu a matsayinsu na Musulmi a duk inda suka tsinci kansu ko da a wajen ƙasar Hausa ne ba don komai ba, sai don riƙo da al’ada da kuma koyarwar addinin Musulunci. A nan ya daɗa jaddada yadda tsarin yanayin suturar Musulmi take don a fahimci cewa koda a wajen waɗanda ba Musulmi ba, suturar ba su ce ba ta dace ba. Daga nan sai marubucin ya tavo bayani na yanayin sanya tufafi na maza da mata da kuma irin dokokin da aka yi tanadi. A nan ya nuna cewa wannan yanayi na sanya sutura musamman a birane a matsayin ƙasar Hausa, ƙasar Musulunci bai dace ba.

Sannan ya cigaba da bayani a kan waɗannan yanaye-yanaye na sanya tufafi da yadda ya kamata a dinga kulawa musamman suturun ‘ya’ya mata.

Dubi baiti na 26, 27, 28 – baiti na 30, za a ga yadda Malam Imam ya cigaba da zayyano waɗannan ƙa’idojin na sanya sutura.

A wasu wuraren an ga yadda mawaƙin ya cigaba da warware mana jigon waƙar ta hanyar ba da shawarwari ga jama’a game da wannan matsala. Ya nuna yadda ya kamata iyaye su kiyaye da kula da tarbiyyar ‘ya’yansu. Dalili a nan shi ne, saboda wasu iyayen a yau suna yi wa tarbiyyar ‘ya’yansu riƙon sakainar-kashi, riƙon ko-in-kula.

Dubi waɗannan baitoci na ƙasa suka ƙunsa don tabbatar da bayanan da aka yi:

“Uzubillah mun neman tsari,

 Wus da lalataccen cigaba”.

“Ya jama’a na yi kiran ku duk,

 Shawara ce nai ba dole ba”.

Kui hanin ‘ya’yanku ga sutturar,

 Da ba za ta rufe surarsu ba.

Har uba na yi wa ‘ya tasa,

 ‘Yan tufafi ba na kininsa ba”.

Mai ya sanya iyaye yin haka,

 Cigaban jahilci ne gaba”.

Dole ne ga iyaye sa ido,

Gun da ‘ya’ya nasu komai cigaba”.

(Bt. na 30, 31, 33, 35, 38, 41).

Idan aka dubi waɗannan baitoci, za a ga yadda jigon waƙar ya daɗa fitowa sosai musamman yadda marubucin waƙar ya ja hankali da nuna cewa waɗannan ɗabi’un zamani da ake cewa wai cigaba ne, to ba cigaba gaba ba ne, lalacewa ce kawai. Don haka, sai ya yi ƙoƙarin kawo wasu shawarwari na yadda iyaye ya kamata su sa ido a kan tarbiyyar ‘ya’yansu a kan yanayin sanya tufafi a wannan zaman. Ma’ana iyaye su yi ƙoƙarin hana ‘ya’yansu yin shigar da ba ta kamace su ba. Sannan ya ƙarasa jan hankalin da cewa wannan cigaba da wasu suke iƙirari, to jahilci ne zalla da rashin sanin ciwon kai. Don haka, iyaye su tashi tsaye, su sa ido.

Ga wasu misalan har ila yau, waɗanda marubucin ya zayyano da za su daɗa taimaka wa iyaye wajen kula da tarbiyyar ‘ya’yansu, wanda hakan da marubucin waƙar ya yi faɗakarwa ce kai tsaye don a samu a shawo kan wannan barazana.

Dubi abin da ya ce a wasu baitoci:

“Don su tashi da kirki hankali,

 Nutsuwa tasu ba shirmansu ba”.

“Don su san haƙƙoƙin lahira,

 Duniyarsu ba ta tozarta ba.

Ɗan’uwa za nai ma shawara,

 Kar ka ɗau hanya ba tasa ba”.

(bt. na 42, 43, 47)

Waɗannan baitoci haƙiƙa sun daɗa faɗakar da iyaye a kan tarbiyyar yara don guje wa munanan ɗabi;un zamani.

Haka ma baiti na 48 - 52 duk cigaba ne a kan wannan ƙaramar manufa.

Ga wasu misalan:

Daina jin ƙaryoyin kimiya,

 Masu ƙaryar su san cigaba”.

Ko su yo injin ɗin rayuwa,

 Maganin mutuwa so jarraba.

Wanda za a saka wa ɗan’adam,

 Yai zamansa ba a bunne shi ba.

Na sani ko da a Amerika,

 Ai dubun miliyan ba a lura ba.

Ko a Faris ko a Ingila,

 A sayar shi ba zai je Rasha ba.

In ko Rasha ce ta fito da shi,

 To Amerika ba ta gan shi ba”.

Kimiyya ta ƙagi abubuwa,

 Wanda ba can duk ba a san su ba.

Ko ga mota ko ga su radiyo,

 Mashinoni da ba a san su ba.

Ka ga ma jirgin sama ga su nan,

 Ko ina tafi ba da gumin ka ba.

(bt. na 53-65)

Idan aka warware manufofin da ke ƙunshe cikin waɗannan baitoci, za a ga yadda marubucin ya yi kira ga jama’a a kan su guje wa ƙaryace-ƙaryace na kayayyakin kimiyya da Turawa suka ƙirƙiro cewa ba su samu damar yin hakan ba, sai da huwacewar Ubangiji; wanda inda a san ransu ne da sun ƙirƙiri wasu na’u’ori da za su hana aukuwar wasu abubuwa. Misali na’urar hana mutuwa balle a binne mutane.

Baiti na 53, shi ne ya ƙunshi manufar da ta bayyana cewa a guji Turawa musamman dangane da wasu abubuwa da suka zo wa da ‘yan ƙasa da su a matsayin cigaba.

Shi kuwa baiti na 54 – 55 marubucin ya buga misali ne da samar da injina da Turawa suka yi, amma duk da haka ba za su iya ƙirƙirar abubuwan ba face waɗanda Allah ya nufa. Don haka, kada a biye musu, a tsaya ga al’ada da addini, a kuma fahimci cewa ba abin da yake wanzuwa sai da izinin Allah.

A baiti na 56-65, a nan ne marubucin ya zayyano wasu kayayyakim kimiyya irin su "radiyo" da "mota" da "mashin" da "jirgin sama" da Turawa suka kawo wa Hausawa, tare da kawo sunayen wasu mashahuran ƙasashe irin su "Amurka" da "Ingila" da "Rasha" da "Farisa" don nuna cewa su ne ƙololuwa a kan harkar cigaba na kimiyya, amma duk da haka waɗannan ƙirƙire-ƙirƙire ba su samu wanzuwa ba, sai da Allah ya nufa, ma’ana duk waɗannan ƙirƙire-ƙirƙire hikima ce wadda take a bayyane daga Allah zuwa bayinsa.

Haka ma wasu baitocin da suka biyo bayan baiti na 65, wato baiti na 66-86 duk bayanai ne da suka ƙunshi mu’ujizozi da halittun Allah da baiwarsa da yadda ya ƙagi duniya da abin da ke cikinta. Sai kuma ya cigaba da bayani a kan yadda jama’a suke danganta waɗannan ɗabi’u na zamani tare da tunanin cewa waɗannan ɗabi’u da wasu suke koyi duk ba su dace ba. Misali ɗabi’ar nan ta ƙin son tara ‘ya’ya, wato tsarin iyali da ƙayyade su.

A nan idan an lura waɗannan manufofi da ke cikin baitocin waɗanda suka shafi kimiyya, za a ga cewa marubucin yana so ne ya ja hankalin jama’a cewa ko su Turawan da suke iƙirarin sun cigaba, Allah ne ya ƙaddara za su samar da waɗannan kayayyakin kimiyya. Don haka, a fahimci cewa tsantsar cigaba shi ne bin Allah da Manzonsa, ba wai bin al’adun Turawa da abubuwan da suka samar (waɗanda sukan shagaltar) su ne cigaba ba; kamar yadda wasu suka ɗauka.

Ga wasu muhimmai daga cikin baitocin waƙar don ƙara fahimtar waɗannan bayanai da aka yi a sama.

“Wanga duk hikima ce bayyane,

 Da dabara ba ƙydyrubsu ba”.

Don ko komai sai sun jarraba,

 Ba karo caya ke ƙago su ba”.

“Wanga Allah ne ya gwada musu,

 Ba da burga ko kirunsu ba”.

Duniya duk ƙaryar kimiya,

 Ba su san ƙaƙa aka yi ta”.

“Masu himmar gyaran haihuwa,

 Sun makance ba ta idonsu ba”.

Lokacin da hana ta ya tabbata,

 Haihuwa a bira sai cigaba”.

Jahilai ba su san himmarsa ba,

 Sai ku bar masa komai Rabbana”.

(bt. na 66,67,68,71,76,80,86).

Baitocin da ke biyewa waɗannan su kuma su ƙunshi bayani ne a kan cigaban jigon dangane da sauran ni’imomin Ubangiji. Don haka, kyautuwa ya yi mutane su kama hanyar Allah da kuma gode masa da ni’imomin da ya yi gare su, don samun tsira, amma ba biye wa ɗabi’un zamani ba wanda kan kai mutum ga halaka.

(Dubi baiti na 87 – 90)

Ga kuma baiti na 91-97 da suka ƙunshi bayani a kan yadda ya kamata jama’a su koma ga Allah ta hanyar yin addu’a da tuba da neman taimakonsa don magance wannan barazana ta ɗabi’un zamani da marubucin ya tattauna a kai. A kuma rungumi kyawawan ɗabi’u da aka san al’ummar Hausawa da su musamman vangaren da marubucin waƙar ya tavo, wato ƙoƙarin gyara a kan munanan ɗabi’un zamani da suka gurvata rayuwar al’umma a yau.

Ga baitocin kamar haka:

“Ya Ta’ala ya Sarki guda,

 Mun yi tuba ba ga waninka ba,

Gun ka ne Allah muka tabbata,

 Taimake mu da babban cigaba”.

Azurta mu da kaifin hankali,

 Jahilai ba su rinjaye mu ba”.

 

Karya kafirci Rabbana,

 Dankwafe shi a dukkan cigaba”.

Rabbi sa Musulunci yai gaba,

 Ɗaukaka shi Ta’ala can gaba”.

(bt. na 91-93 da bt. na 96-97).

Shi kuwa baiti na 98 da na 99 ya ƙunshi addu’ar rufewa ce, inda ya yi salati ga Annabi (S.A.W.), ya kuma rufe waƙar.

Sai baiti na 100 wanda ya ƙunshi ramzi, wato shekarar da ya rubuta waƙa, inda ya nuna cewa a cikin shekara ta 1970 ne ya yi ta.

Daga ƙarshe, wato baiti na cikon 101, ya bayyana sunansa a matsayin shi ne mamallakin waƙar.

Kammalawa

Wannan takarda ta tattauna ne a kan waƙa mai suna “Ɗabi’un Zamani” wadda malam Imamu Sani Gaya ya rubuta tun a shekarar 1970. An tattauna a kan waƙar dangane da jigon na faɗakarwa a kan barazana da baƙin al’adu na zamani suke fuskantar al’ummar Hausawa. Takardar ta tattauna batutuwa a ƙarƙashin turaku guda uku manya.

A sakamakon gudanar da wannan aikin bincike an gano cewa, marubuta waƙoƙin Hausa sun yi jan hankali a kan wannan matsala ta gurvacewar ɗabi’u, domin haka tana sosa musu rai, tana damunsu, tana ci musu tuwo a ƙwarya’ don haka ne ma a matsayinsu na mawaƙa da suka kasance takobin al’umma, suka ɗauki alƙalamin rubutunsu suka takalo wannan mas’ala don samar da mafita. Za a fahimci haka idan aka dubi ita wannan waƙa a matsayin misali.

Sannan binciken ya lura cewa mutane, musamman matasa (maza da mata) sun shagala da kwaikwayon yanayin sanya tufafi irin na Turawa, waɗanda sun sava da ɗabi’u da al’adun Hausawa, su ne marubucin yake jan hankali a kansu.

Binciken ya fahimci cewa akwai buƙatar Musulmi su koma ga Allah, musamman ta hanyar yin addu’o’i da tuba wanda hakan ne zai kai ga samun gyara. Yin hakan ne ko kaɗai mafita.

Wani abin da wannan takarda ta tabbatar shi ne iyaye a wannan zamani suna yin sakaci wajen kula da tarbiyyar ‘ya’yansu ta yadda a yau idan an lura wasu iyayen ma tsoro suke ji su fuskanci ‘ya’yansu don yi masu faɗa, an ƙyale su su ci karensu babu babbaka. Yayin da su ma ‘ya’yan wasunsu sun raina iyayensu, ba sa jin maganarsu. Wannan kuwa babbar barazana ce wadda take bayuwa zuwa ga aikata abubuwa marasa kyau, ciki har da yanayin sanya tufafi ta yadda za a ga idan ma an sanya tufafin, to tamkar a tsirara ake tafiya. Hakan kuma na iya buɗe ƙofar varna kai tsaye. Haka kuwa ba zai haifar da ɗa mai ido ba, wanda hakan ne ya ja hankalin Malam Imamu Sani Gaya wajen rubuta wannan waƙa tasa.

Manazarta

Amin, M. L. (2000). Waƙoƙin Jihadi a Goshin Ƙarni na Ashirin da Ɗaya. Takarda Cikin Hausa Studies Vol. 2. Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Birnin-Tudu, S. Y. (2009). Jiga Salon Rubutattun Waƙoƙin Furu’a na Ƙarni na Ashirin. Kundin Digiri na Uku. Sakkwato. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Ɗangambo, A. (2007). Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa. Zariya Amana Publishing Company

Ɗangambo, A. (2009). Gadon Feɗe Adabi (1990) (Jiran bugu).

Ɗangambo, H. A. (2014). Wasiƙa ko Ƙasida? Tsokaci Kan Jigon Waƙar Wasiƙar So, M. B. Umar. Takarda cikin Zauren Waƙa: Journal of Hausa Poetry Studies. Sakkwato. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Ɗanjuma, M. S. (1982). Rabe-Raben Waƙoƙin Hausa da Tasirinsu ga Rayuwa a Ƙasar Hausa. Kundin Digiri na Biyu. Sashen Koyar da Harsunan Nijeirya. Kano: Jami’ar Bayero.

Goody, I. (1987). The Interface Between the Written and the Oral London: Cambridge Press.

Hisket, M. (1975). A History of Hausa Islamic Verse. London. School of Oriental and African Studies.

Pilaszewicz, S. (2014). The Signs of the Hour in Hausa” Poem on the End of the Time. Takarda Cikin Littafin Garkuwan Adabin Hausa: A Festschrift in Tribute to Abdulƙadir Ɗangambo. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.

Sa’id, B. (2002). Rubutattun Waƙoƙin Hausa a Ƙarni na Ashirin a Jihohin Sakkwato da Kebbi da Zamfara: Nazari a Kan Bunƙasarsu da Hikimomin da ke Cikinsu. Kundin Digiri na Uku. Kano: Jami’ar Bayero.

Sani, A. B. (2018). Waƙoƙin Malam Imamu Sani Gaya. Kano: Shaibah Biz Sharaɗa NNDC.

Yahaya, I. Y. (1988). Hausa a Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin Hausa. Zariya, NNPC.

Yahya, A. B. (2014). Gudale Waƙar Soyayya: Misali Gazal (Ghazal) Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa. Takarda Cikin Littafin Garkuwan Adabin Hausa: A Festschrift in Tribute to Abdulƙadir Ɗangambo. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.

Yahya, A. B. (2016). Salo Asirin Waƙa (Sabon tsari). Sakkwato Country Press.

Yakawada, M. T. (1987) Tarkakken Matanin Waƙar Kanzil Azim ta Aliyu Namangi. Kundin Digiri na Biyu. Zariya: Sashen Koyar da Harsunan Afirka. Jami’ar. Ahmadu Bello.



[1] Duba littafin nan mai suna Waqoqin Malam Imam Sani Gaya (2018) shafi na v (5) wajen da gabatarwar littafin take don ganin cikakken bayani a kan dalilan da suka sa wannan marubuci ya rubuta wannan waqa da kuma sauran waqoqin da ke cikin littafin da ma sauran waqoqin da aka ce ya rubuta a kan wasu xaixaikun mutane da jam’iyyun siyasa, da dai sauransu da dama.

[2] Al’ada tana nufin abubuwan da al’umma ta saba gudanarwa kuma ta yarda da ‘ya’yanta su gudanar. Akwai kyawawan al’adu, haka kuma akwai munanan al’adu. Akwai al’adun gargajiya na al’umma; haka kuma akwai al’adun baqi/baqin al’adu da al’ummar Hausawa suka samu daga maqwabtansu na kusa da na nesa.

[3] Dalilan da kan sa xabi’a ta sauya sun haxa da sauyin wuri ko tasirin mutanen da suka kewaye mutum ko kuma yanayin rayuwa da mutum kan tsinci kansa na jin daxi ko akasin haka.

[4] Ra’i yana nufin dunqulalliyar manufa ce wadda ta qunshi wani aiki na fasaha da hikima da aka qirqira don gudanar da wani aiki ko nazartar ayyuka na ilimi. Sannan hanyar an yarda da ita an gwada ta, masana da manazarta sun yi amfani da ita a cikin aikace-aikacensu, aka kuma ga dacewar hakan.

[5] An samu tarihin wannan marubuci da ya rubuta ita wannan waqa ne daga cikin littafin Waqoqin Malam Imamu Sani Gaya da aka tattara aka rubuta a shekarar (2018) wanda Dakta Abdulbasid ne ya yi wannan aikin rubutawar. A duba shafi na 4 don samun qarin bayani.

[6] Taguwa tana nufin riga. Sai dai a yau wannan kalma “taguwa” za a ga cewa tsohuwar kalma ce wadda ba a yin amfani da ita, ko mu ce ba a cika yin amfani da kalmar ba.

Hausa

Post a Comment

0 Comments