𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mene ne Hukuncin Ɗora Alƙur'ani Ko Littafin Addini a kan Gadon
Da'ake Jima'i Akansa?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله.
Babu saɓani
tsakanin malamai a kan wajabcin girmama Alƙur'ani da kulawa dashi.
Nawawi rahimahullahu ya ce: Malamai sun haɗu a kan wajabcin kulada Alƙur'ani
da girmama shi.
Almaj-Mu'u (2/85)
Malamai sun amabaci halaye dayawa waɗanda sanya ƙur'ani acikinsu wulakantashi ne, daka
cikinsu akwai:
1. Jefar da Alƙur'ani aka sa.
2. Ko ajiyeshi awajan najasa.
3. Ko tofa masa majina.
4. Ko takashi da tuƙun ƙunashi.
Dasauran sifofi wanda suke na wulaƙanta ƙur'anine wanda suke nuna
yiwa zancen Allah hawan kawara da wulakantarwa.
Amma Ajiye Alƙur'ani a kan shimfida ko katifa ko gadon da'ake
jima'i akansa baya cikin wulakanta alƙur'ani yahalatta babu laifi a kan hakan.
Wani mutum yatambayi Abdullahi dan Abbas ya ce: zan iya sanya Alƙur'ani
a kan shimfidar danake jima'i akai? Saiyace: (Na'am).
Abdurrazaƙ yaruwaito acikin Musannaf dinsa (2/171), da Ibnu
Abiy dauda acikin Al-masããhif (446) sannan aduba "muƙaddimar Asasiyyah fy
Ulumul ƙur'an na Abdullahi Yusuf jadeed (562)
Malama lajnatul da'imah sukace: yahalatta mutum ya karanta ƙur'ani
aɗakin baccinsa da
shimfidar baccinsa, idan bashida janaba, dakaranta Alƙur'ani idan yanada
Alwala.
fatawa lajnah (3/67)
Inda ace haramunne sanya Alƙur'ani a kan shimfidar jima'i ko ɗakin da ake bacci wanda galibi acikinsu
jima'i tsakanin ma'aurata yake gudana haramunne da Annabi yabayyanawa sahabbai
hakan dakuma an kuzuzuta abun saboda bukatar mutane zuwa gareshi.
Saboda haka babu laifi dora alƙur'ani a kan shimfidar kwanciya bacci ko gado ko ɗakin bacci matukar wurin yanada tsarki.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp. com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www. facebook. com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t. me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.