Ticker

6/recent/ticker-posts

Yadda Ake Miyar Alayyafu (Alayyaho)

Akwai abubbuwan da ake tanada, idan za a haɗa miyar alayyafu.

i. Alayyafu                  

ii. Albasa         

iii. Daddawa              

iv. Gishiri

v. Gyaɗa ko Egushi     

vi. Kabushi     

vii. Kayan yaji/ƙamshi da tafarnuwa

viii. Magi                     

ix. Mai            

x. Ruwa                      

xi. Sure/yakuwa

xii. Tarugu                 

 xiii. Tattasai    

xiv. Tumatur              

xv. Wake

Za a niƙa tumatur da tarugu da tattasai da kabushi da albasa a ɗan jefa ’yar kanwa kaɗan a aje gefe. A gefe guda kuma, za a tafasa nama da magi da albasa. Idan ya dafu shi ma a a je shi a gefe. Idan kuma kifi ɗanye, za a ɗan tafasa shi da ɗan gishiri a zubar da ruwan a bar shi ya tsane. Idan kuma busashe ne, za a zuba masa ruwan zafi a wanke shi sannan a cire ƙaya. Daga nan sai maganar yanka alayyafu da kuma sure kaɗan.[1] Yayin wanke waɗannan ganyaye, akan yi amfani da gishiri.

Da za rar an kammala wannan, sai batun hura wuta da kuma aza tukunya. Akan saka man gyaɗa ko manja. Bayan sun ɗan soyu, sai a zuba albasa. Bayan sun soyu, sai a sanya jajjagen tumatur a ciki a bar shi ya soyu sosai har mai sai ya fito sama, sannan a zuba daddawa wadda dama an daka ta tare da kayan yaji da tafarnuwa. Idan suka soyu za a yi sanwa a saka nama da ruwansa. Idan ba a buƙata, za a soya tumatur tare da naman. Za kuma a zuba sauran kayan miya irin su magi da gishiri.

Za a bar miyar ta dafu sosai yadda ko’ina za a iya jin ƙamshinta, wanda shi ne alamun nama ya nuna da har zai iya rabuwa da ƙashinsa. Sannan za a samu wuri a kwashe naman inda ba zai huce ba. Sai kuma a saka alayyafu da sure a cikin miyar. Idan ana buƙata za a iya niƙa alayyafun ko a daka a turmi in ba a buƙata a bar shi zai wadatar. Bayan an ɗan saka alayyafun da kimanin mintina biyar, za a zuba gyaɗa ko egusi. Kowane aka saka daga ciki ya wadatar. Wani lokaci ma wake ake sakawa. Idan ta nuna za a burkaka da maburkaki sannan a mayar da naman cikin tukunya ya ƙara jiƙa a ciki. Idan da wake za a yi amfani, to akan surfe waken tare da daka shi ko markaɗe shi sannan a zuba. Za a iya cin miyar da kowane tuwo kamar tuwon shinkafa da na masara da na samo da na sakkwara da na masa da kuma na ɓula da sauran su.



[1] A miyar alayyahu, akan zuba sure ne ɗan kaɗan ba mai yawa ba. Wani lokaci ma ba a zubawa kwata-kwata. 

The book “Cimakar Bahaushe” (Diets of the Hausa People) is a collection of 293 traditional and modern diets of the Hausa people. Detailed explanations of the recipes and ingredients are provided. Comments are provided on the areas of the Hausa land where specific diets are mostly found, the age categories of people that usually use it, as well as the scientific impact of some of the diets to human biology.  Data is collected from interviews with different categories of people including:  i.                    Food sellers within the Hausa land: Mainly to have an idea of recipes on the diets.  ii.                  People of older age: Mainly to have insights on traditional diets of the Hausas.  iii.               Hausa scholars: Mainly to verify and justify the validity of the information obtained as well as provide further expert explanations on the diets.  Moreover, over two hundred (200) pieces of literature were reviewed to have better insight on the topic in question as well as get scientific and professional clarifications on some key concepts relevant to the research. The pieces of literature cover major relevant phenomena such as diet and hunger. Others are on the Hausa land and the Hausas.  The book contains thirty-three (33) chapters. Chapter one is the main introduction in which a concise explanation is provided on the Hausas, their history, their land, social life, and transformations due to globalization, acculturation, and modernity. Chapter two detailly discusses the concepts of diet and food from the Hausa point of view. That includes the meaning and the usage of diets in some Hausa works of literature both verbal and written (i.e. prose, poetry, proverbs, etc.).  Chapters three and four discuss the sources of Hausa diets and their forms accordingly. Chapters five to seventeen discuss some traditional Hausa diets including hard and soft ones. Chapter eighteen concentrates on the influence of modernity and globalization on Hausa diets. It has been discovered that there have been some significant changes in the Hausa diets ranging from recipes to kitchenettes.  Chapters nineteen to thirty-two discuss modern Hausa diets. Some traditional diets are still retained with little modifications, while on the other hand, there are a lot of new ones. Chapter thirty-three discusses “hunger” from the Hausa point of view. The relationship between hunger and food is examined. Additionally, the use of hunger in various Hausa literary works is studied. It is concluded that hunger is like a disease whereby its cure is food.  7th November 2022
Citation (Manazartar Littafin): Sani, A-U. & Umar, H.A. (2022). Cimakar Hausawa. Kano: WT Press. ISBN: 978-978-984-562-9.

Get a copy:
To obtain a copy of this book, kindly send a WhatsApp message to:
+2348133529736

You can also write an email to:

Post a Comment

0 Comments