Ticker

6/recent/ticker-posts

Mande Muhammad Kurfi A Adabin Hausa: Nazarin Littafin Magana Iyawa Ce

Bashir Aliyu Sallau, Ph. D.

Sashen Koyar da Hausa
Jami’ar Gwamnatin Tarayya Dutsin-ma,
Jihar Katsina, Nijeriya 

TSAKURE

Hausawa na cewa, “magana jari ce, yaro kawo kuɗi a gaya maka”. Wannan batu gaskiya ne domin kuwa dukkan wanda Allah Ya ba baiwar iya magana da kowane harshe na duniya zai sami masu sauraron su don ƙaruwa da ire-iren hikimomin da suke ƙunshe cikin waɗannan maganganu. Haka kuma, wasu ba su gajiya da sauraren sa ko da kuwa za su biya kuɗi don shiga wuraren da ake aiwatar da ire-iren waɗannan maganganu na hikima. Ba a bar al’ummar Hausawa baya ba wajen aiwatar da ire-iren waɗannan maganganu na hikima ba, don kuwa Allah Ya ba al’ummar Hausawa da harshen Hausa maganganun hikima masu tarin yawa waɗanda suke ƙunshe cikin karin-magana da baƙar magana da habaici da kacici-kacici da ƙarangiya da zaurence da sauransu da dama. Masana da manazarta da ɗalibai sun yi ƙoƙarin ta hanyar taskace su a bugaggun littattafai da kundaye a jami’o’i da kwalejojin zurfafa ilimi da sauransu. Wasu kuma sun gabatar da su a tarukan ƙara wa juna ilimi, wasu kuma an buga su a mujallu don al’umma ta sami abin karantawa don ƙarin ilimi ko don samun nishaɗi. Domin samun abin karantawa ne ya jawo hankalin Mande Muhammad Kurfi ya rubuta littafi mai suna “Magana Iyawa Ce”. A wannan littafi an kawo nau’o’i daban-daban na maganganun hikima na Hausawa ciki har da karin magana. Dangane da haka, maƙasudin wannan takarda shi ne, ta yi nazari wannan littafi don fito da ire-iren maganganun hikima da suke ƙunshe cikinsa, sannan a yi tsokaci kan wasu daga cikinsu.   

1. 0 Gabatarwa

Marubuta adabin Hausa irin su, Madauci, I. da wasu (1972) da Skinner. N (1980) da Ɗangambo. A, (1984, 1990) da Yahaya, I. Y. (1981, 1988, 1989, 1995) da Gusau (1995) da Skinner. N, (1980) da Umar, M. B. (1984) da Ɗanhausa, A. M. (2012) sun gabatar da muhimman ayyuka waɗanda suka shafi maganganun hikima na Hausawa a kan karin magana da baƙar magana da azancin magana da habaici da ƙarangiya da kacici-kacici da adon magana da take da kirari da sara da sauransu.

A wannan zamani an sami wasu marubuta irin su Mande Muhammad Kurfi RN, CNO, wanda aka fi sani da suna Ali Kano, ya wallafa littafi a kan ire-iren maganganun hikima da al’ummar Hausawa suke amfani da su a bakunansu a yau da kullum. Ya raɗa wa littafin suna Magana Iyawa ce. Tun kafin a yi nisa wannan suna da aka ba wannan littafi ya dace da ƙumshiyar gundarin jawaban da suke cikin littafin.

2. 0 Taƙaitaccen Tarihin Mawallafin Wannan Littafi:

Domin samun cikakken bayani kan tarihin wannan mawallafi, ana iya duba bangon littafin na baya, amma duk da haka, a taƙaice, an haifi Mande Muhammad Kurfi, a garin Kurfi, Ƙaramar Hukumar Kurfi ta Jihar Katsina, a ranar 22 ga watan Afrilu, 1959. Ya yi karatun Firamare a nan Kurfi, na Sakandare a Katsina. Sannan kuma ya yi karatun kiwon lafiya. Ya yi aikin koyarwa a Firamare, kuma ya yi aiki a asibitoci da dama a Jihar Katsina. Ta fuskar rubuce-rubuce, ya rubuta litttattafai masu yawan gaske. Bayan wannan littafin akwai wasu da ya rubuta waɗanda suka haɗa da Ƙamusun Ingilishi da Hausa, sai kuma In Ɓera da Sata, Daddawa ma na da Wari.

3. 0 Zubin Wannan Littafi

Bayan shafi takwas (ɗiii) na gabatarwa, wannan littafi yana da yawan shafuka 179 waɗanda aka wakilta da alamun ƙirga na Romanci. Duk da kasancewar ba a raba littafin zuwa babi-babi ba, amma an shirya shi bisa bin tsarin abjadi, wato daga A zuwa Z. Sakamakon bin wannan tsari, an yi amfani da maganganun hikima waɗanda suka haɗa da karin magana da azancin magana da adon magana da baƙar magana da sauransu a wuri ɗaya, inda suka riƙa yi wa juna shigar giza-gizai, ta hanyar bin baƙin da ya fara fitowa a wannan magana. Haka kuma, baƙaƙe masu laƙwasa Ɗɓɗ da Ɗɗɗ da Ɗƙɗ an kawo magangunun hikima da aka fara da waɗannan baƙaƙe tare da takwarorinsu Ɗbɗ da Ɗdɗ da Ɗƙɗ kamar haka;

 

BAƘI

MAGANAR HIKIMA TA FARKO DA TA ƘARSHE

ADADI

A

A bakin tsoho goro kan tsufa, sai aka ƙare da, A zuba Shinkafa ruwa a ga tashin kwafsa, shafi na 9-29.

546

 

B/Ɓ

Ba a azawa kaza sirdi, aka ƙare da, Buzuzu da ya bugi bango ya ce kai duniyar ma ta ƙure, shafi na 29-44.

417

C

Caca asara ce ga wanda ya santa, sai aka ƙare da Cuta gaba aka yi ko baya, shafi na 44-46.

48

D/Ɗ

Da a’a da a’a majiyaci yake cika cikinsa, sai aka ƙare da Ɗuwawu ne mu dole a zauna da mu, shafi na 46-65.

487

F

Faɗa mai tada taro, sai aka ƙare da, Fuskar da aka zaga ba ta fi ƙarfin mari ba, shafi na 65-66.

51

G

Ga abin kwaɗo babu ƙuli, sai aka ƙare da, Gyara lafiyar wani kai ka ɓata taka, shafi na 66-74.

293

H

“Haba ina mazan su ke” Ɗan Daudu ya shiga layin mata, sai aka ƙare da, Hutun Jaki da kaya a baya, shafi na 74-80.

68

I

Icce gidana inuwa gidan wani, sai aka ƙare da, Iya yi kai mayya ɗaki, shafi na 80-97.

417

J

Jaɓa ba ta jin warin jikinta, sai aka kare da, Juma’ar da ke da kyau tun Laraba a ke gane ta, shafi na 97-100.

67

K/Ƙ

Ka bari a yi da waɗanda suka iya Bamaguje ya shiga maganar addini, sai aka ƙare da, Kyawon wuya a tambayi soja, shafi na 100-126.

699

L

Labari ba shi yin daɗi sai an haɗa da ƙarya, aka ƙare da, Lomar dutse da ga ba hannu ba sai dai jifa, shafi na 126-128.

56

M

Ma’abucin barka ko gidan mutuwa sai ya yi, aka ƙare da, Mutuwa ba ki ƙyamar raggo, shafi na 128-143.

458

N

Na ciki bai san asirin na waje ba, aka ƙare da, Nuna sani kasuwar jahilci wauta ne, shafi na 143-146.

68

R

Raba mugu da makami ibada, aka ƙare da, Ruwan zuma mai haɗa al’umma, shafi na 146-151.

153

S

Sa’a ka sa makaho taka kuɗi ya ɗauka, aka ƙare da, Suri dare ɗaya ka ka girma, shafi na 151-160.

350

T

‘Ta’Allah ba taku ba, in ji matsoraci, aka ƙare da, Tsutsar nama ita ma naman ce, shafi na 160-167.

177

U

Uban kasada zalɓe mai tura ƙafa rami, aka ƙare da, Uwar wani matar wani, shafi na 167-168.

16

W

Wace ni da ɗaura zane uwar miji tsirara, aka ƙare da, Wuyar wuta sainƙarfe, shafi na 168-176.

104

Y

Ya amshi makulli ga zakara, aka ƙare da, Yunwa mai kashe raggo, shafi na 176-183.

175

Z

Zaɓe mai fidda gwani, aka ƙare da, Zuwa da wuri ya fi zuwa da wuri, shafi na 183-186.

72

A – Z

JIMLA

4722

 

A jimlace an sami magangunan hikima da azanci 4722, amma a jadawalinsu cikin littafin an kawo 4724. A shafi na 150 ba a kawo ire-iren waɗannan magangunu ba a lamba ta 3797 da kuma 3798.

A cikin littafin an ƙawata shi da hotunan da suka fito da wasu maganganun hikima na Hausawa waɗanda za su ƙara wa mai karatu nishaɗi da fahimtar saƙon da ake son isarwa.

A gaban bango na wannan littafi an ɗora hoton gidan Bahaushe wanda yake ƙunshe da ɗaki na gargajiya wanda aka zagaye wani ɓangare na gidan da katangar bulo. Ɗaya ɓangaren kuma da dangar kara. Sannan aka nuna hoton wani mutum a tsakiyar gidan, yana zaune a gaban tukunyar dafa abinci yana riƙe da ludayin motsa miya ko abinci. An kuma kawo hoton akuya tana kiwo da kaza ita ma tana kiwo. Wannan zubi da aka yi yana bayyana dukkan abin da za a gani cikin littafin, zai yi bayani ne kan Bahaushe da yadda yake tafiyar da rayuwarsa ta yau da kullum.

A bangon baya kuma, aka kawo hoton mawallafin wannan littafi da taƙaitaccen tarihin rayuwarsa da kuma alama da sunan maɗaba’ar da ta buga littafin.

4. 0 Manufar Wannan Littafi

Kamar yadda aka bayyana dangane da tarihin mawallafin wannan littafi, Ali Kano, yana da matuƙar sha’awar bayar da gudummuwa a fannin rubuce-rubucen tarbiyyantar da al’umma a cikin salo da nishaɗi. Babu shakka wannan sha’awa tasa ta fito a cikin wannan littafi Magana Iyawa ce. Masana da manazarta da ɗaliban adabi da fannin nazarin maganganun hikima na Hausa, irin su Abdulƙadir Ɗangambo da Sa’idu Muhammad Gusau da Muhammad Balarabe, a rubuce-rubucen su sun bayyana cewa, hanyar da al’umma za ta sami nishaɗi na cikin maganganun hikimar da magabata suka bari ta hanyar karin magana da habaici da azancin magana da baƙar magana da sauransu. Dangane da haka, manufar wannan littafi ita ce, a fito da ire-iren baiwar da Allah ya yi wa Hausawa ta iya magana, waɗanda ake yi ta hanyar karin magana da haibaici da azancin magana da baƙar magana da shaguɓe da gugar-zana da hannun-ka-mai-sanda don koyar da tarbiya ga al’umma musamman yara ƙanana da matasa maza da mata, a kuma taskace su yadda al’umma za ta amfana. Wannan marubuci ya yi ƙoƙari matuƙa wajen fito da ire-iren waɗannan maganganun hikima na Hausawa a cikin wannan littafi, waɗanda za mu ɗan tsakuro wasu daga cikinsu ta fuskar karin magana da baƙar magana da azancin magana da habaici, kamar haka;

4. 1. 1 Karin Magana

Karin magana wata hikimar magana ce da Hausawa suke yi a dunƙule a cikin zance da ‘yan kalmomi kaɗan. Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero ya bayyana karin magana, a matsayin, “magana ta musamman wadda sai an yi tsokaci ake ganewa (2006: 235). Mafi yawancin karin magana yana da ɓangare biyu, na farko yana yin jimlataccen bayani ko furuci na wata manufa, ɓangare na biyu kuma yana yin sharhi ko ƙarin bayani, kan abin da ɓangare na farko ya faɗa (Ɗangambo, 2008:67). An kawo karin magana masu ɗimbin yawa a wannan littafi. Ga misalin kaɗan daga cikinsu:

10. A bar yabon ɗan kuturu, sai ya tashi da yatsunsa.

26. Abin dariya, yaro ya tsinci haƙori.

563. Ba a canza wa mage gida, sai an sanya ta cikin buhu.

1199. Ɗan da uwa ta bari, shi yake yin kuka.

2235. In ruga ba ta zauna lafiya ba, rundawa ba su zama lafiya.

3000. Ƙulalliyar kyauta, ita ke tada hankalin mai karɓa.

3678. Raba ni da koken uwa kuturwa, kaka makauniya.

3721. Rana mudun aiki, ko ta gobe sai ta faɗi

3734. Rashin kira, ya sa Karen bebe ya ɓata.

3849. Sabon salo, kukan mutuwa da guɗa.

3869. Sai hali ya yi daidai, ake abota.

4030. Sanin asali, ka sa kare ya ci alli.

4133. Shimfiɗar fuska, ta fi shimfiɗar tabarmi.

4182. Taɓa ka lashe ba shi maganin kwaɗai, sai an ci.

4187. Tabarmar kunya, da hauka kan naɗe ta.

Idan muka nazarci wasu daga cikin waɗannan karin maganganu da aka kawo a sami za mu fahimci kowane daga gare su yana ɗauke da wani saƙo ga al’umma, Misali, karin magana mai lamba 4030 “Sanin asali ya sa kare cin alli”, za a iya bayyana shi da wani abu ko mutum ko dabba wanda aka san asalinsa, idan ya yi wani abu wanda zai ƙara jaddadda sanin asalin abun ne ya sa shi karɓarsa ko yin amfani da shi da sauransu.

Haka kuma, karin magana mai lamba 4187 “Tabarmar kunya da hauka kan naɗe, yana bayyana lokacin da mutum ya yi wani kuskure, misali, yi da wani mutum, a lokacin da ya fahimci lokacin da yake yi da wannan mutum yana wurin ko wani ɗan’uwansa ko abokinsa yana wurin kuma ya ji abubuwan da ake faɗa, shi wanda yake yin magana a lokacin da ya gane kuskurensa sai ya hau borin ƙarya, yana sabbatu don kawar da hankalin wannan mutum ko wanda zai iya gaya masa abubuwan da aka ce game da shi.

A nazarce za a iya cewa waɗannan misalai na karin magana da ka ɗauko daga cikin wannan littafi sun ɗauki dukkan halayen da masana suka ba karin maganar Hausa, don kuwa dukkansu suna da ɓangarori biyu kuma sun isar da wani muhimmin saƙo ga al’umma.

4. 1. 2 Baƙar Magana

Baƙar magana maganganu ne na hikima da ake yi wa wani mutum don ɓata masa rai, kuma a wasu lokuta sukan fito a sigar karin magana ko zance.  Al’ummar Hausawa na danganta masu yin sana’ar fawa da matsayin waɗanda suka fi kowa iya baƙar magana (Ɗangambo, 2008:63). Baƙar magana tana da babban matsayi a maganganun hikima na Hausawa, don kuwa tana ɓata ran wanda aka yi wa ita. A wasu lokuta, baƙar magana kan iya haifar da hayaniya ko rikici kai har ma ta kai ga faɗa da ka iya kawo ji wa juna raunuka ko kisa. Hausawa sun ɗauka baƙar magana cin mutuncin ne mai danganta da zagi, amma Makaɗa Ibrahim Narambaɗa Tubali a cikin waƙarsa ya ce ba zagi ce ba, amma ta ɗari zagi zafi.

Gindin Waƙa:            Gogarman Tudu jikan Sanda,

                        Maza su ji tsoron ɗan Mai Hausa.

 

Jagora :           Ɗan Sarki duka ab ba kowa,

                                    Ɗan Sarki duka ab ba komi,

                                    Sannan yat tsira yawon ƙarya,

‘Y/Amshi      :           Ya san ba ya sarauta,

                                    Sai fa ya kwan nan,

                                    Gobe ya kwan nan, jibi,

                                    Dangi na mashi Allah waddai,

Jagora :           Baƙam magana ba ɓaci ta ba,

Y/Amshi       :           Amma ta ɗara ɓaci zafi (Gusau, 2003:72-73).                                                      

 A wannan littafi an kawo nau’o’in baƙar magana da yawan gaske waɗanda suka ɗauki sigar karin magana kamar haka;

413. An yi gadon ciwo bare na dukiya?

445. Ana wata ga wata, an yi wa shege ƙane.

507. A su wa kwabsar ƙwai a kicin.

508. A taka ruwa a ɗebo ruwa?

550. Ba a ɓarawo makaho.

555. Ba a ba turmi labarin taɓarya.

590. Ba a haɗa ƙwai da dutse.

2241. In so cuta ne haƙuri ma magani ne.

2261. In za ka yi aski ka lura da wanzamin, don kowane da halinsa.

2280. Ina marabarsa da makaho? An watsa wa mai ido ɗaya tasshi.

Yana da matuƙar kyau a fihimci baƙaƙen maganganun da aka kawo cikin wannan littafi su ne ƙunshe da darussa da nishaɗi ga dukkan wanda ya karanta su. Misali, idan muka karanta karin magana mai lamba 508 Ba a taka ruwa a ɗebo ruwa. Ana yin wannan baƙar magana ga wanda ya zo neman wani abu, sai ya tarar da wani wanda yana da wannan abun, maimakon ya nema wajen sa sai ya tura ya nemo masa wajen wani. A mafi yawanci an fi yin amfani da wannan baƙar magana a lokacin da saurayi ya zo wajen wata budurwa. Kafin ya ganta sai ya ga wata budurwa ya bukaci ta kira masa wadda ya zo wajen ta. Saboda rashin jin daɗi wadda aka aika na iya yi wa wannan sarauyi irin wannan baƙar magana.

Bisa nazartar misalan baƙar magana da aka tsakuro a cikin wannan littafi, an fahimci lallai ire-iren zantukan da aka yi amfani da su ka iya ɓata wa dukkan wanda aka yi wa rai, ya ɗauka an ci mutuncinsa.

 4. 1. 3 Azancin Magana

 

Azancin magana kamar karin magana, wasu maganganun hikima ne da Hausawa suke cikin guntayen zantuka. Azancin magana ya bambanta da karin magana ne, don shi ba ya da ɓangarori biyu, wato ɓangare ɗaya ne kawai. Ba a gajiya ba, don kuwa an kawo azancin magana masu yawa a cikin wannan littafi kamar haka;

193. Ai gaba ta fi baya yawa.

196. Aiki ba ya son wasa.

201. Aiki ya kwana.

324. Allah raba ɓarawo da yari.

344. Allah ya fidda A’i ga rogo.

396. Angulu da kan zabo.

601. Ba a jarumi raggo.

606. Ba a ƙarya kusa da gida.

636. Ba a rasa nono ruga.

784. Baƙo bai wuce tsakiyar gida.

926. Biyu gafiyar Ɓaidu

1537. Fitila maganin duhu.

1693. Gudu rawar kare.

 

Idan muka nazarci wasu daga cikin waɗannan maganganu na azanci za a fahimci suna isar da irin hikimar da take ƙunshe cikin harshen Hausa. Misali, azancin magana na 344 “Allah Ya fidda A’i ga rago”, na nufin a cikin kasuwanci akwai faɗuwa da riba. Lokacin da ɗan kasuwa ya sawo kayan sayarwa idan waɗanda suka ga abin da ya sawo da kuma yawan kuɗin da ya sawo abin suka fahimci akwai matsala, suna amfani da wannan azancin magana don bayyana wa wanda ya sawo kayan akwai yiwuwar ya faɗi, sai idan Allah Ya taimake shi ne zai mayar da kuɗin da ya sawo kayan.

Kazalika, wannan littafi yana ɗauke da maganganun azanci masu yawa kamar yadda aka kawo misalansu a sama, don kuwa sun fito da wasu zantuka na hikima kuma a cikin jimla ɗaya, waɗanda sai an natsu kafin a fahimci saƙon da suke ɗauke da shi.

4. 1. 4 Habaici

 

Habaici wata magana ce mai ɓoyayyar manufa. Ana yin ta ne ga wani don mayar da martani ga wanda ya yi wa wani mutum wani abu. Wanda aka yi wa zai jefo wata magana a cikin mutane yadda wanda aka yi domin shi zai fahimce saƙon da aka isar. Dukkan wanda bai san abin da ya faru ba, da yawa ya fahimci irin wannan magana (Ɗangambo, 2008:72). Wannan dalili ne ya sa Hausawa suke yi wa habaici kirari da “mai kashe auren sakarai”. A cikin wannan littafi an kawo zantukan habaici masu yawan gaske kamar haka;

147. A ci na ƙurya a ci na bakin gado.

1187. Ɗan Adam butulu

1195. Ɗan da ya hana uwar sa barci shi ma ko na ya yi ba.

1445. Duk irin ikon sarki bai shafi kadangare ba.

2132. Indararo ba ka ba gida sai daji.

2991. Kunkuru bai yi wa bushiya ba’ar ƙafa.

3454. Marar Gaskiya ko cikin ruwa ya yi jiɓi.

4359. Ungulu ba ta ƙaunar batta.

4413. Wanda bai san yaro ba shi yaro kan rena.

4713. Zubda yawu bai hana tusa wari.

 

Misalan waɗannan habaice-habaice da aka kawo suna ƙunshe da saƙonnin ga al’ummar Hausawa. Idan muka nazarci habaici mai lamba 147 “A ci na ƙurya a ci na bakin gado, na bayyana wani hali ko yanayi tsakanin al’umma ‘yan uwa ko abokai ko waɗanda suke wuri ɗaya. Idan daga cikinsu wani ya ware shi kaɗai, shi yake yin kome, shi kaɗai ake nema wajen yin wani abu, kuma shi kaɗai ake ba wani abu duk da kasancewar ba shi kaɗai ba ne. Don jin zafin abin da ake masu, suna iya amfani da wannan habaici don bayyana masa abubuwan da suke cikin zukatansu.

A wannan littafi dai ba a gajiya ba, don kuwa tarin zantukan habaici da aka kawo suna ɗauke da wasu saƙonni waɗanda duk wanda aka yi wa su, ya san akwai wani abu ɓoye da ya yi ake son bayyana masa don nuna masa an san abin da ya yi, ko ya ce.

5. 0 Ƙunshiyar Wannan Littafi

 

Marubucin wannan littafi ya fito da maganganun hikima na Hausawa masu ɗimbin yawa waɗanda suka tabbatar da littafin ya cancanci wannan suna da aka ba shi Magana Iyawa ce. Wannan kuwa ya samu ne sakamakon ire-iren maganganun hikima na Hausa waɗanda suka haɗa da karin magana da habaici da baƙar magana da azancin magana da sauran dangoginsu sun fito a cikin wannan littafi.

6. 0 Kammalawa

 Idan aka bibiyi tarihin mawallafin wannan littafi za a ga cewa, dukkan karatun da ya yi babu inda aka bayyana ya karanta Hausa. Ta la’akari da ƙoƙarin da ya yi na fito da wani babban sashe na nazarin Hausa, wato maganganun hikima na Hausa, za a iya cewa ya cancanci babban yabo, kuma mai babbar daraja. Wannan littafi Magana Iyawa ce, ya fito da maganganun hikima na Hausa masu yawan gaske waɗanda za su taimaka wa al’ummar Hausawa taskace su don amfanin gobe ga su kansu Hausawa da ɗalibai da manazarta da masana don samun abin nishaɗi da nazari.

Dole ne a yi wa Ali Kano uzuri idan aka ga wasu kurakurai a wannan littafi, don kuwa kamar yadda na bayyana a sama, kuma tarihin rayuwarsa ya nuna, Ali Kano bai karanta Hausa a matsayin darasi a sakandare ko gaba da sakandare ba, amma duk da haka, saboda sha’awa ya yi wannan gagarumin aiki. Hasali ma, shi malamin kula da lafiya, ko a ce, malamin asibiti ne. Hakika! Ya cancanci yabo.

Dangane da haka, ina ba da shawara idan za a sake buga wannan littafi, a sake tsara shi zuwa babi-babi don fito da rukunonin maganganun hikimar da suke cikin littafin waɗanda suka ƙunshi karin magana da baƙar magana da azancin magana da habaici da hannun-ka-mai-sanda da shaguɓe da gugar-zana da sauran makamantansu. Yana kuma da matuƙar muhimmanci a duba ƙa’idojin rubutu da dokokin nahawu da na adabi da shekarar da aka wallafa littafin. Yin haka zai ƙara wa littafin inganci da sauƙin nazari. Haka kuma, littafin zai ƙara samun karɓuwa ga ɗalibai da manazarta da masana da hukumomin shirya jarrabawa irin su WAEC da NECO da makamantansu.

Ina kuma amfani da wannan dama, don yin kira ga matasan marubutanmu waɗanda suke ƙoƙarin rubuce-rubuce da su ɗauki irin hikima da fasahar shahararren marubucin ƙasar Hausa, Marigayi Alhaji Abubakar Imam, OBE, CON, lokacin da ya rubuta Littattafan Magana Jari ce, ta ɗaya zuwa ta uku, inda ya riƙa amfani da karin magana ko azancin magana ko habaici a matsayin kan labari. A cikin labarin zai fayyace ma’anar wannan maganar hikima da ya yi amfani da ita a matsayin kan labari. A rayuwar da muke ciki a yau, akwai abubuwa na zahari da dama da suke faruwa ko suka faru, ko kuma a ƙirƙiri wani labari wanda za a iya amfani da maganganun hikima na Hausawa ire-iren waɗanda Ali Kano ya kawo a wannan littafi, a matsayin kan labari wajen isar da saƙon da al’umma za ta ilmanta ko ta nishaɗanta ko kuwa abin ya zama darasi ga dukkan wanda ya yi shi yadda al’umma za ta amfana.

Daga ƙarshe, ina taya Mande Muhammad Kurfi, RN, CNO (Ali Kano) murna bisa ga wani namijin ƙoƙari da ya yi na wallafa wannan littafi Magana Iyawa ce. Duk da kasancewar wannan littafi ba shi ne littafinsa na farko ba, muna roƙon Allah Ya ƙara ba shi fasaha da juriya da jajircewa wajen ƙara rubuta wasu littattafai waɗanda suka shafi rayuwar Hausawa. Lallai! Hausawa sun faɗi gaskiya da suka ce, “Himma ba ta ga raggo”. Allah Ya sa albarka.

Manazarta

Ɗangambo, A. (1990) “Gadon Feɗe Adabin Hausa (Ba a Buga ba).

Ɗangambo, A. (2008) Rabe-Raben Adabin Hausa (Sabon Tsari) Amana Publishers Limited. Zaria: New Kano Road, Kaduna State.

Ɗanhausa, A. M. (2012) Hausa Mai Dubun Hikima, Kano-Nigeria: Century Research and Publishing Company.

Gusau, S. M. (2003) Jagoran Nazarin Waƙar Baka, Kano. Benchmark Publishers Limited.

Junaidu, I. da Yar’aduwa, T. M. (2007) Harshe da Adabin Hausa a Sauƙaƙe don Manyan Makarantun Sakandare, Ibadan: Spectrum Books Limited.

Kurfi, M. M. (Ba ranar Bugu) Magana Iyawa ce, Katsina: Kanki Classical Media Ɓentures.

Madauci da Wasu (2009) Hausa Customs, (Zaman Hausawa da Tadodinsu) Zaria: Northern Nigerian Publishing Company.

Skinner, N. (1980) An Anthology of Hausa Literature in Translation.  Zaria: NNPC.

Yahaya, I. Y. (1981) “Adabin Gargajiya a Makarantun Sakandare. Lacca da ya gabatar a Makarantar ‘Yammata ta Dala.

Yahaya, I. Y. (2015) Labarun Gargajiya 1, Ibadan: University Press.

Umar, M. B. (1984) Dangantakar Adabin Baka da Al’adun Gargajiya na Hausa. Kano: Triumph Publishing Company.

www.amsoshi.com

 

Post a Comment

0 Comments