Ticker

6/recent/ticker-posts

Ta Yi Aure Da Cikin Shege

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Malam wata ta yi cikin shege da wani mutum, sai ta nemi wani daban ya rufa mata asiri ya aureta, yanzu sun yi auren, yaya hukuncin auren yake?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Zina saɓon Allah ne da kuma yada fasadi a bayan kasa, aure kuwa sunnar Manzon Allah ne, da samar da zuriya mai albarka, kuma an kwadaitar da mu yin sa, amma a mazhabar Malikiyya suna ganin matar da aka yi zinar da ita sai ta yi jini wanda ake kira Istibra'i kafin a daura mata aure domin a raba maniyyin zinar da na aure. Idan har an ɗaura aure ba ta yi wannan jinin ba, to za a raba wannan auren ko da sun haifi ƴaƴa, domin suna ganin an ɗaura auren ne a cikin idda, kuma Allah Ya hana ɗaura aure a cikin idda, don haka a wajansu, wannan auren ɓatacce ne.

A Mazhabar Abu Hanifa da Imam Shafi'i suna ganin macen da ta yi zina, an so ta yi Istibra'i kafin ta yi aure, amma idan har an ɗaura auren ba ta yi Istibra'i ba, auren yana nan daram, ba za a raba su ba, ko da tana da cikin zinar ne aka daura mata aure, to auren yana nan, sai dai mijin da ta aura ba zai sadu da ita ba har sai bayan ta haihu, ko da kuwa cikin zinar nasa ne.

 Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam ya ce: "Duk wadda yayi imani da Allah da ranar lahira, to kada ya shayar da ruwansa ga shukar waninsa", Abu-Dawud (1847). Duba: Al-Mudawwannah al-kubrah 2/173 da Al-mugni na Ibnu-Khudaamah 8/79.``

Fatawar Malikiyya ta fi inganci kafin ayi auren, saboda fita daga saɓanin Malamai abin so ne, sannan kuma za a kaucewa faɗawa haɗari, amma idan an riga an yi auren to fatawar Hanafiyya abar lura ce, saboda akwai bambanci tsakanin zina da aure, sai dai ya wajaba su nisanci saduwa kafin ta haihu, saboda hadisin da ya gabata.

Allah ne mafi sani.

Amsa daga Dr. Jamilu Yusuf Zarewa.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏��👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments