Ticker

6/recent/ticker-posts

Ƙanwata Na Ikilima Adam (Kashi na 6)

Da sunan Allah mai Rahma mai jin kai. Allah kasa yanda na fara lafiya in kare shi lafiya. Wannan labarin ya faru da gaske dan kusan Book dina da nake yi true life ne sai dai in yi masa kwaskwarima dan abun ya fi ba da citta.

Ku biyo ni ku sha labari.

Ku daure ku yi comment dan in ji ra'ayoyin ku a kan Littafin nan......

*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*

_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishaɗantarwa tare da faɗakarwa da jama'a bisa harshen hausa}_

https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo

⚜️©J.A.W📚🖌️

Marubuciyar

* Amince Da Ni
* KAI KA JA WA KANKA

Yanzu kuma gani ɗauke da

ƘANWATA

Paid Book ne

Vip 300
Special 500

Acct No. 3115484026, First Bank, ko kuma Kati MTN (Ba na son VTU)

Idan kin biya ta bank kina iya turo shaidar biyar ki ta wannan 09069080725

kanwata

🌟🌟 ƘANWATA Na Ikilima Adam [Kashi na 6]🌟🌟

Ta ku har kullum kyauta Daga Allah8️6️

Ta ce hoto kuma ban gane ba '' Marwan din ya dauke mu hoto nida kai ''

Eh shi ne ya ɗauke mu'' matso kiga hoton' gallery Din wayar sa ya shiga ya maida hankalin sa gun nemar hoton...

Murmushi ya yi ya ce uhmm zo ki ga' 'matso da ita ya yi kusa da shi tare da nuna mata hoton...

Cikin gigita take kallon hoto cike da zallan mamaki ta ce Marwan din ne ya ɗauki hoton tana kallon hoton bakin ta abude...

Eh Marwan ya ɗauka ya turawa Salma' itakuma Salma ta nunawa Adamu ranar daurin auren naku shikuma ya janye...

Wataran Salma ta kira Marwan saina na dauki wayar agaban sa' 'na Daga inajin muryan mace nace masa kenan kafara bin mata....

Wannan dalilin ya sa nabi diddigin sa nadau wayar tasa naga hoton daya tura mata saida nashiga shock cikin tsananin tashin hankali nasan wannan hoton' 'yana da Burin ya yada shi duniya tagani kinga za a halin mu daya da ubana...

Goge duk wasu hotuna nayi a wayar tasa dan kada ya yi zargin Ko angano shi ne...

Innaliahi Rahama ta shiga maimaitawa ta ce Salma nashiga uku ƙanwata' cikin kuka ta ce Amjad ban san menayi wa Salma ba take tsanata ba '' na dauka kuruciya ce 'Wallahi innaga yaya da kanwa suna kusanci' 'sossai kuma suna kaunar junan su 'burgeni suke.....

Hannayen sa ya sa ya fara goge mata hawayen nata ya ce Hubby kiyi hakuri fa..

Azuciyar sa sai fadi yake dan ma bakisan abun da Salma take shirin aikatawa bane''' uhmm InshAllah zan kareki mata ta cikin maganar zuci yake Rahamaa ta zuba masa idanu ta ce yadai Amjad tunanin me kake..

Murmushi ya sakar mata hade da lakacar hancin ta '' uhmm Hubby kin san in inajin dumin jikin ki..

Kashe min jiki kike...

Zazzare idanu Rahama tasoma tana neman hanyar guduwa cikin kukan shagwaba ta ce Amjad dîna....

Ni ɗai ka kyaleni ba abun da zan iya maka...

Tashi ta yi tana kokarin zillewa hade da masa gwalo '' sossai ya ɗara ya ce uhmm Allah yakaimu ai daren yau namu ne..

Tabe baki ta yi ta ce uhmm ka ga bankira Asiya ba tun da ta tafi ba...

Kuma yakamata ki kirata ita da mamar ki '' anty kike kiran ta...

Eh Anty nake kiran ta my Amjad ''...

Kusan Azahar Samad yana makale da Rahama a dakin Da ƙyar yabar ta '' ta shiga kitchen da kan ta dan daura musu girki....

Isowar Karima ne ya sa Samad barin Sashin yafita dan gudanar da wasu Ayyukan sa...

Yana Fita ya tura wa Yusuf Sani Yaro sako a kan whsap dinsa...

Ya tura masa da :

Salam Alhaji yusuf dafatan kana Lafiya..

Kwana biyu ba ka nemana ya kake yame dakin naka Sumayya...

Cikin Sa'a kuwa yau yana online dan sai ya yi sati behau online ba '' amma datar sa tana kunne da zakayi masa '' whsap call ze shiga amma baza a Daga ba.....

Ganin Sakon Yarima Samad ya sa shi kai tsaye shiga cikin sakon ya san duk yanda akayi Ko zumunci za su yi Ko kuma aiki ne yazo dashi...

Hakan ya sa ya yi maka reply tare da bashi damar su sauka Daga kan whsap '' yakira direct..

Babu Musu Samad ya sauka Daga kan whsap dîn..

Kiran sa ya yi direct Daga cen ɓangaren yana wayar amma kuma yana magana da wasu alamu cikin tarin Ayyuka yake '' kuma manyan yan majalisu ne kusa dashi....

Cikin da fada fada yake musu magana ya ce dan Allah ku fita '' waje ku dawo nan da Sati daya '' Samad dake sauraren yanda yake zuba ruwan masifa acen din ya ce ka ga namijin zaki '' wanda beson takura.....

Muryan Yusuf yadawo da shi duniyar tunanin daya shiga..

Yusuf ya ce dan uwa Dan Sarki. Jikan Sarki wai kana nufin har yanzu bakaga Sarkin Adalai ba...

Samad ya ce ban ganshi ba nasan kaine kadai za ka iya binciko mun shi..

Amma kafun nan wannan baiwar nan wacce Al'amarin ya faru da ita '' ita nake nema ance ta buya a garin kano.....

Kasaitaccen Murmushi Yusuf ya yi ya ce uhmm '' lallai ta yi karamar hauka tarasa inda zata buya sai kano..

Amerika ne kadai zata je inkyale ta..

Tura mun hoton ta '' kaban awa 48 duk inda take zakaji inma kanon Ko wajen kano...

Sossai Samad yaji dadin bayanan Yusuf hakan ya sa ya rinƙa masa adu'oi a karshe ya ce shi ne baka zo biki na ba..

Yusuf ya ce A'h Ah kabari ta haihu mana InshAllah da Mata ta zan zo.

Sossai Samad ya ɗara ya ce to Allah yabata cikin da Ameen suka Amsa tare........

''

Rahama tsaf ta shirya cikin shigar ta ta Alfarma tare da sanya Alkyabba da Karima ta daura mata '' Kallon Karima ta yi ta ce duba kigani shigar nan tamin kyau kuwa...

Karima ta ce sossai ma kinyi kyau shugaba ta' '' sai m'a shugana ya ganki ze kara ruɗewa '' 'murmushi ta yi saida kuncin ta ya lotsa ta ce anjima da dadare zakiban labarin da kika sani wanda ban saniba Karima cike da ladabi ta ce ya shugaba ta' ɗuk yanda kikace haka za ayi...

Muje ki rakani sashin Fulani yau cen zan fara lekawa cewar Rahama....

Babu Musu suka baro sashin nasu khadija kadai aka bari dan ba ta nemi izinin Samad ba' 'babu halin fita harsai yadawo dan doka ya sa mata......

Koda suka fito Farfajiyar Masarautar bayi suna ta shinmfidewa kasa dan gaishe da Rahama..

Cike da ladabi suka fara fadin barkda da fitowa Gimbiya Rahama..

Bakin ta dauke da murmushi take Daga musu hannu ba tare da ta yi magana ba..

Tafiya take tamkar hawainiya duk takun ta daya sai Bayi sun Dago kai suna kallon ta '' cikin zallan mamaki dan ba a taba yin Gimbiya wacce ta iya tafiyar Matar sarakai Ko yarima ba irin ta...

Daidai Mashigar sashin Fulani ta hadu da jakadiya tana horar da bayi da ba sa Jin magana...

Ganin Rahama ya sa ta fadada murmushin ta '' tafara mata kirari......

Ita Ko Rahama murmushi ta yi tare da da mata gaisuwar hannu ba tare da ta tsaya ba....

Kai tsaye suka wuce dakin Fulani ita da Karima....

Bakin su dauke da Sallama

Bayi masu mata hidima suka gani..

Cike da girmamawa suke gaida Rahama..

Cikin sanyin murya Rahama ta kalli bayin dake dakin ta ce uhmm ina Mama Fulani take ne..

Baiwar dake goge goge ta ce ta shiga wanka..

Karima kallon Rahama ta yi ta ce shugaba ta mu je dakin nata mu jira ta Ko..

Rahama murmushi ta yi ta ce to mu je kai tsaye Dakin Fulani suka nufa cikin azzama..

Suna shiga dakin ganin ba ta fito ba ya sa suka fara dube dube a dakin...

Idanu Rahama ta yi ma Karima ganin haka ya sa Karima sanda sanda take wajen kofar bandakin da Fulani ke wanka '' Daga wajen tasawa kofar sakata ta tabbatar yarufe...

Murmushi Rahama ta yi cike da izza tafara nuna wa Karima inda zata hau saman sif din..

Karima cikin azzama tahau tafara dube dube tana sauko da kayan dake kai...

Saida tagama sauko da dukan kayan har tana Zufa cikin maganar kurmanci ta yi mata alamu da hannu ba ta ga komai ba...

..

Rahama alamu ta yi mata data kara bincikawa hakan ya sa tabada azzama wajen bincike '' cikin sa'a kuwa sai gashi taga layoyi guda uku ajere....

Jin karar buga kofar bandakin ya tabbatar musu fulani ta gama wanka so take ta fito ta ji kofar arufe gam..

Zazzare idanu suka yi Rahamaa ta yi mata alamu data miko mata layoyin dukan su '' sunkai talatin '' tana mika mata cikin jakar ta '' tasaka su..

Kayayyakin da suka sauke kasa tafara mikawa Karima '' tana maida su inda suka dauko su..

Jin Fulani ta tsananta da buga kofar bandakin ya sa..

Karima tasauko a hankali...

Gadon da ta taka tahau sama nan da nan tahau gyara shi tsaf yanda ka san basuyi komai ba....

Komawa kujerar dakin Rahama ta yi ta zauna..

Hakan ya sa Karima taje a hankali tabude kofar...

Da karfin tsiya Fulani da bankado kofar tana ta huci sama sama...

Rahama cikin azzama takaraso wajen Fulani ta ce Mama yanzu muka shigo dakin naki '' sai mu ka ga kina ta buga kofar '..

Cikin tsananin bacin Rai ta ce kulle ni akayi ta waje...

Rahama ta ce anya ba Jan blok bane ya shiga ba..

Ke Karima je ki duba kigani..

Karima cikin azzama taduba cike da dalabi ta ce ya shugaba ta' 'maganar ki gaskiya ce Jan blok kofar tashiga

Ajiyar zuciya Fulani tasauke ta ce haba ni nayi mamaki ashe Jan blok ya shiga Abban Marwan ne' ɗaya shiga dazun ya sa shi a kan Jan blok

Maida kallon ta ta yi a kan Rahama ganin ta yi wani mugun haske fatar ta takara yin kyau sossai..

Tabe baki ta yi cike da Fargaba ta ce Amarya mu yau kece har dakina lallai yau kin dauke ni amatsayin uwa...

Murmushi Rahama ta yi ta ce mama Fulani '' yarima ya ce indai ina son insamu Albarka dole inbiku...

Darawa ta yi acikin zuciyar ta'tana bin Karima da kallon banza..

Ganin haka Karima tafara sanda kanta akasa...

Uhmm damar nace Karima tarakoni in gaishe ki akace kina daki nace bara in zo ban san wanka kike ba zan tafi cikin gida....

Fulani dake kallon Rahama cikin tsoron kada abun da take tunani ya tabbata inhar dagaske Rahama ciki ne da ita Asirin nasu ze Tonu..

Mudin Sarki yaji labari zance yakare '' zefara kokarin maida Mulkin hannun Samad...

Sossai hankalin ta ya tashi cikin dauriya ta ce yata har zaku tafi gashi baku ci abinci ba...

Rahama ta ce A'a nagode na koshi Daga haka suka bar dakin ita da Karima...

Kai tsaye dakin Karima suka je tare da Rahma..

Layoyin suka warware akasa....

Cike da mamaki ta kirga su taga wai har guda talatin ne...

Kowani laya saida suka warware su daya bayan daya...

Wasu layun harda Allurai acikin su...

Wani layan takarda ce mai dauke da sunan Salihu farraku shida Turaki...

Sossai Rahama ta Girgiza ganin Yarima Samad '' kada ya haihu...

Batagama mamaki ba '' taga wanda aka rubuta..

Babu Salihu babu gidan masarauta har abada...

Sake da baki suke kallon juna Rahama da Karima.......

Rahama da mamaki take kallon Karima tare da mikewa tsaye zumbur kamar wata soja...

Ta ce Karima kin san gidan Maman Maryam..

Karima ta ce kwarai nasani shugaba na yana aikata awannan gidan..

Miko min wayata Daga cikin jakata...

Cikin hanzari ta mika mata...

Dannawa Samad kira ta yi Shiko yana tuki zeje Filin airport din Samad air plan....

Ganin kiran Rahama ya sa babu ba ta lokaci ya ɗaga...

Cikin begen abun kaunar sa ya ce Amarya bakya laifi koda kin kashe Fulani da Marwan

Sossai ta dara ta ce ban kashe bane 'shi ya sa...

Cikin cool voice din ta.

Ta ce Amjad.

Naam Rahama ta yakarashe zancen yana kokarin tusa hancin motar a airport din...

Inajinki fadi...

Uhmm dan Allah kamun izini zanje gidan Maman Maryam nida Karima ba zan dade ba...

Ziyara ce..

Nazarin kalaman ta yake yanason ya ce A'a ganin wanne karo na farko data tambyeshi zuwa unguwa ya sa shi Fadin Allah yakai ku lafiya...

Zanwa drever magana yakai ku ya kuma jira Yadawo dake...

Sossai Rahama ta ji dadin bayanan sa hakan ya sa ta rinƙa masa adua yana fadin Ameen ameen hubby...

Babu ba ta lokaci suka shirya zuwa gidan Maman Marwan..

Koda suka isa farfajiyar gidan sun iske drever su kadai yake jira su tafi...

Ganin sun fito ne harda khadija..

Babu ba ta lokaci ya bude musu kofa...

Suna shiga motar '' kai tsaye ya ja motar zuwa kan titi..

Rahama cike da murna take kallon garin '' ba ta taba shiga cikin garin kwatano ba...

Sossai yanayi na tsare tsaren nasu yaburgeta.....

Gani ta yi har sun iso Gidan wanda tafiyar basu fi minti shabiyar ba...

Koda Drever ya paka motar tasa.

Basu ba ta lokaci ba wajen fitowa ba..

Maman Maryam da Abban Maryam da maryam suna zaune afalo suna tattauna da alamu a kan Samad ake magana...

.

Sallamar Khadija ya sa suka maida kallo a kan ta....

Ganin Rahama da Karima a bayan khadija '' ya sa suka Mike dukan su...

Maryam cikin.........

Muje zuwa..

Ta ku har kullum kyauta Daga Allah8️7️

Maryam cikin mamaki ta ce wannan kamar Matar Yaya Samad...

Murmushi khadija ta yi ta ce aikuwa ita ce ashe kin gane ta..

Maman Maryam cikin Aro jarumta taje ta rungume Rahama cike da bakin cikin dake cin ta...

Ta ce yata idon ki kenan lale lale da Rahamatullah..

Kallon Maryam ta yi data zama kamar gunki a tsaye ta ce ke Maryam kallon Matar yayar naki kikeyi ne..

Murmushi Khadija ta yi ta ce mommy naga Alama..

Samun wuri suka yi suka. Zauna Karima kasa ta zauna.

Cike da ladabi Rahama ta gaishe DA MOMMY DA Maryam '' da Abban marwan dayanzu yake zama kan kujerar sa...

Mommy ihun kiran yar aikin ta tayi.

Nan da nan yar aikin tazo tana sanye cikin riga da

Wando matsassu.

Abban Maryam yana kallon yar aikin ta kasa idanun sa ya sauka a kan nonuwan da suka ciko rigar...sai hadiye yawu yake.....

Duk abun da yake Rahama tana lure dashi...

Abun sha yar aikin ta zuba musu tare da jera musu agaban su..

Mommy ta ce ku sha lemu laifin Abdul Samad ne. '' inzaku zo ya sanar mana ayi maku girki special..

Amma yanzu ba ta baci ba...

Rahama cikin cool voice din ta ta ce mommy '' Mungode ahanya muke nace muzo mu gaishe ki..

Naga lokacin lasa'ar ta gabato ina son naje 'nayi Alwala..

Mommy ta ce uhmm kije dakin Maryam saikiyi a bandakin ta..

Maryam tabe baki ta yi ta ce la mommy ai pampo na ya tsaya tun jiya sai dai khadija takaita dakin naki..

Maman Maryam ba haka taso ba' ɗan kada su gane ya sa ta fadin uhmm kuje yata akaiki dakina...

Babu ba ta lokaci suka Shiga dakin Maman Maryam' ɗuk yanda Rahama taso khadija tabar dakin abun ya garara saida taje ta yi Alwala ta fito tana kallon khadija dake latsa wayar Rahama..

Ta ce sista jekiyi Alwala Ko muyi Sallah ina jiran ki....

Babu musu khadija ta tashi ta shiga bandakin tana ganin khadija ta shiga taje ta dannawa kofar shigowa key '' cikin Rawar jiki tahau saman sif din jikin ta 'na rawa tana tsoron kada khadija ta ritsata cikin ikon Allah ba ta sha wahala ba..

Taga layun har uku...

Cikin Rawar jiki ta sauko tare da gyara wajen data taka' '.

Key da ta murzawa kofar ta cire.

Sum Sum ta dawo kan sallaya ta zauna kamar yanda khadija tabar ta..

Ita Ko khadija har da bahaya ta yi ya sa ta dade a bandaki..

Tana fitowa kai tsaye Rahama tajasu Sallah...

Suna cikin yin Sallah' maman Maryam ta shigo ita da Maryam din..

Ganin Sallah suke ya sa suka kalli juna suna tabe baki ''

Maman Maryam ta ce in kun idar ina jiran ku...

Tare da komawa Falon ita da yar ta.....

Rahama suna idarwa Ko tsayawa azkar basuyi ba suka tashi daman a ujajjan tazo dan dole...

Fitowar su Falon ya sa Karima tashi Daga zaunen tana ma Rahama kallon andace' '

Rahama gira ta Daga mata Alamun yes..

Agogon wayar ta' ta kallah taga lokaci ya ja gashi tanason takoma gida ta daurawa Amjad din ta girki...

Cikin ba da uzuri take kallon Mommy da Maryam dake hararan ta'' ta ce zamu tafi' ɗaman munzo mu. Gaishe ki ne..

Kafun muzo miki wuni...

Maman Maryam ta ce haba yata ga girki nan andaura muku yakusa dafuwa..

Rahama kasaitaccen murmushi ta yi ta ce Ayya mommy na''' zamu dawo InshAllah..

Mommy cikin Jin haushin jiran girkin da batayi ba.

Ta ce uhmm to nagode da ziyara yata.

Kallon khadija ta yi da suke magana ita da Maryam.

Ta ce khadija tashi kuje '' anty taki ta ce bazama inaga Samad zedawo yasha girki ne.....

Murmushi Rahama ta yi tare da yin kasa da kanta dan kunya.....

Har bakin mota suka raka su banda Maryam da bakin ciki yahanata fitowa tana ayyana irin hukunci da zatayi m'a Rahama..

Babu ba ta lokaci drever ya ja su Rahamaa a mota tare da nufar hanyar gidan nasu....

Ita Ko Maman Maryam '' bakin ciki ya ishe ta kasa komawa cikin gidan take tana ayyanawa aranta anya wannan yarinyar ba ciki ne da ita ba...

Kasa daurewa ta yi hakan ya sa ta yi maza tadannawa bokan jeji waya..

Bugu uku ya ɗaga Daga can ɓangaren Ya ce Farida nasan zaki kirani a daidai wannan lokacin yana tsoron gayamata '' Rahamaa ta kwashe layoyin taki biyan sa '' sauran kudaden sa..

Kuma yanajin shakkar Rahama ta warware layoyin ta wargaza musu shirin nasu..

Matar dan naki tawuce Ko yau ziyara ta musamman ta kawo miki mai cike da dumbun tarihi..

Maman Maryam ta ce ban gane me cike da dunbun tarihi ba......

Dariya ya kekyashe da shi sossai sanna ya ce zaki gane ne Farida ba abakina amma barin infada miki abun da kike son sani....

Matar Samad bin Salihu tana dauke da cikin sa....

Cikin gigita Maman Maryam ta tsala ihu ta ce garin ya haka tafaru kaida kace za ka hana ta samun ciki...

Bokan jeji hade rai ya yi kamar tana ganin shi '' ya ce ke banda shasha ce '' ke kinyi sake '' bare ni da ba haduwa muke da ita ba '' saide intura dan sako....

Yarinyar ce hatsabbiya ce ta karshe duk inda muka bi saita tare mana hanya hatta Samad '' inmuka je masa yanda kika san a jikin ta '' haka take zaburar damu '' '..

Nan da nan Zufa ya ketowa Maman Maryam cikin damuwa ta ce yanzu meye abun yi..

Abun yi shi ne kawai ku ɗau hakuri ta haife abun da ke cikin nata kinga sai ku shayar dasu guba su mutu..

Maman Maryam ta ce kana nufin cikin yan biyu gareta ne....

Boka tuntsirewa da dariya ya yi sanna ya ce '' wannan dai mu jira mugani dan ba zan fadi abun da zai sa wannan bakar Mayyar Matar Samad ba tazo ta hanani barci ba...

Daga haka suka yi sallama.

Tana jinjina Al'amarin nan kiran Fulani ta yi cikin sa'a ta Daga nan take ba ta labari...

Fulani cikin salati ta ce haba biri ya yi kama da mutum shi ya sa yarinyar nan takara haske sossai..... Ga kiba..

Shege Samad da kike gani ya iya cike mace cikin kalilan lokaci jarababbe shida uban nasa...

Maman Maryam ta ce ni dai kinji ya ce sai yaran sunzo duniya za a kashe su..

Amma kisan yanda zakiyi kada mai martaba ya san tanada ciki..

Fulani ta ce uhmm inaga Samad din ma besan da cikin ba ita ma matar batasani ba.....

Cigaba da tattauna suke a kan yanda zasuyi kawo karshen Rahama agidan...

Adaren ranar Rahama tagama warware dukan layoyin tasa su a wuta suna konewa.....

Zuciyar Mai martaba da Abban Marwan '' da Baba Salihu da Marwan dake tuki yadau bugawa gab gab gab da karfi..

Baba Salihu Samad gado yake yana barci hakan yaji gadon na juyawa da shi cikin gigita ya farka yana Salati..

Shima Mai Martaba kusan da Salati ya tashi ya zauna yana Jin wani irin yanayi tattare dashi...

Shiko Abban Marwan zaune yake yana cin Abinci '' kansa yarike da yake sara masa...

Marwan dake tuki kadan yarage beyi hatsari ba '' da taimakon wani soja ne.

Allah yakare shi koda sojan ya fito zeyi fada ganin Marwan jikin Sarki ne ya sa shi fadin Prince Marwan kayi hakuri ban san kai bane..

Marwan da Sam baya cikin hankalin sa ya ce ataimaka akaini gida...

Sojan ya ce subuhannalah Prince bakada lafiya ne....

Shiru ne yaratsa hakan ya sa babu ba ta lokaci sojan ya ja motar tare da da maida Marwan kujerar me baya..

Kai tsaye gida ya nufa dasu babu ba ta lokaci...

Sarki Turaki bakin sa na rawa yake kallon Mama karama ya ce hajiya Nasiba ina ɗana Salihu yake Saboda ance Yayiwa baiwa fyade shi ne yabar gidan nan....

Mama karama da mamaki take kallon sa '' ta ce yau kaine kake tambayar inda dan naka ya shiga bayan da bakin ka kace yana iya barin gidan dan be iya hada idanu da Talakawan sa...

Sarki Turaki zazzare idanu ya yi ya ce haba Nasiba ya zaki ce haka yaushe na fadi haka......

Kuma ya'akayi mulkin yadawo hannuna '' mikewa tsaye ya yi hakan ya sa Mama karama ta yi maza tarike hannun sa ta ce ina za ka je ne adaren nan...

Zanje wajen baiwa Saratu yabata amsa ataikaice....

Cike da tsoron yanayin sa ta ce anya ba iskokai ke damun ka ba...

Saratu shekara da shekaru ba ta gidan nan sai a yau za ka nemeta wai ma kayi mata me.....

Cikin zazzare idanu ya ce kina son kice min Saratu ba ta gidan nan bayan nace ina son ayi bincike ya'akayi tabar gidan nan cike da fada yake magana sossai kamar ita ce ta yi laifin....

Mama Karama ta ce subuhannalah Sarki me ran Karfe ni dai Kayi hakuri zuwa safiya InshAllah zanmaka bayanin komai '' ɗakyar ta lallaba shi yakwanta yana kukan zuci' 'babu abun da yake son gani sai mafi tsoyuwar dan nasa..

Abban Marwan ture kwanun abincin dake gaban sa ya yi yafadi wargas akasa da yake tangaran ne nan da nan ya farfashewa daddaya akasa...

Fulani cike da mamakin sauyin yanayin sa ta yi ta ce kai ta ce lafiya kuwa Sani mêke ɗamun ka...

Wani kallo yake bin ta da shi masu wuyan fassara ya ce Salamatu me kike yi agidan nan '' daman ke na aura...

Rau Rau da idanu Fulani ke kallon sa ta ce kam buhu yauga rainin wayo ya za ka ce me nake yi agidan nan..

Bayan ina matar ka '' har da haihuwa tsakanin mu...

Abban Marwan ya ce nasan inada da Marwan '' kina nufin kece uwar tasa...

Fulani cikin gigita take kallon mijin nata '' ta ce Nice uwar sa kaine uban sa ya da wannan tambayar...

A'a Salamatu wallahi ban san na aureki ba''ni rayuwar dani dake kamar a mafarki yanzu abun yake dawo mun....

. Kinko San irin tsanar danayi miki kuwa....

Kokarin Fita yake ta kamo hannun sa' 'cikin kukan dayazo mata' ta ce ina za ka je ne...

.

Zanje wajen Yayana mana inmasa bayanin yanda akayi kika zama mata ta....

Shan Gaban sa ta yi cikin zafin nama bakin ta na rawa ta ce yaya Salihu baya gidan nan shekara da shekaru kai a yau ka san benan...

Cikin gigita yake kallon ta da Idanun sa da suka kawo ruwa nan da nan ya ce ban gane yaya Salihu baya nan ba....

Hankade ta ya yi ta fadi kasa tare da bude kofar.....

Yana fitowa cikin zafin nama zashi sashin mai martaba ya yi daidai da anshigo da Marwan a ujajan kamar matacce...

Cikin tsananin tashin hankali ya nufi inda sojan yake tare da bâyi da suka taimaka masa wajen ciccibar Marwan....

Bakin Sa na rawa ya ce meya Samu ɗana ne...

Sojan ya shiga bashi labarin abun da ya faru..

Sossai Abban Marwan yarufe tare da tallafa Marwan din suka yi sashin Mamy dashi...

Mamy zaune take ita da Ahmad suna hira '' turo kofar da akayi shi ne ya sa hankalin ta yadawo a kan kofar.

Ganin Marwan a ujajan ake kokarin shigo dasu '' cike da fargaba suka taso ita da Ahmad...

Bakin ta na rawa take kallon Sani Abban Marwan ta ce lafiya meya samun dan namu...

Abban Marwan cikin gigita yake ba ta labarin sojan daya kawo shi.

Babu ba ta lokaci suka daura shi a kan kujerar falon ''..

Ganin haka Mamy ta ce kai Ahmad maza kaje ka kira Samad shida Matar sa..

Abban Marwan da rabon shi daya shigo Sashin mamy tun Salihu yana gidan '' cikin dauriya ya ce Mamy dan Allah kiramun yaya Salihu mana..

Naga kamar Samad ba zai fito dawuri ba..

Rau Rau da idanu Mamy take kallon Abban Marwan ta maimaita Salihu cike da Mamaki ta ce uhmm kaiko Sani yaushe rabon duniya da ayiriri yayan naka da kuka kore shi...

Murya Samad ta ji Daga Sama yana karasowa falon ya ce A'a ba shi ne yakore shi ba...

Asali ma besan an yi ba...

Rahama cikin yarda da zancen mijin nata..

Ta ce Mamy kwarai kuwa Abban Marwan besan da komai ba..

Barin zancen suka yi tare da dukufa a kan Marwan.

Babu ba ta lokaci Rahama ta soma yi masa ruƙya inda Yasoma gurnani Daga karshe ya rinƙa maida numfashi ganin haka Rahama ta ce Alhmdulilah ze iya farkawa normal InshAllah....

Komawa ta yi tazauna tana adu'oi carbi na hannun ta...

Mamaki da mamaki take kallon yanda Rahama ta saita Marwan har ya bude Idanun sa..

Abban marwan ya ce Habiba yanzu kuna nufin yaya na be gidan nan wallahi da sake wai anbawa me kaza kai.

Samad kallon sa yake ya ce duk wannan abun daya faru Matar ka Fulani ce sila...

Abban Marwan ya ce wallahi ban san yanda akayi na auri Fulani ba...

Mamy cike da tausayawa ta ce Rabo ne ya kuka tsakanin ku bakada zabi dole sai hakan ta faru....

Marwan firgit ya tashi Daga kwance yazauna yana kallon yan cikin dakin wani sabuwar soyayyar Samad yaji yana ratsashi ta Ko ina sassa na jikin sa...

Aguje ya tashi ya je ya rungume Samad yana tuna baya '' lokacin daya ta aikata masa laifuka '' cike da rashin sanin meyasa ya muzgunawa yayan nashi ya ce..

Yaya Samad dan Allah kayafemun laifukan ɗana aikata maka abaya..

Shiii Yarima ya yi da yatsar abaki ya ce kada kace komai kanina bakayi mun laifin komai ba '' Ada na daukeka mara gaskiya yanzu kuma na dauke ka me gaskiya.

Kara Rungumar Marwan din ya yi ya ce Marwan nayi mamaki yanda Mamy ta zama uwar dakin ka lokaci daya ka canza '' nayi mamaki yanda nake kula da kai komai naka lokaci daya kazama mugu ashe bayin kanka bane..

Sharrin Fulani ne.....

Marwan cikin gigita yake kallon Abban sa ya ce Abba ka cuce ni ya akayi ka zaba min uwa kamar Fulani...

Abban nasa rintse Idanun sa ya yi ya ce haba Marwan nikaina ban san yanda akayi na aure ta '' da ba mu kama nida kai tabbas zancen kai ba ɗana bane...

Yarima Ahmad dake kallon abun da ke faruwa tabe baki ya yi ya ce nifa bantajin kaunar Fulani ba Mamy...

Samad kallon Abban Marwan ya yi ya fara bashi labarin gwagwarmayan da Rahama tasha..

Dakuma zancen layoyin data kona harda garin layoyin dasuka yi toka ya bude nan ya nuna musu..

Gabadaya wajen aka dauki Salati..

Mamy cikin tashin hankali ta ce meya kawo Anty Farida cikin wannan lamarin oh Allah yaya ta mekike so ne '' meye ban miki ba'''

Kin kasa ganewa ba laifina bane dan Salihu ya zabeni amatsayin matar daze aura ba laifina bane dan Samad be aure Maryam ba...

Kuka take sossai har Idanun ta sun kada ta ce wannan labarin saina gayawa mahaifin mu..

Kuma zan sanarwa Yayyena na da autar mu '' su sani Farida gurbatacciyar jini ce acikin mu...

Kuka take sossai hakan ya sa Rahama zuwa soma rarrashin ta cikin kalamai masu taushi ta ce Mamy karki fushi kibar ta ta girbi abun da ta shuka...

Mamy ta ce wallahi tallahi tun da nake da Farida ban taɓa yin abun da ze cutar da ita ba..

Meyesa ita ba ta kaunar cigaba na...ɗana zuri'a ta...

Gabadaya dakin shiru suka yi Ko wanne da abun da yake sakawa aransa....

Abban Marwan cikin Rawar murya ya ce Rahamaa ke yar halak ce samun ki Rahma ne a gare mu..

Ahmad ya ce kwarai kuwa ita ce fitilar gidan nan..

Yarima Samad ya ce ita ce hasken gidan nan..

Mamy ta ce ita ce babban bangon gidan nan..

Gabadaya suka hada baki wajen Fadi.

Rahama Ba gaba da gaba ba kota baya sai an shirya...

Shiru ta yi tana sauraren su cikin zakin muryan ta ta ce ku Ahlina na ne ku ne Farincikina '' rayuwa ta tadawo hannun ku tabar hannun iyayena.

Dole ne inkare martaba da mutunci ku yan uwa na...

Dan Allah bana son godiya komai nayi ya zame mun dole ne..

Abban Marwan ya ce A'a Rahama mata nawa ne basayin jarumtar ki '' wasu watsa gida suke yi..

Kinada Imani ne...

Shi ya sa kika dage a kan tono gaskiya..

Azabure Abban Marwan ya Mike tsaye tare da kama hannun Marwan da zuciyar sa ke tafasa..

Kai tsaye cikin hanzari suka bar dakin...

Ganin haka Samad da Ahmad suka take musu baya sun San wajen Fulani suka nufa..

Samad Sai gudu yake da sassarfa yana fadin Marwan ku tsaya dan Allah..

Amma ina ba sa Jin abun da yake fade..

Kamar Daga SAMA fulani taga an bankado kofa.

Cikin.........

Ta ku har kullum kyauta Daga Allah

Rahama ta ce yi hakuri Mamy komai8️8️

Cikin Gigita take kallon Abban Marwan daya shako wuyar rigar ta '' saida Idanun ta suka kakkafe sama..

Marwan gefe ya tsaya yana kallon su'' ya kasa magana soyake ya kwace ta tsakanin Uwa da da sai Allah hakanan yaji Beji dadin shakar ba...

Isowar Su Yarima da Ahmad ne ya sa cikin zafin nama suka fara kokawa da shi wajen kwatar Fulani da idanun ta suke asama akafe dan wuya...

Koda suka karbe ta gefe daya takoma tazauna tana haki....

Shiko Abban Marwan cikin ihu ya ce Salamatu kin cuce ni kin cutar da Rayuwa ta' 'sai yau nasan Amfanin Karatun Islamiyya' Wanda naki maida hankalina akai tun ina yaro' '' gashi sakacina a kan Addini ya sa kinyi mugun galaba akaina..

Shi yayan nawa da yake da adu'oi a bakin sa '' kun kasa iyawa da shi '' shi ne kuka bi '' ta makirci da tuggu..

Salamatu ban kaunar ki bankaunar komai naki..

Amma ki sani baki ci bulus ba.....

Na sake ki

Saki daya..

Saki biyu

Saki uku dan uban ki..

Hannun Fulani ta daura akai cikin kuka taje takama kafar sa'' ta ce Dan Allah Samad kace masa ya maida auren ina zanje ina zansaka rayuwa ta.... Wayyo Marwan kayi magana mana tashi ta yi tana Girgiza marwan din 'shiru ya yi yana kallon ta yana hawaye...

Aguje ta yi wajen Samad tana Girgiza shi ta ce Abdul Samad dan Allah kamasa magana' '' 'shima shiru yayi.. Hakan ya sa taje gun Ahmad Ko kan ta karaso wajen nasa..

Hannu ya yi mata Alamun karta kusanto shi...

Yabita da wani mugun kallo ya ce karki kuskura kazamin hannun ki yatabani..

Cak ta tsaya tana kallon Ahmad Idanun ta cike da hawaye...

Ganin shigowar Mamy da Rahama ya sa ta nufe kama kafar Mamy tayi.

Ta ce habiba dan Allah ki sa baki ya sake ni ya zanyi da rayuwa ta nasaba da gidan mulki nan komai nakeso ina samu..

Kuka take sossai

Mamy cike da tausayi takama Hannun ta '' ta mikar da ita..

Fuskanta Abban Marwan ta yi ta ce Sani dan Allah kamaida auren na kuskure yariga ya faru..

Sai asannan yadago kai yana kallon Mamy ya ce Mamy ita jahila ce ta ina ake gyara saki Uku banson ta ban kaunar ta....

Kuma tabar tunanin zatabar masarautar nan ba tare da hukunci ba..

Wallahi gidan kurku zata zauna sai yayana ya bayyana da wannan baiwar sanna za ayi shari'a ayanke hukunci...

Mamy cikin tashin hankali ta ce kash Sani da ina nan ɗana hanaka yin Saki..

Kallon Fulani ta yi ta ce Salamatu kinga yanda rayuwa ta juya miki baya Ko '' Kidau haka a matsayin shiri'a ce Allah yake son ki dashi..

Rahama ta ce haka ne gaskiya MAMA fulani karki gujewa hukunci

Abban Marwan cikin ba da Umarni ya ce ina Karfin iko yake..

Ahmad ya ce yana gidan yari..

Ina son a sake shi dan yau da kan sa zeyiwa Fulani bulala dari sanna ya ajiye mun ita a dakin daya zauna tare da irin horon da Samad ya bashi..

Ahmad maza je ka kiramun gangami..

Cikin hanzari Ahmad yafita dan cika umarni

Mamy nakokarin dakatar da shi amma ina Ko tsayawa beyi ba....

Samad ganin Mamy zata hana ruwa gudu ya sa shi yakama hannun ta cikin dabara ya ce Yww Mamy mu je sashin naki '' kinde San gobe hassana zata wuce '' kince kina son tabi Samad air plan personnel...

Mamy ta ce eh haka nace '' bakace saida tabi wani jirgin ba ''

No Mamy baki FAHIMCE NI bane mu je inganar dake..

Tsare shi da idanu ta yi ganin yanda yarike mata hannayen ta...

Sake da baki ta ce kai Yarima ya da haka inajiran inga dawowar baba na ne..

Rahama ta ce gaskiya kam gâra muga dawowar haka kurum kazo da wata salo da dabara za ka kaita daki...

Sossai ya yi mamaki Mamy da Rahama da suka gano lagon sa...

Cikin da ba ta rai ya ce Mamy nace ba za ki tsaya anan ba meyasa ba za ki gane nufi na bane..

Kama hannun su ya yi ita da Rahama ya rinƙa jansu har zuwa sashin nata...

Yana kai su ya ce kada wanda ya sake ya fito haka kurum...

Mamy sake da baki take kallon sa harya fice ta ce Rahama kinga ikon Allah wai yaron nan yaki bari na insa baki cikin lamarin ni wallahi tabani tausayi duk da muguntar ta...

Rahama ta ce haka ne '' nima saina ji babu dadi wallahi

Koda gangami ya iso Umarni aka bashi yatafi da Fulani gidan kurkuku daman yana cike da jin haushin ta '' tun lokacin data sa '' Aka hanasa abinci agidan sarauta Saboda sharrin sata...

Cikin zafin nama yake Jan ta..

Tana ihu tana fadin Abban Marwan Nice Fulani kar ka mun haka.

Samad kallon Abban Marwan ya yi ya ce muyi hakuri da kaddara...

Itakuma ta zauna nan gidan kurkuku sai anga Abbana da Saratu..

Sannan horon yunwa da kace gaskiya babu shi zata ringa samun abinci a kan lokaci kuma irin wanda takeso...

Gidan kurkuku inda ake ajiye matan sarakuna insunyi laifi nan za a kaita.

Bazata yi amfani da waya ba...

Abban Marwan cikin takaici ya ce duk yanda kuka zartar daidai ne...

Babban bakin ciki na wannan matar ta yi amfani dani wajen shayar da mahaifina maganin Asiri na hana shi gane komai...hatsabibiya ce matar nan.

Sun dade suna shawara tsakanin su..

Ɓangaren Baba Salihu..

Kuwa yana zaune yana salati '' gani yake inbeje gida akwai matsala..

Tun da yabar gida be taba sha'awar zuwan ta ba..

Wayar sa ya dauko tare da kiran mai bashi labari...

Wayar tana ring ɗagacen ɓangaren ya ce ya shugaba na kayi wuyar gani ygida ya Ayyuka..

Baba Salihu ya ce lafiya lau wai ya labarin Samad da Mamy ne da Ahmaɗ ɗa Sarki..

Uhmm ni tun da na rakasu airport lokacin da yan uwan Matar Samad za su koma kasar su...

To bankara zuwa gidan ba...

Shugaban Adalai ya ce to Saboda me..

Cikin tsaita nutsuwar sa ya ce akwai wata yarnya da nakeso' 'shikuma Ahmad yarigani har an nema masa auren nata

Inajin kunyar haduwa da Ahmad..

Shugaban Adalai murmushi ya yi ya ce Ahmad dîna ne ya fito da Matar daze aura wacece ita...

Sunan ta Asiya ya ba shi Amsa...

Kawar Rahama matar Samad..

Shugaban Adalai ya ce Asiya dai ɗana sani..

Cike da mamaki Me bashi labari ya ce ka santa ne ya shugaba na..

Murmushi baba Salihu ya yi ya ce uhmm naga hoton ta mana da Rahama shi ya sa nake magana..

OK yanzu na fahimta..

Cewar me bashi labari...

Ina son kayi hakuri dan Allah a kan abun da ya faru '' inkana so zansa Ahmad ya janye..

A'a nifa narabu da ita Ko yafasa ba zan aure ta ba.

Ahmad kanina ne '' mace bazata hada mu ba...

Sossai yaji dadin Furucin sa..

Ya ce InshAllah za ka dace da mace mafi kyau a nagarta '' akwai yarinyar da zanbaka tana cikin masarautar mu..

Ba khadija ba ce kar kayi tunanin ita ce..

Dan nasamu labarin Anyiwa Khadija miji.....

MashaAllah Ya furta Allah yakaimu '' to wacece wannan matar da shugaba na yake son ba ni Ko ma wacece na amince ya shugaba na...

Sossai yaji dadi ya ce nako gode InshAllah zakayi farin ciki...

Akwai bikin da za ayi nan da Sati biyu..

Zanje kano kai Amarya dakin mijin nata..

In Allah ya yi zamu hade a kanon.

Me bashi labari ya ce ai Samad ya ce akwai bikin surukin shi baban matar sa zekara aure zamuje bikin harda su Mamy kowa ma zeje.

Yayi daidai da zuwan ka kenan...

Nan da nan yaji zuciyar sa na harbawa babu wacce yake so da gani kamar Mamy.

Cikin dauriya ya ce MashaAllah Allah yakaimu babu tabbas mu hadu har yanzu kaci gaba da rike mun sirrina...

InshAllah shugaba na bakada matsala Daga haka suka yi sallama...

Kashe

Mai martaba Tun da sassafe Abban Marwan ya je mishi da labarin komai sossai ya Girgiza ya fara jerowa Salamatu

 Allah ya isa ''

Yana fadin gaskiya matar nan azzaluma ce..

Mama karama dake gefen sa ta ce jinjina Al'amarin ta ce shi ya sa ban taɓa ji ta burgeni ba..

Kuma Sani ban taɓa yarda halin sa bane..

Na dauki abun amatsayin beyi dace da matar arziki bane

Ashe ba banza tabar shi ba..

Mai martaba tashi ya yi tsaye yana kallon Abban Marwan ya ce '' yau dawuri zanje fada asanar wa waziri

Zanshiga ciki inda shirya '' tashi ya yi cike da juyayin Al'amarin..

Ita Ko Mama karama maida kallon ta yi a kan dan nata ta ce Sani Allah ya sa isar muku ta raba Ahlina tasa zukata cikin kunci '' kuka ta fashe da shi Abba Marwan ganin yanayin da take ciki ya sa shi Sakin kuka shima ya ce da wani idanu zan kalli Salihu '' bayan inacikin waɗanda suka tozarta shi...

Mama Karama ta ce kar ka damu Sani Allah ze shige mana gaba '' Amma wannan matar Samad din nan kash ba mu da abun da zamu iya biyan ta '' domin ta yi jarumta...

Kusan karfe tara '' Hassana tagama shiryawa zaune take kusa da Mamy cikin kukan rabuwa ta ce Mamy ke mace ce ta gari harna ji ba na son rabuwa dake...

Mamy cikin kewar da zatayi ta ce '' Hassana da wallahi mijina yana gari dana bashi umarnin ya aure shi dabi'un ki da halayyar ki sun mun sossai wallahi...

Wayar Hassana tafara ring tana dubawa taga Hauwa ce...

Cike da Farin ciki ta ce Daughter dankinji ina nan tafe yau shi ne kika nemeni dawuri ko

Daga can ɓangaren ta ce mommy na kuma Amaryar Abdurrazak '' ace zaki daura aure sai yau muke samun labari uhmm ni dai Ko dani za a kanon na..

Sossai Hassana ta dara tana kallon Mamy ta ce yawwa ga diyarki hauwa ku gaisa mikawa Mamy wayar tayi..

Cikin hanzari Mamy ta mika hannun ta takarbi wayar '' tare da karawa a kunnen ta...

Inawuni daughter yanda ta ji hassana ta fada cike da fara'a

Daga can ɓangaren ta amsa da lafiya lau Mamy daman mama ta tana ba ni labarin ki '' zanso wataran inganki '' kinyi a rayuwa kun rike uwa ta tamkar yar gida '' Allah ya saka muku da Alkhairi Mamy...

Cike da Jin dadi Mamy ta ce Ameen ni dai daughter '' wajena zaki dawo nan da zama in Allah yakawo miji sai kiyi aure Ko..

Sossai Hauwa ta dara hadda rufe Idanun ta '' ta ce mezehana ni zuwa Mamy '' InshAllah in Mama ta tawuce kanon to ni kwatanon zanzo....

Nan da nan fira ta barke tsakanin Mamy da Hauwa..

Ita Ko Hassana kallon su take tana dariya cike da farin ciki...

Suna gama wayar tamika wa hassana wayar ta...

Ƙaramin akwati Mamy ta cika da kaya ta ce hassana wannan kayan nida Rahama ne muka baki dan Allah ba yawa ayi hakuri..

Cikin farin ciki take kallon akwatin ta ce kai MashaAllah '' kaya sunyi kyau fa...

Cike da Jin dadi ta ce Allah ya saka muku da Alkhairi....

Yarima Samad '' kallon Rahama yake cike da mamaki tun safe ba ta ci komai ba..

Amma amai take ta zuba duk ta galabaita......

Da ƙyar ya lallabata yabata ruwan lipton shima saida yasha lemun tsami da kanunfari '' Sannan ta kurba....

Kallon Samad take cikin ciwon cikin daya taso mata tana dafa marar ta..

Ta ce wayyo Amjad Mutuwa zanyi '' '..

Cikin gigita ya ce Ah Ah Rahama ki daina Ambatan mutuwa please na rokeki...

Cikin hanzari yadau wayar sa yakira likitar masarauta...

Koda likitan ya iso..

Khadija ce ta yi masa jagora har dakin Samad..

Ita Ko Khadija cikin hanzari ta nufi sashin Mamy domin sanar musu abun da yake faruwa...

Cin karo ta yi da Su Mamy da hassana harda Ahmad '' za su tafi parking space..

Ganin khadija kamar ba cikin hayyacin ta take ba..

Mamy ta ce lafiya kuwa Auta '' meyake faruwa ne

Ina Samad da Rahama ana jiran su gashi har Hassana zata wuce ita kadai ake jira a filin jirgin....

Hassana itama kallon Khadija take cike da zakuwa ta ce lafiya kuwa yar nan kinyi shiru...

Bakin ta Na rawa ta ce wallahi Mamy matar Samad bâtayi barci ba '' wai ciwon ciki...

Gata cen likita na duba ta

..

Subuhannalah Mamy ta Furta cikin hanzari ita da hassana da Ahmad suka yi Sashin Samad dan ganin abun da ke faruwa...

Koda suka isa iske Rahama suka yi...........

Wata yar uwa acikin members dîna ta ce kusata a adu'ar ku a kan wata damuwa..

Sannan nikaina ina barar adua a kan nawa lalurar ta rashin lafiya '' da kuma yar antina da tasha guba jiya a rashin sani ''

Allah yabata lafiya ya sa ta warware normal...

Ta ku har kullum kyauta Daga Allah...8️9️

Koda suka isa iske Rahama suka yi tana Amai''cikin tashi hankali mamy ke magana ta ce yata jibi yanda kika fada Daga jiya zuwa yau...

Kama hannun Rahama ta yi tana jero mata sannu.

Maida kallon ta a kan likita daya gama auna fitsarin Rahama ta ce likita meya damun ta kardai ace maleria ce...

Takarashe zancen tana kallon Samad dake yarfe hannayen sa...

Cikin nutsuwa likata ya fara magana ya ce ''

Ya ce uhmm ba maleria ba ce..

Samad da Mamy suka hada baki wajen fadi to mene ne...

Tana dauke da ciki ne '' shi ne yake ba ta wahala cewar likita..

Cikin tsananin Farin ciki Samad ke kallon Likita Sam ya mance Mamy na dakin ya ce likita kana nufin Hubby tana dauke da ciki...

Kwarai kuwa dukan alamu sabon ciki ne...

Bakin Samad Yaki rufuwa zuwa ya yi ya rungumi Mamy ya ce kinji ance tanada ciki wayyo dadi...

Cikin tsananin farin ciki yake magana...

Mamy cike da farin ciki ta ce kai Amma yaushe kazama mara kunya haka.

Furucin Mamy ne yadawo da shi cikin hayyacin sa..

Cike da kunya ya fara sosa keyar kansa.

Kallon Ahmad yake shida Khadija yanda bakin su yaki Rufuwa dan Farin ciki..

Ahmad ya ce congrat Yaya Samad wayyo dadi zan zama uba cewar Ahmad..

Hassana dake dariya ta ce kwarai kuwa za ka zama uba kwanan nan..

Cike da Jin dadi ya ce Mama hassana '' mu je mu rakaki airport din kada mu rasa jirgi...

Yarima Samad da farin cikin da yake ciki ya ce Ah Ah Ahmad kayiwa drever na '' na Samad air plan personnel '' kace ya yi maza ya shirya shi ne ze kaita kasar Gabon..

Ba ƙaramin dadi Mamy da hassana suka ji ba'' hassana ta ce godiya nake Yarima Allah ya inganta cikin dake jikin Rahama Allah ya sa ta haifo mana yan hudu..

Ameen ya Allah ya furta kai tsaye ba tare da ya yi shayin komai ba...

Rahama duk kunya ya lullube ta takasa hada idanu dasu Mamy...

Ganin haka Mamy ta ce Rahama kikula da cin abinci kinji ko'Kuma ki daina girki' ɗuk kalan abinci da kike so ki gayamin zan dafa miki..

Gyada kai Rahama tayi' 'cikin muryan Mara lafiya ta ce Mama hassana Allah ubangiji yakaiki lafiya yatsare hanya.

Da ameen suka Amsa dukan su...

Likita cike da Jin dadi ya ce toni zan tafi wannan takardan magunguna ne kuma Daga watan gobe zata fara zuwa awo hakan yana da matukar muhimmanci..

Samad ya ce Ah Ah harsai ankai watan gobe ni yanzu ma tafara zuwa..

Harara Mamy ta watsama Samad ganin haka ya sa ja bakin sa ya yi shiru...

Mamy ta ce likita sannu da kokari inda wani abun zamu nemeka...

Samad ganin likitan ze wuce ya ce likita nabaka kujerar makkah..

MashaAllah MashaAllah kowa dakin ya furta cike da Jin dadi likita ya fara kukan Dadi ya ce watau Allah ya yi kira..

To Allah ya inganta cikin Amarya da Ameen kowa ya Amsa dakin..

Babu ba ta lokaci Hassana suka bar dakin da Mamy da Ahmed '' khadija kadai aka bari dan Samad shima yafita rakiya..

Rahama kallon Yanda Khadija ke kokarin gyara daki take '' tahana ta yin wani abu...

Nan da nan tashare daki ta goge ta kunna turaren wuta..

Ruwan dumi ta hadawa Rahama tadawo dakin tare da kama hannun ta '' ta ce anty tashi mu je Ko..

Babu musu Rahama ta tashi dan ita kanta tasan tana bukatar wankan....

Har Filin Airport Mamy suka Raka hassana..

Suna kallon ta har ta shige jirgin tana ta Daga musu Hannun cike da kewar su...

Koda jirgin ya Daga Samad cike da Jin dadi shida Ahmad suke fadin gaskiya wannan matar tanada kirki ba ta da damuwa....

Mamy ta ce gaskiya ba ta da damuwa jibi yanda Babana ya dame ta Ko ince kuka dame ta amma ba ta taba nunawa ba tadauki hakan ne amatsayin dan bakusan ita wacece ba ''.

Sossai Ahmad ke nadaman rashin kunyar da yake zuba mata inyayi tozali da ita agidan.

Cike da kewa suka bar airport din....

KANO

Sossai sheik ke shirye shirye sabon gidan su.

Da za su tare..

Mama kam cike da Farin ciki ta ce uhmm zanfaso gari fa..

Samun sheik ta yi azaune a dakin nasa ta ce gaskiya yakamata kasai mun mota mana...

Murmushi Sheik ya yi ya ce Aishatu kedai baki rabo da abun dariya..

Akwai kudade da Rahama diyar makiyar ki tabada zanbaki millions 10 '' itama Sa'adatu millions 10..

Abubakar millions 5

Asiya millions 5

Salma 5

Kinga Millions 15 ne nawa.

Inkinga dama ki sai mota da kudin Ki '' duk yanda kika so daidai ne....

Mama cike da takaici ta ce kambuhu nida haihuwar ya wasu da raba kudi..

Sheik ya ce kwarai kuwa ɗanma bansa Abdul jalil ba..

Cikin nawa kudin zanba uwar shi ta ajiye masa millions biyu Ko shima ya san yayar shi Rahama ta mana kyauta...

Aisha yanzu dai nagama bayani '' kudi kuma anjima zanfiddo in baki naki..

Mama sake da baki ta ce uhmm Abdurrazak kenan wai kai wani irin jarabben mutum ne '' duka nawa kake za ka hada mata uku..

Kasaitaccen Murmushi Sheik ya yi ya ce uhmm Indo tawa nikadai '' inbanda abun ki..

Mata suna yawa ne ai bakwa yawa Inde kanada lafiya meye matsalar..

Mama rike da baki ta ce ikon Allah '' yau na gida ya koshi har kake kiran kanka me lafiya..

Sheik kallon ta yake yana nazarin kalamanta ya ce tun da baki koshi '' kibari zuwa ɗare '' sai agani Ko..

Zare idanu Mama ta yi ta ce wallahi bana bukata '' haka kawai '' ina fama da kai ka sakar mun da kasala da ciwon jiki '' inkasa samu abu ba ka san Ana ajiyewa ba.....

Sheik dariya ya yi ya ce Aysha ke fa kikace banda lafiya nayi tunanin kin manta ne ashe kina tune Kinga kenan kun mun kadan keda Sa'adatu saina auri Hassana inje innemo sadakar yalla in hada da ita kinga na cika sunnah kenan

Sossai Ran Mama ya ba ce ta ce aiga yayan ka nan gidan miji kana son ayi masu abun da kamun..

Kwarai kuwa indai karin aure ne ni zanba mijin nasu gudummuwa '' abun farin ciki ne fa '' kuma karuwar su ce...

Mama sake da baki take kallon sa ta ce kam buhu lallai kace wani Abu..

Ni zan tafi sai dai anjima. 'tashi ta yi tafita tana tunanin tayanda zata Koma gidan Malam' ɗan kam bazata bari anty ta haihu ba...

Tana fida Sa'adatu ta shigo ya ce mata ze basu kudin nan..

Da Rahama ta bayar..

Anty ta ce Ah Ah kabar shi a hannun ka' Kaida kake dawainiya damu ba ka taba gajiyawa ba'' bama siyen komai da kudin hannun mu. Kaine kake mana ba mu nema mun rasa ba..

Dan haka kabar shi Nina yafe wallahi...

Sossai Sheik yaji a zuciyar shi kaunar ta na dada ruruwa dan beda kamar acikin matan sa...

Ta cire tuta ita ce mace daya tilo data sace bargon zuciyar sa' 'in babu Sa'adatu bayajin rayuwar sa ze tafi daidai..

Dawo da hankalin sa kusa ya yi ya ce Ah Ah Sa'adatu wannan kudin yar ki tabaki kisiye koda gida ne da shi kisa haya..

Wannan kudin hayar kiringa badashi sadakatul jariya' in canji sun rage ki gina massalaci wanda Ko bayan ranki zaki amfana..

Sossai ta yi naam da shwarar sheik ta ce Allah ya saka maka da Alkhairi...

Ameen ya amsa yana murmushi ya ce gobe ina dakin ki 'nakosa gobe yazo..

Murmushi ta yi cike dajin dadi ta ce InshAllah zata zone..

Daman kan zancen inda Amaryar ka zata zauna nazo' 'yakamata dakin nata y azauna kusa da nawa..

Kaga Mama ita ce shugaban gida.

Sashin nata zefi namu dan girma..

Sheik ya ce kuma haka ne' 'nata zefi girma amma nayi girman irin nata guda uku kinga inkinaso kizauna saman bene mana....

Ita Amarya ta zauna saman bene na uku...

Anty ta ce hakan ya yi ka ga Ko Mama kasar nan ya ishe ta ga dakuna barkatai..

Eh ya isheta kinga har dan nata Abubakar ya samu dakin daze ajiye matar sa kafun yagama nasa tun da ya ce mun aure yake so....

MashaAllah Anty ta furta ta ce wayyo Dadi ɗana zeyi aure '' kar abata lokaci wajen nema masa auren..

***************

Asiya tana zaune a dakin mamar ta baban ta ya shigo ya ce '' yawwa kuna zaune ana kenan ''

Asiya cike da ladabi ta gaishe shi ya amsa da yawwa yata...

Daman magana ne a kan auren ki Asiya..

Saida gaban Asiya ya fara dukan uku uku cike da razani ta ce Abba inajin ka tare da yin kasa da kanta zuciyar ta na bugawa da karfi gab gab......

Kallon Maman Asiya ya yi ya ce yau aka turo kudin auren Asiya harna basu sunce nan da Sati biyu za a daura auren..

Kuma na'amince duba ga irin gidan da mutuntaka irin na gidan da suke neman auren ta.....

Kuma Sheik Abdurrazak ya jagorance su ba zan iya hanawa ba...

Dib Dib haka Asiya ta ji jinta da ganin ta na kokarin daukewa..

Maman Asiya ta ce MashaAllah Abu ya yi Allah ya sa Alkhairi...

Kenan rana daya za ayi bikin ɗana Asiya da Sheik kenan..

Kwarai kuwa cewar Abba.

Ke Asiya ya furta da kakkausar murya hakan ya sa ta Dago jajayen idanun ta da suka kada..

Ta ce na'am Abba '' kindaiji abun da nace dake aure zanmiki duk wani Samari Daga yau ki ajiye su gefe ki fadi abun da kike bukata a sai miki dan lokaci yakusa..

Sannan mijin da zaki Aura ya ce bayason kina chattin..

Maman Asiya ta ce wai yasunan mijin da ze auri Asiyar..

Abban Asiya ya ce kamar Ko Ahamdu ne sunan nashi na manta zankara tambayar Sheik..

Abba na Fita Asiya ta fashe da kuka ta ce shi ke nan anrabani da Faruk mama '' Ko wannan dalilin ne ya sa kwata kwata ya daina nema na...

Kuma shi wanda akace ze aureni ban san shi ban san Daga inda yake ba...

Maman Asiya ta ce kiyi hakuri zaki sanshi ne '' Nina ai aurena da baban ki ban san shi ba''

Aka hada auren gashi yanzu muna zaune kalau.

InshAllah zakiyi Farin ciki' 'bubbuga bayan Asiya ta rinƙa yi Alamun rarrashi.

**********************

Salma zaune take a falon nata ta mimmike kafa kan 3tsr remote na hannun tana canza tasha..

Al'amin ne yashigo ya iske ta zaunen ya ce Amarya kina hutawa fa.

Eh ina hutawa ta ba shi amsa tana yatsine fuska....

Ihun kiran yar aikin take cikin izza da takama.

Nan da nan me aikin nata tazo ta durkushe gaban su..

Wani kallon banza take bin ta da shi ta ce ke je ki kawowa me gidan abinci da lemu..

Al'amin zama ya yi yana kada kai cikin zuciyar sa sai fadi yake wannan yarinyar ta iya rainin wayo fa......

Cike da jin haushi ya ce kewai salma meyasa ba ki da Tarbiyya ne....

Tarbo ne banida shi ba Tarbiyya ba cewar Salma tana huci sama sama banda wulakanci ni baiwar me waina ce....

Dazan dauko maka Abinci cikin Daga Murya take magana...

Al'amin cikin fushi ya tashi ya ce wallahi kedai an yi asarar haihuwar ki..

Kuma zaki ga abun da zanmiki agidan nan.. Shasha kawai fuuuuu ya tashi yawuce tare da barin abincin beci ba yahaura sama..

Dakin sirrin nasa ya shiga kai tsaye kayan jikin sa yacire ya dauko jajayen kaya ya saka...

Zama ya yi tare da nannade kafafun sa ya takkwashe su waje daya fuskakantar kwaryan dake dauke da jini yayi..

Yana wasu kirari '' yana wasu maganganu nan da nan hoton wasu mutane ya bayyana..

Wanda ke nuna sune shugaban yan mafiyan '' 'babban ya ce kai Al'amin tun da matar ka nada ciki basai ka ba mu uwar ba....

Tana haihuwa da wata biyu zamu ashe su dukan su..

Al'amin cikin zazzare idanu ya ce what ban gane harda abun da zata Haifa..

Nifa...........

 

9️0️

Nifa ba zan ba da ɗana ba ita dai nakeson inbaku..

Shugaban yan mafiyan cikin Idanun sa dake cike da bakin abu kamar kwalli yana zazzare su kamar kwai ya ce kai Al'amin abun da dodon tsafi ya nema kenan saikace baza a bashi ba.

Zancen banza kake mu nan da muka ba da matan mu da yayan meya same mu bakaga muna ci gaba ba..

Al'amin cikin Idanun sa da suka kawo ruwa ya ce dan girman Allah kubari dai inbaku Mata ta ita kadai abun da zata haifa mun ina son yazauna ina ganin abuna...

Shugaban ya ce Al'amin zamuyi shawara sai dai kaji mu..

Suna kai karshen magana.

Ya ajiye kwaryan tare lakato Jinin kadan ya latsa a bakin sa....

Barin dakin tsafin nasa ya yi kai tsaye yatafi dakin sa..

Yayi wanka yashirya tsaf cikin kananan kaya..

Shigowar Salma ne ya sa hankalin sa yadawo kanta sanye take cikin doguwar riga '' cikin nata harya dan fara turowa..

Neman wurin zama take tana turo baki gaba '' wayar ta ce tafara ring tana dubawa taga Mama '' kamar bazata Daga ba.

Amma saita daure ta daga cikin kasa da murya take magana..

Mama ta ce haba Salma yau dan nace ki koma gidan mijin ki shi ne kika shareni bakya nemana haba yata '' Nice fa uwar taki..

Salma yatsine Fuska ta yi ta ce mama kenan tun da kika koreni gidan naki harda mun duka..

Keda Abby da Abu saida nasha mari taya zan tuna ki..

Uhmm dadin abun nima mijina ya samu wadata muna cikin daula Ko Rahama bazata nuna mun Jin dadi ba saida ta nuna mun Sarauta...

Mama ta ce MashaAllah yata kice Allah ya ɗauka ki '' kenan basai ankashe auren naki ba..

Salma ganin Al'amin na dakin ta ce Ah Ah kedai kawai zan nemeki..

Naji batun auren Abby wai saura sati biyu..

Yanzu Abby banda tsabar jaraba meze da wata bazawara '' mama ta ce kedai bari Salma kin san halin uban naku '' da shegen naci kamar kurma..

Ya ce zekara sonake insan hanyar dazanbi wajen dakile wannan auren '' har ita Sa'adatu bana tunanin zan barta '' saita bar gidan nan kuma cikin jikin ta '' sai dai abinne..

Wannan gidan da zamu koma ni kadai zan tare Daga ni sai ɗana Abubakar.

InshAllah sai dai ta koma kauyen su ruggar Fulani '' makirar mata kawai...

Salma tabe baki ta yi ta ce mama zan kira zuwa dan anjima ganin Al'amin ba ta iya fadin komai...

Tana ajiye wayar ya nufo soma ja da baya ta yi ta ce haba meye haka me zan maka ne....

Cikin Fada ya ce hakkina zaki ba ni '' taya zaki hana ni '' tun da ki kazo Alkur'an baki isa ba....

Cikin zafin nama ya cakumo ta kasa kwacewa kuka take ta ce wayyo Al'amin zan daina zagin ka..

Cikina ke min ciwo pls kar ka tabani..

Beko saurare ta..

Hakanan yakamata '' ya yi mata dadddaya tare da rabata da kayan jikin ta...

Salma dai tasha wuya hannun sa dan beje mata da wasa ba.....

Cikin Jin zafi da radadi ta rinƙa fadi Allah ya isa mugu Azzalumi kawai..

Wayyo marata '' wayyo cikina hakanan tafara ihu tana fadin innaliahi wa'inna il rajun.

Ganin da gaskiya take salatin ya sa shi ruɗewa tare da daukar ta...

Yakaita bandaki ya yi mata wankan tsarki.... Kaya ya canza mata tare kaita Asibiti babu ba ta lokaci....

Koda likitoci suka rufo cikin hanzari suka kaita umergency '' taimakon gaggawa suka ba ta tare da tsaida Jinin dake mata zuba....

Suna Asibitin har babban su yazo ya yi mata scanin dan ganin lafiyar abun da ke cikin nata.........

Yana dubawa yaga komai normal kawai cikin na barazanar barin jikin ta

Magunguna yabasu tare da yiwa Al'amin gargadi kada yakara kusantar ta harsai cikin nata ya tsufa.........

Al'amin cike da damuwa ya ce InshAllah zekiyaye..

Kashe Gari

Kwatano

Yarima Samad cikin shigar sa ta zuwa aiki '' yana gaban mirror yadau hular sa'ta lauyoyi ya saka' 'yana kokarin tashi dan feshe jikin sa da turaren sa one love..

Wayar sa'' tafara ruri.

Yana dubawa yaga Ansa Yusuf Sani Yaro 'cikin hanzari ya daga' '

Daga can ɓangaren bayan gaisuwa ya fara masa bayanin dalilin kiran nasa...

Ya ce Yarima Ahmad matar nan mun gano inda take tana gwammaja' tagwayen gida nan cikin garin Kano''' daidai lungun yan darika...

Gida mai lamba 111 ansa Garba shehu jikin gidan..

Dan haka zansa wakilai na''suje gobe su dauko ta... In ankamo ta a ina kake so mu ajiye maka ita...

Yarima Samad cike da Farin ciki ya ce Namijin zaki' Kayi kokari sossai banyi tunanin lokacin daka diba za a samu abun da ake so ba...

Wannan Shari'a a kwatano za ayi Shi' Kuma sai Mahaifina ya bayyana...

Yusuf ya ce kana son in zakulo maka inda baban ka yake ne

SAMAD ya ce abun da na shekara da shekaru ina yi kenan babu nasara...

Kasaitaccen Murmushi Yusuf ya yi ya ce' ɗa tuni ka gâyamun dana dade da nemo maka shi' 'amma yanzu ba ta baci ba..

Katuromun hoton mahaifin naka' 'nashi binciken sirri zanyi dan nasan beson asan inda yake..

Samad ya ce haka ne yana mai canza wayar zuwa dayan kunnen sa..

OK Yarima turon hoton sa shi kwana uku zakaban dan akwai tarin Ayyuka gabana dasai ince maka yau sai inbaka informations a kan sa.....

Yarima Samad ya ce meze hana kaduba mun a yau haba Yusuf dîna..

Yusuf cikin gajiya da wayar gashi ana jiran sa '' ya ce Samad inaga nagama da kai infira kake ji mun hade online zuwa ɗare '' matar bakace inda zan ajiye maka ita ba...

Yarima cikin dan nazari ya ce ka ajiye ta a kanon amma in zamu tafi kwatano da kai zamuje Ko zanzo bikin surukina kanina ze daura aure nan da mako biyu..

Yusuf ya ce babu matsala zan gayyato shalelen gidan namu Zahradeen amma shi iyakar sa Kano '' wajen daurin auren nan..

Yarima Samad ya ce kai kai Deen yana gari shi ne Ko Daga hannun babu..

Yusuf ganin firan bekarewa ya ce dakata malam firan ya isheni sai anjima

Bejira cewar Samad ba ya katse kiran.....

Yarima Samad maida kallon a kan Rahama ya yi ya ce kinga ikon Allah '' ya gano inda Saratu take maman nusaiba..

Rahama ta ce MashaAllah abun dadi Amjad gaskiya ya yi kokari amma yusuf dinnan kamar ba jinine a jikin sa ba'

Be gajiya da aiki '' Samad ya ce uhmm haka yake shi besan hutu ba' 'yanzu ma kina ganin yakatse wayar ne dan anajiran sa....

Zanje wajen aiki inna dawo zantura masa hoton abbana

Rahama cikin da ba ta fuska ta ce ayya ni dai ban taɓa ganin sa a hoto ba...

Yarima cikin hanzari da lokaci yatafi ya ce haba hubby na kibari indawo mana '' zaki ganshi ''..

Har wajen sashin nasu ta yi masa rakiya tare da adu'oi Allah yakare ka mijina..

Allah yakare da mugun ido na yan mata..

Shiru yayi.

Ta ce ba za ka ce ameen ba..

Murmushi ya yi to inna ce ameen kina nufin ba zan kara aure ba...

Murmushi ta sakar masa ta ce za ka kara mana amma ba yanzu ba..

Uhmm to Ameen my Rahama bayan ke babu wata zolayar ki nake gimbiya ta nasan ke baki cikin mata masu kishi kawai kina son kare ni Daga fadawa sharrin mata ne..

Kwarai kuwa My Amjad ka gane ka ga inzaka dawo kabiya kasiyo mun agwaluma..

Zazzare idanu ya yi ya ce Agwaluma kuma my hubby..

Eh mana inba sokake in maka kuka ba '' ta marairece fuska...

Cikin shagwaba..

Kallon kansa yake ya ce kin kalli shiga ta kuwa zaki aikeni wajen masu saida agwaluma 'lallai na yarda wayannan yayan sun tasoni gaba Daga na taimaka musu zankawo su duniya sai su takura mana nida kanina..

Hangon Ahmad ya yi cikin shiga ta Alfarma sanye yake cikin babbar shadda gezner' 'sai kamshi yake zubawa

Yarima Samad ya ce yawwa kanina ina za ka je ne kake ta buga uban sauri haka..

Cak Ahmad ya tsaya yana kallon su dan bema lura dasu..

Cikin sakin Murmushi ya ce zanje daurin auren abokina dake sabon zongo' Shamsu ka tuna shi Ko..

Yarima Samad Alamar nazari ya ce eh eh nagane shi Ayya yaune daurin auren nasa to Allah ya sanya Alkhairi ba ka fada min da wuri ba da munyi maka kara..

Yaushe za ka dawo ne..

Ahmad ya ce da an yi la'asar..

OK Good ni inna fita zankai bayan magrib

Anty taka yake son agwaluma kaje kasiyo mata a hanyar ka ta dawowa gida..

Nan da nan Annurin dake kwance saman fuska Ahmad ya ba ce bat kamar bashi ba..

Ya ce kam buhu ran nan danwake muka je nema yau agwaluma duk gidan nan babu me zuwa saini '' haba yaya wai meye haka ne a kalle ni da wannan shigar tawa inje gun masu siyar da kayan tsami...

Sossai Rahama ta dara saida fararen hakoran ta suka bayyana '' cikin cool voice din ta Ta ce My Ahmad dîna kar ka damu '' zan aiki Karima zata je ta zabomun masu zaki..

Shi yayan naka yana Jin kunyar zuwa siye bare kai dan gayu..

Kada kai ya yi ya ce Atoh anty kedai gayamasa ba ajina bane kinga tafiya ta kada ya ce wani abun bayan wannan Bejira cewar Samad ba yakara gaba yana buga uban sauri...

Yarima Samad murmushi ya yi ya ce kinga kanin nan nawa '' matar sa zata sha aiki...

Wai m'a kin san cewar kawar ki Asiya ze aura nan da Sati biyu kuwa..

Zazzare idanu Rahma ta yi ta ce Asiya kuma yaushe hakan ya faru ba ta gayamin ba..

Yarima ya ce kinga tafiya ta karki kira Asiya a kan maganar auren nan inaga ita kanta batasan Waye mijin ba '' cewar Mamy..

Kibari inna dawo zamuyi magana saimu kirata Ko..

Kada kai Rahama ta yi cike da Jin dadi ta ce woww yanzu Asiya zata zauna kusa dani '' cikin masarauta '' Allah na gode maka daka Amshi adua ta a kan kahadamu zama waje daya nida Asiya..

Neman Karima tashiga yi '' cike da girmama Karima tazo ta ce ya shugaba ta gani kiban umarni..

Cike da Jin dadi '' Rahama ta ce yawwa Agwaluma zaki siyo mun'' biyo ni ciki in baki kudin..

Koma ciki ta yi Karima ta take mata baya....

**************************

Gabon 🇬🇦

Dakin hassana cike yake Makil da jama'a dan gaishe ta da masu mata adua Allah ya sanya Alkhairi na auren da zatayi.....

Hauwa cike da murna ita da kanin ta Imran suke zaune kusa da uwar tasu...

Mama kinga yanda kikayi kyau da kiba kuwa cewar Imran..

Hauwa ta ce wallahi nima haka zance gaskiya kwatano zan tafi nima dakin wuce Ai Mamy ta ce inzo..

Hassana kallon su take tana murmushi ta ce uhmm kudai Ko...

Yanzu ku kwashe kwanonin abincin nan nakoshi..

Kuma zanje dakin mahafina ina zuwa ta ce musu tare da mikewa tsaye..

Kai tsaye dakin nasa ta nufa '' koda ta isa iske shi ta yi yana waya..

Cikin Jin dadi tazauna tana jiran yagama wayar..

Yana gamawa yadawo da hankalin sa a kan ta ya ce Hassana ya gajiyar tafiya .

Alhmdulilah yabiki jiki ta amsa cike da Jin dadi..

Imran ya ce kana kirana shi ne nazo takarashe zancen tana sanda kanta kasa...

Yawwa ya furta yana kallon ta ya ce wakilin angon naki yana waje yana jiran ki..

Yazo ganin ki kuma ze baki wayar da zaku ringa gaisawa da wanda zaki aura.

Sannan ya aiko da akwati guda biyu na lefe Makil da kaya..

Gaskiya mutanen nan sunyi kokari bazawara harda lefe cewar baba..

Hassana cikin ladabi ta ce Allah ya sa Alkhairi Abba zanje ingansa kamar yanda kace nasan ba za kamun zaben tumun ɗare ba..

Cike da Fargaban waye wannan wakilin Angon nata' tazura hijab din ta..

Tafita kanta akasa take tafiya cikin fargaba' '

Shiko tsaye yake jikin bakar motar sa mercendez' ganin isowar ta..

Yasa shi Fadin yar kwatano har kin dawo ne yana murmushi gashi nasa kindawo babu shiri...

Dago kai ta yi dan ganin me maganar caraf Idanun su' suka tsarke cikin juna..

Cikin...............

Ta ku har kullum kyauta Daga Allah akwai bonus inhar kunyi comment9️1️

Cikin mamaki '' ta ce shugaban Adalai me kakeyi anan wajen..

Wani kake nema ne dan a zaton ta Ko yazo ne ya ce ya amince ze aure ta..

Murmushi ya yi cikin kasaitar sa ya ce '' Nine bakon da Aka turo ki wajen sa...

Kada kiyi mamaki '' Nine nan na nemawa uban gidana auren ki..

Tun da nasamu labari kina garin kwatano '' nasan kaunar da kike mun ya yi zurfi kada inbar ki haka cikin Adalci na '' shi ne na ha daki da Uban gidana kuma malami 'surukina sheik Abdurrazak kabeer hizqeel makarfi..

Cikin matukar Mamaki ta ce uban Rahama shi ne mijin dazan aura wannan shahararren Malamin Addinin da duniya tasan da zaman sa Yayiwa Addini hidima' 'mijin Sa'adatu baiwar Allah da muka hadu a masarauta' 'hawaye tafara dan kukan Farin ciki ta ce nagode shugaban Adalai niyau sheda ce' 'sunan ka yabika taimakon ka' 'yabika' Kyawun halin ka yabika' Wallahi kai adali ne kuma mai tausayi na kasa da shi jibi irin wannan babban Alkhairin daka hadani dashi..

Durkushewa kasa ta yi tana kukan Farin ciki' ta ce ta ce nagode sossai jazakallahu khairan..

Murmushi ya sakar mata ya ce amshi wannan wayar akwai layi A'ciki na kasar Nigeria' Wanda Inkin je da shi zaki ringa amfani' 'Sannan layin ki na nan zaki ringa siyen data da shi kina hawa online har kibar kasar nan....

Wayar iPhone 12plus yabata cike da girmamawa ta karba tana godiya..

Inkin je gida kisa caji zuwa ɗare zaku yi waya ke dashi..

Ina son ki nuna masa kauna da soyayya mutum ne me saukin kai inka iya zama da shi '' Sannan yana da Adalci '' dan na zauna da shi zakiyi Alfahari..

Hassana cike da Jin dadi ta ce wannan mutumin kowa ya san adaline koda ba ka zauna gidan sa ba wanda yake gina masallatai kowani reshe na kasa '' kuma ya gina gidan marayu yana tallafa musu '' 'yana gidaje sama da hamsin akace amma ance duk haya ya saka' Kuma kudaden gidan marayu ake kaisu.

Kai ka ga yanda mutane ke yaba kokarin sa duk yana boye beson ana fadi hatta gidan sa baya fada musu sirrin Alkhairin sa saboda neman dacewa awajen ubangiji..

Wallahi kabiyani indai Abdurrazak ne' Kaikuma Allah yakawo karshen wata fitina ya hadaka da matar ka Habiba lafiya..

Cike da Jin dadi ya ce Ameen ya Allah godiya nake.

Kinga tafiya ta' 'saide mun hade yar Albarka

Babu ba ta lokaci yabar nan cike da Jin dadi

Ita Ko cike da farin ciki ta shiga gidan tana ba hauwa da Imran labarin yanda suka yi' 'sossai suka yi farin ciki' 'Imran tabe baki ya yi ya ce watau ni kadai za a bari a gabon

Hassana ta ce haba Imran kade san bazamu bar Abba shikadai ba'' tare da zaku zauna da inna....

..

Bayan Isha'i bayan takwanta dan tanada tarin gajiya tare da ita..

Tuno da wayar da Aka kawo mata ta yi hakan ya sa tadauko ta kunna wayar' tana kawo haske babu ba ta lokaci ta yi siye data' Koda ta shiga whsap dînta..

Ganin Nombar sa ansa Sheik Abdurrazak cike da farin ciki tarubuta Salam

Shiko yana online ganin salam din yashigo..

Ya fara shafa gemun sa yana Murmushi..

Maida mata reply ya yi da waalaiki Salam' Amarya Barka da warhaka...

Ganin reply din sa sossai ya yi mata dadi hakan ya sa fira ta barke tsakanin su Kamar sun taba sanin juna a karshe dai harda video call..

. Yana kallon ta yana Murmushi MashaAllah ya furta' ganin ta da ya yi sanye da hijab kuma gata Black beauty' 'bama ka sanin ta haihu Saboda yanayin jikin ta...

Ita ma tana ganin sa wai washe baki take' ta ce yasu anty na...

Suna lafiya lau yabata amsa '' hakadai suka sha firar su '' ta love zuwan mama a dakin ne ya sa ya katse wayar dan kwanan ta ne kuma ya san hali....

Ita Ko Hassana wani shauki takejin kanta harta Kosa ranar yazo....

***********************

Kwatano

Ka sancewa ɗare ya tsala hakan ya sa baban Maryam barin dakin nasa sum sum ya fito Daga dakin matar sa '' 'yabar ta kwance rungume da pillow..

Kai tsaye dakin yar aikin nasu yatafi wacce ba ta wuce shekaru 16 ba matashiya ce' Kuma da aikin suka dogara....

Yana shiga dakin iske ta ya yi ta kwanta a wahalce irin ta sha aiki ta gaji' 'barci take harda munsharri bakin ta' na bude..

Kare mata kallo ya yi Idanun sa nakan cinyoyin ta''nan da nan yaji wani wutar sha'awa takara dibar sa...

Cikin zafin nama yahaye gadon...

Azabure cikin barcin ta tashi tana mutsaka fuskar ta..

Ganin baban Maryam ne tafara zazzare idanu tana kallon yanda yake wasa da boob din ta da daman suna tsokale masa idanu...

Sarrafa ta yake yi cikin kwarewa itako tana neman hanyar guduwa ganin zata ba ta masa lokaci ya sa beyi wata wata ba '' ya fara kokarin isar da sakon shi...

Uban kara ta saki lokacin daya ratsata ihun ta..

Ya zaburar da Maman Maryam da Maryam din..

Cikin hanzarin su suka fito kai tsaye dakin nata suka nufa..

Maman Maryam sai dube dube take yi a dakin tana neman mijin nata yazo suje dakin yar aikin..

Ganin babu shi babu labarin sa '' hakan ya sa kai tsaye suka yi dakin nasa.

Koda suka isa dakin cikin razani take kallon Abban Maryam yanda yake ta sukuwa a kan yar aikin gidan nasa da batasan inda kanta yake ba..

Wani razananne Kara ta saki ta ce Gar.. b.... a ta ja sunan bakin ta na rawa..

Maryam daura hannun ta yi akai tana ihu hade da salati duk abun da suke bemasan sunayi ba '' dan ya yi nisa 'sossai yanata caccakar yar aiki....

Ganin haka ya sa aguje Maman Maryam ta dubo ruwa ta kwara musu akai..

Firgit yadawo hayyacin sa''' cikin tsananin tsoro da fargaba yake kallon ta..

Ya ce ke Maman Maryam meya kawoki dakin nan...

Bakin ta na rawa ta ce uban ka ne yakawoni '' Shege Azzalumi maci Amana...

Tashi ya yi Daga kan yarinyar yadawo yana fuskantar cikin zafin rai da kuma karasa Jin dadin da beyi ba...

Ya ce Amma dai yau nalura ke sa karya ce ya zaki biyo ni har dakin Mata ta ina sunnah

Cak Mama maryam take kallon sa Idanun ta cike da hawaye ta ce dakin Matar ka Ko kwartuwar ka ankawo yar aiki Amana Kaci Amanar iyayen ta wallahi kotu ce zata rabamu da kai...

Maryam dake kuka sossai ta ce Abba meye haka zangani yau wani irin mugun gani ne nayi wa' iyazubullahi na shiga uku ni Maryam tare da daura hannun ta akai....

Kallon banza yabi Maryam din da shi ya ce dan uwar ki da kikeyi lesbien da kawayen ki 'na taba hanaki Ko tona miki Asiri' 'cemiki nake yi ki daina babu kyau' Wannan kuma auro ta nayi a kauyen nasu.

Tun da uwar ki nada bakin kishi ya sa nakasa fada mata na ajiye ta amatsayin yar Aiki..

Ita uwar naki me nake ci da ita na Jin dadi babu' '' bayan zuciyar ta ba ni take so '' mijin kanwar ta takeso '' kawai ina binta ne kamar wani wawa bawai ban san me nake bane..

Nashiga lamarin ne '' dan naga Kina son Abdul Samad bawai dan intayata yaki ba a kan mugun nufin ta.....

Kallon sa ya maida a kan Farida da hawayen ta suka kafe ya ce.

Bana cin haramun wannan mata ta kishiyar ki...

Nasan zakiyi mamaki ne Ko..

Uhmm nayi haka ne dan in inbarki kema ki auri muradin naki wanda kika kasa hakuri da rashin sa '' tun kuruciya da aure na kina bayan sa...

Na Sake ki saki daya dan Allah kifice mun Daga daki.....

Cikin razani Maman Maryam ta ce wallahi Garba ba ka isa ba.

Nice za ka saka acikin daren nan..

Nakama ka kana cin Amana ta..

Cikin fushi Yayiwa Maryam tsawa a kan tafita dakin..

Cikin Rawar jiki tabar dakin tana salati da kuka.....

Ita Ko Maman Maryam take mata baya tayi.

Suna fita yarufe kofar gam.

Tare da komawa kan yar aikin '' yana yayyafa mata ruwa '' cikin kuka ta farka '' tana fadin wayyo Alhaji zafi zan mutu....

Ba za ki mutu ba ya furta yana kokarin kaita bandaki.

Nan da nan ya gasata da ruwan dumi.....

KUKA take yi iya gaskiyar tana '' tana jin tsanar sa duk da tasan auro ta yayi..

Su Maman Maryam da Maryam dakin yakoma kamar gidan mutuwa '' kuka suke sossai babu me rarrashin wani..

Daukar wayar ta yi dan kiran Fulani ta sanar mata abun da ke faruwa ji ta yi wayar Fulani a rufe ''

Cikin tsananin tashin hankali ta dannawa bokar jeji kira '' yana ganin kiran Da ƙyar ya Daga sakamakon wasu kuraje da suka fiffito masa ajiki '' kuma Aljanun sa '' sunce sai dai ya je ya roki duk wanda ya zalunta shi ne wannan kurajen za su bar jikin sa...

Muryan sa cen kasa ya ce Farida yadai karki zomin da sabuwar aiki yana magana yana sosa jikin sa..

Ta ce kamarya kada inzo da sabon aiki bokan jeji ''

Mijina yaci Amana ta da yar aikina ''

Duk da Azabar da yake ciki be hanashi dariya ba..

Ya ce uhmm ke yanzu dan yaci Amanar ki meye abun jin haushi bayan sana'ar ki ce '' shima ya iya..

Kinga naki matsalar da sauki dan haka sai anjima..

Ɗif ya kashe wayar tare da cigaba da tsine mata ya ce da ina aikina lafiya saida in hana aure '' in kashe aure '' in hana samun haihuwa da sauran su..

Amma tun da nafarayiwa Salamatu da Farida '' komai ya rinƙa lalacewa..

Kuma harda zuwan wannan fitsararriyar Matar Samad....

Ita Ko Maman Maryam kuka takara fashewa da shi hakan ya sa tafara kiran layin yar autar su Firdausi..

Bugu daya ta Daga Daga can ɓangaren ta ce Uwar cin Amana kece yau kika kirani maciya Amana

To bari kiji jiya na iso gari kuma gobe Yaya auwal da Sani za su zo..

Kadan ya rage Abban mu be tsine miki dan ma Habiba ta hana shi da yake tanada hakuri..

Wallahi kin cuce mu kin cuci kanki kijira hukinci daze biyo baya ɗif itama ta kashe wayar '' maman Maryam sake da baki take kallon Wayar

Wani sabon kuka takara fashewa da shi me cin rai..

Maryam rungume ta ta yi suka cigaba da rera kukan tare...

Yarima Samad yau ya yi ɗare sossai cikin gari Agajiye yadawo gida '' Ko sashin Mamy beje ba..

Yana zuwa iske Rahama ya yi ta yi uban tagumi ita kadai tana jiran sa sai kallon agogo take...

Ganin isowar sa ya sa ta fadada murmushin ta cike da ladabi ta ce welcom Amjad wai Allah ka gaji Ko tare da karasowa kusa da shi yana kokarin zama..

Eh wallahi hubby daga ji yau Ayyuka sun mun ca badan nagama ba' 'nadai dawo ne dan inga maman baby na..

Murmushi ta sakar masa tare da tashi takawo masa abinci da abun sha..

Ayya Baby na lemun kadai zansha banajin yunwa yakarashe zancen yana shafa cikin sa..

Bata fuska Rahama ta yi ta ce uhmm kodai wata tabaka abinci awaje ne'Wunin yau ba ka gida amma kace ba za ka ci ba..

Murmushi ya yi yana me jawo ta tafada jikin sa cikin cool voice ya ce wacece zata ba ni abinci inci inbanda Mamy saike '' uhmm kishirya zuwa jibi zamuje garin iyayen Mamy '' autar su Mamy tazo '' gobe yayyen ta dasuke saudiya za su iso.

Cike da Farin ciki Rahama ta ce Allah yakaimu rai da lafiya.

Ameen ya Allah....

Kako turawa Yusuf hoton Abban namu kuwa'Kuma nima ina son naga hoton nasa...

OK bantura ba gwamma da kika tuna mun' ɗauko wayar ya yi Daga Aljihu ya shiga gallery yana sashin hoton Abban nasu...

Idanun Rahama nakan wayar sa..

Hoton na fitowa ya danna a kan hoton' 'ya ce amshi kiga hoton mahaifina yau zanhuta da tambaya...

. Hannun ta na rawa ta karbi wayar' '

Zumbur tamike tsaye cikin Rawar Murya ta ce Baba........

Ta ku har kullum kyauta Daga AllahƘANWATA

09069080725

9️2️

Cikin Rawar murya ta ce Baba salihu '' ina kasamo hoton sa tana zazzare idanu ''

Maida kallon ta ta yi a kan Samad dake sake da baki yana kallon ta ''

Ya ce ina kika sanshi wannan shi ne mahaifina wanda kike da buri da sha'awar ganin hoton sa..

Rahama cikin kidima 'nan da nan tunanin ta ya hargitse ta ce wannan bawan Allah nasan shi' Wallahi shi ne inma bashi bane suna mugun kama..

Shi ne wanda ya ce yana nemawa dan sa aurena da yatafi dauko dan nasa bedawo ba' 'sai Abby ya ce Adamu yaturo tun da da shi nake tsayawa.....

Yarima Samad da gabadaya yagama gigicewa ya ce Rahamatullah ki nutsu kiban labarin wannan baba salihu da kikace 'sanin kanki ne Mahaifina sunan sa Salihu' Wannan yana nufin shi ne dai wanda kike magana akai my Hubby....

Dafata ya yi suna fuskantar juna ya ce Rahama' Kinkosan shekaru nawa' 'nadauka ina neman wannan bawan Allah' Kigayamin yana ina yanzu dan Allah rokeki' '

Rahama cikin tsananin damuwa ta ce gadi fa yake yi agidan namu tsawon shekaru biyar da suka wuce inaga yazo gidan ina yar karamata..

Ban san inda suka hadu da Abby ba' 'amma Ada a massalaci yake kwana' ɗaga baya yadawo gadi gidan namu...

Sai dai inajin Abby na yawan ce masa yakamata yakama sana'a amma ya Noke ya ce beson kowace aiki sai na gadi....

Nice nan nasa masa baba salihu ka sancewa naga yara da manya kowa salihu yake ce masa babu girma...

Yanda suka ji ina ambatar sunan sa da baba salihu sai kowa ya ɗauka..

Baba Salihu yana daya Daga cikin mutane da nake kauna Ko Ada cen '' sau da dama Salma zata min Sharri shi ne yake kare ni ya ce bahaka zancen yake ba...

Badan Shiba dukan tsiya zansha a hannun mama..

Amjad kana nufin wannan shi ne mahaifin naka '' kana nufin shugaban Adalai ya yi basaja ya zauna agidan namu...

. ba mu kara ganin sa tun da bikin namu ya saura sati biyu....

Yarima Samad ya shiga shock sossai cike da mamaki da Al'ajabi ya ce kenan wannan mutumin ɗana gani A massalacin unguwar ku '' bayan mun idar da sallah yanata zuba uban gudu harna bi bayan sa ashe shi ne..

Kuka yake sossai ya ce haba Abba na ya zakamin haka '' bayan ka san duk duniya insun yarda ka aika ta ni ba zan taba yarda ka aikata ba.....

Kana gudun mu hada idanu nida kai Abba why ya zakayi haka..

Rahama soma rarrashin sa ta yi ta ce '' katuna mama ta ce kamar ta taba ganin hoton ka a dakin nasa '' dukan mu 'mun dauka kila kama ce bakai bane..

Wannan ke tabbatar mana da hoton ku yake yawo yana matukar son ku da kaunar ku...

Wannan abun daya faru da kunya wallahi ashe amsa sharri kuma kowa ya ɗauka koni ce ba zan so mu hadu da kai adaidai wannan lokacin ba....

Yanzu meye Mafita Amjad '' maza katurawa Yusuf dan Sani Yaro hoton nasa ze maka binciken inda yake....

Kuma InshAllah Daga yau zanfara Tsayuwar ɗare a kan sa '' ina adua duk inda yake zeji beda nutsuwa inba yazo gare ku ba kar ka damu Amjad dîna..

Rungumeta ya yi sossai yana kiss dinta a goshi ya ce Rahama ke Rahma ce agareni nagode da kulawa my life.

Tare zamu ringa Tsayuwar daren nan....

Yanzu bara kiga inturawa Yusuf hoton..

Babu ba ta lokaci ya tura hoton iske Yusuf ya yi baya online '' hakan ya sa ya yi masa sakon voice tare da fada masa yana son binciken nan umergency..

Sossai Rahama ta rinƙa kawo fira masu Jan hankali wanda ya sa ya dan rage damuwar da yake ciki

Kashe Gari..

Mai Martaba kiran Mamy ya yi ita da Ahmad da Samad da Marwan da Abban sa..

Harda mama karama..

Saida ya fara da bawa Mamy hakuri a kan abun da ya faru a baya '' ya ce dan Allah su yafe masa..

Mamy ta ce Sarki bakayi komai ba illa a rashin sani..

Cewa ya yi yatara su ne a kan yanda za ayi adawo da Salihu gida..

Samad ya ce Sarki me ran karfe nayi magana da wani shahararren sojan nan mataimakin shugaban kasa a harkan tsaro..

Ya ce inba nan zuwa gobe InshAllah ze gaya mana inda yake...

MashaAllah MashaAllah Sarki ya furta cike da Jin dadi ya ce Allah ya bayyana shi '' wallahi nakosa inga ɗana '' ban san da wani idanu zan kalle sa ba...

Sannan ina son wannan matar nan Farida '' a je akamo ta akaita station ba na son tasamu labari ta gudu...

Habiba kiyi hakuri nasan ba za ki ji dadi ba tun da yar uwar ki ce..

Amma dole ta fuskanci hukuncin cin Amana har cikin masarauta ba Daga waje ba..

Da ba da shawara a kan buga masa makami akai wanda da rai yana kusa yana iya zama ajalin sa...

Mamy cikin sanyin Murya ta ce A'a Sarki kar ka damu koni ce nayi laifi akamani.....

Mama karama ta ce gaskiya Habiba ke ya ce kuma ta gari '' wace mata ce za a hana ta bin mijin ta kuma ta zauna babu ita awannan zamanin.

Shima Salihu ya yi kokari da ya yi biyayya yabar ta.... Allah ya yi muku Albarka..

Da ameen kowa ya amsa...

Abban Marwan ya ce aini nafi kowa laifi nida sai abun da Fulani ta ce shinake yi '' tana juyani gashi tasa na yi wa dan uwana rashin mutunci...

Ahmad cikin kwantar da murya ya ce Abban Marwan ance rana dubu ta barawo rana daya tame kaya...

Yarima Samad ya ce haka ne kanina..

Marwan cikin kuka ya ce Samad ka yafemun yanda na ringa diban kudaden ka''ina bawa Fulani duk a zatona daidai nake aikatawa duk da wani lokacin inajin ba dadi araina...

Yarima ya ce kar ka damu Marwan kaima ba yin kanka bane' ''

Sarki ne ya yi gyaran Murya ya ce sai magana ta gaba..

Zancen auren Ahmad yataso nan da kwana 12.

Dan haka na gama hada lefe '' komai sashin nasa duk angyara shi...

Sannan ina son ahada auren ɗana khadija..

Samad cikin zazzare idanu ya ce Khadija kuma Ah Ah nifa bayanzu zamu aurar da ita ba..

Sarki ya ce to uban me zatayi maka agida ne...

. Ahmad ya ce kaide Sarki kacika rigima inbanda abunka duka nawa Khadija take kuma wai waye za ka ba ta muji inbe mana ba Alkur'an ba za a daura auren yanzu ba sai nan gaba intayi hankali......

Abban Marwan saida ya murmusa ya ce kam buhu lallai ma...

.

Sarki dake sauraren su ya ce kungama Ko...

Suka eh..

Ya ce uhmm daman Adamu dan Ambassador libya Abdullahi shi ne nabawa khadija..

Kun san meyasa nayi haka..

Dukan su suka Girgiza kai da A'a suna sauraren shi...

Kunga dai abun da ya faru wajen auren Adamu yaro ya birkice kaman mai Aljanu kuma nayi Imani baya cikin hayyacin sa ya yi haka..

Shi ya sa bayan biki da Mahaifin sa ya sauko Daga dokin fushi nace masa kawai abashi khadija kanwar Samad din '' tun da shi ya Auri muradin sa...

Hakan zekara mana karfin zumunci..

Yarima Samad ya ce ALLAHU Akbar kabiran.

Sarki sake da baki ya ce ka ga Yarima banson iya Shege me kake nufi ne...

Mamy da Mama karama dariya suke ta kasa kasa..

Yarima gyaran Murya ya yi ya ce tome laifina kayi abun da Alkhairi na jinjina maka...

Cewa kayi zumunci za ka hada '' naga aiga Marwan nan shi ne inka hada kayi auren zumunci wancen kam ba auren zumunci bane auren hadi ne irin wanda kamun...

Abban Marwan sossai ya ɗara ya ce yau dai naga Sarki da Yarima a fili mun ganku a rana..

Ahmad ya ce Abban marwan kabar shi ya ba shi Amsa muji me ze ce....

Sarki sake da baki ya ce Ahmad kaci uban naka kaida Samad din yan rainin hankali '' to na ji auren hadi zanyi '' kai Samad ɗanayi maka auren hadi ai kafi kowa samun Albarka..

Yarima Samad ya ce OK na ji tun da bakada amsa ta..

Badai kaba Adamu ba to Allah ya sa Alkhairi.

Tabe baki ya yi ya ce inafatan ka gama jawabin naka ni zan tafi...

Mamy cikin fada ta ce haba Yarima ya ana magana za ka tashi..

Komawa ya yi ya zauna ya ce yi hakuri Mamy wallahi barci nakeji shi ya sa bana fahimta bayanin sa sossai...

Sarki ya ce na ji dai Yarima auren kuma ya badu '' kace kishi kake da Adamu.

Yarima Samad Dago kai ya yi yana kallon Sarki tare da nazartan kalaman sa ya yi murmushi ya ce ikon Allah indai haka zakabi da zancena tona amince dari bisa dari ya auri khadija kaika san Inde banson auren nan bame yuwa bane kuma d kake cewa kishi a kan me zanyi kishi da shi bayan '' be kasa ni ba a soyayya....

Sarki ya ce wayasani to..

Sossai suka yi tsare tsare yanda za a gudanar da shagalin bikin.

Nan take Sarki yakira Ambassador Abdullahi ya sanar masa '' ga lokacin da ake bukatar a kawo lefe..

Sossai Ambassador ya yi murna ya ce InshAllah muma jibi zamu dawo dukan mu Daga england..

Amma yakamata ahada Adamu da yarinyar daze aura tun kafun ranar auren sudan Saba...

Sarki ya ce InshAllah za ayi haka yau za a ba ta waya kuma za a bashi lambar ta...

Daga haka suka yi sallama..

Hatta ankon za su yi ranar bikin da wanda za a raba wa bayi kyauta da jama'ar cikin gari duka an tsara komai..

Sarki ya ce ni dai kam ba zani daurin aure Kano ba... Zan tsaya anan ayi na khadija gaba na...

Kema Mamy ba za ki je ba..

Mama Karama ce zata je ta wakilci Ahmad ita da Abban Marwan ga yarima Samaɗ' kuma nasan yan uwan mahaifiyar ku duk za su tafi kanon gara araba biyu..

Kinga Mamy zaki zauna ku amshi suruka..

Kuma kibada Yar ki..

Mamy ta ce haka ne Allah ya sanya Alkhairi ya nuna mana lokacin lafiya da ameen kowa ya amsa....

Wuni Ranar Yusuf Sani yaro

bincike ya wuni sossai a kan Sarkin Adalai '' amma ɗuk kasar daya duba babu shi babu me kama dashi...

Hakan ya sa ya shiga nauyin kasashen french dan yagani Ko ze dace..

Yabarshi a kan gobe tun da Asuba zefara gudanar da binciken sa kafun lokacin daya diba yacika....

Kusan Karfe biyar na yamma Dakarun sojoji suka ce gidan Maman Maryam..

Iske Abban maryam suka yi waje yana waya..

Cike da mamaki yake kallon motar sojoji ya yi parking kofar gidan nasa...

Kashe wayar da yake yi ya yi yadawo da hankalin sa a kan su dasuke durowa Daga motar sa..

Babban cikin su ne ya karaso gaban sa tareda cire madubin glas dake Idanun sa '' ya ce sunana Sulaiman gaba tare da nuna masa ID Card dinsa..

Munzo ne mu tafi da Hajiya Farida a kan zargin ta

Da ake yi tanada sa hannu wajen yiwa Shugaban Adalai sharri in kuna neman karin bayani kuzo office din mu..

Yanzu ina take ne...

Abban Maryam bakin sa na rawa ya ce tana cikin gidan ni Mijin ta ne..

Dan Allah kubari mu sasanta '' babban nasu ya ce zancen banza ka ga wasa a tattare damu ne..

Maza kayi mana jagora mu je ciki...

Babu musu ya bude gidan jikin sa na rawa yashigar dasu har cikin gidan...

Koda suka isa Falon iske Maman Maryam suka yi tana dukan Yar aiki kishiyar ta..

Yarinya tana ihu tana fadin wallahi hajiya zan bar miki gidan in koma kauyen mu...

Sake da baki sojojin suke kallon junan su suna kada kai...

Ganin ba ta gansu ba.

Babban cikin su ya ce hajiya ayi mata rai hakanan Ko..

Cak ta Dago kai cikin gigita take kallon sojojin da suka kewaye dakin nata...

Sakin yar aikin ta yi bakin ta na rawa ta ce ku kuma Daga ina haka....

Babban cikin su ya ce ina fatan kece hajiya Farida..

Kada kai ta yi Alamun ita ce......

Hajiya munzo mu tafi dake Umarni ne Daga Sarkin kwatano...

.

Cikin Rawar murya ta ce what.............

Taku Har kullum Kyauta Daga Allah9️3️

Ta ce what laifin me nayi muku..

Angwa suka nuna mata cikin tsawa ya ce wannan ma dukar da kike wa yar aikin naki shima ya shiga laifi duk da bamusan me ta yi ba amma hakan ya nuna duk cikin zalunci ne wannan dukar da ake mata....

KUKA tasoma tana kallon mijin nata ta ce Abban maryam dan Allah kace wani abu mana za su tafi dani..

Abban maryam ya ce Farida mezan yi musu bayan sunce sai sun tafi dake kije kawai zan zo gashi Maryam ba ta gida inta dawo zamu zo tare....

Hijab din ta ya shiga daki ya dauko mata tareda mika mata '' tasaka tana kuka ta ce na ba ni wayyo ni Farida Nice za a tafi dani gidan Maza...

Basu ba ta lokaci ba wajen sa mata ankwa ba hakan ya sa nan da nan suka jata har cikin motar su....

....

Fulani tana zaune cikin dakin nata gangami yazo mata da abinci' 'hade da ruwa bakin ta na rawa ta ce nagode gangami saura lemu....

Tsawa ya daka mata ya ce shegiya munafuka ai ana ba ni lemu inbaki shanyewa nake' ''

Badan ba a ba ni dokar zaneki ba dayau kinsha bulala..

Sossai take kuka ta ce waini yar kwalisa Nice ke kwana awannan dakin...

Gangami ya bushe da dariya harda rike ciki.

Ya ce sannu yar kwalisa '' bari ayi shari'a kigani inhar kotu ta daure ki..

Alkur'an saikin gwammance da nan fiye da cen shasha kawai yafice yabar ta yana wake waken sa hade da fito..

Yarima Samad mikawa Khadija wayar ta daya kwace ya yi tana ta murna ya ce uhmm yarinya bakisan aure zakiyi bane shi ya sa kike kaudi...

Afili kuwa fadi yake yawwa khadija ta '' zauna muyi magana....

Zama ta yi tana fuskantar shi ta ce yaya inajin ka.....

Ya ce khadija nasan kin san kaddara mekyau Ko mara kyau..

Khadija cikin sanyin murya ta ce nasani yaya tun da malamin mu '' yana gaya mana...

Jawo ta ya yi jikin sa ya ce yawwa yar ƙanwata..

Kin san yayan ki Ahmed zeyi aure kuma Asiya kawar Rahama ze aura..

Kekuma Adamu zaki aura dan abokin Sarki ambassador libya....

Arazane ta Dago kai tana kallon sa ta maimaita aure a fili.

Make kafada ta yi cikin kuka ta ce wayyo ni khadija yaushe nakai aure '' yaya kubari nakara girma wayyo Mamy banaso..

Kallon ta yake yana Murmushi da shikadai ya san ma'anar sa '' ya ce uhmm dijat dîna auren babu fashi banine na hadaba tsoho me ran karfe ne '' Inkinada ja je ki same shi.

Kawo wayar insaka miki lambar Adamun '' zan kira shi ince kinbude waya 'yakira ki' Wallahi inkika masa rashin kunya zaki sani..

. Khadija sossai take kuka wai ita ce za a ma aure kuma auren dole' 'mijin maci Amana' 'maganar zuci take ita kadai..

Ganin haka Yarima Samad tashi ya ce kinga zanshiga ciki ina Antyn ki..

Tana ciki ta ba shi Amsa atakaice koda ya shiga dakin iske ta ya yi zaune tana karatun Alkur'an ahankali muryan ta ke fita..

Samun wuri ya yi ya zauna kusa da ita...

Ganin zuwan sa ya sa tana kai karshen aya '' tayanke karatun '' Murmushi ta sakar masa mai sanya shi a gajimare...

Ya ce hubby karatu ake '' nazo bita..

Dariya ta yi saida fararen hakoranta suka bayyana '' habawa '' ai sai dai ka koya mun shugabana takarashe zancen tana kokarin tashi tsaye..

Kusan tare suka tashi '' cikin kallon da yake binta da shi 'mai wuyar fassara ya ce za a ba ni Ko..

Uhmm Amjad wai kai ba za ka barni in huta bane' 'ina fama da danka A'ciki na' kaikuma uba ka hanani sakat..

Uhmm Rahama ta ai duba lafiyar dan namu zanyi kema kin sani..

A'a ban sani be cewar dan haka ka kyaleni barci nakeji kace gobe zamu garin su Mamy sokake in tashi da gajiya ne.....

Uhmm Hubby duk wayon naki saifa nayi haka kurum yau kwana uku kenan ana jamin rai....

Dariya take ta ce wayyo Mamy zoki dauke ni a dakin Amjad 'sai ya cinyeni tass ya ajiye kashi....

Dariya ta ba shi harda rike ciki ya ce uhmm watau Mata ta ta yi baki' 'har kin iya fadin cinye wa...

Hakadai yajata suka yita hira be mata komai ba. amma tasha murza' ɗan yana kiyaye abun da likita ya ce a kan barin ta' tahuta har cikin jikin ta ya yi kwari....

Kashe Gari....

Tun da sassafe bayan yadawo Daga Sallah Asuba kiran Yusuf ya shigo wayar sa...

Yana ganin Yusuf ne cikin hanzari ya Daga...

Daga can ɓangaren ya ce' '' Yarima Samad na samo inda mahaifin ka yake yana kasar Gabon..

Cikin ruɗewa Samad yake maimaita Gabon '' ya ce tome yakai sa wannan kasar kuma a Gabon din wani unguwa yake.....

Nan da nan Yusuf ya tura masa duk wani bayanai na gidan da yake ciki.....

Ya ce masa a yau dinna za su je daukar Saratu amma Yaran sa '' ze tura ''

Yarima Samad cike dajin dadi ya ce ina son a ajiye mun ita a kano innazo bikin Surukina da Kanina zan tare da ita zamu tafi kwatanon ka ga shari'a ze tafi daidai

Yusuf ya ce kar ka damu yau InshAllah za a je a dauko ta kuma zamu ajiye maka ita a kano..

Godiya Yarima Samad ya shiga yiwa yusuf tare da masa Adua Allah yajikan baban sa da wan sa da magabata '' yusuf ameen ameen ya furta Daga haka suka yi sallama..

************************

Kano

Dakarun sojoji mota daya suka tafi unguwar rijiyar lemu '' gidan wani Alhaji mai naira '' nan gidan Saratu take zaune basu ba ta lokaci ba..

Kai tsaye suka nufi gidan '' bindigogi da suka nunawa yan cikin gidan ba ƙaramin razana suka yi ba..

Babban su cikin zazzare idanu ya ce Ina Saratu take..

Baki narawa matar megidan ta ce tana kwance daki tana barci......

Cikin tsawa ya ce ina dakin yake ?

Nuna masa dakin ta yi da yatsa hakan ya sa su uku suka nufi dakin '' hankada kofar suka yi da kafafun su '' koda suka Shiga dakin sai dube dube suke suka hangota kwance tana buga uban munsharri bakin nata abude tama mance inda kanta yake...

Da bindiga suka tashe ta Arazane ta tashi tana salati ganin sojoji har uku a kanta kokarin ta yi magana take..

Babban ya ce kitashi mu je inmunje cen kin karasa barcin naki...

Cikin Rawar murya ta sauko Daga kan gadon tana neman hijab din ta..

Ta ce dan Allah menayi muku ne..

Anturo mu ne Daga shugaban sojoji Yusuf Sani Yaro...

Jin anbanci yusuf hankalin ya yi mugun tashi tasan case din baƙarami bane Sam ta mance da batun Masarauta na neman ta '' shi ya sa batakawo Ko su bane...

Sata gaba suka yi 'cikin izza suke suna mata hanyar da zatabi..

Matar megidan baki na rawa ta ce ranka ya dade inane zaku kaita in mun tashi..

Babban cikin su ya ce kika zo sunan ki sorry zamu hada dake mu rufe..

Jin hakan ya sa ta ja bakin ta ta yi shiru suna kallo suka tafi da Saratu 'cike da izza da takama......

Unguwar makil yake da jama'a ganin yanda suka jefa saratu cikin mota..

Gulma ya barke a unguwar' Wasu na fadin wannan matar Kodai yar damfara ce kullum dai sai dai muka tana fita asirrince'' kuma sai ɗare.

Na kusa dasu ya ce Falyakul khairan auliyas mut.

Mudai bamusan dalili kamata ba Koma daidai mene ne Allah yakyauta da Ameen kowa ya amsa..

Suna kallo motar tabar unguwar.

Ayau ne su Mama da anty suka tare sabon gidan nasu.

Sabon fourniture sheik ya yi masu..

Yan uwan da a bokan arziki kowa yazo yana ta kallon gidan' 'sake da baki ake ta yaba kyau da tsaruwan gidan...

Mama ta cewa Aminiyar ta kinga Sheik yanzu ya fara sakar mana mara muyi fitsari' 'ai wannan gidan shi ne gidan sa na farko daya fara siya a' kano..

Amma ya ajiye mu acen gidan Duk da cen din ma babu laifi....

Aminiyar mama ta ce kedai Aisha kibar zancen wani gida'' ki dawo da hankalin ki kusa' auren sheik befi saura sati daya ba za a ce me kika shirya koko kin zuba idanune wata takara zuwa ta kwace miki miji...

Daga Sama ta jiyo muryan Sheik na Fadi ba idanu ta zuba ba har kafa..

Ahankali yake taku har ya iso gaban nasu..

Cikin hada Fuska ya ce uhmm ke Suwaiba kike Ko Sharifa nakasa haddace sunan ki...

To bari kiji duk abun da kuke ina sane gidan yan bori da gidan malamai duk ina sane Kallon ku nake ita Aysha da yake sakarya ce bagidajiya takasa gane me son ta..

Yo mai son ta mana.

Taya kullum kike barin gidan ki kina zuwa tarwatsa mun nawa...

Sossai Suwaiba ta tsoro ta ganin yanda Sheik yakoma kamar wanda ze buge ta..

Wallahi Daga yau na rabaki da Aysha mata ta kuma inna kara ganin kafafun Ki nan gidan uhmm basai na fada ba..

Kekuma Aysha wallahi kika kara zuwa gidan ta koda satar hanya ne inhar nasani nidake har Abada mun rabu inbanda jahilci da biye biye ake samun kan miji '' kiyi biyayya kigani in baki rabauta ba..

Kullum kina yawo da zani daban riga daban '' babu kitson kirki bare burgewa '' kullum babu gyara ahaka kike son maganin bokan naku ya yi aiki...

Sannan kina maganar cikin mata ta Sa'adatu zaku zubar Ko uhmm tun da kune kuka busa musu rai to sai ku kashe su kar nake kallon ku..

. Aysha ina hakuri dake bakya ganewa wannan auren Saboda ke nayarda zanyi shi da inajin dadin zama dake tabbas babu auren da zan kara '' itako Anty ba ta iyawa ita kadai kekuma kinyi sake dan Allah gyara kanki nace ki gyara kanki...

Sassaita nutsuwar sa ya yi yana kallon Suwaiba ya ce yanzu kina iya tafiya Ko na sallame ki babu ke babu indo....

Cike da Jin kunya Suwaiba ta rinƙa rabawa ta gefe gefen gidan tafita tana fadin amma mutumin nan ya shammace ni..

Millions daya kacal na samu hannu aisha na so insamu suka yi goman..

Amma bakomai dankoli yaci riba tafada cike da takaicin rabasu da sheik yayi...

Tana Fita yadawo da kallon sa a kan Mama da ta yi kasa da kai ya ce ke indo ina rabaki da kawayen banza bakyaji Ko uhmm ta yaro kyau take ba ta karko..

Yana fita gidan kai tsaye kofar gida ya je ya samu waje yazauna tare da bude WhatsApp dinsa..

Ganin Sakon hassana ya shigo..

Ta rubuta..

Haba Masoyina uban yaya na muna hira najika shiru uhmm my love kaifa nake jira kayi shiru kafa San auren namu yau saura sati uhmm...

Murmushi ya yi yana karanta sakon ta...

Voice ya yi mata ya ce habibity na yi hakuri na dan je gun uwargida ne.

Kin san ku Mata '' saida kulawa...

Tabe baki ta yi tare da rubuta kace kana gun Babban antin tamu yaushe za ka hadani da ita...

Sheik ya rubuta kibari dai kizo yanzu kanta yadau zafi anata hada hadan tarbon Ki gimbiya ta..

Sossai ta dara Daga kwancen da take '' ta ce masoyina ya ce naam habibity inajin ki...

Nifa in ankawo ni gidan naka ka san me..

Ya ce A'a saikin fada habibity na..

Ni dai ranar dazan tare dakin angona uhmm sujjada zanyiwa Allah dan godiya ingayamaka sati daya za ka dauka ba ka je aiki ba...

Shafa gemun sa ya yi yana murmushi ya ce habibity na inban je aiki ba sokike su Sa'adatu suce dadin angon ci ne yahana...

To mene ne da sun fada babu komai fa ka san wata bazawarar tafi budurwar wallahi...

Sossai ya dara ya ce kash habibty lokacin Sallah ya yi zanje ba da Sallah saide zuwa ɗare bayan isha'i kafun na kwanta zamu hade yau fa dakin Uwargida nake dakin nata ba a waya fa..

Sossai ta dara ta ce ayya nima nakusa mallakar ka ka ga babu me hana Jin ka ranar kwana na...

Sheik ya ce haka ne habibty bye sai anjima inmun hadu...

Mama Sheik na fita tarusa uban kuka ta ce shi ke nan yarabani da suwaiba kuma ya san sirrina yazanyi ne...

Uhmm Wallahi zanfara adu'a ina hana idanuna barci a kan Allah ya tarwatsa wannan auren itakuma Sa'adatu Allah ya sa kada ta haihu lafiya........

Anty ce suke saukowa Daga sama ita da yan uwan ta cike da farin ciki ta ce Kunga ga Maman salma cen ku gaisa..

Cike da farin ciki suka taho gun mama '' yayar anty da kanwar ta suka ce Maman salma inawuni dafatan kuntare lafiya to Allah ya sa kundawo Asa'a..

Mama dariyan dole ta yi ta ce Ameen ameen har zaku wuce ne..

Suka ce eh zamu tafi munga gida ya yi kyau sossai musamman sashin naki ya fi daukar idanu..

Mama ta ce kai haba wai dagaske kike hindatu..

Kwarai kuwa wllh dagsk muke suka karashe zancen tare da fita...

Mama bakinta awashe sun yabi sashin nata ta ce Allah yakaiku gida lafiya...

Cike da mamaki Anty ta yi Jin furucin Mama duk zaman da suka yi ba ta tabajin ta yi adua mekyau a kanta Ko yan uwan ta ba...

AMEEEN dukan su suka amsa.......

*************************

Salma zaune take tana shirin zataje gidan iyayen ta..

Kai tsaye motar da Al'amin yasiye mata ta bude ta shiga.

Mai gadi bude mata get ya yi cike da takama take tuki tare da hawa kan titi... Tuki take tana kada kai cike dajin dadi wai yau ita ce da motar kanta uhmm nasan Matar Samad ba ta da mota... Uhmm innaje ma zanje gun Abby in karbi kudin da shegiyar ta ce abani Ko mai na rinƙa sawa mota ta....

Asiya tsaf tashirya itama dan zuwa sabon gidan su Mama' ita da mahaifiyar ta zuwan su ya yi daidai da isowar Salma sake da baki suke kallon wacece wannan tazo a bakar mota '' duk da ba sa gani sossai amma sun tabbatar wannan tukin mace ce..

Asiya sake da baki take kallon Salma dake kokarin fitowa cikin motar tana sanye cikin doguwar shadda gezner ta yafa farin gyale hannun rike da ash din jaka da takalmi hash mai tsini' simple makeup ta yi hakan ya sa ta yi kyau ta yi fresh.

Asiya fuskar ta dauke da mamaki ta ce Kai Salma kece

Rufe motar nata ta yi tare da karasowa kusa dasu '' ta ce Uhmm anty Asiya kenan ke bakisan nayi nisa bane nawuce raini ba..

Asiya ta ce uhmm Salma ba ni labari arziki mijin naki yayi..

Salma tabe baki ta yi Anty Asiya ai nima dawowa nayi na iske Al'amin ya yi Arziki..

Asiya ta ce Kai salma wani irin aiki Al'amin ya samu ne...

Salma ta ce inaruwana da aikin da yake yi ni dai kawai daula muka samu '' kudai yan bakin ciki bakwa ganin mutum yaci gaba saiku ringa neman mugun suna suka daura masa...

Asiya ta ce haba Salma meye abun bakin ciki dannace meye sana'ar Al'amin '' kina matar sa bakisan aikin sa ba mekenan akai..

Allah yabaki hakuri Salma Allah yakara arziki da daukaka..

Ameen ta furta inda gaske kike dan keda Rahama mugun hali gare ku..

Asiya barin Salma ta yi tana tabe baki tare da yin cikin gidan tabi sahun maman ta...

Salma na kokarin shiga cikin gidan...

Sheik ya dakatar da ita tahanyar ihun kiran ta..

Cak ta tsaya tana kallon sa harya karaso..

Ya ce yanzu Salma gyale kika koma yafawa ina hijab dinki Ko ba ki da sune kar inkara ganin ki cikin wannan shigar ta gyale..

Naji labari acikin gari wai mijin naki ya sai gida da mota surutu ake mun ba a San sana'ar sa ba..

Ba za ki shiga mun gida ba harsai kin fadamun meye sana'ar da mijin naki yake...

Maza juya ki wuce inajin Asiya tana miki magana harda zagin ta dan ta gayamiki gaskiya to badaniba ba.....

Cikin kunan rai da tafasar zuciya salma ta juya tana kuka ahaka ta ja motar tata tawuce gidan nata..

******************

England

Adamu ne zaune yana chattin da khadija wacce Da ƙyar take maido masa reply..

Ya ce Amarya ta yakike ygida ya antyn ki Rahama da yayan ki Samad...

Lafiya lau suke ta ba shi Amsa atakaice...

Adamsy cike da Jin dadi tamasa reply ya ce yawwa Amarya nan da kwana uku zamu zo kwatanon nida Abba na...

Lefe kuma jibi yan uwana za su kai sai su jira sai andaura sai su koma...

Shiru ta yi tarasa mezata ce masa...

Khadija ya furta hakan ya sa ta kara maida hankali a kan wayar ta ce naam...

Wai naga kin kasa sakin jikin ki dani kona miki laifine dan Allah ki gayamin...

Cikin yin kasa da murya ta ce to bakai bane wanda ya fasa auren.........

Taku har kullum kyauta Daga Allah9️4️

09069080725

Toba kai bane wanda yafasa auren anty Rahama ba '' sokake in saki jiki da kai nima kazo kace kafasa Ko.

Sake da baki Adamu yake sauraron ta ikon Allah ya furta afili sannan ya ce haba khadija waye besan kaddara ba..

Haka Allah yatsara tun farko niba mijin ta ne bane '' ki fahimceni kuskure ne yariga ya faru 'badaman ayi tariya bare a gyara shi..

Shiru khadijat ta yi tana sauraren sa' 'cikin takaita zancen ta ce Allah yakyauta..

Ameen ya Amsa mata kokarin yajawo hankalin nata yake dan ta sake da shi sossai..

Haka dai ya lallabata suna hira.......

Yarima Samad makale da Rahama a la dole shi ne ze saka mata kayan ta kala biyu da zata saka a jakar ta..

Uhmm Amjad dîna kabari na saka mana '' ka ga kwana zamuyi Ko..

Haba hubby na ni ne nadace da in zaba miki kayan da zaki saka.

Cike da mamaki take kallon sa ya fiddo mata tare da shirya su tsaf a jakar ta..

Cikin marairaice fuska ya ce baby na adan taimakamin na kwana biyu ban taba ba...

Rike da baki take kallon yanda yakoma kaman ƙaramin yaro yana kokarin cire mata riga..

Kasa hanashi ta yi '' ganin haka ya sa yakara azzama wajen isar da sakon shi..

Awannan ranar dai ahankali ya gudanar da komai wai kada babyn shi ya wahala..

Rahama kam 'sossai hakan da ya yi ya mata dadi' kusan a tare suka yi wanka.

Bayan sun fito 'suka sake yin sabon shiri' inda Rahama ta sanya babban leshi na malaysia har wani shaining yake.

Dinki riga da zani sossai ya karbe ta ka sancewa Milk color..

Shima Yarima Samad irin wannan less din ya sa an yi masa aiki da Milk din zare rigar iya gwuiwar sa ta tsaya sossai shigar ta masa kyau ga hular sa yadaura Milƙ' cikin hanzari ya sako takalmin sa haf cover tare saka farin glass..

Sake da baki Rahama ke kallon sa ta ce wannan kwaliyar fa '' yau shirin yarbawa kayi..

Mukayi dai zaki ce yabata amsa a atakaice.

To na ji mukayi amma dai nasan harda yan mata za ka nunawa wannan adon naka...

Uhmm Keko Hubby yan mata me za su yi da mijin naki '' wanda Sam ya makance a kan son ki.

Ko sun shigo wahala za su sha ɗan kwalliya bazata biya kudin sabulu ba.

Tabe baki ta yi tana dariya uhmm Amjad anya kuwa' kana samun sabuwa cewa zakayi ai aure kaddara ce waya mutu Waya dawo..

Hubby na kenan tun da Abbana beyiwa Mamy kishiya ba' Kema haka ba zan miki ba...

Kai kai ni dai Amjad banson daukan AlKawari da ba za ka iya cikawaba..

Nifa inma auren za ka kara kasamo mai hankali wacce zamu zauna lafiya' ɗan ma dai Ahmad ya yi mana shigo ba zurfi Asiya na so inbaka ka aura' yanda zamu hade nida Aminiyata Ko bayan raina inada tabbaacin Asiya zata rike mun yayana bisa Amana...

Dariya ya sakar mata tare da lakacar mata hanci 'uhmm hubby na Keko'' mubar zancen Allah babu ke babu kishiya tun da na ji m'a kinaso..

Dariya ta fashe da shi ta ce au kana nufin daman mata dan suna nuna basu son kishiya shi ya sa ake musu..

Eh mana dan muga iya gudun ruwan su'' da kuma mu ragewa kan mu wahala..

Sossai ta dara hakan ya sa ya yi Murmushi ya ce wife naci gari fa kin san kalmar da kike min rowa kuwa..

 Girgiza kai ta yi ta ce A'a maigida na saika fada..

 Baki taba furta mun kalmar je taime 💜 Ma'ana ilove you..

Rufe fuskar ta ta yi da tafukan hannayen ta ta ce uhmm kaima ai ba ka taba gayamin ba' saini ce mara aji..

 Haba Hubby me abun rashin aji anan bayan 'nasan komai tattare dake ina kwanciya dake..

 

Sake da baki Rahama take kallon sa ta ce uhmm nifa haryanzu ban yarda kana sona ba..

Kaga mu je inmun dawo mun karasa zancen' '

 

 Please hubby matso kusa dani ki gayamin kalma me tsada tare da rufe idanun sa' 'hannayen sa ya bude Alamun tazo' ganin haka ya sa tafi ce zuwa falo.

Koda ta fito falon iske khadija batanan Faruk da Aminu ta tarar zaune suna jiran sa....

 Faruk bakin sa dauke da Murmushi ya ce Amarya bakya laifi ina Yarima yake ne..

 Murmushi ta sakar musu tare da gaishe dasu.

Uhmm yana ciki tafada atakaice tare da zuwa sashin nata..

Ganin tafita zuwa ɓangaren ta ya sa Faruk fadin kai Aminu bara inleka wannan dan Iska shi kadai ake jira yana ba ta mana lokaci...

 Koda ya shiga dakin iske Samad ya yi Idanun sa arufe yana fadin haba My Rahama kizo ki rungume ni 'mana nace miki wannan kalmar zaki fada min in samu sukuni...

 Rike da baki Faruk ke kallon sa yana Murmushi ya ce a zuciyar sa wannan yaron an yi jarababbe wallahi..

 Ganin Samad na kara bude hannun yana wani karya murya oya matso nan hubby' tun da ba za ki zo ba' 'bari ni inje'..

Aguje yakaraso wajen Faruk yarungume shi..

Jin kamar ya rungimi kato beji dukiyar Fulani ba '' ya sa shi bude Idanun cikin Sauri...

Caraf Idanun su ya tsarke cikin juna shida Faruk....

 Zazzare idanu ya yi ya ce wai Allah dan iska me kakeyi anan wannan ai daukan Alhaki ne...

 Faruk dake dan gyara rigar sa da Samad yajawo dan runguma ya ce akwai dan Iskan daya kaika ka kwana daki daya da mace amma kuma ba muda sukuni Kodai za ka fasa tafiyar ne Malam Tabe Tabe...

 Tsaki Samad keta jerowa ya ce kash wannan game over na buga.

Amma bakomai zan rama ne na ji din ni Tabe Tabe nake kaikuma fa..

 Kai bara kaji ingaya maka nidin nan uhmm.

Fadi mana cewar Faruk yana kallon kwayar Idanun sa..

Kawai abar zancen da na so in maka Rashin M.

 

Faruk ya ce ni yanzu akwai rashin mutunci da ban sanka da shi ba..

Ni dai maza ka fito mu je tabe tabe..

Kuma na ji Karima ta ce da ita za a..

Yarima Samad ya ce eh da Karima Za a je tama kusa barin Masarautar nan ita da Iya Firdausi...

 

Faruk ya ce Saboda me zatabar masarautar nan yarinya mai hankali.

Ka yantata ne ?

Shiru Yarima Samad ya yi ya ce Karima ba baiwa ba ce ''

Zazzare idanu Faruk ya yi ya ce kamarya kenan fahimtar dani...

Samun wuri suka yi bakin gadon nasa suka zauna suna face din juna..

Kamar yanda kaji nace maka haka zancen yake Karima ba baiwa ba ce...

 

Diya ce ga shugaban Kasar Niger.

Mahaifiyar ta

Mata ce ga shugaban kasa...

Faruk cikin Razana ya ce Samad kai za ka warware mun wannan maganar ta matukar daure mun kai...

Wayar Yarima Samad ne ya fara ring yana dubawa yaga Mamy ce...

Yasan fada zatayi a kan su kadai ake jira..

Uhmm Faruk kabari inmunje bohicon zanbaka tarihin Karima yanzu ga Mamy na kira babu lokaci tashi muje...

 Tashi suka yi suka fito iske Aminu suka yi hankalin sa ya kar kata a kan TV..

 Ganin fitowar su ya sa ya Mike ya ce kai Faruk meya rikeka daga za ka kirashi..

Jikin Faruk a mace yake Jin wannan zancen a kan Karima..

Babu komai Aminu mu je Ko yafada asanyaye...

Samad ihun Kiran Rahama ya shiga yi..

Aminu ya ce yanzun nan tafita da jakar ta dan haka mu tafi kawai...

Koda suka iso Rarfajiyar Mamy na ganin Samad tasoma Fada..

Ta ce haba kai kullum in za a je inguwa da kai sai rai yabaci tun dazu ka shanyamu har Rahama ta gaji da jiran ka... Ta fito ta barka ciki.

Kwantar da kai ya yi Alamun ban hakuri ya ce natuba Mamy.

Babu ba ta lokaci suka ɗau hanyar zuwa bohikon dukan su harda su Faruk da Aminu da Karima 'su Khadija ana Murna za a je gun kaka ziyara..

Samad Sam beso Rahama ta shiga motar su Mamy ba..

Ba haka yaso ba..

Faruk duk jikin sa a mace tun lokacin da Samad yasoma bashi labarin Karima..

So yake ya kalle ta dakyau'' cike da mamaki..

Aminu Da Samad kadai ne ke fira a motar su biyu ke bayan kujerar mota..

Faruk na Tuki Ahmad nakusa da shi a gaba..

Shi Ahmad murmushi yake a kan Asiya Sam haryanzu Ko waya betaba hadasu ba..

Yana lissafin yanda zeci gidan ta badai shi ta zaga

Wata zuciyar ta ce Anya Ahmad yin haka ba kuskure bane 'inka sake ta za ka samu matsala da iyayen ka kuma ka basu' kunya..

Tabe baki shiyakadai yana maganar zuci ya ce uhmm to koda na saketa din Ko sunyi fushi na kwana biyu ne za su huce...

Samad dake kallon keyar Faruk Ya ce kai kabi damu a hankali fa kar ka jefamu cikin rami kajawa mata ta asara...

Darawa Dukansu motar suka yi harda Ahmad.

Aminu ya ce kai Tabe Tabe tun da kayi aure shi ke nan ba mu da ta kan mu ka ishe mu ka gallabe mu..

Nima dai auren nan zanyi inhuta haba dan Allah..

Faruk dake murmushi yana Tuki ya ce meye dan mun mutu iyaka dai ta yi maka takaba da ankwana biyu ta samu wani mijin ta aura...

Sossai Yarima Samad ya Girgiza Jin wai zata samu wani mijin ta aura.

Ya ce dan bakin cikine kai Faruk ta Allah ba takaba ga Kabari na ga na Rahama InshAllah tare zamu mutu..

 Sossai suka ɗara haka suka yi ta fira har suka isa garin bohikon....

Kai tsaye gidan Liman Ahmad suka nufa..

 Iske shi suka yi waje yana koyar da dalibai.

 Ganin motocin su yaga tambarin gidan Sarauta ya san eh lallai bakin kwatano ne suka iso.....

 

Nan da nan ya sallami dalibai tare da koma ciki..

Koda suka iso.

Parkin space suka paka motocin su...

Lale Lale Lale cewar *Iya Gari* kakar su Samad wannan sunan ake kiran ta agarin Asalin sunanta Amina....

 

Samad bakin sa dauke da murmushi ya ce Iya Gari lallai matar nan bakya tsufa..

 Tabe baki ta yi ta ce taya zan tsufa kuna ta dankaromin kishiyoyi harda maigida na Ahmad shima kishiyar zemin..

 Dariya suke nan da nan suka nufi masaukin su..

 

 Firdausi Autar su Mamy ce ta fito Daga dakin ta aguje tanufo Mamy ta rungume ta '' ta ce anty Habiba kin zama me iyali.

Kallon Rahama take wacce suke gaisawa da Iya Gari tana mata tsiya a kan ta kwace mata miji....

 Firdausi ta ce kai kai wannan ce Matar Samad kamar nasan fuskar nan..

Rahama juyawa ta yi tana kallon Firdausi ta ce '' la la anty fiddo kece..

Sossai Firdausi ta rungume ta '' ta ce Rahamatullah wai dan Allah dagsk kece matar ɗana '' shiru ta yi tana murmushi..

Yarima Samad ya ce Mama firdausi kin santa ne..

Kwarai kuwa nasan Rahama Abdurrazak.

 Mun hadu da ita Asaudiyya ita tana karatu ne''ni kuma munje umra' sossai ta ringa koyamin karatu Katuna wataran muna waya da kai lokacin inacen' 'har nacemaka wallahi wata yar karamar yarinya ta burge ni sossai ga tarin ilimi a kan ta har daurani take a kan karatuna' nace maka 'nima da Allah zai sa yata Aisha zata zama kamar ta danaji dadi.

Kacemin ai abun rabone da dagewan iyaye...

Yarima Samad cike da Jin dadi ya ce kwarai kuwa natuna ashe ita ce uhmm Allah ya yi kunsake hadewa' a matsayin yar ki..

Mamy cike da Jin dadi ta ce MashaAllah abu yayi..

Wai ina yaya Auwal ne.

Da Sani..

Bata gama rufe baki ba sai gasu '' sun taho harda baban nasu...

Cike da. Jin dadi suka kara gaisawa da mamy.

Abban su sossai yaji dadin ganin su.

Ya ce yau dai Samad yazo mun da Amarya kuma babu wanda ya isa yatafi da ita..

Yarima Samad sossai ya ɗara ya ce uhmm banga kana aiken kudin cefane ba..

Liman Ahmed kallon Rahama ya yi ya ce ke Rahama kullum bakina Jin alert awayar ki ba..

 Cikin zazzakar Muryan ta ce Ko yanzu ma sun shigo kudin.....

 Gabadaya dakin dariya suka sa...

 Bayan sunyi ciye ciye dukan su..

Rahama tabi Firdausi zuwa dakin nata..

Sossai Samad ya takura..

 

Sai bayan Ish'ai Liman Ahmad yakira dukan yayan sa harda Su Faruk da Aminu Samad da Ahmed.

 Cike da nutsuwa kowa ya zazzauna kasa.

Ya ce yawwa game da maganar Farida ne..

Gaskiya yarinyar nan ta cuceni ta cuci kanta nabata tarbiyya Allah ne shedata' kuka yake sossai ya ce shi ne zata janyo abun da ze ba ta martaban gida ni Liman.

Duk hukunci da Aka zartan a kan ta babu ruwana wlh ita tajawa kanta..

Sannan zancen Maryam zata dawo nan hannuna tun da mahaifiyar ta ba ta gida Kuma na ji ance uban nata ya yi aure..

Auwal ya ce haka ne gaskiya gwamma ta dawo hannun ka.

Zatafi samun kulawa kuma zata nutsu..

Sannan maganar mijin Habiba da baya kasar nan shekara shidda.

Anya wannan zaman me billewa ce ba na son abun da ze kawo mace ta fada halaka..

Dan haka asan abun yi...

Yarima Samad ya ce Liman mun gano inda yake..

Nan ya shiga bawa liman labarin abun da ya faru a masarautar da dalilin barin gidan nasa dakuma inda yazauna ɗakuma inda yake ayanzu..

Sossai Mamy ta Girgiza Jin wai aikin gadi ya yi agidan su Rahama....

Kuma yana da masaniya a kan inda yake amma be sanar mata ba..

Tabe baki tana kallon shi

Ta ce kai Samad ka san inda yake shi ne ka bar ni a duhu.

Kuma har gidan su Rahama yazauna Daga kai har ita babu wanda yataba faɗa min..

 Yarima ya ce ita kanta Rahama batasan shi ne ubana ba saida taga hoton sa..

Kuma kin san ba ta da surutu ba ta fiye magana ba..

Inhar ba annemeta da zancen bane..

Firdausi ta ce haka ne Tome zata ce miki kina uwar mijin ta..

Faruk ya ce gaskiya ne kam bazata ce komai ba Inde Rahama ce..

Nan. Dai. Fira ya bârke tsakanin su

Liman ya ce maryam gobe yake so ta taho bohikon din in bikin khadija ya tashi taje tadawo....

Sun zauna suna ta tsara yanda za su yi shagalln bikin Ahmad da Khadija..

Kwanan su uku agarin duk dangi saida aka zazzaga da Rahama '' masu zuwa ganin ta kuwa makil ka sancewar ta diyar sheik Abdurrazak....

Karima kuwa sossai ta rinƙa bin Rahama duk inda zata sa kafa a garin.

Duk yanda Faruk yaso Samad ya ba shi labarin Karima abin yaci tura yabar shi sai sun koma kafun su tafi Kanon ze matsa masa dan yaji labarin komai..

Koda Maryam ta iso bohikon Liman Ahmad '' cikin Almajiran masu daukar karatu wajen sa ya yi masa AlKawarin bashi auren Maryam 'sa daki da iyayen sa kawai yake bukata..

Maryam ta yi kuka harta godewa Allah yanzu ita ce aka ba da auren ta kamar mara yanci' uhmm.

IYA GARI NAN NAN TA RINƘAYI DA Mamy da Rahama '' ita da yayan ta firdausi da Auwal da sani..

Suma sunce za su je biki.

Amma iyakar kwatano.

Rahama tasamu kyautuka agun yan uwa da a bokan arziki....

Karfe biyu suka baro garin cike da kewa....

Sai bayan la'asar suka isa kwatano da yake babu nisa sossai.....

Suna isa gida.

Kai tsaye kowa ya yi sashin nasa...

Faruk hango Karima ya yi tana ta buga uban sauri zata wuce dakin nasu..

Muryar sa ta sinkayo yana fadin dakata dan Allah....

Cak ta tsaya gaban sa cike da ladabi ta ce naam yaya Faruk gani...

Kallon ta yake cikin idanu yakura mata idanu 'sossai ganin mugun kyawun ta dabe taba lura ba saida ya firgita shi yau ne karo na farko da ya yi mata kallon tsafta...

Kallon da yake bin ta da shi ya yi yawa hakan ya sa ta ce uhmm yaya Faruk inajin ka kayi shiru sonake inje in yi sallah...

Dawo da nutsuwar ya yi ya ce yawwa Karima.

Daman ke yar Shugaban Kasar Niger ce..

Cikin zazzare idanu take...........

Taku har kullum kyauta Daga Allah9️5️

09069080725

Cikin zazzare idanu ta ce ina kaji wannan zancen..

Sake da baki take kallon sa zuciyar ta na tsananta bugawa..

Murmushi ya yi ya ce yanaga duk kin rude Daga tambaya..

Daga bakin dabe mun karya na ji kema kin sani..

Shiru ne ya ratsa na wasu dakiku ta ce kabari shugaba na inyabani izini zan gayamaka..

Tabe baki ya yi ya ce nima ai shugaban naki ne nida shi duk daya ne Karima...

Haka ne yaya Faruk '' to kabari zuwa dare na nutsu inka dawo zanbaka labari...

OK to Allah yakaimu ya furta tare da barin wajen itakuwa tawuce cike da mamaki ya akayi Yarima Samad yagaya masa.

Bayan Isha'i kuwa sai ga Faruk yakara dawowa wannan karan Gun Samad yatafi direct.

Koda ya isa sashin Yarima ya iske shi zaune a falon sa shikadai système na gaban Idanun sa sanye yake da medical glass.

Yayi zurfi acikin aikin da yake yi hakan ya sa beyi saurin Jin Sallamar Faruk..

Dafashi ya yi ya ce kai Tabe Tabe wai aikine yatashi haka..

Dago kai ya yi yana kallon Faruk ya ce kai yada zuwa gidan masu aure awannan time din..

Faruk darawa ya yi ya ce na ji dai dan iska gunka nazo.

Bismillah Samad ya ce yana nuna masa wajen zama..

Hakan ya sa Faruk y azauna yana fuskantar Samad dake kokarin rufe système din sa..

Uhmm inajin ka kazo ne a kan tafiyar mu Kano ne..

Faruk ya ce Duka dai amma abu na farko shi ne kaban labarin Karima daka fara ba ni munje bohicon kaki karasa mun sauran bayanai....

Yarima Samad cike da mamaki yake kallon sa ya ce kai kai yanzu kan wannan zancen kasa harna rufe système dîna ban gama aiki ba..

To meye dan karufe système din kai din ma ai gulma ce bawai aikin zakayi ba...

Ni dai gayamin kaine saurare..

Idan naki gayamaka meze faru ne ya tsare sa da idanu..

Uhmm Aikuwa inkaki gayamin babu inda zanje kuma wallahi ba ka isa ka tashi Daga nan ba.

Zanga ta inda Rahama zata ganka..

Jin haka Yarima Samad ya ce uhmm tun da kace haka zauna inbaka labari nasan ba mutunci ne da kai ba saika aikata abun da ka fada din yanzu ni nayi hankali banson banje naga sahibata ba...

Kamar yanda nagayamaka Karima ba baiwa ce diyar shugaban kasar Niger 🇳🇪 ce..

Shugaban Adalai ya ce kasar niger wajen wani taro da Aka gudanar na sarakuna..

Bayan anwatse taron gidan Shugaban kasar ya sauka maimakon Hôtel.

Cewar shugaban kasar Alh Salihu yawuce zama hôtel Saboda irin Adalcin sa.....

 Bayan ya isa fadar shugaban kasa ya samu masauki me kyau cike da kulawa...

Koda shugaban kasa yazo dan zantawa da shugaban Adalai..

Zama suka yi ya rinƙa tsara masa yanda ze tafiyar da mulkin sa ba tare da hakkin kowa ba..

 Sossai shugaban kasar Niger yaji dadin jawabin sa kuma ya gamsu da duk hujjojin daya bashi...

Suna zaune suna tattauna suka ji ihun Iya Firdausi ita da Karima ɗaman Shugaban kasar ya saba Jin haka...

Shugaban Adalai ya ce suwaye ne suke wannan ihun kamar mata..

Shugaban kasar ya zabga tagumi ya ce wallahi tun da wata Kanwar ta tazo gidan sabani yashiga tsakanin su a kan ba ta sakar mata kudi' amatsayin ta na matar shugaban Kasa ita Firdausi nuna mata take saina ba ta sanna itama tabata amma kanwar Sam taki fahimta ta ce Ko motar hawa ba ta da shi amma yayar ta tana hawan na million dari.

Aranar dai da suka yi wannan fadan ina falon.

Karshen zancen ta gayamata InshAllah saita zama abun gudu Kuma daulan sai ya gagareta indai sunan ta Asma'u zata gani..

In gayamaka adaren ranar ihu suke ta ita da yar ta Karima.

Har suna neman hanyar guduwa subar gidan dan akwai securite hakan ya sa basu samu dama ba...

Yanzu shekara daya kenan suna cikin wannan yanayin har yanzu *Kanwar ta* ba ta tako gidan ba...

Iyayen ta duk sun rasu daman su biyu suka rage sai dangi da abokan arziki.

Amma rufe matsalar nan nayi kan duniya ta dauka shi ya sa ban shiga nemar musu magani a kasar nan ba...

Sossai Shugaban Adalai ya jinjina wannan Al'amarin ya ce bakomai ba ce illa cutar hauka ne yake son ya kama su..

Inka amince zan tafi dasu kwatano acen zan musu magani har su warke '' kuma zankaisu ne amatsayin bayi amma zanwa mata ta da yayana bayani sunsan ba bayi bane..

Yin haka zecire Idanun mutane a kan su.

Sossai shugaban kasar Niger ya yi naam da zancen nasa..

Kuma ya ba shi shawara yakara aure dan wannan za a dade Ana nema musu magani....

 Wannan shi ne dalilin daya shugaban kasar Niger yakara aure..

Akayi ta cece kuce kanwar ta ta.

Tayita farin ciki an saki yayar ta tashi ga duniya.

Wannan shi ne takaita cen tarihin Karima da iya Firdausi.

Ni Samad ni ne nan yasha dawainiya dasu wajen nema musu magani har bohicon nakai su gun liman bohicon shima ya yi iya nashi kokarin har suka samu waraka...

Yau befi Sati daya da mukayi waya nida shugabar kasar a kan maganar yana son iyalin nasa su dawo '' saina ce masa yabari ayi bikin khadija..

To ya amince da magana ta dan haka zezo daurin aurenn khadija kwana uku kacal zeyi tare za su koma wanda hakan ze Girgiza makiyan su...

Duk da ba sa waya amma kullum yana bibiyar lafiyar su kuma yana adua Allah ya bayyana Sarkin Adalai..

Kafun nayi aure har cemin ya yi wai in inaso na auri Karima mana..

Ni kuma nace masa Kanwace na dauke ta inada wacce nakeso..

Ya ce babu Matsala halarci da mukayi masa besan da me zai saka mana ba..

Karima yar halak ce ka ga akaina tasha gwagwarmaya '' koda Uwar ta take hannu Fulani '' ba ta yarda uwar ta tashi ga sashina tasan Fulani na iya juya uwar ta da magani..

Nine nabawa Fulani iya Firdausi amatsayin baiwa Saboda naga hankalin na ba ta anya kuwa bayi ne..

Yin hakan danayi ya sa nacire mata shakku...

Ajiyar zuciya Faruk ya sauke ya ce dankale lallai Labarin Karima da uwar ta akwai ban tausayi..

Tun da kaban labarin nata da ba ka karasa ba nakasa sukuni 'maganar gaskiya ina son Karima sona hakika ina son in uban ta yazo ka sanar masa amma kuma ka dakata tukunna an yi mun AlKawari ba ni Mata acikin masarautar nan indai ita ce zanyi farin ciki inkuma ba ita ba ce zanshiga damuwa dan ina mata mugun so abaya na so Asiya amma ban san radadin so ba sai a kan Karima duk yanda na so nayi hira da ita dazun taki ba ni dama.....

Yarima Samad Murmusa ya yi ya ce aibazata taba kulaka ba harsai na ba ta dama wannan ka'ida ne...

Maganar ance za abaka mata wanene ya yi maka AlKawari mai martaba ne..

Girgiza kai ya yi ya ce uhmm kadai zamuyi magana zanje gida saida safe Kar ka ce mata komai harsai na tabbatar da wacce za a ban..

Yarima Samad ya ce basai inba Aminu ba..

Zare idanu ya yi ya ce haba Tabe Tabe ya da haka..

Wallahi ina mugun sonta inhar ba ita ba ce wacce za a ban zan hada biyu in aura' Kayi mata magana a shirye nake...

Yarima Samad ya ce na ji na mince zan duba lamarin ka..

. Tashi ya yi ya ce yawwa mu je gidan kurku zanje induba Fulani...

 Tare suka tafi koda suka je sun iske ta zaune ta zabga uban tagumi.

 Ganin su ya sa hankalin ta yadawo kansu..

 Tafashe da kuka ta ce dan Allah Yarima Samad ka taimakeni in bar nan wajen...

Faruk ya ce inkinbar nan ina zakije kibari kawai ayi zaman kotu inhar kotu ta yi belin dinki shi ke nan kin rabauta..

In hukunci suka yanke miki duka daidai ne yakarashe zancen yana duba wayar sa....

Yarima Samad dake kallon duk yanda ta rame ta yi baki duk ta zube ya ce kai Mama Fulani kenan 'nida kike neman sabautawa a yau kike neman taimako na...

 Na mugun taimaka miki ɗanasa ake baki abincin da kike bukata.

Sannan ina mai shaida miki a kan Mahaifina angano inda yake atakaice bayan bikin Ahmad da kwana daya zanje indauko sa.....

Fulani zazzare idanu ta yi cike da mamaki ta ce kana nufin ansa inda Salihu yake..

Kuka ta fashe da shi ta ce nayarda Allah keyi jibi irin abun da mukayi amma kuma zekara dawowa masarautar nan..

Wayyo dan Allah kuyafemun na tuba

Yarima Samad kallon ta yake ya ce uhmm Abban Marwan aure ze daura bayan Auren Khadija da Sati daya aranar indai ba a je kotu ba zansa a kawo miki abinci biki..

Daga haka yakama hannun Faruk suka bar gidan kurku.

Gangami da gidan Iko sai kirari suke masu...

Khadija kwance a dakin Rahama tana waya da Adamsy da dukan Alamu tanajin dadin wayar duk da ba magana take ba amma tana murmusawa...

Suna cikin wayar ne Rahama ta shigo dakin....

Adamsy najin muryan Rahama tana fadin ke dijat zantafi saida safe yayan ki nakirana.

Kada mata kai ta yi Alamun ba matsala...

Shiko Adamu ya ce kiba Rahama wayar mu gaisa mana..

Ihun kiran Anty Rahama ta soma wance ta waigo ta ce yadai dijat kina bukatan wani abu ne....

 Khadija ta ce ga Adamu ya ce zaku gaisa.

Kada kai Rahama ta yi ta ce A'a dijat ba zan amsa wayar nan ba har mijina yaban dama ''..

Daga haka tasakai tawuce tasan halin Yarima inyaji labari tofah ze ce da wani abu....

 Dijat ta ce ka ga anty tamu har ta wuce kabari zuwa gobe kun gaisa...

 Haka dai su kaci gaba da hirar su.....

Kashe Gari..

Ayaune yan uwan Adamu su kazo Daga katsina kawo lefe na gani na fada..

Akwatuna goma sha biyu har fadar Sarki aka kai kaya......

Sarki ya yi Murna ya sa Albarka '' nan ma aka kai kayan sashin mama karama itama har da taka rawa..

Ana kai kayan sashin Mamy yan uwanta da suka zo bikin tun wuri suka fara bubbude kayan suna sa Albarka....

Sossai yan kawo lefe suka samu tarba me kyau tare da babban masauki hôtel da Aka sauke su inda Sarki ke ajiye baki yan biki...

 

 Rahama da Samad da Ahmad suna ta shirye shirye suma gobe Alhamis za su wuce kano kai lefe.

Ranar juma'a daurin aure....

Sossai Ahmad ke murna zeje dauko fitsaratu yakawo gidan sa...

 Dan cewa ya yi da ba zai zauna masarautar da ita ba saida cikin gidajen baban sa..

Mai martaba ya ce tun da Samad ya zauna shima yazama dole yazauna anan da matar sa.....

 Asiya da Rahama suke waya tana ba Rahama labarin daulan da Salma take ciki kuma ba asan sana'ar mijin ta ba...

Rahama ta ce subuhannalah kiban lambar Salma koma kawai ki barta ai dani za a kanon InshAllah zanje in same ta in mata fada ta farga tun wuri banson abun da ze taba min yar ƙanwata....

Ke kuma banda munafunci Ashe Ahmad zaki aura shi ne kike boye mun 'sossai ta ɗAnne dariyar ta..

Asiya da ba ta gane kan zancen ba ta ce wane Ahmad kike magana dan sunan mijin da zan aura ne...

Rahama ta ce angon naki mana' kin san gobe zamu kai l'efen naki...

ZUMBUR Asiya ta tashi zaune ta kam bala'i kina nufin wannan yaron mara kunya nan shi zan aura...

Fashewa da kuka ta yi ta ce wallahi Rahama soya ke ya gana mun badan Allah ze aureni ba tuntuni danasan shi ne 'aida nayi ta magiya a kan a fasa auren nan...

Rahama ta ce Ko kukan jini zakiyi baza a fasa ba nida aka auramun Samad mutuwa nayi....

Asiya ta ce haba Rahama karki hada auren ki da nawa.

Shifa akwai mugun nufi azuciyar sa..

 Uhmm kanin mijina beda mugun nufi kece baki fahimce shi ba Asiya..

Dan Allah karki biye masa koda anzo daurin auren

Koda ankawo ki nan gidan sa dan Allah ki kwantar da kanki duk iskanci sa ze bari inma da mugunta ne zekasa aikata abun da yakeda niya....

. Cikin sheshekar kuka Asiya ta ce Rahama na ji zancen ki kuma InshAllah nadauka baki taba ba ni shawara nabi na tabe ba..

Sossai Rahama ta ji dadi ta ce shima Abby jibi ne daurin auren nasa '' amma ance nasa a 🇬🇦 za a daura Amarya kawai za a kawo masa Daga can...

Uhmm haka na ji nima Rahama ai baban naki yana ta zumudi har sun tare sabon gida '' ya gyara musu Ko ina..

Rahama ta ce anty da mama sun gayamin..

Kice zumudi yake uhmm Abby kenan Allah dai ya sanya Alkhairi....

Daga haka suka yi sallama.

Kai tsaye sheik ta danna kira.

Babu ba ta lokaci ya Daga.

Bayan sun gaisa ta ce Abby jibi ne daurin auren namu to Allah ya sanya Alkhairi

.

Ameen ya Allah ya furta ya ce Rahamatullah dafatan kina lafiya na ji Aisha ta ce gobe zaku zo Ko..

Nasan ɗai sashin Sa'adatu zaki sauka nasa an gyara miki daki daughter..

Sossai ta ji dadi ta ce eh sashin anty zan sauka dole ne wannan Abby.

Yakamata ka hadani da Amaryar tamu Abby..

. Dariya ya yi yana shafa gemu ta tsotsa masa inda ke masa kai kayi ya ce karki damu yanzu zantura miki nombar kuma ai zaku hadu da ranar juma'a da yamma jirgin su ze sauka....kano.

Rahama cike da Jin dadi ta ce Abby uhmm da'ace ka nemi shawara ta dazance kada ka kara aure....

 Murmushi ya yi ya ce Ko kina taya Sa'adatu kishi ne..

 Zazzare idanu ta yi kamar yana ganin ta ta ce A'a Nina San Anty babu ruwan ta...

Kuma kin san da haka ne kike son ki hana '' gayamin Ko matar batayi miki bane...

Tun Farko da kin nuna mun bakyaso inna gamsu da hujjojin ki zan iya hakura innemi Zabin Allah.....

 Kin san banda kamar ki Rahama duk acikin yaya na.

 a kan ki zan iya yin komai 'nasan kinada tarbiyya ba za ki so muyi abun da mutuncin gidan mu ze zube ba..

Rahama ta ce haka ne Abby na kar ka Adamu' itama wannan din Allah yakawo ta da Alkhairi..

 Ameen ya Allah ya furta yana mejin kaunar yarsa na kara ruruwa acikin zuciyar sa...

Daga haka suka yi Sallama...

Shiko Sheik Hassana ya dannawa kira..

Ya ce Amarya bakya laifi koda kin kashe karen gida na..

Murmushi ta yi Daga zaune ta ce my husband ai cewa ake koda na kashe dan masu gida..

Darawa ya yi ya ce Ah Ah dan baki kashe bane dakin ni awajena kinyi laifi my love.

Uhmm yanzu de jibi daurin auren mu karfa kisa aranki Daga ke babu kari ɗuk lokacin ɗana samu dama zan cike' inkuma banyi ba to haka Allah yatsara...

 Tabe baki ta yi Daga zaune ta ce haba angon hassana Kai Adali ne Ko goma ake yi nasan zakayi adalci uhmm kaide wani abu sai jibi ranar daurin aure na ji bakin cikin da ba za ka zo ba..

 Kiyi hakuri Amarsu ta angon ta' akwai wata diya ta Asiya ɗa kanin mijin yata Rahama ze aura' kuma Nine na jagoranci komai na auren nasu..

 Am sorry kinji baby na yakashe murya.

 Hakan ya sa ta Jin kanta a nishadi ta ce uhmm yawuce tun da ka kawo uzuri..

Amma fa nazo zamu ɗau hotuna zafafa nida kai.

 Sossai ma zamu dauka yabata amsa.

 Amma ki tabbatar da hijab jikin ki kafun muyi hoton kin san irin wannan hoton yawo suke a social media' Kuma ni gida na ba' a yafa mayafi hubby kizo da hijabai in sun miki karanci zan ha daki da Sa'adatu zata dinko miki..

 Uhmm na ji my love dîna uban yaya na sirrin zuciyata 'mai gyara tunani na me sani farin ciki...

 Sheik cire hular kansa ya yi yana dan shafa kansa' Wani kayataccen Murmushi ya yi yana ayyanawa aransa uhmm shima yazama ƙaramin yaro yau....

 Amarya ta ina godiya sossai zan shiga Daga ciki..

 Uhmm yanzu har ka gaji da hira dani..

 Ah ah banki mu kwana chat ba' yau ina dakin Sa'adatu Kuma ita ba ta son jira' gara in je kin san yau da gobe duk wajen ta nake jibi kuma ina tare da sweety na..

 Sossai ta dara katse firan ya yi da Fadi ki tabbatar kinyi mafarki na.

Da haka suka yi sallama.

Kai tsaye dakin Anty ya nufa iske ya yi zaune ta ce Abban Rahama Kaga yanda kayi kyau kuwa...

Allah Ko Sa'adatu tun da muke ban taba miki kyau ba sai yanzu..

 Kai ka san kullum ina gaba wajen yaba kyawun halittar ka..

 Shi ya sa nake adua Allah ya sa in haifo mai kama da kai kamar Rahama...

 Sossai ya dara ya ce yawwa dan matso zanwa baby na adua kin san jiya ina dakin Maman Salma 'babu damar ayi adu'ar..

 Haka ne ta furta tare da matsowa yana tofa adua tana lumshe idanu..

Nikam nace bara inbaro dakin nan kada Sheik ya hango yaci ni tara.....

Asuba ta gari......

Kashe Gari.

Kwatano.

Tun da sassafe masarautar gheuzo ta tashi da Ayyuka tare da baki ta Ko ina daga garuruka harda gyare gyare ake yi inda sarakuna za su sauka cikin su harda Sarkin kano.....

Yarima Samad dasu Ahmad ɗa Rahama' tsab suka shirya '' su Faruk da Aminu sammako suka yi dan zuwa jidan akwatunan lefen suka yi airport.....

 Mama Firdausi wanda da ita za a tafi tsaf suka shirya tare da wasu yan uwan nasu Daga bohicon..

Karima ta ce baza a abarta abaya ba duk suna cikin matafiya...

Khadija harda kuka wai ba da ita za a je ba..

Yarima Samad ya ce kije ina gobe daurin auren ki' muma jibi zamu dawo InshAllah da Amarya.

Mamy da Mai Martaba Adua suka yi masu ɗa fatan Allah ubangiji yakai su lafiya..

Abban Marwan tuni yawuce aiport dan dole yakamata ace ga kanin uban Ahmad a wajen daurin auren.....

Basu ba ta lokaci ba Samad Personnel air plan.

Jirgin nasu ya Daga sararin Samaniya.......

Sai Kano...

🇬🇦 Gabon

Hassana tasha lalle hadadde ta yi wani fresh tasha gyara tsaf harda maganin tsaida Brest tasha dan haka boob din ta yakoma kamar sabuwa

Magungunan gyara ba a cewa komai gidan nasu ancika tun a ranar aka fara daura tukunya ana sauke wa...

 Me kitson dakewa Hassana kitso ta ce 'sai dai aturawa sheik hoto yagani yabiya ta....

Daukan hoton suka yi' 'shi kuwa Sheik yana cen yanata hada hada tarban bakin sa da suka zo Daga nesa irin su saudiya' Soudan...

Ganin sakon nata ta whsap ya shiga cikin hanzari..

Cin karo ya yi da wannan tsalelen kitson nan..

Cikin.

Muje zuwa

Ta ku har kullum kyauta Daga AllahƘANWATA

09069080725

Post a Comment

0 Comments