𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Inaso agayamin haƙiƙanin
yadda Annabi yakeyin sallar daren ramadan?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Toh Aisha Allah ya ƙara
mata yarda tace shi Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam) baya wuce Raka'a 11
acikin Ramadan ko a wajen Ramadan. Kuma idan kakoma Rubuce Rubucen da Malamai
sukayi akan Sallar Daren Ramadan zaka samu su Magabata sunayin Tarawihi iri
biyu ne.
Na farko shine abunda suke
kiransa Tarawihi, ita kuma yadda suke yinta shine bayan anzo anyi Sallar Isha'i
Angama se kowa yatafi gida aje aci Abinci aɗan
huta se Asake dawowa Masallaci afara yin Sallar dare, kuma Sallah sukeyi Mekyau
sosai ba wai Haya-Haya sukeyiba A'a sallah ce sukeyi me tsawo tayadda kafin
Agama Raka'a Biyu kowa ya gaji, se ace toh atsaya aɗan huta masu Buƙatu suje suyi Buƙatunsu
se adawo aƙara
ɗaurawa asake yin
wasu Raka'a Biyun. Toh ahaka akeyi ana hutawa har agama Raka'a 11 wannan shine
suke kira Tarawihi, kuma ana cemasa Tarawihi ne saboda wannan Hutawarda akeyi a
tsakani.
Watarana kuma sesuce yau ba
Tarawihi zamuyiba Tahajjudi zamuyi, shikuma Tahajjudi yadda yake shine bayan
angama Sallar Isha'i se ace kowa yaje ya kwanta ayi Bacci a huta, bayan anyi
Bacci anhuta se aƙara tasowa adawo Masallaci akama Sallah itama haka zasuyita
Raka'o'i masu kyau masu tsawo anayi ana Hutawa. Toh ita kuma suna Kiranta
Tahajjudine saboda ansamu wannan Baccin kafin akazo aka fara yinta. Kenan
Tarawihi da Tahajjudi dukansu abu ɗayane
kawai Bambancinsu shine wancan anyi bacci wannan babu bacci. Kokuma kace wannan
a Farkon Dare waccan kuma Tsakiyar Dare Kuma su bawai se a Goman ƙarshe
Magabata sukeyin Tahajjudiba A'a koda yaushe suna iya yinta acikin Ramadan.
Amma mu ayau Raunine irin namu da
Kasala shiyasa Mukeyin Tarawihi daga Alamtara kaifa zuwa Nasi shikenan angama.
Kokuma wasuma sekaji kawai ana Karanta wasu gajerun ayoyi se ayi Ruku'u wannan
shima kaga ba daidai bane son zuciyane amma dai Sallar tayi tunda dama Asalinta
ba wajibi bane, sedai in kunaso ku samu Cikakkiyar lada to sekuyi koyida irin
wacce Magabata sukeyi.
Sannan kuma duk wata Sallarda
wani zebaka ko wata Addu'a yace wai ga Addu'arda akeyi kullun a Ramadana wannan
Sheɗancine da son
rai kuma Bidi'ane. Annabi Sallallahu alaihi Wasallam beyi wata Sallah ba acikin
Dararen Ramadana inbanda Tarawihi.
Allah Yasa mudace
✍🏼Jameel Alhasan Haruna
Kabo (ABU ZULAIKHA)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayaDaAnsa
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.