𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Miji ne ya saki matarsa saki ɗaya, amma
sai ya ce ta zauna a gidansa ta yi iddah, to tana iddar kuma ya je mata kamar
sau uku (ya Sadu da ita) sai daga baya ya ga ta yi jini uku saiya ce wai
iddarta ta kare za ta iya tafiya gida. to ya ya wannan mu'amalar da ya yi da
ita akwai aure ko ya lalace sai an sake sabon daurin aure?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Idan mutum ya saki matarsa, kuma wannan sakin ya kasance shi ne na farko ko
na biyu to bata fita daga idda ba, idan ya so zai iya maido ta da furuci, misali
ya ce na maidoki ko na ci gaba da rikonki. Koya maidata ta hanyar wani aiki da
yake nufin mayarwa, kamar ya kusanceta da niyyar mayarwa to mayarwar ta yi.
Iddar macen datake haila shi ne: Al'ada uku (jini uku) idan ta samu tsarki
daga wannan jini ukun ta yi wanka, to tagama iddarta.
Iddar macen da bata haila saboda yarinta kota daina hailar, wata uku ne za
tayi.
Iddar mai ciki kuwa shi ne ta haife abin da ke cikinta, abin da ya gudana
na jima'i bayan wannan aikin haramun ne.
Wajibine Wannan mijin ya tuba zuwaga Allah maɗaukakin sarki a kan afkawa jima'in dayayi
tareda ke, bisa rashin kudurce komai na dawo dake ba, kuma ya zama wajibi Ku
sake daura wani auren da Sharuɗɗansa
na WALIYYI da SHEDU da SIGA da SADAƘI idan kowannenku ya na kwadayin hakan.
Ba ya halatta a gareshi ya sake kusantarki, harsai ansake daura muku aure
sabo.
Saboda haka wannan kusantarki dayayi batareda ƙudurce yai maidake ta
sigogin da malamai suka tattauna wanda suke nuna mutum yadawo da matarsa ba, haramunne
yanzu agareshi ya sake yi miki duk wani abu daya halatta tsakanin miji da
matarsa harsai an daura muku sabon Aure da sadaki da shaidu da waliyyi
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .
MIJINA
YA SADU DA NI INA CIKIN IDDA A GIDANSA
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu malam
mijine ya saki matarsa sai ta zauna dan tayi iddah kafin tagama iddan kuma sai
ya kwanta da ita kuma baice yamaida itaba, to malam ya matsayinta yake???
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis Salaam Wa Rahmatullah wa Barakatuhu:-
Malamam Malikiyya Suka Ce ko Hannun ta ya Kama toh
ya Maida ta Ma'ana yanzu tana a matsayin Matar sa. Bare kuma ya sadu da ita
wato ya yi Jima'i da ita kin ga ai shikenan ta koma a matsayin Matar sa.
Amma dai Maganar Gaskiya sai an Binciki Niyyar sa
tukuna?. Shin Yana Nufin Iskanci Ne ya sa ya sadu da ita, Ko kuma yana Nufin ya
Maida ita a matsayin Matar sa?
Duk Abin da ya fadi, toh da shi za'a yi Amfani,
Sabida Hadisin INNAMAL A'AMALU BINNIYYATI.
Sa'annan Ku ma Matan ai da naku, ai irin wannan
duk Zumudin ki duk Sha'awar ki, yakamata ya yi ku yi shi Kai a waye, mene ne da
naku? An San Cewa har gobe kina matsayin Matar sa ne, Kuma Shari'a ya yarda ki
yi iddar ki a Cikin Gidan sa, toh Amma yakamata Idan kina idda a Cikin Gidan sa
duk Lokacin da ya zo Miki da Cewa Zai Sadu da ke, Sai ki tambaye shi Malam a
wani Matsayi kenan za ka Sadu Dani ko ka manta cewa ka Sake ni Ina Idda ne sai
ki tsaya ki ji?
Ya Gaya Miki matsayin ki tukuna a yanzu kafin ki
ba shi Kanki ya yi Jima'i da ke, Idan Ya ce Miki ya Dawo da ke ne yanzu kina a
Matsayin Matar sa, kin ga Kin ji da Kunnen ki kina iya yin recording ki ajiye
hujja domin kar ya gama ya ce ai shi bai Fadi hakan ba, idan Kun yi haka yanzu
kin San matsayin Jima'in da zai Yi da ke.
Idan Kuma ya yi Shiru ya Ƙi ya ce Miki komai ya ƙi ya amsa ko ya yi niyyar cewa ya dawo da ke, ko
Kuma ya ce shi kawai ki ba shi Kanki ba tare da ya Gaya Miki Cewar ya dawo da
ke ko a'a ba, kawai ya ce ki ba shi kanki, toh sai Ki Ƙi ba shi kanki kar ki ta6ba yarda, Sai ki Ji ya ce
ya dawo da ke, toh Yanzu kin dawo Matar sa sai ki ba shi Kanki ya yi abun da
yake so, domin gudun abun da zai zo ya dawo, Saboda zai iya yin Jima'in da ke
sannan ya dawo kuma ya ce ai Bai dawo da ke ba, ya ce Iskanci ya yi da ke, Kin
ga an koma wani Ɓangaren kuma.
Saboda haka Shari'a ya Gama bayanin Komai, idan
zakuyi Abu duk zumudin ki da kwaɗayin ki da
Sha'awar ki yakamata kiyi tambaya, ki San matsayin ki tukuna kafin nan ki Mika
Masa kanki ya yi abun da yake so, amma Kuna tare Jiya Bai ce ya ce dawo da ke
ba, Dazun ma bai ce ya dawo da ke Kafin ya Sadu da ke ba, bai ce ya dawo da ke
kawai ya zo yanzu ya ce ku yi Jima'i! ke Kuma ba ki tambaye shi a wani Matsayi
ba kawai Kika ba shi Kanki, idan shi a Niyyar sa bai Yi Niyyar dawo da ke fah?
Kuma ga shi ya yi Jima'i da ke ya za ki yi toh? akwai wadda hakan ya taɓa faruwa da ita sai da suka gama Jima'i ta ce toh yanzu
Ina matsayin Matar ka ai shikenan Allah ya Kara haɗa kan mu! ya ce ina ai shi bawai ya dawo da ita ba ne,
kin ga kenan Sha'awar ta da zumudin ta ya jawo mata wani abun.
Sabida Haka ki tambaye shi ya Gaya Miki duk abun
da ya ce sai ayi Amfani da shi. Sannan ku kiyaye irin wannan ko Hannun ki ya taɓa kin dawo ballatana ace ya Sadu da ke. Toh amma me
Niyyar sa? iskanci ya yi da ke ko me?
Allah Shine Masani.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp. com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www. facebook. com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t. me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.