𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum,Allah ya qarawa mallam Ameen, tambaya na anan shine shin Mallam zamu iya cin yankan arna? waɗanda ba musulmai ba?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
EH ya halatta mu ci yankan da Kirista ko Yahudawa suka
yanka. Amma da sharadi kamar haka
1. Ya zamto yankan ba su yi shi
domin wanin Allah ba. Saboda faɗin
Allah (swt)
حُرِّمَتْ عَلَيْكُمُ الْمَيْتَةُ وَالدَّمُ وَلَحْمُ الْخِنْزِيرِ
وَمَا أُهِلَّ لِغَيْرِ اللَّهِ بِهِ وَالْمُنْخَنِقَةُ وَالْمَوْقُوذَةُ وَالْمُتَرَدِّيَةُ
وَالنَّطِيحَةُ وَمَا أَكَلَ السَّبُعُ إِلَّا مَا ذَكَّيْتُمْ وَمَا ذُبِحَ عَلَى
النُّصُبِ وَأَنْ تَسْتَقْسِمُوا بِالْأَزْلَامِ ۚ ذَٰلِكُمْ فِسْقٌ ۗ الْيَوْمَ يَئِسَ
الَّذِينَ كَفَرُوا مِنْ دِينِكُمْ فَلَا تَخْشَوْهُمْ وَاخْشَوْنِ ۚ الْيَوْمَ أَكْمَلْتُ
لَكُمْ دِينَكُمْ وَأَتْمَمْتُ عَلَيْكُمْ نِعْمَتِي وَرَضِيتُ لَكُمُ الْإِسْلَامَ
دِينًا ۚ فَمَنِ اضْطُرَّ فِي مَخْمَصَةٍ غَيْرَ مُتَجَانِفٍ لِإِثْمٍ ۙ فَإِنَّ اللَّهَ
غَفُورٌ رَحِيمٌ
An haramta muku mũshe da jini da
naman alade da abin da aka ambaci sũnan wanin Allah a gare shi, da maƙararriya
da jefaffiya da mai gangarõwa
da sõkakkiya, da abin
da masu dagi suka ci, face abin da kuka yanka, da
abin da aka yanka a kan gunki (shĩ
ma an haramta). Kuma kada ku yi rabo da kibiyoyi na caca wannan fasiƙanci
ne. A yau waɗanda suka
kafirta sun yanke ƙauna daga addininku. Sabõda haka kada ku ji tsõronsu kuma ku ji tsõroNa. A yau Na
kammala muku
addininku, Kuma Na
cika ni´imaTa a kanku,
Kuma Na yarda da
Musulunci ya zama addini a gare ku. To, wanda aka sanya wa lalũra a cikin yunwa mai
tsanani, ba yana mai
karkata zuwa ga wani zunubi ba, to, lalle ne Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai. (suratul Ma'idah aya ta 3).
2. Ya zamto sunan Allah suka
ambata yayin da za su yanka dabbar.
Idan suka yanka da Sunan Jesus ko Holy spirit ko sunan wani pastor, to ba za a ci ba. Allah (swt) yana cewa
وَلَا تَأْكُلُوا مِمَّا لَمْ يُذْكَرِ اسْمُ اللَّهِ عَلَيْهِ
Kada ku ci daga abin da ba a
ambaci sũnan Allah ba a kansa. (suratul An'am ayah ta 121).
3. Ya kasance abin da suka yanka ɗin ba ya
daga cikin irin dabbobin da Allah ya haramta mana. Misali, alade ko kare ko
jaki ba zai halatta aci ba koda sun yanka shi tare da ambaton sunan Allah.
Amma bai halatta musulmi ya ci abin da 'yan addinin Buddah ko Hindu suka yanka ba. Ko da sun ambaci sunan Allah yayin da za su yanka dabbar.
HUKUNCIN CIN YANKAN KIRISTA
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Kiristoci ne suka yanka Dabba daga Coci Suka kawo mana shin ya halatta
mu ci? Shin cin yanke-yanken Kiristoci a wannan zamani namu na yau yana halatta,
duk kuwa da cewa hanyoyin yanka a wurinsu sun yawaita, watau kamar yin amfani
da injuna, da kuma abubuwa masu daskarar da kwakwalwa a wurin yankan?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Cin yanke-yankensu yana halatta, matukar dai ba a san da cewa an yanka
dabbar ne ta hanyar da ba ta dace da Shari'a ba, saboda asalin lamari shi ne
halaccin cin sa, kamar dai yankan musulmi, saboda faɗin Allah Maɗaukaki:
وَطَعَامُ
الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ حِلٌّ لَكُمْ وَطَعَامُكُمْ حِلٌّ لَهُمْ
Da abincin waɗannan
da aka ba su littafi halal ne yake a gare ku, kuma abincin ku halal yake gare
su. (Surah Al-Maa’idah: 5).
Ya halatta muci yankan da Kirista ko Yahudawa suka yanka. Amma da
sharadi kamar haka:
1. Ya zamto yankan basu yishi domin wanin Allah ba. Saboda faɗin Allah (swt):
حُرِّمَتْ
عَلَيْكُمُ الْمَيْتَةُ وَالدَّمُ وَلَحْمُ الْخِنْزِيرِ وَمَا أُهِلَّ لِغَيْرِ اللَّهِ
بِهِ وَالْمُنْخَنِقَةُ وَالْمَوْقُوذَةُ وَالْمُتَرَدِّيَةُ وَالنَّطِيحَةُ وَمَا
أَكَلَ السَّبُعُ إِلَّا مَا ذَكَّيْتُمْ وَمَا ذُبِحَ عَلَى النُّصُبِ وَأَنْ تَسْتَقْسِمُوا
بِالْأَزْلَامِ ۚ ذَٰلِكُمْ فِسْقٌ ۗ الْيَوْمَ يَئِسَ الَّذِينَ كَفَرُوا مِنْ دِينِكُمْ
فَلَا تَخْشَوْهُمْ وَاخْشَوْنِ ۚ الْيَوْمَ أَكْمَلْتُ لَكُمْ دِينَكُمْ وَأَتْمَمْتُ
عَلَيْكُمْ نِعْمَتِي وَرَضِيتُ لَكُمُ الْإِسْلَامَ دِينًا ۚ فَمَنِ اضْطُرَّ فِي
مَخْمَصَةٍ غَيْرَ مُتَجَانِفٍ لِإِثْمٍ ۙ فَإِنَّ اللَّهَ غَفُورٌ رَحِيمٌ
An haramta muku mũshe da jini da nãman alade da abin da aka ambaci
sũnan wanin Allah a gare shi, da mãƙararriya da jefaffiya da mai gangarõwa da sõkakkiya, da abin da mãsu dãgi suka ci, fãce abin da kuka yanka, da abin da aka yanka a
kan gunki (shĩ ma an
haramta). Kuma kada ku yi rabo da kibiyoyi na cãca wannan fãsiƙanci ne. A yau waɗanda suka kãfirta sun yanke ƙauna daga addininku.
Sabõda haka kada ku ji tsõronsu kuma ku ji tsõroNa. A yau Nã kammalã muku
addininku, Kuma Nã cika ni´imaTa a kanku, Kuma Nã yarda da Musulunci ya zama addini a gare ku.
To, wanda aka sanya wa lalũra a cikin yunwa mai tsanani, bã yana mai karkata zuwa ga wani zunubi ba, to, lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai. (suratul Ma'idah
aya ta 3).
2. Ya zamto sunan Allah suka ambata yayin da zasu yanka dabbar. Idan
suka yanka da Sunan Jesus ko Holy spirit ko sunan wani pastor, to ba za'a ci
ba. Allah (swt) yana cewa:
وَلَا
تَأْكُلُوا مِمَّا لَمْ يُذْكَرِ اسْمُ اللَّهِ عَلَيْهِ
Kada ku ci daga abin da ba a ambaci sũnan Allah ba a kansa. (suratul
An'am ayah ta 121).
3. Ya kasance abinda suka yanka ɗin baya daga cikin irin dabbobin da Allah ya haramta mana. Misali,
alade ko kare ko jaki ba zai halatta aci ba koda sun yanka shi tare da ambaton
sunan Allah.
Amma bai halatta musulmi yaci abinda 'yan addinin Buddah ko hindu suka
yanka ba. Koda sun ambaci sunan Allah yayin da zasu yanka dabbar.
Sheik Uthaimeen ya ce cikin littafinsa Ash-Sharhul Mumtii 12/148:-
ﻓﺎﻟﺤﺎﺻﻞ
: ﺍﻥ ﺍﻟﺬﻱ ﻋﻠﻴﻪ ﺟﻤﻬﻮﺭ ﺍﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﺍﻥ ﻣﻦ ﺗﺪﻳﻦ ﺑﺪﻳﻦ ﺍﻫﻞ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻧﺘﺴﺐ ﺍﻟﻴﻬﻢ ﻭﻟﻮ ﻛﺎﻥ ﻳﻘﻮﻝ
ﺑﺎﻟﺘﺜﻠﻴﺚ ﻓﺎﻧﻪ ﺗﺤﻞ ﺫﺑﻴﺤﺘﻪ، ﻭﻳﺤﻞ ﻧﻜﺎﺣﻪ
Ma'ana: ((A takaice dai: Abin da majoratin masu ilmi suka ce shi ne duk
wanda ya yi Addini da addinin Ahlul kitabi, ya kuma danganta kansa zuwa gare su
koda kuwa yana cewa Allah uku ne, to lallai ne cin wannan yankan halal ne, kuma
auren su halal ne)).
Sa'annan Al Imamul Dabarani, Abul Dar'da, wata an yi masa Fatawa akan
cin Yankan Kirista, suka ce masa Kiristoti ne suka yanka Dabba daga Coci Suka
kawo mana shin ya halatta mu ci? sai da ya girgiza kansa yace Allah yafe mana,
sai ya tambaye su shin su ɗin ba Ahlul-Qitabbi bane? Sai suka ce ahlul-qitab ne, sai yace ai
Abincin su halal ne, sabida haka cewar ba'a San ya suka yanka ba a Ina suka
yanka, duk wannan ba hujja bane na nuna Haramcin cin sa ba. Kawai in kana
Bukata ka ci in ba ka Bukata ka bari, shikenan shin ba Allah ya halatta mana
cin abin Yankan su ba? Mun yi bayanin Ayar jiya a Dayan Fatawar mu, sa'annan
Duk Imaninka duk Tsarkinka duk Kyan-Kyaminka, shin mun Kai Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wa Sallam ne? Duk Ayar da mutum zai karanta ko ya fassara ka
tsaya ka dubi ya rayuwar Annabi yake?
Har kullum Ahlus Sunnah wal Jama'ah a duk inda suke suna gina Addinin
su ne a kan abin da ya tabbata daga Alkur'ani Mai girma da kuma ingantattun
hadithan Annabi mai tsira da amincin Allah masu daraja. Amma sabanin su, su kan
gina Addinin su ne kawai a kan abin da ya dace da son zuciyar su.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.