Ticker

6/recent/ticker-posts

Nazari Akan Kirkirarrun Kalmomin Siyasa A Jihar Zamfara Daga 2007 Zuwa 2023

 Takardar ƙara wa juna sani da aka gabatar a ajin ALH 400: Seminars, a Sashen Nazarin Harsuna Da Aladu, Jamiar Tarayya Gusau, Nijeriya, (2022/2023 Academic Session).

Federal University Gusau (FUG) Nigeria

Nazari Akan Kirkirarrun Kalmomin Siyasa A Jihar Zamfara Daga 2007 Zuwa 2023

Na

Muhammad Mustapha Ɗanmanga

Phone number:09031113464

Email: mdmanga88@gmail.com

Tsakure

Wannan muƙala mai taken Nazari akan ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara daga 2007 zuwa 2023 an gudanar da ita ne domin ganin kalaman da al'umar jahar Zamfara ke yi a lokacin siyasar jahar Zamfara da yayin gudanar zaɓe, wannan muƙala zata mai da hankali ne wajen nazarin ƙirƙirarrun kalmomin siyasa da ma'anar siyasa ita kanta,tare da fito da ainihin samuwar ƙirƙirarrun kalmomin a fili.

Fitilun kalmomi

Ƙirƙira,siyasa

1.0 Gabatarwa

Kamar yanda aka sani cewa,duk wanda ya zo zangon ƙarshe na kammala karatun digiri na farko a jami'a,to yakan ruhuta muƙala domin cikamakin karatunsa.

A wannan babi na ɗaya a cikin wannan muƙala da aka gudanar mai taken nazari akan ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara daga 2007 zuwa 2023an yi bayanin dalilin bincike, manufar bincike,da sauransu.

1.1 Dalilin Bincike

Dalilin wannan bincike shi ne domin gano wasu ƙirƙirarrun kalmomin siyasar jahar Zamfara, waɗanda akayi amfani da su a lokacin siyasar jahar, kafin zaɓe da kuma bayan zaɓe.

1.2 Manufar Bincike

Manufar wannan bincike ita ce a ruhuta wannan muƙala domin ya zama cigaba akan wasu ayyuka da suka gabaci wannan, an yi rubuce-rubuce da yawa a kan fannoni daban-daban masu dangantaka da harshe da adabi da kuma al'adu a wannan sashe na nazarin hausa.

Manufar wannan bincike shi ne zai taimaka wajen fahimtar nazari akan kalmomin ƙirƙira da nazari akan siyasa,yin nazari irin wannan a cikin al'umma da ke siyasa zai taimaka wa ɗalibai da masu sha'awa har ma malamai wajen bunƙasa tunaninsu akan ganin yanda ake siyasa da kuma ƙirƙirar sabbin kalmomi a cikin siyasar, tare da fatan ya zama jagora ga masu buƙatar gudanar da bincike irin wannan.

1.3 Maƙasudin Bincike

i. domin nazartar ƙirƙirarrun kalmomin siyasa na jahar Zamfara

ii. Nazartar dalilan da ke haifar da sabbin kalmomin

iii. Nazartar tasirin ƙirƙirarrun kalmomin a siyasar jahar Zamfara

iv. Binciko miye ke haifar da ƙirƙirarrun kalmomin na siyasar jahar.

1.4 Tambayoyin Bincike

i. Me ya sa ake ƙirƙiro kalmomin siyasa a jahar Zamfara?

ii. Mene ne dalilin da ke haifar da sabbin kalmomin?

iii. Waɗanne dalilai ke haifar da tasirin ƙirƙirarrun kalmomin a siyasar jahar Zamfara?

iv. Miye ke haifar da ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara?

1.5 Muhimmancin Bincike

Daga cikin muhimmancin wannan bincike akwai

i. Domin gano tasirin ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara

ii. Domin fahimtar wasu tasirin ƙirƙirarrun kalmomi ga shuwagabanni

iii. Domin bin diddigin ƙirƙirarrun kalmomin ga shuwagabanni da kuma tasirinsu ga al'uma

iv. Domin magance cin mutuncin shuwagabanni ta hanyar furta ƙirƙirarrun kalmomi ga shuwagabanni.

1.6 Kadadar Bincike

Kadadar wannan bincike zata ta ƙaita ne a kan sabbin kalmomin siyasar jahar Zamfara kawai tun daga shekarar 2007 zuwa 2023.

Binciken namu zai taƙaita ne kawai ga iya ‘yan siyasa da kuma al'umar jahar Zamfara.

Sakamakon samun sabbin ƙirƙirarrun kalmom da al'uma ke yi na siyasa, ya haifar da samun ƙirƙira ta sabbin kalmomi daga al'uma zuwa ga ‘yan siyasa a jahar Zamfara.

Wannan aiki ya taƙaita ne a kan nazari akan ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara, wannan kadada ta taɓo amfani da harshe a ɓangaren siyasa,haka kuma an duba yana yin ƙirkirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara.

1.7 Kalmomin fannu

Nazarin ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara na da salon ko-ba-daɗe-ko-bajima, al'umma sai sun jefa ‘yan siyasa da wata sabuwar kalma ƙirƙirarra da ke nuna aibunsa ko alfanunsa, ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara abu ne da keda tsohon tarihi da aka fara tun bayan shuɗewar mulkin soji wato tun fara mulkin farar hula a jahar ta Zamfara.

Dabarun gudanar da bincike

An bi hanyoyi daban-daban domin samun nasarar gudanar da wannan bincike ta hanyoyi daban-daban kamar haka

An yi dabarar nemo wasu ayyuka da suka yi shige da wannan domin fahimtar yanda za'a tsara aikin.

Bayan wannan kuma sai kundayen bincike kama daga digiri na farko da na biyu da littafai da muƙalu da jaridu da sauransu,duk suna cikin dabarun da aka tsara domin samun nasarar gudanar da wannan bincike.

Wata muhimmiyar dabara ita ce, ta bin wasu daga cikin manyan ‘yan social media na gwamnati waɗanda suke da alaƙa da siyasa,hasali ma gunsu ake samun wasu ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar ta Zamfara, domin kawai samun nasarar gudanar da wannan bincike.

2.0 Siyasa

Asalin kalmar siyasa kalma ce ta larabci ma'anarta shi ne, tafiyar da shugabancin jama'a.

Haka kuma larabawa suna amfani da wannan kalmar a duk lokacin da suke nufin shugabanci mai shiryarwa(wato ba wanda zai kai waɗanda ake shugabantar zuwa ga rashin nasara ko halaka ba).

Tarihi ya nuna cewa Farkon wanda ya fara fito da ilimin siyasa wani mai hikima ne daga cikin girkawa,wato masanin falsafar nan wanda ake kira Aristotle wanda ya rasu a cikin ƙarni na huɗu kafin haihuwar Annabi Isa (A,S).

Taƙaitaccen tarihin jahar Zamfara

Jahar Zamfara ta yi suna tun ana cewa “Bature zaki” ma'ana tun tana a matsayin daula, daular Zamfara daɗaɗɗiya ce, tarihi ya nuna cewa daular Zamfara ta kafu ne tun a ƙarni na goma sha uku (13), Kuma tana ɗaya daga cikin daulolin ƙasar Hausa tsofaffi (wato waɗanda suka daɗe da kafuwa).

A ɗaya ga watan Oktoba (1996) ne aka ƙirƙiro jahar Zamfara a lokacin mulkin janar sani Abacha, inda gwamnan soji na farko shi ne Lieutenant kanal jibril Bala Yakubu.

Jahar Zamfara ta samu Gwamnan farar hula na farko a shekarar (1999), a ƙarƙashin mulkin Alhaji Ahmed Sani (Yariman bakura) daga nan sai mulkin siyasar jahar ya ci gaba har zuwa yanzu a yau.

Wani muhimmin abu shi ne jahar Zamfara tana da kasuwanci iri daban-daban, haka kuma jahar ta bunƙasa ne a kan noma.

An yi wa Zamfara jaha a shekarar (1996), a lokacin janar Sani Abacha.

A jahar Zamfara akwai ƙananan hukumomi guda goma sha huɗu (14 local government) waɗanda suka haɗa da

. Anka

. Bakura

. Bukkuyum

. Birnin Magaji

. Bunguɗu

. Gusau

. Gummi

. Ƙauran namoda

. Maru

. Maradun

. Shinkafi

. Tsafe

. Talatan mafara

. Zurmi

2.1 Ma'anar siyasa

Siyasa na nufin tafiyar da shugabancin al'umma.

Siyasa na nufin wani shugabanci ne na al'umma wanda ake bada shi ga wasu daga cikin al'ummar domin su jagoranci sauran jama'a a yankunansu dama ƙasa da jahohi baki ɗaya.

2.2 Ƙirƙira

Masu bincike na farko fannin nazarin harshen Hausa sun gudanar da bincike daban-daban a kan ƙirƙira daga wasu harsuna zuwa Hausa.

Idan akace ƙirƙira ana nufin ƙirƙiro wani abu wanda babu a wurin da aka ƙirƙireshi.

Ƙirƙira na nufin ƙirƙiro wani abu ko wata kalma sabuwa da ake amfani da ita wurin furta wata magana domin ta bada ma'ana a wurin da aka faɗeta.

2.3 Ƙirƙirarrun Kalmomin Siyasa a Zamfara

A duka Najeriya ana samun wasu ƙirƙirarrun kalmomi da ake amfani da su idan siyasa ta matso,wasu Kalmomin kuwa suna zuwa ne a cikin mulkin da wani shugaba keyi, wani akan ƙirƙiro wani suna a dinga kiransa da shi ko kuma a kira yana yin mulkin nasa da sunan wanda za'a ƙirkiro,

Ana samun ƙirƙirarrun kalmomin siyasa ne galibi a wurin matasa ko kuma a ɓangarorin jam'iyar adawa, a jahar Zamfara ma kuwa, bayan matasa da kuma masu amfani da kafar sadarwa (social media)da kuma ɓangaren masu adawa, to a kan samu harda malamai suna ƙirƙiro da wasu sabbin kalmomin a siyasar.

3.1 Samuwar ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara

i. Daga shekarar (1999) lokacin da aka fara mulkin farar hula a jahar Zamfara, wato zamanin mulkin Gwamnan farar hula na farko Alhaji Ahmed Sani (Yarima) tunanin mutanen jahar ya fara canzawa daga rakiyar mulkin soji a jahar,inda suka fara laƙanawa shuwagabanni da ‘yan siyasa waɗansu sunaye da zasu bayyana halayyar su ta fili, amma a wancan lokacin zamanin mulkin yarima, bincike ya nuna babu wata kalma ƙirƙirarra da akayi aiki da ita a lokacin wajen nuna gazawa ko yaba ƙoƙarinsa, har ya kammala mulkinsa a shekarar 2007.

ii. A shekarar (2007) a zamanin mulkin Mamuda Aliyu Shinkafi an samu sabbin ƙirƙirarrun kalmomi a lokacin mulkinsa, an samu kalmomi kamar haka

(A) Mas

(B)  Damo

Kalmar (mas) da aka laƙawa Gwamnan a lokacin, masoyansa ne da jama'ar gari ne suka ƙirƙiro ta saboda soyayyar da ake yi masa, kalmar ta samo asali ne daga sunayen matan shi gwamnan a lokacin,

(A) Mariya

(B)  A'isha

(C)  Sarari

(D) Maciji

Wadannan sune sanadiyar ƙirƙiro kalmar mas.

Damo, a shekarar ( 2007) an samu wata ƙirƙirarrar kalma da aka yi masa a lokacin mulkinsa wato kalmar Damo kalmar Damo ta samu ne sanadiyar hakurn shi gwamnan a lokacin, shi ya sa al'umma sukayi masa laƙabi na sunan Damo.

Kalmar maciji kuwa tasamo asali ne daga ‘yan ɓangaren masu adawa, a lokacin neman zaɓen gwamna a shekarar dubu biyu da shaɗaya( 2011) in da suke kamfen sai suce yanzu damo sunansa maciji, haka kuma wani mawaƙi yayi waƙar in da yake cewa yanzu damo sunansa maciji yau babu lema ta ƙare.

iii. A shekarar (2011) a lokacin mulkin Alhaji Abdul'azizu Abubakar (yari) an samu ƙirƙirarrun kalmomi a siyasar wannan lokacin, in da aka samu wasu ƙirƙirarrun kalmomi kamar haka

(A) Ɗanmakau

(B)  Gajere

(C)  Shehi

Kalmar ɗanmakau wani mawaƙi ne ya ƙirƙirawa gwamnan ita, in da yake cewa a cikin wakar tasa riƙe ƙwarai gwamna ɗanmakau saura kaɗan ka ida kashemu”

Mawakin yayi wakar ne saboda duba da yanda gwamnan ya faro solon mulkinsa.

Kalmar gajere itama mawaƙi ne yafara ƙirƙiro da ita a zamanin mulkin Gwamna Alhaji Abdul'azizu Abubakar (yari), wannan kuwa yayi wakar ne saboda shi yana ɓangaren adawa ne in da yake cewa a cikin waƙar tasa gajeree-gajere, kutara ku buge bayan gidanmu yake.

Kalmar shehi kuwa an kira gwamnan da ita ne saboda ilimi da yake da shi musamman ilimin addini.

iv. A shekarar dubu biyu da goma sha tara(2019) a lokacin mulkin Bello Muhammad (matawalle) an samu ƙirƙirar sabbin kalmomin siyasa a jahar Zamfara a lokacin mulkinsa, kalmomin sun haɗa da

(A) Dodo

(B)  Kwalhewa

(C)  Taliya ba ta zaɓe

Kalmar dodo da ake yiwa gwamna matawalle, shi da kansa ya faɗi ma'anarta a wata zanta wa da yayi da ‘yan jarida in da yace musu kalmar dodo an samo ta ne sabo da ina ba ‘yan adawa tsoro kuma ina firgita su

Kalmar kwalhewa kuwa, tasamo asali ne daga ‘yan siyasar jahar Zamfara a lokacin neman yaƙin zaɓen matawalle karo na biyu, matasa ne ke amfani da kalmar domin moriyar kansu, matasa da sun faɗi kalmar kwalhewa to suna nufin zasu je gidan ɗan siyasa ne su ƙarɓi kudin banza, ma'ana dai duk wanda basu so shi ne ake zuwa wurinsa a kwalhe.

Haka ita ma kalmar taliya ba ta zaɓe, tasamo asali ne a lokacin mulkinsa, in da ‘yan siyasar jahar Zamfara ke raba taliya domin a zaɓesu amma mutane suka fahimci abun da ake nufi da taliyar, bayan an yi zaɓe masu bada taliyar sun faɗi zaɓe ne sai matasa da yara ƙanana suka dinga waka suna faɗin cewa “ taliya ba ta zaɓe”.

V. A shekarar dubu biyu da ashirin da uku (2023) ne gwamna mai ci ya hau kujerar Gwamna wato Dr Dauda Lawal Dare PhD, an samu sabbin kalmomi ƙirƙirarru da aka zo da su a lokacin wannan mulkin nasa kamar haka

(A) Buge-buge

(B)  Langaɓu

(C)  Laka da Gawai

Kalmar buge-buge ta samo asali ne daga bakin gwamnan jihar Zamfara mai ci a yanzu wato Dr Dauda Lawal Dare PhD, a lokacin da ake wata zanta wa da shi da manema labarai an tambaye shi akan yawan fita da yake yi sai yace “yana fita buge-buge ne a wurin maƙotan ƙasashenmu domin ciyar da jahar Zamfara gaba to a wannan lokaci ne kalmar tayi tasiri kuma ta yaɗu a tsakanin al'umar jahar Zamfara.

Kalmar langaɓu kuwa tasamo asali ne daga ‘yan ɓangaren adawar siyasar jahar Zamfara, in da suke alaƙanta Gwamnan ta kalmar langaɓu ma'ana (mutun wanda bayada kuzari)

Kalmar laka da gawai kuwa an samu wani malamin jahar ta Zamfara ne yayi amfani da wannan kalmomin ya jefi gwamnan da kuma mataimakin sa da su, kalmar laka ita ce malamin ya danganta Gwamnan da ita in da ake ganin kalmar na nufin rashin karfi ko kuma rashin kuzari,

Kalmar gawai kuwa ita ce ya jefa ma mataimakin gwamnan ita, in da ake ganin saboda yana da baki ne ya faɗi kalmar akansa.

3.2 Amfanin ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara

Ƙirƙirarrun Kalmomin Siyasa a jahar Zamfara na ɗaya daga cikin manyan makaman da al'umma da ‘yan adawa ke riƙewa a matsayin babban makamin suka ko yabo ga ‘yan siyasa, kalmomin na yin tasiri matuƙa, za'a iya cewa cikin kaso ɗari kashi tamanin ko tamanin da biyar na bayyana halin ‘yan siyasa kai tsaye na alheri ko saɓanin haka

Kalmomin na matukar jawo hankalin al'uma da ƙara musu ƙaimi wajen kambama ‘yan siyasa da kururuta kalmomin ko sunan da aka ƙirƙirar musu da su wajen yiwa al'umma aiki da kuma shayar da su romon dimokuraɗiyya, har ila yau kalmomin na tunzura ‘yan siyasa suji kansu kamar sarakuna ko matasan dawakai masu harbin iska

Misali

Kamar zamanin mulkin Gwamna Bello Muhammad matawalle, al'umma sun ƙirƙirar masa da wata kalma da ke sa shi jin daɗi a duk lokacin da aka ambata masa wannan kalmar wato (Dodo) bincikenmu ya gano cewa ita wannan kalmar ta Dodo tana nufin dodo tsorata maƙiya,(‘yan adawa) wannan kalmar tasa mawaƙa da ‘yan bangar siyasa da maroƙa harma da mutanen gari sukan yi amfani da ita musamman a duk lokacin da sukayi kitiɓis da gwamnan a lokacin hakan keba gwamnan damar yi musu alheri da kuma ɗaukar musu wasu alƙawulla na roman dimokuraɗiyya, sakamakon jin daɗin faɗar wannan kalma gareshi.

Haka kuma wasu Kalmomin suna tasiri ga ‘yan siyasa, sakamakon suna tsoron ‘yaɗa kalmomin da ake yi, hakan na saka su idan aiki ne basuyi ba ya sa akayi musu jifa da wata sabuwar ƙirƙirarrar kalma, to sukan yi ƙoƙarin yin aikin domin magance wannan kalmar.

3.3 Rashin Amfanin ƙirƙirarrun kalmomin siyasa a jahar Zamfara

A ɓangare ɗaya kuma jam'iyun adawa da magoya bayan su da kuma ɗai-ɗaikun wasu mutane sukan yi amfani da damar da suke da ita a kundin tsarin mulkin ƙasa da ya basu damar faɗar albarkacin bakinsu wato(freedom of speech) a turance, wajen jingina wa ‘yan siyasa ko ƙirƙirar musu da munanan kalmomi da ke tunzura ‘yan siyasar harma da magoya bayan su,wanda waɗannan kalmomin na iya haddasa sarewar guiwa ga ‘yan siyasa da kuma haddasa fitina da faɗace-faɗace a cikin al'umma.

Misali

A cikin wannan mulki mai cike da taraɗi na jam'iyar adawa mai mulki wato PDP wadda gwamna mai ci wato Dr Dauda Lawal Dare PhD ke shugabanta a jahar,an samu wasu baƙin ƙirƙirarrun Kalmomi da aka jefa masa da shi da mataimakin sa wato malam Mani mumini wanda aka jiyosu daga bakin wani malami wanda waɗannan kalmomin sun tunzura al'ummar jahar Zamfara in da suka karaɗe yanar gizo (sosai media) ga baki ɗaya.

A ɓangare ɗaya kuma jam'iyar adawa sun yi matukar farin ciki da waɗannan kalmomin wajen amfani da su wurin suka ga gwamnan da mataimakinsa, wanda wannan ya haifar da ka-ce-na-ce a tsakanin al'umar jahar Zamfara, wannan ya nuna ƙirƙirar wata kalma a wani lokacin a jefe shugaba da ita, musamman waɗanda suka saɓawa tarbiyya, ka iya haifar da rashin zaman lafiya a tsakanin al'umar jahar Zamfara.

4.0 Sakamakon Bincike

Kowanne bincike da aka gudanar na ilimi, za'a tarar yana da sakamakon da aka cimma na wannan binciken, wannan bincike namu ya cimma abubuwa kamar haka

i. Ƙirƙirar wata kalma a jingina wa wani daga cikin ‘yan siyasa na yin matuƙar tasiri wajen zaburar da su (‘yan siyasa) ko sanyaya musu guiwa, sakamakon kyawon kalmar ko munin kalmar.

ii. Ƙirƙirarrun Kalmomin Siyasa na faruwa ne sakamakon kamun ludayin shi ɗan siyasar a cikin al'umar da yake mulka, Da kuma irin adawar da al'umma suka nuna masa.

iii. Ƙirƙirarrun Kalmomin Siyasa a jahar Zamfara na yin tasiri har a zukatan al'umma da kuma su kansu ‘yan siyasa har a rumfunan zaɓensu,kamar yadda bincikenmu ya gano.

4.1 Kammalawa

A cikin bayanan da suka gabata na wannan aiki,an yi ƙoƙarin fitowa da ma'anar siyasa da kuma ƙirƙira,haka kuma an yi taƙaitaccen bayani a kan tarihin siyasar jahar Zamfara, tare da bayyana dalilan da ke haifar da ƙirƙirarrun Kalmomin Siyasa a jahar Zamfara, tare da bayyana amfaninsu da kuma rashin amfaninsu.

Manazarta

Hira da ‘yan social media na siyasa, akwai na ɓangaren gwamnati mai ci yanzu da kuma ɗayan ɓangaren adawa (waɗanda suka faɗi zaɓe)

Prof S.A Yakasai (2020) Jagoran Ilimin Walwalar Harshe.

Post a Comment

0 Comments