Ticker

6/recent/ticker-posts

Fasihiya Binta Labaran (Fati Nijar Da Wakokinta)

Sani, A-U., Kabir, H.D., & Bashir, A. (2024). Fasihiya Binta Labaran (Fati Nijar Da Waƙoƙinta). SAS Publishers. ISBN: 978–978–795–635–7.

Domin mallakar littafin, a tuntuɓi:

Phone: +2348036481158
WhatsApp: +2348133529736

FASIHIYA BINTA LABARAN
Fati Nijar Da Waƙoƙinta

Abu-Ubaida Sani
Halima Daura Kabir
Abdullahi Bashir

Muƙaddima

Dukkan yabo ya tabbata ga Maɗaukakin Sarki Allah, Ubangijin talikai, wanda bai haihu ba kuma ba a haife shi ba. Tsira da amincin Allah su dawwama ga shugabanmu Annabi Muhammadu, da alayensa da matayensa da sahabbansa da ‘ya’yayensa da waɗanda suka bi tafarkinsu har zuwa ranar tashin alƙiyama.

Tun kafin zuwan Turawa ƙasar Hausa, Hausawa suka mallaki hanyar rubutu da karatu cikin sigar harshen Larabci. Wannan ya ba su damar naƙaltar adabin Larabci da lugga da nahawu da balaga da tasarifi da furu’a da tarihi da falsafa da tafsiri da sauran sassan ilimin addinin Musulunci. Mallakar waɗannan fannonin ya ba su damar sarrafa haruffan Larabci wajen rubuta harshen Hausa. Wannan nau’in rubutu shi ake kira rubutun Ajamin Hausa. Da irin wannan salon rubutun ne Hausawa suka taskace adabinsu na gargajiya, musamman adabin baka wanda ya danganci waƙoƙin baka na makaɗa. Sai dai ba abu ne da aka taskace ba domin koyar da shi ga almajiran makarantun allo da na ilimin zaure. Hasali ma masu sha’awa ne daga cikin almajirai kan rubuta ire-iren waɗannan waƙoƙin cikin sigar Ajamin Hausa domin su sami abokin hira yayin da suka nisanta da ƙasar Hausa a sakamakon tafiye-tafiyen fatauci.

Daga ire-iren waɗannan matafiya ne dangogin Turawa suka sami damar mallakar waƙoƙin makaɗan baka na ƙasar Hausa. Daga bisani suka sarrafa su cikin sigar rubutun Romanci. Akwai tabbacin cewa, dangogin Turawa sun koyi harshen Larabci da na Hausa a mahaɗar alhazai da fatake a Tarabulus (Libiya). Wasunsu ma a Ingila suka koyi harshen Larabci kafin su baro ƙasarsu domin ƙoƙarin cimma muradansu na binciken Kogin Kwara.

Kundayen Bajamushen nan da ake kira Dokta Prietze su ma wata shaida ce. Domin shi ma ya yi ƙoƙari tattara ire-iren waɗannan waƙoƙin baka na makaɗan Hausa da ya same su a rubuce cikin sigar rubutun Ajamin Hausa. An kuma wallafa su ne fiye da shekaru ɗari da suka shuɗe kafin su shiga hannunsa. Wannan ɗan taliki ya yi ƙoƙarin taskace abubuwa da dama da suka danganci adabin Hausa, ciki kuwa har da waƙoƙin baka na makaɗan Hausa. Daga cikin ire-iren waƙoƙin akwai waƙoƙin Sarkin Makaɗa Ɗanmadugu, makaɗan Sarkin Damagaran Tanimu, wanda ya yi mulki daga shekarar 1841 zuwa 1843 da kuma 1851 zuwa 1884. Wannan wata manuniya ce da ke ishara da cewa, Hausawa ba wani baƙo ne ya koya musu taskace dangogin adabinsu na gargajiya ba.

Idan ban yi kuskure ba, a iya sanina, fara ƙoƙarin samar da diwanin matanonin waƙoƙin baka na Hausa ya faru ne a ƙarshen ƙarni na ishirin (Ƙ20). Wanda ya aza harsashin shi ne shaihin malamin nan da aka fi sani da Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau., wanda ya kasance ƙwararre a fannin sassan adabi da al’adun Hausawa. Daga cikin aikin da ya aiwatar a wannan fuskar sun haɗa da:

a.      Waƙoƙin Baka: Zaɓaɓɓun Matanoni Na Waƙoƙin Baka Na Hausa, wanda ke ƙunshe da waƙoƙin fada 89 da waƙoƙin gama-gari guda 54. Shaihin malamin ya wallafa aikin nasa a shekarar 2009.

b.      A cikin shekarar 2014, ya sake wallafa juzu’i na biyu da aka kasa shi zuwa rukuni biyu. Rukuni na ɗaya yana tattare da waƙoƙi 75, yayin da na biyu ke ɗauke da waƙoƙi 98. Wannan ne ya bayar da jimillar matanonin waƙoƙin da suka kai 173 a diwanin.

c.       A cikin shekara ta 2018 kuma, ya wallafa juzu’i na uku wanda aka taskace waƙoƙi Alhaji Dr. Mamman Shata Katsina. Wannan diwanin yana ƙunshe da waƙoƙi 142, duk waɗanda mawaƙin ya rera.

Sauƙin kan Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau da tawali’unsa da himmarsa wajen horarar da na baya tare da nuna kishinsa ga fanninsa sun yi tasiri matuƙa musamman ga matasan malaman harshen Hausa waɗanda ya koyar da waɗanda ɗalibansa suka koyar da su, har ma da waɗanda ɗaliban-ɗalibansa suka koyar da su, tare ma da waɗanda suka yi hulɗa da shi. Saboda haka ba abin mamaki ba ne a cikin wannan ƙarni na 21 a sami jajirtattun ɗaliban-ɗalibansa su bi sahunsa ta hanyar ƙoƙarin taskace waƙoƙin shahararriyar fasihiyar mawaƙiya Binta Labaran, Fati Nijar wadda ta shahara a fagen waƙoƙin zamani na ƙarni na 21. Shahararta ba inda ba ta kai ba a duk tarsashin farfajiyar ƙasar Hausa. Abu ne mawuyaci a tantance iyakar nahiyar da waƙoƙinta suka kai. Saboda haka ba abin mamaki ba ne a ga malamai kamar: Malam Abu-Ubaida Sani da Malama Halima Daura Kabir da Malam Bashir Abdullahi, sun yi namijin ƙoƙarin gudanar da irin wannan aikin mai wuyar lamari da cin lokaci da uwa-uba masu gida rana a cikin irin yanayin da ake ciki na rashin tsaro. Ko a cikin yanayin zaman lafiya, tattara waƙoƙinn mawaƙi tare da taskace su ba ƙaramin aiki ba ne, ballantana a a haɗa da tarihin mawaƙin. Ga shi kuwa diwanin ya ƙunshi kusan duk ilahirin fitattun waƙoƙin da ta aiwatar tun daga lokacin da ta soma waƙa har zuwa shekarar 2023. Babu shakka sun yi abin a yaba. Allah ya saka musu da kyakkyawan sakamako duniya da gobe ƙiyama. Allah ya ba malamai da ɗaliban Hausa har ma da na wasu harsuna damar cin moriyar wannan aikin. Amin.

Dr. Adamu Rabi’u Bakura
Department of Languages and Cultures,
Faculty of Humanities,
Federal University Gusau,
Zamfara State, Nigeria.

Sa Albarka

Na fara haɗuwa da Hajiya Binta Labaran (mai laƙabi da Fati Nijar) a cikin 2007 lokacin ina Editan jaridar Leadership. A lokacin wata 'yar hatsaniya ta tashi tsakaninta da wani makusancinta a da, wanda ya yi mata gori, abin ya baƙanta mata rai. Sai na shiga cikin lamarin, da yake ina da kusanci da shi, na yi ƙoƙarin kwantar mata da hankali. A lokacin na fahimci cewa Fati mace ce mai tsananin haƙuri da basira, wadda ta san abin da take yi, kuma jajirtacciya.

Tun daga wancan lokacin na kasance makusancinta, kuma muka ci gaba da yin hulɗa mai amfani. Haka kuma, na ci gaba da sha'awar sauraren waƙoƙinta waɗanda suke cike da basira, hangen nesa, da salo kala-kala masu ratsa zukata.

Fati Nijar tana daga cikin manyan zabiyoyin Hausa na zamani. Ta yi shuhura da waƙoƙi mabambanta, masu jan hankali. Ta fara yin fice da waƙoƙin soyayya, kafin ta faɗaɗa zuwa na bikin aure, siyasa, kamfanoni, da zamantakewar yau da kullum. Kusan duk irin waƙar da ake buƙata Fati ta yi, to ta yi ɗin, kuma ta ciri tuta. Haka kuma ta yi waƙoƙin haɗin guiwa tare da manyan mawaƙa a cikin masana'antar finafinai da waƙoƙi na Kannywood, irin su Aminu ALAN Waƙa, Abubakar Sani (Ɗanhausa), Ali Jita, Maryam A. Baba (Sangandale), da sauransu da dama.

Wani abu game da ita shi ne tana da muryoyin zinari guda biyu a maƙogwaronta; idan ka saurara za ka ji su. Ita kaɗai ce a mawaƙan Hausa na wannan zamanin take da muryoyi biyu da take amfani da su a lokaci guda, a waƙa ɗaya, ɗaya na sauka ɗaya na tashi. Wannan wata baiwa ce da Ubangiji ya ba ta.

Fati Nijar ta ci moriyar sana'ar waƙa, domin kuwa ta samu arzikin dukiya da ta jama'a da kuma sanayya. Ta je Makka. Ta taimaki iyayenta da 'yan'uwanta da maƙwabta da sauran jama'a.

Zan iya cewa a fage ɗaya ne kaɗai ta kasa yin tasiri, wato fagen fitowa a fim a matsayin jaruma. A nan, ta ɗan tsoma ƙafa, to kuma sai ta janye ba ta ci gaba ba. A ganina, in da ta ci gaba to da ta yi fice a nan ɗin ma. To amma kuma sai ta tsaya a inda Allah ya yi za ta fi cin abinci, wato fagen waƙa. A nan kam, sai dai ka kwatanta ta da Barmani Choge ko Uwani Zakirai!

Rubuta wannan littafi kan tarihin Fati Nijar da waƙoƙinta ya dace matuƙa. Ta wannan littafin ne za a ƙara sanin wace ce ita, da gwagwarmayar da ta sha, da irin ɗimbin basirar da Allah ya ba ta, da ra'ayoyinta. Su kuma ɗaliban adabi, sun samu abin karantawa. Don haka ina murna da ganin wannan littafin. Allah ya sa jama'a su ci moriyarsa yadda ya kamata. Kuma Allah ya albarkaci rayuwar marubutan littafin da wadda aka yi shi a kanta, wato Hajiya Binta Labaran (Fati Nijar), amin.

Malam Ibrahim Sheme
National Open University of Nigeria (NOUN), Abuja

Tsokaci

Game da GIMBIYAR MAWAƘAN BARGU, Binta Labaran wacce aka fi sani da suna Fati Niger, akwai batutuwa masu tarin yawa a fanni rayuwarta da kuma fannin da duniya ta san ta a kai, wato fagen tsarawa da sadar da waƙoƙi a cikin al'umma a faɗin ƙasar Hausa da kasashen da Hausawa suka yi mazauni a Afirka da kewaye.

Idan aka kalli fannin mu'amala a mahangar addini kamar yadda Ma'aikin Allah (SAW) ya faɗa, Hajiya Fati Niger ta ciri tuta a wannan sashe don ba a san abokin faɗanta ba a wannan masana'anta ta Music Industry, a iyakacin sanina da ita. Ko ba a faɗa ba, mu'amalarta da abokan aiki mata 'yan uwanta zai shaida haka, musamman in aka yi la'akari da zumuncinta hannu da ƙafa. Daga cikin halayen Fati Niger bayan zumunci tana da kyauta. Abin hannunta bai tsone mata ido ba. Sannan tana da wahalar samu a waya ko a zahiri, amma in ka haɗu da ita za ka shaida ba ta da wulaƙanta mutane. Yana daga sirrin ɗaukakarta haziƙa ce mai juriya da jajircewa. Don haka ne ma ta yi tsawon zamani fiye da na sauran tsararrakinta.

A ɓangaren aikin waƙa kuwa kamar yadda ita da kanta take faɗi a wani ɗan wakarta cewa "Ni ko muryata, ita ce jarina"... Duk wanda ya ji salon amon muryarta ya san zabiya ce da ta mori baiwar murya tsurarta daga kyautar Allah. Bayan samun baiwar muryar kuma, Allah ya hore mata iya sarrafa muryar cikin bin amon sautin kiɗa a yayin shirya ɗiyan waƙa a kan ma'aunansu a sitidiyo ko a yayin sadarwa a daɓe.

Mawaƙiya ce da ta ƙware a wajen riƙe hankalin masu saurare a yayin gabatar da waƙa a bainar masu kallo da saurare. Sannan gwana ce ta musamman a wajen ado da tsafta, ma'abociyar son ƙamshi. Duka waɗannan suna daga abubuwa da ka ɗarsa ƙauna da soyayya a bainar jama'a.

Matsayina a wajenta ba abokin aiki ba ne kaɗai, har ta mai da ni matsayin yayanta kamar yadda ta bayyana, duniya ta ji a cikin waƙarta mai taken Girma-Girma. Wannan ya tabbata a aikace domin kuwa duk inda aka ga Sarkin Ɗiyan Gobir, za a ga Gimbiyar Bargu.

Muna godiya ga Allah da muka riski wannan littafi da aka yi na Diwanin rayuwar Fati Niger a halin muna raye ba mu ƙaura ba. Madallah da tunanin waɗanda duk ke da hannu a wannan kyakkyawan yunƙuri na wannan littafi da aka yi shi a bisa cancanta don amfani ga makaranta da ita kanta Zabiyar Bargu.

Aminu Ladan Abubakar (ALAN Waƙa)
10/02/2024

EXECUTIVE SUMMARY

This anthology unfolds the captivating narrative of Hajiya Binta Labaran, known by her stage name, Fati Niger. The book is meticulously organized into ten compelling chapters. Chapter One serves as the foundational exploration, delving into the early years of Binta Labaran's life, from her moment of birth through the transformative teenage period and into her pursuit of Islamic education.

In this chapter, the narrative skillfully weaves through the tapestry of her formative years, providing an intimate portrayal of the artist's upbringing. From the tender moments of her birth to the critical juncture of adolescence, readers gain insights into the influences that shaped her character and ambitions. A noteworthy aspect of Chapter One is its dedicated effort to unravel the familial ties, offering a glimpse into the lives of her parents and grandparents. This elucidation not only enriches the reader's understanding of Fati's background but also underscores the profound impact of her cultural and familial milieu on her artistic journey.

Chapter Two delves into the pivotal phase of Fati Niger’s life, focusing on the myriad struggles, challenges, and triumphs she faced in the realm of Hausa music. This chapter methodically highlights her initial forays into the Hausa musical industry, shedding light on her early works and the genesis of her musical journey.

In the early stages of this chapter, readers are introduced to her inaugural compositions in Hausa music, marking the beginning of an illustrious career. The narrative vividly captures the essence of her initial struggles, painting a picture of the perseverance and dedication that defined her early career. This exploration not only showcases her artistic development but also sets a backdrop against which her future successes are magnified.

Further, the chapter delves into the intricate process behind Fati Niger's song preparation, offering a behind-the-scenes look at her creative process. This insightful section provides a deeper understanding of her artistic methodology, from conceptualization to the final execution of her music. It highlights the meticulous attention to detail, cultural sensitivity, and creative ingenuity that Fati Niger brings to her craft.

Additionally, the chapter presents an evaluation of her standing and influence among her peers in the music industry. It explores her interactions with fellow musicians, her influence in shaping the genre, and the respect she garners within the musical community. This section not only underscores her status as a pivotal figure in Hausa music but also illustrates the impact of her work on the industry and her contributions to the cultural tapestry.

3 through 10 serve as a captivating compilation of transcribed songs by the prolific artist, Hajiya Binta Labaran, AKA Fati Niger. Each chapter commences with a thoughtful introduction, designed to seamlessly guide readers into the thematic essence of the upcoming collection, offering a curated journey through the diverse realms of her musical prowess.

Chapter 3 opens the lyrical anthology, presenting a collection of Religious Songs. The introductory passages provide readers with context, setting the stage for a spiritual exploration of Fati Niger's musical expressions, capturing the essence of her devotion and reverence in the realm of Islamic religious themes.

Chapter 4 unveils Enlightenment Songs, ushering readers into a world of intellectual stimulation and thought-provoking narratives. The introduction to this chapter prepares the audience for a musical experience that goes beyond entertainment, delving into the artist's insightful perspectives on societal and philosophical matters.

Love takes center stage in Chapter 5, where readers are introduced to the realm of Love Songs. The introduction artfully prepares the audience for a melodic journey through the Fatis's expressions of love, heartache, and the myriad emotions woven into the tapestry of romantic narratives.

Chapter 6 shifts the focus to the political landscape, with Political Songs that reflect Fati Niger's engagement with contemporary issues. The introduction sets the tone for a collection that not only entertains but also serves as a mirror to societal and political realities.

Leisure Songs come to life in Chapter 7, offering a refreshing interlude with Binta Labaran's musical renditions that celebrate moments of joy and leisure. The introductory passages invite readers to indulge in the lighter side of her artistic repertoire.

Chapter 8 introduces Featured Songs, showcasing collaborations and featured performances that highlight Fati Niger's versatility and ability to harmonize with other artists. The introduction illuminates the collaborative spirit that permeates this chapter, offering a unique perspective on her artistic collaborations.

Songs dedicated to individual persons unfold in Chapter 9, providing a personalized and intimate experience. The introduction sets the stage for a heartfelt exploration of Fati Niger's lyrical tributes and expressions tailored for specific individuals.

Lastly, Chapter 10 delves into Opinions, revealing Fati Niger's insights and commentary on a diverse array of topics, especially “gender.” The introduction sparks curiosity, inviting readers to engage with the artist's perspectives and opinions, creating a space for contemplation and dialogue.

Together, these chapters create a comprehensive anthology, capturing the essence of Hajiya Binta Labaran's multifaceted talent and offering readers a rich and varied musical experience.

Abu-Ubaida SANI
Dr. Halima Daura Kabir
Abdullahi Bashir


Sadaukarwa iii
Godiya iv
Peer Reviewer’s Report I vi
Peer Reviewer’s Report II ix
Muƙaddima xii
Sa Albarka xv
Tsokaci xvii
ƘUNSHIYA xix
EXECUTIVE SUMMARY xxv
BABI NA ƊAYA
HAJIYA FATI NIJAR A FAIFAN TARIHI
1.0 Shimfiɗa 1
1.1 Taliyon Tsatson Hajiya Fati Nijar 1
1.1.2 Kakannin Fati Nijar Na Ɓangaren Mahaifi 2
1.1.2.2 Malam Muhammad (Baban Kakan Fati Nijar) 3
1.1.2.3 Malam Ibrahim (Kakan Fati Nijar) 3
1.1.2.4 Iyayen Hajiya Fati Nijar 3
1.1.2.5 Haihuwar Hajiya Fati 4
1.1.2.6 Sunanta da Laƙabinta 4
1.1.2.7 Tasowarta 5
1.1.2.8 Karatunta 6
1.2 Naɗewa 6
BABI NA BIYU
IN KA JI WANE... ƊAUKAKAR HAJIYA FATI NIJAR A DUNIYAR WAƘA
2.0 Shimfiɗa 7
2.1 Fara Waƙar Fati Nijar 7
2.2 Waƙoƙinta na Farko 7
2.3 Ɗaukaka Da Ficen Fati a Fagen Waƙa 9
2.4 Ƙalubale a Cikin Gwagwarmayar Rayuwar Fati 10
2.5 Naɗewa 11
BABI NA UKU
WAƘOƘIN FATI NIJAR MASU JIGON ADDINI
3.0 Shimfiɗa 12
3.1 Fuskar Ma’aiki da Haske 12
3.2 Yaa Na Khadija 16
3.3 Yaa Rasulullah 20
3.4 Yaa Sahabu Rasulu 26
3.5 Yaa Rasulu Ɗa Ga Amina 30
3.6 Watan Ramadan 34
3.8 Da Daraja Yake Manzon Tsira 40
3.9 Son Annabi Ne Abin Nema 50
3.10 Naɗewa 54
BABI NA HUƊU
WAƘOƘIN FATI NIJAR MASU JIGON FAƊAKARWA
4.0 Shimfiɗa 55
4.1 Matasa Ku Ajiye Makamai 55
4.2 ‘Yan Matan Arewa 57
4.3 Ka Yi Rawa 60
4.4 Fati Ban Mutu Ba 62
4.5 Duniya Makaranta 64
4.6 Carmagadai 66
4.7 Ku Kula Da Haƙƙinmu Mata 67
4.8 BBC Hausa 68
4.9 Naɗewa 71
BABI NA BIYAR
WAƘOƘIN FATI NIJAR MASU JIGON SOYAYYA
5.0 Shimfiɗa 72
5.1 Masoyi 72
5.2 Habibi 74
5.4 Aure Ka 79
5.5 Sha kallo 81
5.6 ‘Yar Gata 83
5.8 Alagidigo 89
5.9 Tatsuniya 92
5.10 Son Maso Wani 95
5.11 Nijeriya Da Nijar 98
5.12 Mai Asayyaro – ‘Yar Auta 100
5.13 Kabiru 102
5.14 Fati Nijar Bankwana 105
5.15 Nijar Nijeriya Masoya 107
5.16 Yaudara 110
5.17 Uwa 112
5.18 Ritaya 113
5.19 Usman Yakaka 115
5.20 Girma-Girma 118
5.21 Dawo Dawo 120
5.22 Sansani (Sabuntawa) 122
5.23 Mai Bargu Ango, Samira Amarya 127
5.24 Amaryar Sarkin Bargu 132
5.25 Auren Sunna 138
5.26 Musa Daura Ango, Hauwa Amarya 140
5.27 Aure Na So Da Ƙauna 144
5.28 So Ne 149
5.29 Na’ima Amarya, Saminu Ango 151
5.30 Naɗewa 155
BABI NA SHIDA
WAƘOƘIN FATI NIJAR NA SIYASA
6.0 Shimfiɗa 157
6.1 Gwamna Sule Lamiɗo 158
6.2 Muhammadu Buhari Da Muhammadu Issufu 176
6.3 Ku Ƙara Jan Ɗamara 178
6.4 Gwani Lamiɗo 182
6.5 Kashim  Shettima 197
6.6 Kashim  Shettima Dawo Dawo Uban Aiki 203
6.7 Komai Makirci Lamiɗo 210
6.8 Gwamna Ibrahim Geidam Dokin Ƙarfe 221
6.9 Ibrahim Geidam 2011 236
6.10 In Da Ni Ce Buhari 254
6.11 Bola Tinubu 2023 256
6.12 Naɗewa 262
BABI NA BAKWAI
WAƘOƘIN FATI NIJAR MASU JIGON NISHAƊI
7.0 Shimfiɗa 263
7.1 Ga Ni Na Zo 263
7.2 Naɗewa 265
BABI NA TAKWAS
WAƘOƘIN FATI NIJAR NA ƊANI
8.0 Shimfiɗa 266
8.1 Gamayyar Ta’aziyyar Ɗanmaraya Jos 266
8.2 Sakamakon Canji 267
8.3 Naɗewa 269
BABI NA TARA
WAƘOƘIN FATI NA ƊAIƊAIKUN MUTANE
9.0 Shimfiɗa 270
9.1 Bikin Sunan Sarkin Cuma 270
9.2 Iyan Zazzau 272
9.3 Kebbi Sai Godiya 277
9.4 Buratai 281
9.5 Muhammadu Sharif Ɗan Halima ‘Yar Buhari 288
9.6 Abubakar Umar Dutsimmari 291
9.7 Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo Happy Birthday 297
9.8 Honourable Ali Bashir 300
9.9 Uban Dawakin Bauchi 305
9.13 Naɗewa 310
BABI NA GOMA
WAƘOƘIN FATI NIJAR MASU JIGON RA’AYOYI
10.0 Shimfiɗa 311
10.1 Mata Adon Gari 311
10.2 Kar Mu Raina Yaren Hausa 313
10.3 In Ba Mata Ba Gida 317
10.4 Mata Gishiri A Miya 319
10.5 Samu Da Rashi 321
10.6 Naɗewa 323
Manazarta 324
Fasihiya Binta Labaran (Fati Nijar Da Wakokinta)

To obtain a copy, contact:
Phone: +2348036481158
WhatsApp: +2348133529736

Post a Comment

0 Comments