Ticker

6/recent/ticker-posts

Fifita Miji A Kan Iyaye

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum. Iyayena ne suka ɗauki nauyin karatuna har ga shi yanzu ina aiki a gidan mijina. Kowane wata ina taimaka musu daga albashina, mijina kuma ina yi masa hidimar da ta fi haka. To menene hukuncin wannan ɗin a addini?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.

Ɗaukar nauyin karatu da iyaye suka yi miki wannan wani haƙƙi ne na ki a kansu da suka yi ƙoƙarin saukewa kafin zuwan mijinki. Kuma wajibi ne ki kyautata musu a yau, domin sakayya a gare su, da kuma girmamawa da martabawa gare su a matsayinsu na iyaye, musamman ma idan suna cikin buƙatar irin wannan taimakon.

Amma a bayan aure miji shi yake da haƙƙi mafi girma a kan mace fiye da iyayenta. A cikin hadisi Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya faɗi cewa

لَا يَصْلُحُ لِبَشَرٍ أَنْ يَسْجُدَ لِبَشَرٍ ، وَلَوْ صَلُحَ لِبَشَرٍ أَنْ يَسْجُدَ لِبَشَرٍ ، لَأَمَرْتُ الْمَرْأَةَ أَنْ تَسْجُدَ لِزَوْجِهَا ، مِنْ عَظْمِ حَقِّهِ عَلَيْهَا وَالَّذِي نَفْسِي بِيَدِهِ ، لَوْ كَانَ مِنْ قَدَمِهِ إِلَى مَفْرَقِ رَأْسِهِ قُرْحَةٌ ، تَجْرِي بِالْقَيْحِ وَالصَّدِيدِ ، ثُمَّ اسْتَقْبَلَتْهُ فَلَحِسَتْهُ ، مَا أَدَّتْ حَقَّهُ

Ba ya kyautatuwa ga wani mutum ya yi sujada ga wani mutum: In da zai kyautatu wani mutum ya yi sujada ga wani mutum, da na umarci mace ce ta yi sujada ga mijinta, saboda girman haƙƙinsa a kanta. Ina rantsuwa da Allaah wanda raina ke hannunsa! In da a ce tun daga tafin ƙafafuwansa har zuwa ƙoƙoluwar kansa miji ne yana zubar da ruwan ciwo da jini, kuma sai matar ta tashi ta sanya harshe ta lashe shi kaf, da kuwa ba ta biya haƙƙinsa ba! (Sahih Al-Jaami: 7725).

Bai faɗi irin wannan game da iyayen mace ba.

Kuma akwai hadisin Waathilah Bn Asqa’i (Radiyal Laahu Anhu), daga Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce

لَيْسَ لِلْمَرْأَةِ أَنْ تَنْتَهِكَ شَيْئًا مِنْ مَالِهَا إِلَا بِإذْنِ زَوْجِهَا

Bai halatta ga mace ta bayar da wani abu daga dukiyarta ba sai da izinin mijinta. (As-Saheehah: 775).

Bai faɗi irin wannan ma game da iyaye ba.

Don haka dai duk da kasantuwar iyaye suna da matsayi mai girma, amma kuma miji shi ma ba a baya ya ke ba. Lallai mace ta san wannan kuma ta ɗauki matakin bai wa kowane sashe haƙƙinsa ba tare da tawayewa ko naƙasa komai ba.

Wannan shi ne adalci.

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Ga masu tambaya sai su turo ta WhatsApp number: 08021117734

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇 https://chat.whatsapp.com/K7RkQRMf2b57l3UENoJ1Or

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments