Table of Contents
Citation: Muhammad, A.L. & Kyambo, S.B. (2024). Yanayin Halayyar Mutanen Fada a Zubin Ɗiyan Wasu Waƙoƙin Narambaɗa. Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture, 3(1), 276-281. www.doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i01.031.
Yanayin Halayyar Mutanen Fada a Zubin Ɗ iyan Wasu Wa ƙ o ƙ in Naramba ɗ a
Na
Amin Lukman Muhammad
PhD
Federal College of
Education
,
Zaria
08037753401
Lmameen@yahoo.com
Da
Safiyanu Bayero
Kyambo PhD
Federal College of
Education
,
Zaria
08069299860
Kyambohausa2010@gmail.com
Tsakure
Wannan aiki ne da ya yi
nazarin yadda aka yi amfani da harshe wajen fito da wasu
ɗ
abi’un al’ummar da ke
rayuwa a cikin fada. Duk da cewa wa
ɗ
annan
ɗ
abi’u ana iya samun su a kusan kowane irin rukunin al’umma, to amma
kasancewar maka
ɗ
a Ibrahim Naramba
ɗ
a shahararren maka
ɗ
in fada wanda ya kwashe lokaci mai tsawo na rayuwarsa yana gogayya a fada
har ya kasance yakan rattabo wasu halaye da suka yi fice a fada ya-Allah a
wajen yin yabo ko zambo ko habaici da sauransu. Wannan ma
ƙ
ala ta nazarci wasu
ɗ
iyan wa
ƙ
o
ƙ
insa da kuma fito tare da taskace wa
ɗ
annan
ɗ
abi’u da suka mamaye rayuwar fada. Wajen ganin an cimma wannan
ƙ
udiri, binciken ya bi hanyar sauraron wa
ƙ
o
ƙ
in Ibrahim Naramba
ɗ
a da aka na
ɗ
a a faifan c.d tare da tattaunawa da wasu tsofaffin fadawa na fadar Zazzau
wa
ɗ
anda suka yi mu’amala da Naramba
ɗ
a lokacin rayuwarsa.
Binciken ya
ƙ
ara tabbatar da cewa
,
ana iya nazarin
ɗ
abi’ar al’umma ta hanyar nazarin furucinsu.
1.0 Gabatarwa
Kasancewar harshe ma
ƙ
unsa al'adu da adabi, wanda da shi ake nazarin kowannensu, wannan ne ya
sa aka nazarci walwalar harshe don fito da wasu al'adu na jama'ar Fada. A fizge
takardar ta yi kamar da wadda aka nazarci
ɓ
angaren al'ada to amma ba al'ada ba ce, domin kuwa a
ɓ
angaren al'ada ana la'akari ne da al'ada ta zahiri
da ta ba
ɗ
ini, wato material and non
material. Ita ko wannan, takarda ce da ta kalli walwalar harshe don gwada yadda
al'ada take.
Ba
ɓ
oyayyen abu ne ba a fagen
nazarin kimiyyar harshe cewa kowanne rukunin jama'a yana da nasa kalmomi, kamar
a fagagen kasuwanci da shari'a da ilimi har ma da rukunin dattijai da samari da
malamai da kuma sarakai.
Idan ka ji ana ambaton kalmomi irin su 'ranka ya da
ɗ
e' ko gyara kintsi ' ko' gyara gaba' da su 'sunkuye
masgaye' to ba ko shakka tunanin da zai wa mai sauraro shi ne al'amarin Fada ko
na saraki.
Kasancewar Naramba
ɗ
a maka
ɗ
in Fada ta sa an fahimci wasu
ɗ
abi'u daga harshensa da ya yi amfani wajen gina wa
ƙ
o
ƙ
insa. Hasali ma, kusan a iya
cewa, wa
ɗ
annan
ɗ
abi'u su suka mamaye Fada.
Wannan ma
ƙ
ala, ta nazarci ilimin walwalar harshe ne, ta inda ta
fito da wasu
ɗ
abi’un fada da maka
ɗ
a Ibrahim Naramba
ɗ
a ya girke su a cikin
wa
ƙ
o
ƙ
insa wa
ɗ
anda da zarar mai karatu ya karanta su zai fahimci
yanayin zamantakewarsu. Ibrahim Naramba
ɗ
a ba
ɓ
oyayyen maka
ɗ
i ba ne a
ƙ
asar
Hausa
,
amma dai zai yi kyau a
ɗ
an
ƙ
ara fito da tarihinsa domin a samu kwalliya ta biya ku
ɗ
in sabulu. Ibrahim
Naramba
ɗ
a shahararren mawa
ƙ
i ne na sarkin Gobir na Isa da ya yi fice a shekarun
gabanin mulkin kai a Nijeria. Bunza
,
(
2009
)
ya
bayyana cewa abu ne mawuyaci a ce ga shekarar da aka haifi Naramba
ɗ
a saboda ba a cika
kiyaye shekarar da aka haifi mutum ba a wancan lokacin sai dai a yi kirdadon
wasu muhimman abububuwa da suka faru a zamanin, har wa yau ba a sami wani
abokin
ƙ
uruciyarsa ba. A
sakamakon tattaunawa da Gusau
(
1995
)
ya
yi da wani yaron Naramba
ɗ
a, sun yi kirdadon
cewa an haifi Ibrahim Naramba
ɗ
a a shekarar 1894 a garin Tubali a unguwar Dembo cikin
Gundumar Zungeru a
ƙ
aramar hukumar
Shinkafi ta jihar Zamfara.
Wannan mawa
ƙ
i a cikin hikimominsa ya fito da
ɗ
abi’un fada a cikin
wa
ƙ
o
ƙ
insa da dama. Wa
ɗ
annan
ɗ
abi’u sun ha
ɗ
a da kyauta da karimci da rowa da guri
da gulma da
ƙ
iyayya da asararu da
ri
ƙ
on addini da
ƙ
wazo da ragonci da kuma hamayya
.
1.1 Fada Da Fadawa
Muhalli ne na rukunin
al’umma inda ake gudanar da harkar jan ragamarta. Mutanen da suke zaune a fada,
wato hakimai da ‘ya’yan sarki da barorin sarki su ake kira da fadawa. Bunza
,
(
2009
)
ya
bayyana cewa fadawa
ne
suke iso ga sarki, su ke ba da
lokacin da za a zo a yi hira, su ke zuwa da kyautar da aka yi a ba su tukuici,
su ke ba maka
ɗ
a labarin abubuwan da
ba su sani ba, domin su sarrafa su a wa
ƙ
a.
1.2 Ɗ abi’a
Ƙ
amusun Hausa na Jami'ar Bayero ya bayyana ma'anar
ɗ
abi'a da cewa ita ce halin mutum ko al'adarsa.
1.3 Walwalar Harshe
Yakasai (2012) ya yi sharar fage cewa, harshen Hausa yana da fa
ɗ
i da yalwa ta yadda har ya kai ga samar da kare-karensa
masu daman gaske, ya kuma nuna cewa wannan yalwar tasa ce ta haifar da nau’o’in
Hausa daban-daban. Dangane da wannan zance nasa ya yi wa tufka hanci, inda ya
nuna kowane rukunin jama’a a Hausa yake da nasa za
ɓ
a
ɓɓ
un kalmomi na musamman da yake amfani da su a sadarwarsa ta yau da kullum.
Ya ma
ƙ
ara da cewa kowane rukunin al’umma ba ya yin tarayya da
wani dangane da kalmomin fannu a cikin magana. Ya kawo misalai kamar haka:
Hausar
kasuwanci
ana samun kalmomi irin su: Saye sayarwa tayi
.
Hausar malamai:
Akwai kalmomi irin
su:
Ga’i
ɗ
i da bawali da mawafa
ƙ
a
.
Hausar dattijai:
Akwai kalmomi irin
su:
Mai
ɗ
akina da makwanci da yaron
gidana
.
Hausar
samari/ ‘yan mata:
Akwai kalmomi irin su: Yaya dai? Da ji mana
kin ha
ɗ
u
.
Daga cikin rukunan al’umma da Yakasai 2012 ya bayyana akwai rukunin fada,
inda ya bayar da misalai kamar haka:
Hausar sarakuna: Akwai kalmomi irin su: Ranka ya da
ɗ
e da mu muka ce da fadawa da fada rangadi da fare da
barori da jakadiya da hawan daba.
2.
0
Halayyar
Mutanen Fada a Wasu Wa
ƙ
o
ƙ
in Naramba
ɗ
a
2.1
Kyauta
Wata irin
ɗ
abi’a ce da akan ba
ko mallaka wa mutum wani abu kamar sutura ko ku
ɗ
i ko dabbobi ko kuma kayan gona, domin
kyautata masa. Kyauta fitacciyar
ɗ
abi’a ce da aka san fadawa da ita musamman
daga ma
ɗ
aukaka a cikin
al’umma zuwa ga wa
ɗ
anda ba su kai su
ɗ
aukaka ba ko kuma
daga fadawa zuwa ga maro
ƙ
a.
Ana iya fahimtar haka a harshen maka
ɗ
a Ibrahim Naramba
ɗ
a a wurare da dama
cikin
ɗ
iya
r
wa
ƙ
o
ƙ
insa. Misali:
2.1a. Jagora:
“Na zaka barka da shan ruwa na zaka don in
yi godiya
.
‘Yan amshi Wata
kyauta tana ba ni shawa jikan Hassan dut ta yau ta hi
.
Jagora:
Ai sai
da so anka kyauta
.
‘Yan amshi
In babu so ba a yin komai
.
Jagora:
Dokin
nan da kab ba ni kyauta jiya
.
‘Yan amshi
Ko da uban mutum as sarki iri nai yakan hau sai
.
”
(Wa
ƙ
ar Amadun Bubakar)
2.1b. Jagora:
“Ya ba ni dawaki na
ƙ
warai
.
‘Yan amshi
Sa’akka Amadu
ɗ
an Iro
.
Komai
ƙ
asarnan, ban rasawa
.
”
(Wa
ƙ
ar jikan Sanda arna
suna shakkar haye ma)
2.1c. Jagora:
“Kyautar doki da ba da riga
,
Du
ɗ
ɗ
ai suke ga
ɗ
iyab Basharu
.
‘
Yan amshi
Zama shi abu na iskakke
.
”
(Wa
ƙ
ar ya ri
ƙ
a ka da girma)
2.1d. Jagora:
Amadu naka lokaci da yawa nai
komi
,
Zamakin na aje kuramen sunag gero
,
Manyan riguna akwai
ƙ
arfe nai shanu
.
‘Yan amshi
Yo bana doki bakwai garan hab barga niy yi
,
A! dum matan gidanmu sun sai gorat tatsa
,
Yau kowace na da nagge saura matak kurma
.
(Naramba
ɗ
a: Bakandamiya)
Sharhi:
A-
Doki yana daga cikin manyan kayan
ƙ
awa
a duniya ba ma kawai al’ummar Hausawa ba. Ko a cikin dawaki akwai na musamman
wa
ɗ
anda kyawunsu
da
nagartarsu sun isa abin nunawa
.
Irin wa
ɗ
annan dawaki ba kowa
ke iya mallakarsu ba sai wane da wane. Saboda isa wasu har kyauta suke yi da
irin wa
ɗ
annan dawaki kamar
yadda aka yi wa Naramba
ɗ
a.
B-
Naramba
ɗ
a ya
ƙ
ara
fito da yadda ka yi masa kyautar dawaki na
ƙ
warai
kuma ya
ƙ
ara nuna cewa komai
yake so a duniyar nan za a iya ba shi kyautarsa.
C-
A nan, Naramba
ɗ
a yana nuna cewa manyan abubuwan kyauta kamar
doki da riga abubuwa ne da yake da tabbas idan ya je wurin
ɗ
iyan sarki to tabbas
zai same su.
D-
A wannan diya
n
wa
ƙ
a Naramba
ɗ
a ya lissafo manyan
abubuwan da ya mallake su duk ta hanyar kyauta da aka yi masa a fada. Wa
ɗ
annan abubuwa su ne
manyan dami na gero da manyan riguna da tsabar ku
ɗ
i da kuma shanu da dawakai har guda
bakwai. Har wa yau, a sanadiyyar kyauta da aka yi wa Naramba
ɗ
a a fada, ba shi ka
ɗ
ai da yaransa ba har
da
matan gidansa kowacce ta sami kyautar nagge.
2.2 Rowa
Ɗ
abi’a ce akasin
kyauta wadda akan hana mutum abubuwan da ake mallaka masa a matsayin kyauta.
Rowa babbar alama ce da ake fahimtar
ɗ
abi’ar fadawa a ciki harshen mawa
ƙ
an fada da dama irin su Ibrahim Naramba
ɗ
a.
2.2a. Jagora:
“
Ka ga
ɗ
an sarki da kunnuwa da
h
wa
ɗ
i
,
‘Yan amshi
Ga shi da
ƙ
arya ga shi da rowa
,
Ko ka g
irmama shi ba ya sarki
.
”
(Naramba
ɗ
a: Masu gari mazan gabas
tsa
yayye)
.
2.2b.
Jagora:
“Ai
mutanen
Ƙ
aura suna
h
wa
ɗ
in
,
Samun wane ya zamo samun mujiya
,
Matanai ba su ci bare danginai su ci…..”
(Naramba
ɗ
a: Alhaji
Ɗ
an Durgu)
.
2.2c. Jagora:
“
Abin sarauta abin rabo na
,
In an sama a ba mutane
.
‘Yan Amshi:
Sai ka ga kullun yana shigowa
,
Amma shi wanda bai sani ba
,
Sai ya ci shi
ɗ
ai yana ta gyatsi…..”
(Naramba
ɗ
a: Tattaki maza
ɗ
an Shehu na babba)
.
Sharhi:
A-
Rowa fitacciyar
ɗ
abi’a ce da ake samu a fada wadda kuma maka
ɗ
an fada da dama sukan yi amfani da ita su zambaci ko su
yi habaici ga masu wannan
ɗ
abi’a kamar yadda muka gani a wannan
ɗ
iyan wa
ƙ
a.
B-
An fito da
ɗ
abi’ar fada ta rowa a wannan
ɗ
iya
n
wa
ƙ
a, ta inda aka nuna saboda tsabar rowar wani
ɗ
an sarki ko matansa
ba sa
cin
abin hannunsa ballantana mawa
ƙ
a.
C-
Wannan
ɗ
iya
n
wa
ƙ
a ta fito da
ɗ
abi’ar rowa da ake samu a fada ta inda wani
da yake i
ƙ
irarin cewa shi mai
sarauta ne to amma kuma ba
ya ba kowa komai sai
da
i
ya
ɓ
uya shi ka
ɗ
ai ya ci abinsa.
2.2
Ƙ
wazo
Yana daga cikin
kyawawan
ɗ
abi’u na fadawa wanda
akan yaba wa mutum idan yana da
shi har wa yau yakan zama abin fa
ɗ
i idan ya kasance
mutum bai da
shi.
Ana iya fahimtar haka a harshen Naramba
ɗ
a a wurare dama kamar haka:
2.3a Jagora: An gamu
Hausa kullufin jama’a duk sun zo
,
Kowane
Kam
f
wani shina tsaye bakin garka
.
‘Yan Amshi:
Mai
duka yat taho da shi da su Gatau
,
Amadu dum magana wadda kay yi
,
Anka ji daidai tay yi
,
Tun rannan Amiru ya
ƙ
ƙ
ara
ma girma
,
Kuma rannan waziri ya
ƙ
ƙ
ara ma girma
,
Amadu bai hito ga dattijon banza ba.
(Naramba
ɗ
a: Bakandamiya)
2.3b Jagora:
In
mahaukaci kake duk
ɗ
ai na
,
In
ɗ
an bori kake duk
ɗ
ai na
,
In
ɗ
an tauri kake duk
ɗ
ai na
.
‘Yan Amshi:
In ka ta
ɓ
a sarki ka gane ya gwada
,
Maka bai san wargi ga
.
(Naramba
ɗ
a: Bai
ɗ
au wargi ba na Jekada)
.
2.3c Jagora:
Ai yanzu
ƙ
asar Maradun Habu,
kai Jallah yab ba
.
Yan Amshi:
Zama in ka yi
ƙ
ulli ina mai walwalewa?
(Naramba
ɗ
a: Buwayi maza na Jekada)
.
2.3d Jagora:
Yanzu
Amadu ilmi garai na
ɗ
aure ashararu
.
‘Yan Amshi:
Yau
ƙ
asatai duka babu ko
guda sun ce sun tuba
.
Jagora:
Amadu
mai tawakkali na maji-da
ɗ
i
.
‘Yan Amshi:
Uban malami ka kai duw wurin da Ibrahim shi yak kai
,
Zamakin an kira shi Sarkin Gobir Hausa
,
Kai ko an kira ka sarkin Gobir Hausa
.
(Naramba
ɗ
a: Bakandamiya)
Sharhi:
A-
An yi gagarumin taro a Sakkwato wanda ya sami halartar
ɗ
imbin jama’a, a wannan taro kowa sai yabon sarkin Gobir
Amadu yake yi saboda tsabar
ƙ
wazonsa, a sanadiyyar haka har sai da Sarkin Musulmi ya
yaba da wannan namijin aiki na sarki.
Don haka,
ƙ
wazo
babbar
ɗ
abi’a ce da ake samu
a fada kamar yadda aka gani a wannan
ɗ
iyar wa
ƙ
a
ta Naramba
ɗ
a.
B-
Mahaukaci da
ɗ
an bori da
ɗ
an tauri wasu mutane ne wa
ɗ
anda aka san su ta
ƙ
adarai a cikin al’umma, a nan, Naramamba
ɗ
a yana nuna cewa
komai ta
ƙ
adarancin mutum in ya
zo fada ya ha
ɗ
u da sarki sai ya
raina kansa saboda
ƙ
wazon sarkin. Don
haka,
ƙ
wazo
ɗ
abi’a ce ta fada da
muka gani a wa
ƙ
ar Naramba
ɗ
a.
C-
A nan kuma an nuna
ɗ
abi’ar
ƙ
wazo
ta inda ake nuna saboda
ƙ
wazon
sarki idan ya fa
ɗ
i wani abu babu wanda
ya isa ya canza abin da ya fa
ɗ
a.
D-
A
ɓ
angaren farko na
wannan
ɗ
iyar wa
ƙ
a, an nuna
ɗ
abi’ar
ƙ
wazo
ta yanda duk ashararancin ashararai sai
da suka sadu
da
su
suka
tuba. A
ɓ
angare na biyu kuwa,
an nuna kamar yadda aka kira kakansa Sarkin Gobir na Isa, shi ma yanzu ya yi
ƙ
wazo an kira shi da sunan Sarkin Gobir.
2.4
Ƙ
iyayya
Ɗ
abi’a ce mummuna
wadda jama’a kan tsani mutum ba tare da wani dalili ba. Irin wannan
ɗ
abi’a takan sa a sa
w
a
mutum laifi alhali kuma bai yi ba
. Haka kuma mutum yakan
yi abu mai kyau kuma
ƙ
iri-
ƙ
iri ana nuna cewa ba shi ya yi wannan aikin alheri ba.
Wannan mummunar
ɗ
abi’a ta mamaye zaman
fada, kuma ana iya fahimtar haka a harshen Naramba
ɗ
a. Ga misalai kamar
haka:
2.4a Jagora:
Mai kai dungu ya kai mari
,
Bai zauna ba safe dut
.
‘
Yan Amshi:
Mun san
ƙ
ulle-
ƙ
ulle ya yi mai yawa
,
Ba ya samun komai gidan ga sai
h
warin
ƙ
wafa
.
(Naramba
ɗ
a: Garba
Ƙ
i-gudu
ɗ
an Mori)
2.4b Jagora:
Ya kwance batutuwa na Jekada ya taho gida
.
‘Yan Amshi:
Kunya ga ta nan gare ku mutanen banza
.
Jagora:
Yau
mai ashararu ya ka
ɗ
e duniya ta yi mai
h
washi
.
‘Yan Amshi: Babu
zama garai zama fitina yat tayas
,
Ya san ba ya kwarjini ga mutanen Hausa
,
Kowacce yana iyawa ga hili nan
,
Sai ya
ƙ
etare gidanai ba ban
kwana
.
(Naramba
ɗ
a: Ba
kandamiya
)
SHARHI:
A-
Wannan
ɓ
alo-
ɓ
alo ya nuna cewa akwai masu yin
ƙ
ulle-
ƙ
ulle
a fada wa
ɗ
anda saboda
ƙ
iyayya ne suke yi domin su samu su zama sarki ko wani
nasu ya zama sarki ko ya sami wata sarauta.
B-
A nan kuwa, Naramba
ɗ
a ya yi habaici ne ga
ma
ƙ
iyan sarki masu kai
tsegumi saboda tsagwaron
ƙ
iyayya
da suke da ita. Don haka, wannan
ɗ
iyar wa
ƙ
a
tana nuna cewa ana iya fahimtar cewa akwai
ƙ
iyayayya
tsibe a cikin fada.
2.5 Hamayya
Ɗ
abi’ar
ɗ
an
’
adam
ce da takan kasance a zukatan mutum biyu ko fiye da haka da suka nemi wani abu
guda
ɗ
aya, a sakamakon haka
dole mutum
ɗ
aya ne zai samu, shi
kuma
ɗ
ayan ko sauran
jama’ar dole su ha
ƙ
ura. Komai yawan
ɗ
iyan sarki dole mutum
ɗ
aya ne za a za
ɓ
a kuma sauran ‘yan
takaran su ha
ƙ
ura. Naramba
ɗ
a ya fito da wannan
ɗ
ai’a ta fada a wurare
da dama cikin wa
ƙ
o
ƙ
insa kuma galibi yakan yi haka ne don muzanta abokan
hamayyar sarki ko wani mai sarauta.
2.5a Jagora: Ai ga
fa gidan suna gani sai zago
.
‘Yan Amshi:
Ga mai shi nan kowat taho ya
tsai da
ƙ
a
h
watai garka
.
”
(Naramba
ɗ
a: Baban Dodo)
2.5b Jagora:
Ku dangana tun ga uwaye
.
‘Yan Amshi:
Ba duka
ɗ
an sarki ba ka samun sarki
.
Jagora:
Ɗ
an sarki duka ya ga sarauta ga
ta
kamar kusa tai ma shi nisa
.
‘Yan Amshi:
In dai bai yi sarautan nan ba sai ya tsufa da mikin zuci
.
Jagora:
Ɗ
an sarki duka ab ba kowa
,
Ɗ
an sarki duka ab ba komi
,
Sannan ya tsira yawon banza
.
‘Yan Amshi:
Ya san
ba ya sarauta
,
Sai fa ya kwan nan gobe ya kwan nan jibi
,
Dangi nai mishi Allah waddai
.
(Naramba
ɗ
a: Gogarman Tudu)
.
2.5c Jagora:
Ga Ummaru
ɗ
an Alu gidanai na Isa
.
‘Yan Amshi:
Ya yi sarki kuma ga
ɗ
iyad da ya hai
h
wa nan sun yi
,
Kuma yau ga gadonsa nan jikanai ya hau
,
Dangi sai ku han
ƙ
ure shi
na ham Madi
.
(Naramba
ɗ
a: Baban Dodo)
.
2.5d Jagora:
Wa
ɗ
anga da kak kayar ga
shi an
h
wa
ɗ
a min
.
‘Yan Amshi:
Wai an ce da ni sukaf fushi
.
Jagora:
Bamin kokowa
kodayaushe shi aka shammata bai iya ba
,
‘Yan Amshi:
Ga wata kokowa an wuce da shi karsanai
kakka
ɓ
e mashi
ƙ
asa.
(Naramba
ɗ
a: Ibrahimu na Guraguri).
Sharhi:
A-
Wannan yana nuna cewa mutane da yawa ne suka nemi wannan kujerar sarauta
ammam mutum
ɗ
aya ne daga cikinsu ya yi nasara.
Don haka Naramba
ɗ
a ya fito mana da
wannan
ɗ
abi’ar hamayya a
cikin
ɗ
iyar wa
ƙ
arsa.
B-
Ana iya ganin
ɗ
abi’ar hamayya daga cikin
ɗ
abi’un fada a wa
ƙ
o
ƙ
in Naramba
ɗ
a ta inda ya nuna
cewa ba duka
ɗ
an sarki ne kan zamo
sarki ba, domin kuwa a wata
ɗ
iyar wa
ƙ
ar,
Naramba
ɗ
a cewa ya yi duk
ɗ
an sarki so yake ya
zama sarki. Ashe kenan, masu neman sarkin suna da yawa, don haka ga hamayya ta
fito sarari a wannan
ɗ
iyar wa
ƙ
a.
C-
A nan, maka
ɗ
a Naramba
ɗ
a ya nuna cewa Sarkin
Gobir na Isa Amadu ya gaji gadon mahaifinsa wanda shi ma mahaifin nasa ya gada
daga nasa mahaifin. Don haka sauran dangi ya zama wajibi su ha
ƙ
ura domin Sarkin Gobir Amadun shi zai ta ri
ƙ
e ragamar sarautar har abada.
D-
Naramba
ɗ
a ya kwatanta neman sarauta da kokuwa
inda mai
ƙ
arfi da dubara da
sa’a yakan kayar da abokin kokuwarsa. Don haka, wannan
ɗ
abi’a ta hamayya tana
nan jibge a fada.
2.6 Guri
Ɗ
abi’a ce ta
ɗ
an
’
adam
wadda take sa masa matu
ƙ
ar soyyayyar samun
wani abu. Kusan duk wani
ɗ
an sarki yana da
gurin ya ga ya zamo sarki, ko da kuwa ya san sarautar ta fi
ƙ
arfinsa, wata
ƙ
ila
a sanadiyyar kasancewarsa bai mallaki wasu sifofi da akan gane masu alamun
zamowa sarki ba. Tun zamanin da har yanzu akwai wa
ɗ
ansu alamu a al’adar
zamantakewar al’ummar Hausawa da sukan sa a gane wane zai iya zama sarki.
Naramba
ɗ
a ya fito da wannan
ɗ
abi’a ta guri a
wurare da dama cikin wa
ƙ
o
ƙ
insa wa
ɗ
anda za
su sa a fahimci cewa lallai guri yana daga
cikin
ɗ
abi’ar mutanen fada.
Misali:
2.6a Jagora:
Gurin
ɗ
an sarki ya yi sarki Allah ya ba ka
ƙ
asar Isa
.
‘Yan Amshi:
Ri
ƙ
e bayinka ri
ƙ
e barwanka ka yi addini ka yi alheri
,
Ka tuna daga sarki sai mutuwa
,
Mu ka ga muna ro
ƙ
on Allah
,
Allah ya cika ma
imani kuma yai maka kyakkyawa
ƙ
ƙ
arko.
(Naramba
ɗ
a: Bai
ɗ
au wargi ba
na
Jekada)
.
2.6b Jagora:
Ko dauri
ƙ
o
ƙ
arin
ɗ
an sarki ya kai gadon tsohonai
,
Iro ya kai ga gadon
magaji Danko
ɗ
an Garba
ga ya ko hannunai
.
Jagora:
Kai am Muhammadun Badarawa gadanga yau kai a’ Audu
.
‘Yan Amshi:
Yun
ƙ
ura duk
ɗ
an sarkin dak kag ga bai zam sarki ba
bai
h
washe haushi ba
.
(Naramba
ɗ
a: Ginshimin gidan Halliru Uban Zagi)
.
2.6c Jagora:
Duk
ɗ
an sarki son yake ya zam sarki sai in ba ta samuwa
.
‘Yan Amshi:
Ta tabbata ko ban
h
wa
ɗ
i ba in gandu ya samu ya fi gamana
.
Sharhi:
A- Guri
babbar
ɗ
abi’a ce ta fada wadda Naramba
ɗ
a ya
ƙ
ara fitowa da ita sarari a wurare da dama cikin wa
ƙ
o
ƙ
insa kamar yadda aka gani
ɓ
alo-
ɓ
alo a wannan
ɗ
iyar wa
ƙ
a.
Haka nan, idan an cimma wannan guri na
samun sarauta akan so ta dawwama har
ƙ
arshen
rayuwa.
B-
A nan kuwa maka
ɗ
a Naramba
ɗ
a ya nuna cewa
ɗ
abi’ar gurin zama
sarki ba ta yau ba ce ko can da ma akwai ta. Kamar yadda ya nuna a wannan
ɗ
iyar wa
ƙ
a da ke cewa: “Ko dauri kwarjin
ɗ
an sarki ya
hau
gadon tsohonai
.
”
Sa’annan ya
ƙ
ara da cewa: “
Ɗ
an sarkin da kag ga
bai zam sarki bai
h
washe haushi ba
.
”
C-
Ha
ƙ
i
ƙ
a, kamar yadda Ibrahim Naramba
ɗ
a ya bayyana a wannan
ɗ
iyar wa
ƙ
a duk wani
ɗ
an sarki yana da gurin zama sarki ko
da kuwa bai da halin zama sarki, to amma ba a rasa shi da wannan
ɗ
abi’a.
2.7 Gulma
Ɗ
abi’a ce ta
ɗ
an’adam wanda wani yakan
ɗ
auki zancen wani ya kai wa wani, wanda kuma aka
ɗ
auki maganar tasa idan ya ji ba zai ji da
ɗ
i ba.
Kalmomi dangin gulma sun ha
ɗ
a da munafunci da kissa da kuma
makirci. Gulma
ɗ
abi’a ce marar kyau a
zamantakewa kuma dabi’a ce da ta mamamye jama’ar fada.
2.7a Jagora:
Ɗ
an
sarkin da kag ga ya jahilce ya
ƙ
i batun Allah
,
Yai nan
ya yi makirci yai nan da munafunci
.
‘Yan Amshi:
Bai sani ba ya lalace ba ya zama komai
.
Jagora:
Irin
su ko cikin dangi
,
‘Yan Amshi:
Su anka mayar baya
.
(Naramba
ɗ
a: Ni
ƙ
atau
Bajimin Macci
ɗ
o)
.
2.7b Jagora:
Bari kau yarda da munafiki
.
‘Yan Amshi:
Mai
ɓ
anna
ƙ
auye da birni
kowa ya
san shi da
ƙ
arya
.
”
(Naramba
ɗ
a: Abu na Namoda Shiryayye)
.
2.7c Jagora In ka ga mutum na ‘yan zage-zage sarki bai gyara mai ba
,
‘Yan Amshi:
Ran da yag gyara mai sai bugun gaba
.
(Naramba
ɗ
a: Ya ci maza ya kwan yana shire)
.
Sharhi:
A-
A wannan
ɗ
iyar wa
ƙ
a an nuna yadda
ɗ
abi’ar gulma ta sami wuri a fada kamar yadda aka ga
wannan
ɗ
an sarki yake zuwa can ya kai wani
gutsiri-tsoma, haka kuma ya kwaso abin da aka yi a can ya kawo nan.
B-
A nan, Naramba
ɗ
a ya fito mana da
ɗ
abi’ar gulma a fada, ta inda ya nuna mana cewa aikinsu kenan munafurci daga
birni har
ƙ
auye kana ya nuna mana cewa wa
ɗ
annan mutane ba
ɓ
oyayyu ba ne a cikin al’umma kowa ya san su.
C-
Ɗ
abi’ar fadawa ce kaiwa
gulma wajen abokan hamayya da yin zage-zage kamar yadda Naramba
ɗ
a ya fito mana da ita a wannan
ɗ
iyar wa
ƙ
a inda ya ce: “In ka ga mutum na ‘yan zage-zage.” Bugu da
ƙ
ari saboda rashin kunyar bafade a duk lokacin da wani zai ba shi wani abu
nan da nan zai juyo ya ri
ƙ
a yabonsa.
3.0 Sakamakon Bincike
Wannan aiki na ilimin walwalar harshe, ya yi nazari kuma ya fito da wasu
ɗ
abi’un fada a cikin wa
ƙ
o
ƙ
in maka
ɗ
a Ibrahim Naramba
ɗ
a tare da taskace su.
Har wa yau, ma
ƙ
alar
za
ta
taimaka wa masu son yin bincike da ya shafi halayya da al’adun
ɗ
an
’a
dam
(sociologist and anthropologist) wajen
fito da irin
ɗ
abi’un da suke
tattare a fadojin Hausawa. Haka kuma, ma
ƙ
alar
za
ta
da
ɗ
a haskaka wa masu
bincike a kan walwalar harshe, wajen fasalta irin binciken da za su yi, domin
kuwa, da na gaba ake gwada zurfin ruwa.
Mana
zarta
Bunza,
A. M. (2009)
.
Naramba
ɗ
a.
Lagos: Ibrash Islamic Publications Centre Ltd.
Fromkin
d
a
Wasu (2007)
.
An Introduction to Language.
U.S.A: Thomson
Wadworth.
Haugen,
E (1972)
.
“Dialect Language and
Nation
”
In Pride J.B & Holmes, J (Ed) England (UK): Cambridge Uni
v
ersity Press
Jami'ar
Bayero (2006)
Ƙ
amusun Hausa. Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya,
Jami'ar Bayero.
McDa
v
id, R.I (1965)
.
American
Social
Dialect. College English.
Pride, J.B and
Holmes, J (eds) (1972) Sociolinguistics: Selected Readings, Harmondsworth:
Pengiun
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.