Ticker

6/recent/ticker-posts

Ba Ta Son Wata Mu’amala Ta Hada Ta Da Namiji Ko Ta Soyayya Ce

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum. Malam, don Allaah wai menene illar macen da ba ta da abokan mu’amala sai mata kawai. Ba ta son wata mu’amala ta haɗa ta da namiji ko ta soyayya ce?

Ba Ta Son Wata Mu’amala Ta Haɗa Ta Da Namiji Ko Ta Soyayya Ce

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh

A asali da ma ai abin da ya kamaci mace ke nan ta zama mai mayar da harkokinta da mu’amalarta da ’yan uwanta mata kawai. Ta yi magana da wasa da raha da cin abinci da ciniki da sauran harkoki dai da su. Wannan daidai ne, ban san wata magana da ta ƙyamatar da hakan ba.

Allaahumma! Sai dai ko in abokan hulɗa ko harkar ba matan kirki ba ne, ko kuma idan suna da shirin ƙulla waɗansu ayyukan assha ne da ba su dace da koyarwar Addini ba.

وَتَعَاوَنُوا۟ عَلَى ٱلۡبِرِّ وَٱلتَّقۡوَىٰۖ وَلَا تَعَاوَنُوا۟ عَلَى ٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡعُدۡوَ ٰ⁠نِۚ وَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَۖ إِنَّ ٱللَّهَ شَدِیدُ ٱلۡعِقَابِ

Kuma ku taimaki juna a kan alheri da taqawa, kuma kar ku taimaki juna a kan zunubi da ƙetare haddi, kuma ku ji tsoron Allaah. Haƙiƙa Allaah mai tsananin uƙuba ne. (Surah Al-Maaidah: 2)

Amma idan abin ya koma ga harkar soyayyar aure ce, to ai abu ne sananne cewa: Ita mace ba ta aure sai da namiji. Ko da kuma an ga cewa ba ta son mu’amala ta haɗa ta da wani namiji, haka nan dai za a janyo hankalinta har ta fahimci cewa: Abin da Allaah ya tsara kenan watau: Mace ta yi aure da namiji, kamar yadda Surah An-Nisaa’i: 23 ta bayyana

حُرِّمَتْ عَلَيْكُمْ أُمَّهَاتُكُمْ وَبَنَاتُكُمْ وَأَخَوَاتُكُمْ وَعَمَّاتُكُمْ وَخَالَاتُكُمْ وَبَنَاتُ الْأَخِ وَبَنَاتُ الْأُخْتِ وَأُمَّهَاتُكُمُ اللَّاتِي أَرْضَعْنَكُمْ وَأَخَوَاتُكُمْ مِنَ الرَّضَاعَةِ وَأُمَّهَاتُ نِسَائِكُمْ وَرَبَائِبُكُمُ اللَّاتِي فِي حُجُورِكُمْ مِنْ نِسَائِكُمُ اللَّاتِي دَخَلْتُمْ بِهِنَّ فَإِنْ لَمْ تَكُونُوا دَخَلْتُمْ بِهِنَّ فَلَا جُنَاحَ عَلَيْكُمْ وَحَلَائِلُ أَبْنَائِكُمُ الَّذِينَ مِنْ أَصْلَابِكُمْ وَأَنْ تَجْمَعُوا بَيْنَ الْأُخْتَيْنِ إِلَّا مَا قَدْ سَلَفَ ۗ إِنَّ اللَّهَ كَانَ غَفُورًا رَحِيمًا ٣٢۝

An haramta muku uwãyenku, da ´yã´yanku, da ´yan´uwanku mãtã, da goggonninku, da innoninku, da ´yã´yan ɗan´uwa, da ´ya´yan ´yar´uwa, da uwãyenku waɗanan da suka shãyar da ku mãma, da ´yan´uwanku mãtã na shan mãma, da uwãyen mãtanku, da agõlolinku waɗanda suke cikin ɗãkunanku daga mãtanku, waɗanda kuka yi duhũli da su, kuma idan ba ku yi duhũli da sũ ba, to, bãbu laifi a kanku, da mãtan ´yã´yanku waɗanda, suke daga tsatsonku, kuma kada ku haɗa tsakanin ´yan´uwa biyu mãtã, fãce abin da ya shige. Lalle ne, Allah Yã kasance Mai gãfara ne Mai jin ƙai. (sūratun Nisá'i : 23)

Mu’amalar da take kai wa ga saduwa a tsakanin mace da mace (maɗigo) kuwa babbar haram ce, kamar yadda na tsakanin namiji da namiji (luwaɗi) take zama haram ita ma.

Don haka wajibi ne a yi nesa da duk abin da zai kai musulmi ga faɗawa a cikin wannan alfashar. Kamar dai yadda ake haramta mu’amalar da ke kai wa ga hakan a tsakanin mace da namiji kafin aure, haka kuma ake haramtawa a bayan aure a tsakanin waɗanda babu ƙullin aure na Sunnah a tsakaninsu. Allaah ya kiyaye.

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

ƘARIN BAYANI

TAMBAYA: Assalamu Alaikum. Malam, mene ne hukuncin mace da take kyamar mu’amala da maza kwata-kwata, har ta kai ga cewa dukkan abokan hira da hulɗarta mata ne kawai? Shin akwai wata illa ta fuskar shari’a idan mace ta ƙi amincewa da kowace irin alaƙa da maza, har ma da batun soyayya da nufin aure, sakamakon wannan zaɓi nata?

AMSA: Wa'alaikumus Salam wa Rahmatullahi wa Barakatuh.

A asasin koyarwar Musulunci, mutuncin mace yana cikin kiyaye kanta da kuma taƙaita mu’amalarta da maza waɗanda ba muharramanta ba. Kasancewar mace tana jin daɗin zama da sauran ’yan uwanta mata don yin hira, kasuwanci, ko neman ilimi, wannan abu ne abin yabo muddin ana yin hakan ne a cikin iyakokin alheri. Shari’a ba ta tursasa wa mace lallai sai tana da abokan mu’amala maza ba a rayuwar yau da kullum. To sai dai kuma, wannan keɓancewar tana iya zama illa idan har ta kai ga mace tana ƙin abin da Allah ya halatta mata na aure, ko kuma idan zaman nata da mata ya zama silar ƙulla wasu ayyuka na saɓon Allah. Allah Maɗaukakin Sarki ya yi kira ga muminai da su taimaki juna kawai a kan ayyukan kwarai:

وَتَعَاوَنُوا۟ عَلَى ٱلۡبِرِّ وَٱلتَّقۡوَىٰۖ وَلَا تَعَاوَنُوا۟ عَلَى ٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡعُدۡوَ ٰنِۚ وَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَۖ إِنَّ ٱللَّهَ شَدِیدُ ٱلۡعِقَابِ

Kuma ku taimaki juna a kan alheri da taƙawa, kuma kada ku taimaki juna a kan zunubi da ƙetare haddi. Kuma ku ji tsoron Allah, lalle Allah Mai tsananin uƙuba ne.” (Suratul Ma'idah: 2)

Idan kuma wannan yanayi na kyamar maza ya shafi batun aure, to hakan ya saɓa wa dabi’ar da Allah ya halacci mutane a kai. Aure tsakanin mace da namiji wani tsari ne na Ubangiji wanda yake tabbatar da dorewar zuria da kuma kiyaye mutuncin ɗan Adam. Manzon Allah (SAW) ya ƙarfafa matasa maza da mata a kan yin aure domin shi ne mafi kiyaye gani da farji. Rashin son mu’amala da maza har ta kai ga ƙin aure babban kuskure ne, domin Allah ya fayyace matan da suka haramta wa namiji, wanda hakan ke nuna cewa waninsu halas ne ga juna ta hanyar shari'a:

حُرِّمَتْ عَلَيْكُمْ أُمَّهَاتُكُمْ وَبَنَاتُكُمْ وَأَخَوَاتُكُمْ وَعَمَّاتُكُمْ وَخَالَاتُكُمْ وَبَنَاتُ الْأَخِ وَبَنَاتُ الْأُخْتِ وَأُمَّهَاتُكُمُ اللَّاتِي أَرْضَعْنَكُمْ وَأَخَوَاتُكُمْ مِنَ الرَّضَاعَةِ وَأُمَّهَاتُ نِسَائِكُمْ وَرَبَائِبُكُمُ اللَّاتِي فِي حُجُورِكُمْ مِنْ نِسَائِكُمُ اللَّاتِي دَخَلْتُمْ بِهِنَّ فَإِنْ لَمْ تَكُونُوا دَخَلْتُمْ بِهِنَّ فَلَا جُنَاحَ عَلَيْكُمْ وَحَلَائِلُ أَبْنَائِكُمُ الَّذِينَ مِنْ أَصْلَابِكُمْ وَأَنْ تَجْمَعُوا بَيْنَ الْأُخْتَيْنِ إِلَّا مَا قَدْ سَلَفَ ۗ إِنَّ اللَّهَ كَانَ غَفُورًا رَحِيمًا

An haramta muku uwayenku, da ’ya’yanku, da ’yan’uwanku mata, da goggonninku, da innoninku, da ’ya’yan ɗan’uwa, da ’ya’yan ’yar’uwa, da uwayenku waɗanda suka shayar da ku, da ’yan’uwanku mata na shan mama, da uwayen matanku, da agololinku waɗanda suke cikin ɗakunanku daga matanku waɗanda kuka yi duhuli da su... Lalle Allah Ya kasance Mai gafara, Mai jin ƙai.” (Suratun Nisa’i: 23)

Bugu da ƙari, akwai babban haɗari idan mace ta takaita mu’amalarta ga mata kawai har hakan ya kaita ga kyamar maza, domin hakan na iya zama ƙofar sheɗan wajen jefa ta cikin alfasha irin ta maɗigo (lesbianism). Wannan aiki ne na la’ana wanda ya yi kama da luwaɗi, kuma dukkaninsu manyan zunubai ne da Musulunci ya yi Allah wadai da su. Manzon Allah (SAW) ya tsine wa mata masu kwaikwayon maza da maza masu kwaikwayon mata. Saboda haka, mace ya kamata ta tafi a kan tafarki madaidaici: ta kiyaye mutuncinta ta hanyar kauce wa mu’amala da maza maras amfani, amma kuma kada ta ƙi abin da Allah ya shar’anta mata na soyayya da zaman takewar aure da namiji.

Wallahu A'alam.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments