Citation: Ɗangambo, H.A. and Mainasara, A. (2024). Barazanar Ɗabi’un Zamani ga Al’umma: Nazari Kan Jigon Waƙar Ɗabi’un Zamani Ta Imamu Sani Gaya. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 233-241. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.028.
BARAZANAR
ƊABI’UN ZAMANI GA AL’UMMA: NAZARI KAN JIGON WAƘAR ƊABI’UN ZAMANI TA IMAMU SANI
GAYA
Halima
Abdulƙadir
Ɗangambo
Sashen
Koyar da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Bayero, Kano
Adamu
Mainasara
Sashen
Koyar da Harsunan Afirka
Jami’ar Alƙalam, Katsina
Tsakure:
Yadda barazana da ɗabi'un zamani suka
dabaibaye rayuwar al’ummar Hausawa a yau, babban ƙalubale ne da ya daɗe ana tattaunawa a kai,
wanda marubuta waƙoƙin Hausa ba a bar su a baya ba wajen bayar da gudummawa a
wannan vangare, a ƙoƙarinsu na isar da saƙon don kwalliya ta biya kuɗin sabulu. Hakan ce ta sa
aka tsara wannan takarda ta hanyar nazartar waƙar “Ɗabi’un
Zamani”, ta Malam
Imamu Sani Gaya, don fito da wannan barazana da ɗabi’un
zamani ke tattare da su don kamo bakin zaren; wanda wannan ita ce babbar
manufar takardar. Hanyoyin da wannan takarda ta bi wajen cim ma manufarta sun
haɗa da karantawa tare
da nazarin baitocin waƙar wadda aka samo daga wani littafi mai suna Waƙoƙin
Malam Imamu Sani Gaya (2018). Sai kuma tattaunawa da wasu jama’a don ƙara
fahimtar ire-iren ɗabi’u
waɗanda zamani ne ya
kawo su. Dangane da ra’in bincike, wannan takarda, an yi amfani da ra’in
Gudummawar Adabi ga Al’umma da kuma ra’in Ɗangambo (2007) don cim ma manufarta. A
sakamakon gudanar da wannan bincike an fahimci cewa, marubuta waƙoƙi sun
taka rawa wajen kakkave ire-iren waɗannan
munanan ɗabi'u, da
zamani ya kawo a cikin waƙoƙinsu. Sannan an gano cewa munanan ɗabi’u sun yi kaka-gida a zukatan jama’a waɗanda idan aka yi ƙoƙari
wajen magance su, to za a samu tsaftatacciyar al’umma.
Fitilun Kalmomi: Barazana, Ɗabi’un Zamani, Al’umma, Waƙar Ɗabi’un Zamani, Imamu Sani Gaya
Gabatarwa
Kamar yadda
aka fara nunawa tun a tsakure, manufar rubuta wannan takarda ita ce, yin nazari
a kan wannan waƙa mai suna
“Ɗabi’un zamani”, da niyyar jan hankali
ga al’umma wajen kiyayewa tare da kauce wa waɗannan
ɗabi’u waɗanda idan an lura zamani ne da ya yi tasiri a kan al’umma
Hausawa ya haifar da su. A
daidai wannan wuri, bari mu gabatar da abubuwan da wannan takarda ta ƙunsa a taƙaic.
Da farko, akwai bayanai a kan dalilin
da ya sa aka rubuta waƙar.
Sannan sai bita a kan ayyukan magabata da kawo bayanai a kan ma’amar kalmar
“barazana” da ma’anar “ɗabi’a/ɗabi’u” da kuma me ake nufi da ɗabi’un
zamani. Daga nan sai bayanin da ya shafi ra’in bincike. Sai kuma gundarin
nazarin wanda ya haɗa da abubuwa kamar su tarihin
marubucin waƙar da
kuma cikakken nazari a kan jigon waƙar
da kuma sharhin jigon waƙar
bisa ra’in gudummawar adabi ga al’umma.
Bita
Dangane da bitar ayyukan da aka
gudanar a ƙarƙashin inuwar rubutattun waƙoƙi, a kan abin da ya shafi jigoginsu, za a ga cewa ba baƙon abu ba ne; domin an sha
gudanar da aikace-aikace masu tarin yawa. Sai dai abin da za a lura da shi a
nan shi ne, kowane jigo yana da nasa irin tasirin da muhimmanin matsayi a
tsakanin al’umma. Sannan marubuta suna tsara shi ne gwargwadon bukatar al’umma
ga wani muhimmin al’amari da ya dangance shi.
Wasu aikace-aikace an gudanar da
su a matsayin kundayen neman digiri na ɗaya zuwa na uku. Sannan akwai
wasu aikace-aikacen da aka rubuta a matsayin littattafai. Da takardu na ilimi
da sauransu da suka shafi nazarin jigo a rubutattun waƙoƙin Hausa.
Waɗannan
aikace-aikace sun haɗa da: Ɗangambo (1990) da Mukhtar (2005)
da Ɗangambo (2007) da Yahya (2016)
da Birnin-Tudu (2009) da (2011) da Dunfawa (1990) da Auta (2017) da Bunza
(2014) da Halima A. Ɗangambo
(2021) da (2014) da (2011) da (2002) da (Sa’id 2002) da dai makamantansu da
yawa.
Manufar
Rubuta Waƙar
Babbar manufa da rubuta wannan
waƙa, wadda ta kasance ɗaya ce daga cikin waƙoƙin da Malam Imamu Sani Gaya ya
rubuta, a cikin littafin nan mai suna Waƙoƙin
Malam Imam Sani Gaya (2018) wanda
Dakta Abdulbasid Imam Sani ya tattara tare da rubutawa, ita ce saboda koyar da
al’umma wa’azi da kuma nusar da su al’amuran rayuwarsu. Wannan kuwa ya yi
daidai da tunanin cewa shi wannan marubuci yana ɗaya
daga cikin malaman da suka rubuta waƙoƙi a fannoni daban-daban, kamar
fiƙihu da tauhidi da wa’azi da faɗakarwa da siyasa da sauransu[1].
Ma’anar
Kalmar Barazana
Wannan kalma idan an yi mata
kallon tsanaki, za a ga cewa Bahaushiyar kalma ce, ma’ana kalma ce ta asali ta
Hausawa, ba aro ta aka yi daga wani harshe ba. A nan za a iya bayyana wannan
kalma da cewa tana nufin haɗari ko ban-tsoro ko kuma wani
abu da zai iya haifar da ko kawo wani naƙasu
ko wata matsala ga rayuwa.
Ma’anar
Ɗabi’a/Ɗabi’u
Kalmar “ɗabi’a”, tana nufin halayya. Ɗabi’a tilo ke nan, yayin da kuma “ɗabi’u” jami’i ne na ɗabi’a. Ɗabi’a/halayya iri biyu ce: akwai
mai kyau, akwai kuma marar kyau (mummunar ɗabi’a). A al’adance, al’ummar
Hausawa tana horon ‘ya’yanta da su gudanar da kyawawan ɗabi’u, su kuma guje wa munanan, ba don komai ba, sai don
samun ingantacciyar al’umma. Babu ala’da[2]
ta mutum ɗaya, sai dai akwai ɗabi’a/halayya ta mutum ɗaya. Haka kuma ɗabi’a tana da wuyar sauyawa, a wasu lokutan kuma takan sauya
cikin ɗan ƙaramin lokaci saboda wasu
dalilai da kan taso[3].
Ɗabi’un Zamani
Ɗabi’un zamani nau’i ne na ɗabi’u wanda kan wanzu a tsakanin al’umma sakamakon cuɗanyarsu da baƙi.
Ire-iren waɗannan ɗabi’u suna kawo sauyi tare da yin tasiri a tsakanin al’umma
musamman matasa. Waɗannan ɗabi’u har ila yau, ɗabi’u ne baƙi mabambanta da ake samu. Dalili
a nan shi ne ɗabi’un kan kasance daban-daban
gwargwadon ire-iren al’ummomin da suka maƙwabci
wata al’umma. Sannan gwargwadon yadda al’umma ta karvi waɗannan ɗabi’u, to iya gwargwadon yadda
waɗannan ɗabi’u kan samu gurbin zama ke nan, su yi kaka-gida. Ma’ana
idan al’umma ta gamu da wannan barazana, to hakan kna yi sanadiyyar sauyawarta
ta fuskoki daban-daban, musamman dai vangaren munanan ɗabi’un irin su kwaikwayon sanya sutura na wasu al’ummu da
tarbiyyarsu da sha’anin zamantakewarsu da sauransu.
A taƙaice, ɗabi’un zamani suna nufin, ko mu ce suna nuni ne da ɗabi’u, waɗanda sauyawa da jujjuyawar
lokacin rayuwa kan haifar su kuma zama jini da tsoka a lokaci guda. A irin haka
ne al’umma kan faɗakar da ‘ya’yanta da su riƙi ɗabi’u
na gari, da kuma yin watsi da na banza; da dai sauran abubuwa makamantan waɗannan.
Ra’in[4]
Bincike
Wannan takarda ta zavi ra’o’i
guda biyu don gudanar da wannan aiki. Sannan kowane ra’i daga cikin waɗannan ra’o’in da aka zava, akwai dalilin zavensa. Ma’ana, an
lura cewa ra’o’in sun dace da manufar takardar. Misali ra’in “Gudummawar Adabi
ga Al’umma”, an zave shi ne saboda dacewarsa ta fuskar kallon yadda ya kasance
cewa, ya yi tanadi a kan nazarin adabi game da tsarin zamantakewar al’umma, da
kuma yadda adabi yake tafiya da al’adu da kuma gudumamwarsa ko tasirinsa ko
amfaninsa. Za a fahimci haka idan aka dubi jigon waƙar da ke magana a kan ɗabi’u/halaye na al’umma don kawo gyara a cikin al’umma. Haka
kuma an zavi ra’in Ɗangambo
(2007) saboda dacewarsa da manufar takardar dangane da abin da ya shafi matakan
nazarin rubutacciyar waƙa.
Idan kuma an duba za a ga cewa wannan waƙa
da aka nazarci jigonta ta kasance rubutacciya ce.
Barazanar
Ɗabi’un Zamani Daga
Alƙalamin Malam Imamu
Sani Gaya
Da farko, bari mu fara kawo taƙaitaccen tarihin rayuwar
marubucin waƙar kafin
mu shiga nazari da sharhi, dangane da yadda ɗabi’un
zamani suka zama barazana a tsakanin al’umma, kamar yadda alƙalamin rubutu na wannan marubuci
ya nuna mana daga wannan waƙa,
mai suna “Ɗabi’un
Zamani”; kamar yadda aka fara nunawa a can baya.
Tarihin
Marubuci[5]
An haifi Malam Imamu Sani Gabaya
a shekara ta 1943 a garin Gaya da ke cikin Jihar Kano, mahaifinsa Malam Sani
Gaya, wanda aka fi sani da Malam Maidarasu, Alamarma ne kuma shahararren
malamin addinin Musulunci ne da ke zaune a garin Gaya. Malam Imam ya tashi
wajen mahaifinsa inda ya fara karatu a gabansa tare da taimakon ‘yan’uwansa ya
haddace Alƙur’ani
tun yana ƙarami a
lokacin da bai wuce shekara 15 ba. Sannan ya yi saukoki na satu da dama. Bayan
haka, ya rubuta Alƙur’ani
har sau bakwai.
Daga baya Malam ya duƙufa wajen neman ilimin addinin
Musulunci a wajen mahaifinsa, ya karanta littattafai da ake karantawa a karatun
zaure tun daga Ahlari har Mukhtasar. Haka a vangaren lugga ya
karanta littattafan nahawu da waƙoƙin Larabci, kamar su Alburda da Hamziyya da Ishiriniyya
har Muƙama
da Sha’ara’ul Jahiliyya.
Haka zalika, ya karanta littafin Kifaya
a vangaren Tafsir.
Wannan malami bai tsaya a nan
ba, domin kuwa ya dage wajen zurfafa a vangarori daban-daban musamman ilimin Tajwid inda ya halarci wato Daura da
Larabawa suka gabatar a birnin Kano domin ba da horo a kan ilimin Tajwid a ilimance da aikace.
Malamin ya tashi a gidan
makaranta, wannan ta sa ba abin da yasa a gaba illa harkar koyo da koyarwa.
Saboda haka ya duƙufa wajen
havaka makarantarsu da taimaka wa mahaifinsa, inda ya dage wajen havaka wannan
makaranta har sai da ta zama shahararriyar makaranta a Kano.
Malam Imamu ya rasu, Allah ya yi
masa rahama a garin Gaya cikin shekarar 1993, ya bar tarin waƙoƙi a vangarori da fannonin ilimi da dama. Wasu ya rubuta su
da Hausar boko, wasu kuma da Hausar Ajami”.
Jigon
Waƙar
Abubuwan da wannan vangare ya ƙunsa sun haɗa da furucin ƙwayar
jigo na waƙar da taƙaita jigon waƙar da kuma warƙarar da shimfiɗa na jigon waƙar.
Wannan waƙa kuma tana yin magana ne a kan
yadda sababbin ɗabi’u na zamani suka mamayi
al’ummar Hausawa.
Furucin
Gundarin Jigo
Dangane da furucin gundarin
jigo, wato ƙwayar
jigon wannan waƙa shi ne
faɗakarwa ne a kan illar da ɗabi'un zamani suka yi ga al’ummar Hausawa, musamman yanayin
sanya suturu wanda ake alaƙantawa
da cigaba, amma a zahiri lalataccen cigaba ne, ko ma mu ce cigaban mai haƙan rijiya ne.
Dubia abin da marubucin waƙar ya ce:
“Kan abin da ya zo wa zamani,
Wai ana cewa ma cigaba”.
“Sai ka hangi mutum ya kai mutum,
Suttura tasa ba suturarsa ba”
(baiti
na 8-9).
A cikin waɗannan baitoci guda biyu, ƙwayar jigon wannan waƙa
ya fito, inda marubucin ya nuna cewa waƙar
ta ƙunshi faɗakarwa ne a kan abin da ya zo wa wannan zamani na yadda ake
kauce wa kyawawan ɗabi’u na gargajiya, ana biye wa ɗabi’u da ma al’adun baƙi,
musamman munanan. Misali yadda aka riƙi
suturu musamman na Turawan yamma da kuma yadda mata kamar mazan ba a bar su a
baya ba wajen yin koyi da waɗannan ɗabi’u na zamani ta vangarorin rayuwa iri daban-daban.
Jigo
a Gajarce
Wannan waƙa idan mun dube ta za mu ga cewa
tana da yawan adadin baitoci guda 101 a cikin zubin ƙwar biyu. Waɗannan adadin baitoci su ne marubucin ya sarrafa ya zuba
manufofin har ya gina jigonta. A nan za a ga yadda marubucin ya karkasa
manufofin a cikin waɗannan baitoci.
Ga waƙar a gajarce:
Bt. na 1-7: Addu’ar buɗewa baitocin suka ƙunsa,
inda Malam Imamu ya yi godiya ga Allah da kirari da kuma salati ga shugabanmu
Annabi Muhammadu (S.A.W.) da sahabbansa da dai sauransu.
Bt. na 8-9: Furucin gundarin
jigo na waƙar.
Bt. na 10-17: Bayanai ne da suka
shafi irin yadda mutane suke sanya suturu da suka kauce wa al’adar Hausawa. Ya
kuma kawo bayanai na yadda maza da mata suka raja’a ga waɗannan ɗabi’un zamani musamman yanayin
sanya sutura.
Bt. na 18-20 :Magana ya yi a kan
yadda ire-iren waɗannan ɗabi’u na zamani suka bayyana ƙiri-ƙiri
a nan ƙasar
Hausa birni da ƙauye.
Bt. na 21-29 :Ya danganci
bayanai ne a kan ƙoƙarin marubucin wajen nusar da
jama’a cewa su daina kwaikwayo wasu a kan abubuwan da ba su dace ba
Bt. na 30-40 :Waɗannan baitocin sun ƙunshi
bayani ne a kan shawarwarin da marubucin ya yi ƙoƙarin
bayarwa ga mutane a kan wannan matsala.
Bt. na 41-52: Baitocin sun shafi
magana ne a kan cigaba ko bayanan jigo na shawarwari a kan yadda iyaye za su
kiyaye tarbiyyar ‘ya’yansu don samun tsira duniya da lahira.
Bt. na 53-69 :Bayani ne tare da
yin kira ga jama’a da cewa su guje wa bin ƙawace-ƙawacen da rayuwar ƙarya da Turawan yamma suka zo wa
Hausawa da su.
Bt. na 70-86 :Ya shafi bayanai a
kan mu’ujizozin halittu na Allah da yadda duniya take dangane da yanayin yadda
Allah ya ƙage ta
don ya zama izini a kan komawa ga Allah don buwayarsa. Sai bayani a kan yadda
jama’a suke koyi a kan wasu munanan ɗabi’u da suka shafi ƙayyade iyali da tsara su.
Bt. na 87-90 :Ya ƙunshi bayani a kan yadda
ni’imomin Ubangiji da kyautarsa take ga bayinsa.
Bt. na 91-97 :Ya ƙunshi bayani a kanyadda za a
koma ga Allah ta hanyar yin addu’o’i da tuba da neman taimakon Allah.
Bt. na 98: Addu’ar rufewa
Bt. na 99-100 : Waɗannan baitoci sun ƙunshi
Ramzi, inda ya nuna cewa ya yi waƙar
ne a shekara ta 1970.
Bt. na 101: Bayyana sunan wanda
ya yi waƙar, wato
Malam Imam Sani Gaya.
Warwara
da Shimfiɗar Jigon Waƙar
Jigon wannan waƙa kamar yadda aka fara nunawa a
baya shi ne faɗakarwa a kan yadda aka rungumi
al’adu da ɗabi’un zamani. Haka kuma kira ne
da babbar murya ga iyaye a kan waɗannan ɗabi’u na zamani da matasa maza da mata suka ara suka yafa,
kamar yadda marubucin ya yi ƙoƙarin nunawa a ƙoƙarinsa na isar da jigon waƙar.
Misali dubi wannan baiti na
farko inda furucin gurdarin jigo na waƙar
ya bayyana:
“Kan abin
da ya zo wa zamani,
Wai ana cewa ma cigaba”.
(baiti na 8).
Lallai kuwa idan aka dubi wannan
baiti za a ga yadda ɗabi’un zamani suka zama barazana
a tsakanin al’ummar Hausawa duba da yadda abin ya zama ruwan-dare game duniya.
Wannan kuwa barazana ce kuma babban ƙalubale
ne duba da yadda al’umma take yawan kokawa da matsalar, wanda hakan kan haifar
da illoli a rayuwa ta fuskoki iri daban-daban; musamman ma ga matasa maza da
mata.
Baiti na 9, wanda shi ma ya daɗa fito da gundarin jigon waƙar, ya bayyana yadda mutane suke sanya suturu da suka kauce
wa al’adar Hausawa, suke kuma aikata ɗabi’u marasa kyau da sunan
cigaba.
Dubi abin da baitin yake cewa:
“Sai ka hangi mutum ya kai mutum,
Suttura tasa ba suturarsa ba”
(bt. na 9).
A nan wajen za a ga yadda Malam
Imamu ya bayyana yadda mutane a yau suke kwaikwayon ɗabi’u musamman wajen yanayin sanya tufafi ta yadda da ka ga
mutum ba za ka ce Bahaushe ba ne, sai idan ya yi magana, dalili shi ne yanayin
shigarsa bai dace da suturu irin na al'ummar Hausawa ba.
Haka kuma dubi waɗannan baitocin da suke ƙasa:
“Kyan Musulmi dai a ga suttura,
Tai ba za a ga
alarassa ba.
“Wadda za ta suturce ko’ina,
Ba ka
gan shi ka kau da idonka ba”.
Inda ma munin ya ta’azzara,
Ka ga mata
ba da shigarsu ba”.
Sai su sa wando na matsar jiki,
Taguwar
ba za ta zarce cibi ba.
Ko su ɗaura sikel ɗan
tofi ne,
Wanda bai
kai inci goma ba”.
Ba
zama ba tsuguno da shi,
Sunkuyo
ma ba zai samu ba”
(Bt. na 12-17)
A cigaba da warware jigon wannan
waƙa da ke nuni da faɗakarwa a kan barazanar da ke tattare da yadda ɗabi’u na mutane suka lalace a wannan zamani musamman a
sakamakon zuwan Turawa, waɗannan baitoci guda shida (6) da
ke sama sun bayyana cigaban warware wannan jigo.
Misali, idan aka duba baiti na
12 da na 13, za a ga yadda marubucin ya nuna yadda ya kamata suturar Musulmi da
ya amsa sunansa na Musulmi ta kasance sutura ce yalwatacciya wadda za ta rufe
masa tsiraicinsa ba wadda za ta bayyana ba. Haka kuma suturar ta kasance mai
ma’ana ba wadda da an kalli mutum a kawar da ido ba, saboda rashin dacewa;
musamman kan abin da ya danganci suturta al’aura.
Mawaƙin bai gushe ba, sai da ya tavo
vangaren mata, musamman ‘yammata masu sanya suturun banza don kwaikwayon
al’adun baƙi,
musamman ma Turawa. Idan aka duba baiti na 14 da na 15 da na 16 da kuma na 17;
za a ga yadda marubucin ya tattauna a kan ɗabi’un banza na zamani da suka
zama barazana ga ‘ya’yan Hausawa, inda a daidai nan ya buga misali da yara
‘yammata saboda ta’azzara da matsalar ta yi. Misali a cikin bayanan jigo na waƙar da ke ƙarƙashin waɗannan baitoci an ji inda ya nuna
cewa mata suna sanya wando mai matse jiki, wanda wannan ba ɗabi’a ce mai kyau ba, hasali ma ba suturar Hausawa ba ce.
Sannan marubucin ya cigaba da nuna yadda mata suke sanya taguwa[6]. Har ila
yau, ya ce ita wannan taguwar ma da suke sanyawa ‘yar mitsil ce, ma’ana ‘yar ƙarama ce wadda ko cibiya ba ta
rufewa idan an sanya ta.
Haka kuma waɗannan baitoci sun ƙara
fito da yanayin yadda mata suke sanya sikel wanda shi ma ba a sanya wadatacce,
maimakon zani da Hausawa suka saba amfani da shi. A nan sai da marubucin ya ma
bayyana kwatankwacin girman sikel ɗin da matan yanzu (Hausawa) suke
sanyawa, inda ya ce bai kai inci goma (10) ba. Da an dubi wannan bayani na
sigar wannan nau’i na sikel, za a ga cewa lallai ƙanƙani
ne wanda ba zai suturce jiki ba.
Dubi kuma wasu misalan:
“Kyan Musulmi ko’ina yake,
Ko ƙasa
tasu ko ba tasu ba.
Suturar
muslinci suttura,
Ce da arne
ma bai ƙi ba.
Gun
maza na faɗa haka ba gurin,
Mace
wadda ta kai girmanta”.
(bt. na 20, 23, 25)
Waɗannan
baitoci sun bayyana yadda mawaƙin
ya nuna yadda ya kamata mutane su dinga suturce jikinsu a matsayinsu na Musulmi
a duk inda suka tsinci kansu ko da a wajen ƙasar Hausa ne ba don komai ba, sai don riƙo da al’ada da kuma koyarwar
addinin Musulunci. A nan ya daɗa jaddada yadda tsarin yanayin
suturar Musulmi take don a fahimci cewa koda a wajen waɗanda ba Musulmi ba, suturar ba su ce ba ta dace ba. Daga nan
sai marubucin ya tavo bayani na yanayin sanya tufafi na maza da mata da kuma
irin dokokin da aka yi tanadi. A nan ya nuna cewa wannan yanayi na sanya sutura
musamman a birane a matsayin ƙasar
Hausa, ƙasar
Musulunci bai dace ba.
Sannan ya cigaba da bayani a kan
waɗannan yanaye-yanaye na sanya
tufafi da yadda ya kamata a dinga kulawa musamman suturun ‘ya’ya mata.
Dubi baiti na 26, 27, 28 – baiti
na 30, za a ga yadda Malam Imam ya cigaba da zayyano waɗannan ƙa’idojin
na sanya sutura.
A wasu wuraren an ga yadda mawaƙin ya cigaba da warware mana
jigon waƙar ta
hanyar ba da shawarwari ga jama’a game da wannan matsala. Ya nuna yadda ya
kamata iyaye su kiyaye da kula da tarbiyyar ‘ya’yansu. Dalili a nan shi ne,
saboda wasu iyayen a yau suna yi wa tarbiyyar ‘ya’yansu riƙon sakainar-kashi, riƙon ko-in-kula.
Dubi waɗannan baitoci na ƙasa
suka ƙunsa don tabbatar da bayanan da
aka yi:
“Uzubillah mun neman tsari,
Wus da lalataccen
cigaba”.
“Ya jama’a na yi kiran ku duk,
Shawara
ce nai ba dole ba”.
“Kui hanin ‘ya’yanku ga sutturar,
Da ba za ta rufe surarsu ba.
“Har uba na yi wa ‘ya tasa,
‘Yan tufafi ba na kininsa ba”.
“Mai ya sanya iyaye yin haka,
Cigaban jahilci ne gaba”.
“Dole ne ga iyaye sa ido,
Gun
da ‘ya’ya nasu komai cigaba”.
(Bt. na 30, 31, 33, 35, 38, 41).
Idan aka dubi waɗannan baitoci, za a ga yadda jigon waƙar ya daɗa fitowa sosai musamman yadda marubucin waƙar ya ja hankali da nuna cewa waɗannan ɗabi’un zamani da ake cewa wai
cigaba ne, to ba cigaba gaba ba ne, lalacewa ce kawai. Don haka, sai ya yi ƙoƙarin kawo wasu shawarwari na yadda iyaye ya kamata su sa ido
a kan tarbiyyar ‘ya’yansu a kan yanayin sanya tufafi a wannan zaman. Ma’ana
iyaye su yi ƙoƙarin hana ‘ya’yansu yin shigar
da ba ta kamace su ba. Sannan ya ƙarasa
jan hankalin da cewa wannan cigaba da wasu suke iƙirari, to jahilci ne zalla da rashin sanin ciwon kai. Don
haka, iyaye su tashi tsaye, su sa ido.
Ga wasu misalan har ila yau, waɗanda marubucin ya zayyano da za su daɗa taimaka wa iyaye wajen kula da tarbiyyar ‘ya’yansu, wanda
hakan da marubucin waƙar
ya yi faɗakarwa ce kai tsaye don a samu a
shawo kan wannan barazana.
Dubi abin da ya ce a wasu
baitoci:
“Don su tashi da kirki hankali,
Nutsuwa
tasu ba shirmansu ba”.
“Don su san haƙƙoƙin lahira,
Duniyarsu
ba ta tozarta ba.
“Ɗan’uwa
za nai ma shawara,
Kar ka ɗau
hanya ba tasa ba”.
(bt. na 42, 43, 47)
Waɗannan
baitoci haƙiƙa sun daɗa faɗakar da iyaye a kan tarbiyyar
yara don guje wa munanan ɗabi;un zamani.
Haka ma baiti na 48 - 52 duk
cigaba ne a kan wannan ƙaramar
manufa.
Ga wasu misalan:
“Daina jin ƙaryoyin
kimiya,
Masu ƙaryar su san cigaba”.
Ko su yo injin ɗin rayuwa,
Maganin
mutuwa so jarraba.
Wanda
za a saka wa ɗan’adam,
Yai zamansa ba a bunne shi ba.
Na sani ko da a Amerika,
Ai dubun miliyan ba a lura ba.
Ko
a Faris ko a Ingila,
A sayar shi ba zai je Rasha ba.
In ko Rasha ce ta fito da shi,
To Amerika ba ta gan shi ba”.
Kimiyya
ta ƙagi abubuwa,
Wanda ba can duk ba a san su ba.
Ko ga mota ko ga su radiyo,
Mashinoni
da ba a san su ba.
Ka ga ma jirgin sama ga su nan,
Ko ina tafi ba da gumin ka ba.
(bt. na 53-65)
Idan aka warware manufofin da ke
ƙunshe cikin waɗannan baitoci, za a ga yadda marubucin ya yi kira ga jama’a
a kan su guje wa ƙaryace-ƙaryace na kayayyakin kimiyya da
Turawa suka ƙirƙiro cewa ba su samu damar yin
hakan ba, sai da huwacewar Ubangiji; wanda inda a san ransu ne da sun ƙirƙiri wasu na’u’ori da za su hana aukuwar wasu abubuwa. Misali
na’urar hana mutuwa balle a binne mutane.
Baiti na 53, shi ne ya ƙunshi manufar da ta bayyana cewa
a guji Turawa musamman dangane da wasu abubuwa da suka zo wa da ‘yan ƙasa da su a matsayin cigaba.
Shi kuwa baiti na 54 – 55
marubucin ya buga misali ne da samar da injina da Turawa suka yi, amma duk da
haka ba za su iya ƙirƙirar abubuwan ba face waɗanda Allah ya nufa. Don haka, kada a biye musu, a tsaya ga
al’ada da addini, a kuma fahimci cewa ba abin da yake wanzuwa sai da izinin
Allah.
A baiti na 56-65, a nan ne
marubucin ya zayyano wasu kayayyakim kimiyya irin su "radiyo" da
"mota" da "mashin" da "jirgin sama" da Turawa
suka kawo wa Hausawa, tare da kawo sunayen wasu mashahuran ƙasashe irin su
"Amurka" da "Ingila" da "Rasha" da
"Farisa" don nuna cewa su ne ƙololuwa
a kan harkar cigaba na kimiyya, amma duk da haka waɗannan ƙirƙire-ƙirƙire ba su samu wanzuwa ba, sai da Allah ya nufa, ma’ana duk
waɗannan ƙirƙire-ƙirƙire hikima ce wadda take a
bayyane daga Allah zuwa bayinsa.
Haka ma wasu baitocin da suka
biyo bayan baiti na 65, wato baiti na 66-86 duk bayanai ne da suka ƙunshi mu’ujizozi da halittun
Allah da baiwarsa da yadda ya ƙagi
duniya da abin da ke cikinta. Sai kuma ya cigaba da bayani a kan yadda jama’a
suke danganta waɗannan ɗabi’u na zamani tare da tunanin cewa waɗannan ɗabi’u da wasu suke koyi duk ba
su dace ba. Misali ɗabi’ar nan ta ƙin son tara ‘ya’ya, wato tsarin
iyali da ƙayyade
su.
A nan idan an lura waɗannan manufofi da ke cikin baitocin waɗanda suka shafi kimiyya, za a ga cewa marubucin yana so ne
ya ja hankalin jama’a cewa ko su Turawan da suke iƙirarin sun cigaba, Allah ne ya ƙaddara za su samar da waɗannan kayayyakin kimiyya. Don haka, a fahimci cewa tsantsar
cigaba shi ne bin Allah da Manzonsa, ba wai bin al’adun Turawa da abubuwan da
suka samar (waɗanda sukan shagaltar) su ne
cigaba ba; kamar yadda wasu suka ɗauka.
Ga wasu muhimmai daga cikin
baitocin waƙar don ƙara fahimtar waɗannan bayanai da aka yi a sama.
“Wanga duk hikima ce bayyane,
Da dabara ba
ƙydyrubsu ba”.
“Don ko komai sai sun jarraba,
Ba karo
caya ke ƙago
su ba”.
“Wanga Allah ne ya gwada musu,
Ba da
burga ko kirunsu ba”.
“Duniya duk ƙaryar
kimiya,
Ba su
san ƙaƙa aka yi ta”.
“Masu himmar gyaran haihuwa,
Sun makance ba ta idonsu ba”.
“Lokacin da hana ta ya tabbata,
Haihuwa
a bira sai cigaba”.
“Jahilai ba su san himmarsa ba,
Sai ku bar masa komai Rabbana”.
(bt. na 66,67,68,71,76,80,86).
Baitocin da ke biyewa waɗannan su kuma su ƙunshi
bayani ne a kan cigaban jigon dangane da sauran ni’imomin Ubangiji. Don haka,
kyautuwa ya yi mutane su kama hanyar Allah da kuma gode masa da ni’imomin da ya
yi gare su, don samun tsira, amma ba biye wa ɗabi’un
zamani ba wanda kan kai mutum ga halaka.
(Dubi baiti na 87 – 90)
Ga kuma baiti na 91-97 da suka ƙunshi bayani a kan yadda ya
kamata jama’a su koma ga Allah ta hanyar yin addu’a da tuba da neman taimakonsa
don magance wannan barazana ta ɗabi’un zamani da marubucin ya
tattauna a kai. A kuma rungumi kyawawan ɗabi’u da aka san al’ummar
Hausawa da su musamman vangaren da marubucin waƙar ya tavo, wato ƙoƙarin gyara a kan munanan ɗabi’un zamani da suka gurvata rayuwar al’umma a yau.
Ga baitocin kamar haka:
“Ya Ta’ala ya Sarki guda,
Mun yi
tuba ba ga waninka ba,
“Gun ka ne Allah muka tabbata,
Taimake
mu da babban cigaba”.
“Azurta mu da kaifin hankali,
Jahilai ba su rinjaye mu ba”.
“Karya kafirci Rabbana,
Dankwafe shi a dukkan cigaba”.
“Rabbi sa Musulunci yai gaba,
Ɗaukaka
shi Ta’ala can gaba”.
(bt. na 91-93 da bt. na 96-97).
Shi kuwa baiti na 98 da na 99 ya
ƙunshi addu’ar rufewa ce, inda ya
yi salati ga Annabi (S.A.W.), ya kuma rufe waƙar.
Sai baiti na 100 wanda ya ƙunshi ramzi, wato shekarar da ya
rubuta waƙa, inda
ya nuna cewa a cikin shekara ta 1970 ne ya yi ta.
Daga ƙarshe, wato baiti na cikon 101,
ya bayyana sunansa a matsayin shi ne mamallakin waƙar.
Kammalawa
Wannan takarda ta tattauna ne a
kan waƙa mai
suna “Ɗabi’un
Zamani” wadda malam Imamu Sani Gaya ya rubuta tun a shekarar 1970. An tattauna
a kan waƙar dangane
da jigon na faɗakarwa a kan barazana da baƙin al’adu na zamani suke
fuskantar al’ummar Hausawa. Takardar ta tattauna batutuwa a ƙarƙashin turaku guda uku manya.
A sakamakon gudanar da wannan
aikin bincike an gano cewa, marubuta waƙoƙin Hausa sun yi jan hankali a
kan wannan matsala ta gurvacewar ɗabi’u, domin haka tana sosa musu
rai, tana damunsu, tana ci musu tuwo a ƙwarya’
don haka ne ma a matsayinsu na mawaƙa
da suka kasance takobin al’umma, suka ɗauki alƙalamin rubutunsu suka takalo
wannan mas’ala don samar da mafita. Za a fahimci haka idan aka dubi ita wannan
waƙa a matsayin misali.
Sannan binciken ya lura cewa
mutane, musamman matasa (maza da mata) sun shagala da kwaikwayon yanayin sanya
tufafi irin na Turawa, waɗanda sun sava da ɗabi’u da al’adun Hausawa, su ne marubucin yake jan hankali a
kansu.
Binciken ya fahimci cewa akwai
buƙatar Musulmi su koma ga Allah,
musamman ta hanyar yin addu’o’i da tuba wanda hakan ne zai kai ga samun gyara.
Yin hakan ne ko kaɗai mafita.
Wani abin da wannan takarda ta
tabbatar shi ne iyaye a wannan zamani suna yin sakaci wajen kula da tarbiyyar
‘ya’yansu ta yadda a yau idan an lura wasu iyayen ma tsoro suke ji su fuskanci
‘ya’yansu don yi masu faɗa, an ƙyale su su ci karensu babu
babbaka. Yayin da su ma ‘ya’yan wasunsu sun raina iyayensu, ba sa jin
maganarsu. Wannan kuwa babbar barazana ce wadda take bayuwa zuwa ga aikata
abubuwa marasa kyau, ciki har da yanayin sanya tufafi ta yadda za a ga idan ma
an sanya tufafin, to tamkar a tsirara ake tafiya. Hakan kuma na iya buɗe ƙofar
varna kai tsaye. Haka kuwa ba zai haifar da ɗa
mai ido ba, wanda hakan ne ya ja hankalin Malam Imamu Sani Gaya wajen rubuta
wannan waƙa tasa.
Manazarta
Amin, M. L. (2000). Waƙoƙin Jihadi a Goshin Ƙarni
na Ashirin da Ɗaya.
Takarda Cikin Hausa Studies Vol. 2.
Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Birnin-Tudu, S. Y. (2009). Jiga
Salon Rubutattun Waƙoƙin Furu’a na Ƙarni na Ashirin. Kundin Digiri
na Uku. Sakkwato. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Ɗangambo, A. (2007). Ɗaurayar Gadon Feɗe
Waƙa. Zariya Amana Publishing
Company
Ɗangambo, A. (2009). Gadon Feɗe
Adabi (1990)
(Jiran bugu).
Ɗangambo, H. A. (2014). Wasiƙa ko Ƙasida? Tsokaci Kan Jigon Waƙar Wasiƙar So, M. B. Umar. Takarda cikin
Zauren Waƙa:
Journal of Hausa Poetry Studies. Sakkwato. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Ɗanjuma, M. S. (1982). Rabe-Raben
Waƙoƙin Hausa da Tasirinsu ga Rayuwa a Ƙasar Hausa. Kundin Digiri na
Biyu. Sashen Koyar da Harsunan Nijeirya. Kano: Jami’ar Bayero.
Goody, I. (1987). The Interface Between the Written and the
Oral London: Cambridge Press.
Hisket, M. (1975). A History of Hausa Islamic Verse.
London. School of Oriental and African Studies.
Pilaszewicz, S. (2014). The
Signs of the Hour in Hausa” Poem on the End of the Time. Takarda Cikin Littafin
Garkuwan Adabin Hausa: A Festschrift in
Tribute to Abdulƙadir
Ɗangambo. Sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.
Sa’id, B. (2002). Rubutattun Waƙoƙin Hausa a Ƙarni
na Ashirin a Jihohin Sakkwato da Kebbi da Zamfara: Nazari a Kan Bunƙasarsu da Hikimomin da ke
Cikinsu. Kundin Digiri na Uku. Kano: Jami’ar Bayero.
Sani, A. B. (2018). Waƙoƙin Malam Imamu Sani Gaya. Kano: Shaibah Biz Sharaɗa NNDC.
Yahaya, I. Y. (1988). Hausa a Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin
Hausa. Zariya, NNPC.
Yahya, A. B. (2014). Gudale Waƙar Soyayya: Misali Gazal
(Ghazal) Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa. Takarda Cikin Littafin
Garkuwan Adabin Hausa: A Festschrift in Tribute
to Abdulƙadir
Ɗangambo. Sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.
Yahya, A. B. (2016). Salo Asirin Waƙa (Sabon tsari). Sakkwato Country
Press.
Yakawada, M. T. (1987) Tarkakken Matanin Waƙar Kanzil Azim ta Aliyu Namangi.
Kundin Digiri na Biyu. Zariya: Sashen Koyar da Harsunan Afirka. Jami’ar. Ahmadu
Bello.
[1] Duba littafin nan
mai suna Waqoqin Malam Imam Sani Gaya
(2018) shafi na v (5) wajen da gabatarwar littafin take don ganin cikakken
bayani a kan dalilan da suka sa wannan marubuci ya rubuta wannan waqa da kuma
sauran waqoqin da ke cikin littafin da ma sauran waqoqin da aka ce ya rubuta a
kan wasu xaixaikun mutane da jam’iyyun siyasa, da dai sauransu da dama.
[2] Al’ada tana nufin
abubuwan da al’umma ta saba gudanarwa kuma ta yarda da ‘ya’yanta su gudanar.
Akwai kyawawan al’adu, haka kuma akwai munanan al’adu. Akwai al’adun gargajiya
na al’umma; haka kuma akwai al’adun baqi/baqin al’adu da al’ummar Hausawa suka
samu daga maqwabtansu na kusa da na nesa.
[3] Dalilan da kan sa
xabi’a ta sauya sun haxa da sauyin wuri ko tasirin mutanen da suka kewaye mutum
ko kuma yanayin rayuwa da mutum kan tsinci kansa na jin daxi ko akasin haka.
[4] Ra’i yana nufin
dunqulalliyar manufa ce wadda ta qunshi wani aiki na fasaha da hikima da aka
qirqira don gudanar da wani aiki ko nazartar ayyuka na ilimi. Sannan hanyar an
yarda da ita an gwada ta, masana da manazarta sun yi amfani da ita a cikin
aikace-aikacensu, aka kuma ga dacewar hakan.
[5] An samu tarihin
wannan marubuci da ya rubuta ita wannan waqa ne daga cikin littafin Waqoqin Malam Imamu Sani Gaya da aka
tattara aka rubuta a shekarar (2018) wanda Dakta Abdulbasid ne ya yi wannan
aikin rubutawar. A duba shafi na 4 don samun qarin bayani.
[6] Taguwa tana nufin
riga. Sai dai a yau wannan kalma “taguwa” za a ga cewa tsohuwar kalma ce wadda
ba a yin amfani da ita, ko mu ce ba a cika yin amfani da kalmar ba.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.