TAMBAYA (127)❓
Assalamualaikum .Mutun ne ya ke ta mafarki da shuwagabin Nigeria,tun daga alhaji shehu shagari har zuwa Bola Ahmed Tinubu cewa gashi ya zauna tare da kowane dayan su alokacin shi cikin walwala da anashuwa.Gafarta malam meke fasarar wannan mafarki ?
✍️AMSA A TAQAICE
(Mafarkin shugabanni yana nuna nasara da kuma albishir na
alkhairi)
AMSA❗
Waalaikumussalam, Warahmatullahi, Wabarakatuh
Alhamdulillah
To dan uwa, mafarkin ganin, shugabanni, dattawa, manya, masu
fada aji, masu tunani, malamai dukkan fassarar wadannan yana nuna nasara da
kuma albishir na alkhairi kamar yanda Tabi'i Muhammad Ibn Seerin (Rahimahullah)
yayi bayani a cikin littafinsa na "Qamus din fassarar mafarki"
SHARHI
Sanin kanmu ne cewar shi mulki siffar Allah ne. Yana bada
mulki ga wanda Ya so kuma a lokacin da Ya so. Shine ya bawa Fir'auna mulkin
Misra (Egypt) don ya jarraba shi kamar yanda ya bawa Annabi Sulaiman (Alaihis
Salam) mulkin duniya don ya jarrabashi. Na farko ya samu damar mulkar gari guda
daya tak saidai bai tafiyar da mulkin yanda Allah yake so ba, shi kuma na biyu
ya samu damar mulkar duniya gaba daya amman hakan bai rude shi ba, yayi mulkin
adalci yanda Allah Yake so
Kenan mafarkin shugabanni mabanbanta kuma an zauna dasu
zaman walwala da annashuwa yanada alaqa da wanda yayi mafarkin
Masu zagin shugabanni basa irin wannan mafarkin la'akari da
kullum suna kwantawa ne da bakin cikin shugabancin da ake musu sabanin shi kuma
wanda yake addu'a gare su da nema musu yafiyar mahaliccinsu kullum kokari yake
ya ga an yada alkhairinsu komai kankantarsa da kuma boye sharrinsu komai
girmansa
Haquri akan halayen shugabannin da kuma tawakkali ga Allah
akan zama a Nigeria ba komai bane face jarabawa daga Allah wannan dabi'a ce da
take bayyana musamman ga dattawa nagari
Don haka wanda yake irin wadannan mafarkan sai ya ci gaba da
riqo da addininsa da koyi da sunnar wanda yazo da addinin da kuma ci gaba da
yin addu'a ga shugabanninsa don samun kubuta daga halin da mutane suka tsinci
kansu na zagi da aibanta shugabanni
Ya Allah ka shirya mu ka rabamu da fasiqanci (zagin musulmi)
domin kuwa daga cikinmu ai ake samun shugabannin
Wallahu ta'ala a'alam
Subhanakallahumma wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta
astaghfiruka wa'atubi ilayk
Amsawa
Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.