Ticker

6/recent/ticker-posts

Ƙanwata Na Ikilima Adam (Kashi na 5)

Da sunan Allah mai Rahma mai jin kai. Allah kasa yanda na fara lafiya in kare shi lafiya. Wannan labarin ya faru da gaske dan kusan Book dina da nake yi true life ne sai dai in yi masa kwaskwarima dan abun ya fi ba da citta.

Ku biyo ni ku sha labari.

Ku daure ku yi comment dan in ji ra'ayoyin ku a kan Littafin nan......

*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*

_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishaɗantarwa tare da faɗakarwa da jama'a bisa harshen hausa}_

https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo

⚜️©J.A.W📚🖌️

Marubuciyar

* Amince Da Ni
* KAI KA JA WA KANKA

Yanzu kuma gani ɗauke da

ƘANWATA

Paid Book ne

Vip 300
Special 500

Acct No. 3115484026, First Bank, ko kuma Kati MTN (Ba na son VTU)

Idan kin biya ta bank kina iya turo shaidar biyar ki ta wannan 09069080725

kanwata

🌟🌟 ƘANWATA Na Ikilima Adam [Kashi na 5]🌟🌟

7️0️

Yasa shi tashi tsaye ya ce karta ga laifin Karima dan doka ne aka kindaya mata '' amma kuma maganar cin zarafi zanji dalilin daya sa ta yi hakan...

Aminu ya ce OK gara haka ai.

Ya za ai ta shigo ne ta ce tanason ganin yayar ta..

Murmushi Samad ya yi yana kallon Rahama dake kokarin rufe jikin ta da bargo '' ya ce uhmm kudai ba ta hakuri nima ina nan fitowa ni kadai yanzu.

Mu hadu Sashin Mamy.

Aminu ya ce Tabe Tabe saika zo din Daga haka ya katse wayar..

Kallon sa yadawo a kan Salma ya ce kindaiji abun da ya ce '' hakuri yake baki a kan ba za ki samu ganin Rahama a yau ba.

Sai dai gobe.....

Kallon sa yamaida a kan Faruk ya ce kai kuma mene ne damuwar ka naga tun da akai maganar Asiya ka canza Daga yanayin ka

Faruk ya ce Ah Ah ba haka bane yanzu dai mu je Sashin Mamy din..

Barin Salma suka yi awajen zaune..

Ganin lallai suma sun raina mata wayau ya za ai tana kanwar matar gida za su taka ta..

 

Saida ta Share minti goma zaune bayan tafiyar su Faruk.

Tashi ta yi jiki asanyaye zata wuce masaukin su...

Jin karar takun takalmi ya sata waigawa taga me zuwa...

Caraf Idanun su ya tsarke cikin juna ita da Samad wani kallo yake bin ta da shi masu tarin ma'anoni....harya iso gaban ta batasani ba dan ta shagala da kallon sa....

Tsintar muryan sa ta yi yana Fadin Salma mekikeyi anan ke kadai..

Bama tasan yana magana ba Sam hankalin ta baya kusa ta shagala da kallon sa..

Da Mamaki yake kallon yanda ta kura masa idanu... Sunan ta data ji ya Ambata da karfi ya ce Salmaaa firgit tadawo hayyacin ta.. Cikin Jin kunya tafara Murmushi yake.

Shiko kawar da kan sa ya yi Daga kallon ta..

Ya ce mekike yi anan maza ki wuce daki '' ba na son yawo fa..

Kin ce kina son magana da yayar ki naga kusan wuni kukayi da ita a yau..

Dan haka kibari gobe zata zo da inda kuke..

Wannan kallon da kike yawan yimin na mene ne yafada tare da rungume hannayen sa a kirji.

Cikin Jin kunyar kalaman sa da rikattatun Idanun sa daya zuba mata akaran farko na rayuwar ta..

Cikin sanyin murya ta ce meye A'ciki danna kalle ka kaifa mijin yaya ta ne..

Samad dake nazartan kalaman ta ya yi shiru cen kamar ba zai magana ba..

Har ta cire rai sai ta ji yana fadin eh lallai ni mijin yayar ki ce...

Wannan ba hujja ba ce kiyi ta kallona har in tsargu da kaina.

Dan haka ina son Daga yau ki daina inba da wata manufa kukeyi ba.....

 Salma da bakin ta ya mutu ta ce ni dai ba da wata manufa nake yi ba''

Saide kaine ba ka yarda da kanka ba..

Cak yatsaya da shirin tafiya da yake yi..

Waigowa ya yi yana kallon ta tun daga kasa har Sama

Kamar ya ban yarda da kaina ba''' Daga nace miki ki daina abun da beda amfani. Ke Ƙanwata ce inna sameki da kuskure to zan hukuntaki daidai da abun da kika aikata koda khadija ce haka zan mata kisa ki rubuta ina binki bashi daya karki bari yazama uku kinji Ko ya saki wani shu'umin Murmushi tare da barin wajen cikin isa da izza...

Kallon sa take harya ba ce mata da gani lallai ta yarda yarima duk yanda take tunanin sa ya zarce ta..

Yana bin ta bashi daya take ta maimaitawa tome yake nufi kenan rasa me ba ta amsa ya sa

Jiki babu kwari ta yi hanyar dakin nasu...

Bakin ta dauke da Sallama ta shiga dakin iske Asiya da Anty suna karatun Alkur'an tare..

Sallamar ta ya sa suka katse karatun suna mata kallon ina ta fito..

Cikin inda inda tasoma kame kame uhmm daman ina tare da su Faruk ne dan ciwon ciki na ya tashi...

Anty ta ce yanzu akwai wanda ya tambayeki inda kika fito.

 Girgiza kai ta yi ta ce A'a..

Asiya dake tabe baki ta ce to ai yawo beda amfani agareki kina matar aure kardai sashin Rahama kika je dan Allah kibarta ta huta da mijin ta Karki kashe mata aure..

 Salma da Ranta yagama baci ta ce au nice ma zan kashe mata aure..

Innayi haka meye riba ta..

Asiya ta ce ribarki shi ne kiga kun rasa dukan ku.

Ma'ana ta rasa Yarima kema kinrasa kinga babu wanda yake da shi cikin ku..

Salma zatayi magana Anty ta yi mata hannun stop..

Ta ce ke me kike tunani ne bamusan lagon ki ba..

Kin hana Adamu auren Rahama yanzu zaki kashe mata auren ne...

Ni dai nasan take taken ki bewuce kiga kin rabata da gidan Sarauta nan...

Wallahi kika kuskura kika kashewa yata aure uhmm wlh ko ubanki be isa yarabani dake ba..

Tun da nake da shi ba mu taba fada ba amma a kan haka zamuyi inhar ya ce ze daure miki gindi..

 Salma sai hura hanci take yi cikin tsananin bacin rai ta ce zato zunubi ne koda yazama gaskiya...

Banda zuciyar ku babu Allah taya zaku yi mugun tunanina akaina...

Auren nata da Adamu mugun halin ta ya sa ya fasa auren ta....

Bata karasa fadin abun da zata ce ba ta ji anty ta wanke ta da gigitaccen mari wanda ya sa nan da nan tafara ganin taurari..

Anty zata kara mata marin Asiya tarike hannun ta ta ce kiyi hakuri InshAllah zata canza halin ta....

Karmu biye mata muzama irin ta..

Salma rushewa da uban kuka ta yi hakan ya sa tadau wayar ta takira mama cikin sheshekar kuka ta sanar mata da abun da anty da Asiya suka yi mata..

Daga can ɓangaren mama ta ce shegu yan iska ɗangin matsiyata sun je maula aidole su wulakantanki.

ita Rahama dan uban ta tun da ta yi aure sau daya takirani kuma Koda zata tafi yakamata tazo tamun sallama ki rabu dasu wallahi har Rahama sainayi maganin ta....

.

Salma cikin Jin dadin kwantar mata da hankali da Mama ta yi ta ce mama.

Wai ina Abdul jalil ne.

Mama Ta ce shege baya wuni gida tun da yaga shegiyar uwar sa ba ta nan

 a hanse free Salma tasa wayar yanda su Anty za su ji abun da suke fade...

Ita Ko Anty banda kukan zuci babu abun da take yi...

So take ta sanarwa sheik gaskiya ya raba masu gida ita da Mama Ko kuma ita takoma gidan su tazauna har asamu mafita hakanan takeji zuciyar ta be aminta da komawa gidan nan ba..

Salma suna gama wayar ta katse tana ta jijjiga jikin ta ta ce uhmm kalan dangi kawai..

Dukan ku babu wanda ya hada jini da Rahama..

Anty ta ce ninan na hada jini da Rahama Saboda inkika ga Abdul jalil to kamar kinga Rahama ne suna mugun kama.

Jinina da nata sun gwauraye wuri daya.

Asiya cikin bacin rai tagama karanta sakon Faruk daya shigo wayar ta...

Dago kai ta yi tana kallon Salma ta ce wawiyar banza watau sharri kika kulla mun wajen Faruk meye ribarki algunguma...

Inkina son shi kije ki kashe auren naki sai inhada ku aure....

Anty ta ce ke kuma meya ha daki da Salma ne tana kallon Asiya da Ranta yake aba ce..

Asiya taba Anty labarin abun da Faruk ya fada mata, ..

 Cikin takaici Anty ta ce Asiya karki damu matar mutum kabarin sa kalaman sa karsu ba ta miki rai kidai bashi hakuri.

Ke KUMA SALMA kindai ba ni wlh halinki sai ke shasha......

Mamy zaune ita da su Samad

 Faruk na yar rubuce rubuce Samad ya dago kai yana kallon Mamy ya ce wai Mamy ina Maryam take da Mamar ta..

Mamy ajiyar zuciya ta yi ta ce uhmm ai sun tafi gida tun da taro ya tashi amma Maryam ta ce zata dawo zuwa gobe.

Good ya furta ya ce to ita bakuwar nan taki hassana Daga ina take ne.

Mamy wani kallo take binsa da shi ta ce TO Sarkin tambaya ina ruwan ka ko a kan ka take ne...

Haba Mamy Daga tambaya sai kiji haushi na Allah yabaki hakuri..

Ameen ta furta tana masa hararan wasa.....

Faruk yagama rubuce rubucen yadago kai yana kallon Samad ya ce gaskiya awannan watan ba a samu riba masu yawa ba...

Ribar ba ta wuce millions 50 ba..

Mamy dake sauraren su ta ce to garin ya haka ta faru ne..

Samad da ransa yasoma baci ya ce duk laifin Marwan ne...

Yana zuwa Samad air plan yana diban kudade na a banza da sunyi magana ce musu yake aina dan uwan sa ne..

Saboda ke Mamy nake kyale su yanzu lokaci ya yi fa ba zan kara barin takwana ba...

Mamy cikin kwantar murya ta ce ni dai kar ka masa komai iyakar dai ka dakile hanyar da yake bi wajen kwasan maka kudade shi ne kawai mafita...

Faruk ya ce kwarai kuwa shi ne mafita dan manager ya ce yana sawa lissafi ya kunce masu idan kullum zeje ya amsa bayan komai a rubuce yake a computer....

Yarima ya ce babu matsala Mamy tun da kin ce haka nadau shawarki. InshAllah gobe zamu shiga kotu kan wannan case din matar nan.

Daga goben nakeson infara bin diddigi wannan baiwar nan da ake nema..

Mamy cikin jin dadi ta ce Yarima Allah ya sa Adace yabada sa'a...

Ameen dukan su suka amsa...

Wai ina khadija take ne cewar Yarima yana tambayar Mamy..

Mamy ta ce yawuce tana dakin ta kaje cen kaduba amma ka san babu inda take zuwa Ko...

OK ya furta ya ce Aminu kujira ni bara in leka dakin khadija ina zuwa...

Da to suka amsa masa suna cigaba da hada takardu waje daya....

Ahankali yake tafiya ba bayason ta ji takun tafiyar sa...

Handle din kofar ya bude hankali a sannu Ahankali ya tura kofar..

Jin muryan Khadija tana waya ne ya sa shi kasa kunnen sa wajen Jin me take fade...

Ita Ko khadija data shagala dayin waya sai fadi take haba Maryam ya zaki hadani kawance da yar lesbien.. Kuma bayan.... Ganin Yarima gaban ta yana mata mugun kallo ya sa...........

Ta ku har kullum kyauta Daga AllahƘANWATA

7️1️

Mugun kallo ya sa hannun sa ya wabce wayar Daga hannun ta..

Kara wayar a kunnen sa ya yi yana sauraren abun da ake fadi..

Daga cen ɓangaren ta ce haba khadija meye dan na ha daki da Yar lesbien bafa harkan nan zaku yi ba..

Nima din da mukayi da ita yanzu natuba nadaina dan haka ina rokon ki kiyi hakuri zumunci zaku ringa yi tanada waye wa zata koya miki wasu abubuwan da bakisan dasu ba...

Hankalin yarima ya yi mugun tashi jikin sa yadau rawa kamar mazari jijiyoyin hannun saida suka tattashi Saboda tsananin bacin rai Idanun sa suka canza launi zuwa ja...

Daga can ɓangaren Maryam sai Fadi take khadija ya kikayi shiru sai magana nake yi.

Cilla wayar ya yi a bango nan da nan ta fashe wargas akasa..

Ita Ko khadija karshen gadon ta zauna tana baya baya ganin ya nufo inda take azuciye..

Kuka tasaki tun kan ya isa gareta...

Kamar kura haka yayo kanta bugun ta yake yi babu sassauci sai ihu take tana fadin wayyo Mamy wayyo Mamy ze kashe ni..

Wani mugun shaka ya yi mata wanda ya sa numfashin ta yin sama sama Idanun ta azare kamar wacce rai yake gab da barin jikin ta....

Mamy aguje sukayo ciki ita da su Faruk harda Hassana..

Har tuntube Mamy keyi wajen rige rigen shiga dakin.

Innaliahi mamy tashiga maimaitawa me zan gani haka Yarima za ka kashe ta ka saketa nace Ko..

Ina Ko Jin Mamy baya yi yaci gaba da bugun ta..

Faruk cikin zafin nama ya je ya rike hannun Samad da karfin tsiya Sannan ya sake khadija...

Ita Ko khadija yana sakin ta faduwa ta yi kamar matatta tana numfashi sama sama...

Faruk da Aminu cikin Fada suka ce haba Samad wannan aiba karfin ku daya ba..

Wani irin abune ta yi mai girma da zakai mata wannan mugun hukunci ni dai gaskiya BANJI dadi ba...

Duk abun da suke ta fade be ce masu komai ba....

Mamy cikin kuka ta ce ku duba mun khadija bede kashe ta ba Ko...

Hassana dake yayyafa wa khadija ruwa ta ce mamy da Ranta karki damu ta jigata ne kawai amma zata dawo normal...

Yarima Samad tashi ya yi tsaye cikin bacin rai ya ce dakun barni da ita inga wanda ya ɗaure mata gindi agidan nan...

Ahmad ne yashigo bakin sa dauke da sallama ya ce nasan za ai haka ai tuntuni ina gayamiki ki ki yaye kada Yaya Samad yadawo amma kika saura kina biyewa Maryam Ko...

Yakarashe zancen yana jifan ta da mugun kallo..

 Mamy cikin kidima ta ce wai mêke faruwa ne kunbarni cikin duhu..

Ganin su Faruk da Hassana a dakin ya sa Samad da Ahmad kin fadin abun da ke faruwa...

Yarima cikin isa ya ce Mamy maza ta hada kayan ta Daga yau sashina zata zauna wajen mata ta.. Kuma wlh kada kice komi a kan ƙanwata...

Mamy dake kallon sa yanda duk ya canza kamar bashi ba..

Ta ce nasan yanzu jira kake ince wani abu ka dawo kaina...

Cikin sassaita muryan sa ya ce A'h Ah taya zan dawo kanki Mamy kefa uwa ta ce itakuma ƙanwata ce da banbanci ba zan yarda ba amun iko a kan ta ba...

Gabadaya dakin hakuri suka Shiga bashi harda Ahmad..

Amma ya noke dole abun da ya ce shi za ai Mamy babu yanda ta iya hakanan tanaji tana gani ta hada kayan khadija tsaf..

Cikin kuka khadija ke fadin Mamy yanzu har kina kallo ze wuce dani...

Mamy ta ce duk da ban san laifin da kikayi ba.

Kin san ban iya hana shi da kina jin magana ta da haka ba ta faru ba....

Faruk da Aminu bayan sun Kammala komai suka yi Sallama da Mamy kusan tare suka fito Sashin Mamy da Yarima...

Khadija na biye dasu abaya da akwatin kayan ta...

Saida safe suka yi da Su Faruk inda ya yi Sashin nasa '' tana bayan sa tafiya take kamar wata kadangaruwa cikin tsoro ko bin takanta beyi ba kawai tafiya yake tana bin bayan sa...

Faruk tsaida Aminu ya yi suka je ɓangaren su Asiya...

Kiran layin Asiya ya rinƙa yi tana ganin kiran amma taki Daga wa...

Anty ce ke Lure da ita ta ce kamar wayar ki ce.

Ke ring baki Daga ba..

Asiya cikin tabe baki ta ce ai dan rainin wayau nan ne Faruk mana..

Anty ta ce meye laifin Faruk abun da aka fada masa shi ze dauka haka ne dan Allah Daga wayar ban san ki da fushi ba...

Cikin kunkuni ta Daga wayar ta yi shiru taki magana...

Shiko Faruk cewa ya yi gani a kofar dakin naku ki fito sauri muke..

Ganin anty ta tsare ta da idanu ya sa ta fadin gani nan zuwa...

 Murmushi Anty ta yi tasan ba hakan ta yi niyar fada ba..

Allah ya sani tana kaunar Rahama da Asiya har ita Salma din kawai de halin Salma ne bataso amma tabbas batason mummunar abu ya faru da ita..

Cikin hanzari Asiya ta saka hijab din ta tafita..

Iske Faruk ta yi tsaye shida Aminu...

Sai kallon agogon hannun sa yake Alamun ta dade ba ta fito ba...

Cike da nutsuwar ta.

Ta iso wajen su a ladabce ta gaishe su suka Amsa fuska sake...

Aminu ya ce uhmm masoya sun hadu kun kasa magana Ko bara inkauce kun sake.

 basu waje ya yi dan su tatttauna..

Murmushi Farruk ya ce ya ce ka ga damar tafiya ne amma ai komai sai ayi agaban ka.

Aminu beko tsaya sauraren Faruk ba yafice.

Faruk Murmushi ya yi yana kallon yanda ta hada rai kamar an mata dole ne ta fito..

Ya ce haba Asiya me laifina dan nayi miki fada a kan wayar ɗare..

Asiya ta ce wayar ɗare kenan yar iska ka daukeni wani irin waya ne

ba zanyi shi a wuni ba sai cikin ɗare nifa ba na son zargi duk abun da akace maka akaina ka tambayeni zan fada maka gaskiya

ba kazo ka yanke mun hukunci ba..ehee takarashe zancen cikin tsiwa..

Faruk cikin yin kasa da murya ya ce Afuwan nayi laifi daman sonake inga kyakkyawa fuska ki shi ya sa na leko dan Allah yimun Murmushi mana..

Yana kashe mata idanu.

Shiru ta yi tarasa tayanda ake murmushin..

Au baki huce ba kenan...

Girgiza kai ta yi ta ce komai yawuce.

Murmushi ta sakar masa tana kokarin shiga Daga ciki..

Ya ce ba komai wannan ma dakikai kin biyani zuwa dasafe zamuyi waya tun da kince bakya wayar ɗare..

Asiya dake kokarin shiga daki kada kai ta yi tare da komawa cikin dakin nasu..

Shikuwa zuwa ya yi ya ja Aminu suka wuce...

Yarima suna shiga sashin nasa kai tsaye dakin Rahama ya je da khadija iske Rahama ta yi harta rufe dakin nata...

Karar bubbuga kofa ne.

Yatashe ta Daga barci tasan shi ne cikin tsoro ta tashi batasan dame yazo ba..cikin kuka zuci ta sauko Daga kan gadon ta.

Taku take yi ahankali harta isa bakin kofar.

 Ahankali tabude kofar tana murza Idanun ta..

Caraf Idanun ta ya sauka a kan Yarima da Khadija dake tsaye da akwatin kayan ta tana sheshekar kuka kanta aduke

Rahama cikin.........

Taku har kullum kyauta Daga AllahƘANWATA

7️2️

RAHAMA cikin Rawar murya ta ce khadijat lafiya kuwa mêke damun ki.

Gayamin naga kamar kuka kike nan da nan duk ta rikice tana me jawo hannun khadija zuwa dakin nata...

Shiko Yarima dake tsaye yana kallon su ya ce Hubby nan zata dawo da zama har muga Abun da Allah zeyi...

Rahama cikin damuwa ta ce na ji dadin hakan amma meye dalilin dayasa take kuka takura mata kayi a kan saita zo nan sashin mu...

Yarima dake kallon ta yanda duk ta rude tana sharewa khadija kwalla ya ce gâta nan ki tambeye ta da kanta ta ce zata dawo gun anty ta kila wani abun ke mata ciwo..

Khadija da duk jikin ta ciwo yake mata ta ce Anty Rahama ina son in shiga wanka..

Rahama cikin hanzari zatayi bandakin da hada mata ruwan dumi na wanka

Yarima yarike hannun ta ya ce ina zakije ne Sarki aiki Kibar ta da kanta zata hada ruwan wanka..

Babu yanda ta iya hakanan tasa idanu khadija ta shiga bandakin...

Dawo da. Kallon ta yi a kan sa cikin kalan tausayi ta ce yanzu tun da ka ga khadija tadawo nan sashina tare zanringa kwana da ita..

Wani kallo yake binta da shi masu cike da baki isa ba..

Ya ce uhmm Rahamatullah dauko hijab dinki mu. Tafi Saboda Sallah Asuba..

Rahama ta ce ya zanbar khadija ita kadai..

Uhmm ni dai mu je yafada yana kokarin Jan hannun ta...

Ganin zata ba ta masa lokaci ya sa hannayen sa ya dauke ta..

Sai zazzare idanu take ta ce Amjad meye haka ne idan khadija ta gan mu ahaka fa girma yafadi...

Uhmm ya ce be ba ta Amsa ba kai tsaye dakin nashi yakai tare da sauke ta a kan gadon sa..

Yana ajiye ta yadawo tsakiyar dakin kokarin cire kayan jikin sa yake'ganin tana kallon sa ya ce ba za ki tayani cirewa ba....

Kaida kasa abunka kaine ka san yanda za ka cire su takarashe zancen tare da Jan bargo zata lullube jikin ta...

 Yarima beko tsaya sauraren ta ba..

 Ya shiga ya yi wanka yana fitowa Daga shi sai boxer gashin jikin sa luf suka kwanta Saboda damshin ruwa..

Bakin gadon nasa yazauna tare da dauko wayar sa yana bin sakonni dake shigowa takan whsap din sa...

Duk sakon dayaga New number ne baya shiga ciki sai inhar yaga profile din wanda ya sani ne...

 Sakon ya shigo masa a kan hassana dake gidan sarauta ba aiki yakaita ba....

Ta dalilin Salihu Turaki tazo dan tasan sirrin sa...

Kuma son Salihu Turaki take dan har haduwa suke yi...

Kallon number data turo masa sakon ya yi yaga nomber Gabon ce...

Shiga cikin message ɗin ya yi yana kara karanta wannan sakon...

Maganar zuci yake ya ce eh tabbas ta ce Gabon take inhar mutumin nan dayayi masa magana yana da.masaniya a kan hassana Kenan ya san inda Shugaban Adalai..

Ba tare da ya ba shi Amsa ba ya kashe datar sa..

Tagumi ya yi Daga zaune yana nazarin yanda ze dauko lamarin da warware sa ganin babu mafita ya sashi ajiye wayar gefen gadon nasa tare da jona ta a caji...

Kallon Rahama yake ji ya san ba barci take ba amma ta lumshe Idanun ta...

Hawa gadon ya yi yana kokarin jawo ta jikin sa tare da kai hannun sa saman boob din ta...

Zumbur ta tashi tazauna cikin muryan wacce ke shirin kuka ta ce wayyo nace maka ban warke ba..

Tun da baki warke bara induba wajen ingani..

Ganin yana kokarin cire mata pant tarike masa hannun cikin tsoro ta ce haba Amjad kayi hakuri mana da wasa nake maka na warke..

Au kin warke kikace

 

Gyada masa kai ta yi cikin Kosawa da tambayar sa..

Ban yarda ba saina gani da idona..

Duk yanda taki yarda ta kasa kwatan kanta saida yakwantar da ita tare da duba wajen gani ya yi kamar babu rauni tsabar raki ne ke damun ta.....

Dawo da kallon ya yi a kan ta ganin tarufe fuskar ta da pillow ya sa shi murmusa.

Haba Amarya meye na Jin kunya Daga ina duba wajen kada asamu matsala kuma naga babu wata illa a wajen dan haka pls kidan ba ni inkara namiki Alkawari ba zan wuce awa daya ba cikin marairaice fuska....

Rahama zazzare idanu ta yi tasoma hawaye shar ta ce wayyo Allah Anty ki taimakeni dan Allah kayi hakuri wallahi har yanzu ban koma daidai ba yanda take kukan iya gaskiyar ta ya sa shi darawa ya ce ok kin amince Mala'ikun Rahama suyi ta tsine miki Albarka..

Zazzare idanu tasoma ta ce uhmm ni dai bazasu tsinemun ba dan ba da ganganci na hana ba...

Yanda take zaro zancen sossai ya shagala da kallon ƙaramin bakin ta...

Hakan ya sa shi lacuto bakin nata yana kokarin hade shi da nashi.

Ya ce uhmm amma dai zaki barni in rage zafi Ko dan dai. Gaskiya ban iya kwana hakanan..

Babu yanda ta iya duk yanda taso ta yi barci Yarima yaki ba ta damar haka...

Sossai ya raya daren ba tare da ya kusance ta ba..

Tun tana kaucewa har ta biye masa...

Kusan karfe ukun ɗare Sannan barci barawo ya yi awon gaba dasu dukan su......

Asuba tagari

Kasar Gabon....

Karfe tara daidai jirgin sheik da Aminin sa ze tashi zuwa garin kano...

Tun karfe bakwai na safe yashirya tsaf komai nasu harda siyayyan da suka yi..

Sheik harda kayan baby masu kyau ya siya a cewar sa ya yi kewar yan kananan baby yanzu gashi zai samu....

Texte din Anty ne yashigo wayar sa yana dubawa ya yi Murmushi ya ce madam kina raina..

Daga can ɓangaren ta ce ya Abban Rahama dafatan kuna ta shirye shiryen koma.

To Allah yakaiku lafiya.

Damar so nake in rokeka wata Alfarma..

Jin ta ambaci Alfarma ya sashi ba ta damar ta fadi abun da take bukata...

Anty ta ce tun da muke da kai ban taɓa kawo maka wani abu sabanin hankalin ka ba..

Sheik ya ce Sa'adatu haka ne zancen naki ki fadi kai tsaye Alfarma InshAllah zan miki..

Cike da tsoro da Fargaba ta ce ina son dan Allah ka raba mana gida nida Maman Salma..

Cikin tsananin mamakin furucin ta ya ce to Saboda me Sa'adatu zan raba muku gida...

Anty tashiga bashi labarin wayar da salma ta yi da Mama agaban ta...

Numfashi ya fesar yana nazarin kalaman ta...

Ya ce yanzu watan cikin ki nawa ?

Wata hudu ta ba shi amsa tana mamakin meya kawo zancen ciki bayan ba maganar suke ba...

Sheik ya ce Sa'adatu kiyi hakuri kibari watan haihuwar ki nakamawa zan canza muku gida..

Amma kowa da part din sa..

Sai kunso zaku ga juna hakan ya yi miki sabon gida sabon baby....

Sossai ta yi dariya ta ce hakan ya yi nagode da Fahimta.

Suna gama fira da Anty...

Yakira Mama awaya cikin gadara ta ce harka iso ne...

Sheik ya ce babu zancen gaisuwa Ko Allah yakawo mu lafiya wai ke Aysha yaushe zakiyi hankali ne..

Bama wannan ba ina Abdul jalil yake..

Hankalin mama ya tashi Jin wannan tambayar inda inda tasoma ta ce yanzu yafita Daga gidan...

Sheik ya ce au sammako ya yi kenan.

To ki aika akirawo shi yadawo gida yanzu nan..

Banson na iso ban same shi ba....

Mama rike da baki ta ce uhmm nasan Algunguma ta fadamai ne shi ne ze fake da siyasa...

Ni yanzu ma ina nasan yaron nan yakwana tashi ta yi tadau hijab din ta..

Tana ta shiga makota cigiyar sa duk inda taje sai ace ba a gan shi ba..

Cike da takaicin yaron ta ce amma dai wannan yaron mugun dan banzan yawo gare shi ace yau kwanan sa biyu be kwana gida cike da damuwa take bin layi kwararo neman sa duk inda taje sai a je ba a gan sa ba....

Wayar tazare cikin jakar ta tashi ga kiran layin Abubakar.....

Har ta kusa tsinkewa ya Daga..

Cike da damuwa ta ce ABU wai ina Abdul Jalil tun shekaran jiya da safe bankara sashi a idanuna ba..

Abubakar dake tuki ya ce aikuwa gida yakwana jiya ma inaga sammako ya yi nasan sai ɗare kibari zan dubo shi kila yana gidan su Asiya ne..

Mama kwata kwata ta mance taje gidan su Asiya hakan ya sa ta yi hanyar gidan cikin hanzarin ta isa gidan su Asiya....

Bakin ta dauke da Sallama..

Maman Asiya hajiya hussaina cikin washe baki har fararen hakoran ta dake dauke da hakorin makkah suka bayyana...

Cikin sakin Fuska ta ce Maman Salma yau kece agidan namu lale lale..

Mama cikin tabe baki ta ce eh Nice dafatan dai kuna lafiya..

Lafiya lau tabata amsa ta ce mu shiga Daga ciki mana...

Mama ta ce Ah ah basai na shiga ba a kan hanya nake.

Abdul Jalil nake nema Ko yazo gidan nan kuwa...

Maman Asiya ta ce yana ciki kamar Abinci yake ci..

Maman Ranta dubu yabaci cikin ɗAnne fushin ta ta ce Ayya idan yagama yazo gida ya sameni yau baban su ze dawo....takarashe zancen tare da juyawa...

Ita Ko Maman Asiya da mamaki take kallon ta ta ce uhmm haryanzu dai Aishatu kinki canza halin ki.

Mijin ki ma beji dadin ki ba bare yaya bare makota uhmm Allah ya sa ki gane takarashe zancen tana kar kada kai tare da shiga dakin ta iske Abdul Jalil harya gama cin abinci duk hirar da suke yana jinsu...

Kallon Maman Asiya ya yi ya ce nasan Abba yau zedawo bara inje inshirya indan gyara masa daki...

Maman Asiya ta ce to kadaiyi hakuri duk abun da zatayi maka.

KADA kai ya yi ya ce babu damuwa.....

Wajen karfe daya na Rana su sheik suka iso garin Kano...

Abubakar ne ya je yadauko su ya sauke Aminin sheik agidan sa..

Shi kuma suka yi nasu gidan kai tsaye.....

Sheik cike da hamdala ya ce Allah ya yi mun dawo kasar tamu..

Abubakar dake tuki ya ce Abba da bakanan kaida Anty gidan babu dadi...

Murmushi sheik ya yi ya ce to ina maman taka take ba ta tayaka hira ne..

Tana yi ya ba shi amsa atakaice yana cigaba da tukin nasa....

Kano

Tun da sassafe Fulani tashirya tsaf cikin shigar ta na Alfarma hannun ta rike da wata bakar leda mai cike da mugun sirri da bokan ta ya aiko mata

Cike da izza da takama take taka kasa iya Firdausi tana bayan ta sai kirari take zuba mata...

Barka da Fitowa gimbiya Fulani takawan ki lafiya uwargida agun Sani Turaki.

Ba gaba da gaba ba kota baya sai anshirya shuga ta...

Kasaitaccen Murmushi ta yi tana cigaba da takun ta izuwa Sashin Yarima.

Har ta kusa kai kofa ta ji muryan Karima na fadin..

Gimbiya Fulani dakata !

Cak Fulani ta tsaya cikin tsananin mamaki ta wai..................

Ta ku har kullum kyauta Daga Allah7️3️

Cikin tsananin mamaki ta wai ga tana kallon Karima..

Dake kokarin isowa gareta kan aduke ta ce.

Gimbiya Fulani Yarima ya sa doka hana kowa shiga Sashin nasa saida izinin sa....

Wani kallo mai wuyar fassara Fulani ke jifan Karima da shi cikin tsananin bacin rai ta ce ke shasha dabba karya mara hankali kaskantaciyyar baiwa har kin isa ki gayamin doka bayan mune masu ba da doka da oder to bari kiji ingayamiki badai takamar ki Yarima ba to zansa asauke ki Daga kan mukamin ki.

Zaki shigo cen cikin bayi kina aiki..

Shasha dan Allah matsa kiban hanya maza kisa key ki bude mun...

Karima dukar da kanta kasa ta yi ta ce ina kara baki hakuri Gimbiya ba zan iya bude miki kofar nan ba...

Iya Firdausi dake bayan su cikin tsoron abun da zeje yadawo ta ce haba Karima Gimbiya Fulani ce gaban ki......yakamata ki gyara kalaman ki..

Karima cikin karfin hali ta ce mama nasani kawaide ba zan iya budewa bane...

Saukar Mari Karima ta ji afuskar ta wanda ya gigita ta rike da kuncin ta da Idanun ta ɗa suka kada take kallon Marwan sai huci Sama sama yake cikin tsawa ya ce ke har kin iya kihana Fulani shiga Sashin Yarima to yanzu zaki ga hukunci da zansa ayi miki wanda ze koya miki hankali....

Ihu ya fara yana fadin ina bayin gidan nan suke nan da nan duk suka bayyana na daki ma agurguje suke ta fitowa dan zuwa wajen nasa....

Koda suka jeru kallon su yake kamar yaga kashin Awaki tare da yamutsa fuskar sa..

Cikin zafin Rai ya ce cikin ku mutum daya ya je yakira mun..

Karfin Iko na gidan Yari..

Babu ba ta lokaci daya Daga cikin su ta tafi dan kiran sa..

Shikuwa Karfin Iko yana zaune bakin kofar Gidan Yari sai hura hanci yake yana tauna asawaki ya mimmike kafafun sa kan doguwar kujera ga redio kusa dashi...

Isowar wannan Baiwar ya sashi sauke kafafun sa akasa yana kallon ta cikin zakuwa..da son Jin abun da yakawo ta

Cikin Rawar Murya ta ce Karfin Iko '' jikan Sarki Marwan ke son ganin ka ya ce mu taho tare..

Jin Marwan ya sa babu ba ta lokaci ya tashi yabi bayan ta ya san aikin mugun ta ce zeyi..

Karima banda innaliahi babu abun da take maimaitawa acikin zuciyar ta....

Iya firdausi ta shiga tashin hankali ganin za a hada Karfin Iko da Karima sossai tsoro ya bayyana A fuskar ta....

Murmushi Fulani ta yi ganin Sarkin iko ya iso shida baiwar nan..

Cike da ladabi ya gaishe da Marwa da fulani....

Marwan cikin Daga Murya ya ce wannan baiwar Karima ina son ka kaita gidan Yari tare da horon yunwa na kwana uku hade da bulala dari...

Idanun Karima nan da nan suka kawo Ruwa cikin Rawar Murya ta ce Allahumma arjini fi musibati...

Wayyo Allah gani gareka za su cutar dani ba tare da da hakki ba.

Kan kace me karfin Iko ya yi mata wata muguwar cafka

 bayi maza masu tsaron sashin Yarima da suke sanye cikin uniforme din su ''suka yo wajen aguje su uku kallon karfin Iko suke yanda yake Jan Karima akasa.

Bayi mata dasuka jeru awajen Ko wanne kansu akasa kwalla suke suna tuna irin wahalar da Karima zata sha hannun Karfin iko..

Dan sun taba dandana wannan azabar a hannun sa..

Fulani ganin har sunkai bakin kofa da Karima cikin Daga Murya ta ce Karfin Iko ina son yanzu kayi mata jina jina bakin nata dake rashin kunya ka murje mun su...

Karfin Iko kallon Fulani ya yi cikin babban muryan tasa ya ce an gama Ranki yadade an gama '' amma makullai na hannun ta yakamata akarba...

Marwan dake karasowa inda suke ya ce amsa ka miko min '' Karfin iko wabce makulli ya yi hannun Karima tare da bawa Marwan....

Kai tsaye ya yi gaba da Karima cikin zafin nama....

Fulani cikin Jin dadin wannan abun ta ce Marwan ba ni makullan nan '' 'mika mata ya yi ya ce inaga sune makullan kofar dakunan Yarima da Matar sa...

Babu ba ta lokaci ganin abun da akayiwa Karima ya sa bayin dake gadin kofar shiga suka ba Fulani damar shiga ba tare da sunce uffan ba.....

Shiko Marwan cikin kallon banza da yake bin bayin da shi ya ce Ko acikin ku akwai me magana ne..

Kada kai suka yi Alamun babu....

Cikin karaji ya ce To mama Nina tafi in wani abu yataso ki sanar mun Daga haka yafice cikin isa yana tafiya kamar wani bajimin sa...

Ita Ko Fulani tafiya take a hankali tanayi tana waige waige sai adu'a neman sa'a take cikin saurin ta..

Ta iso gab da kofar dakin nasu....

Khadija Daga cikin dakin tana moppin dan yarima ya ce babu wata baiwar da zatayi aikin sai ita rashin aikinyi ne ya sa har suke shashanci awaya '' cikin gajiya da aikin da ba ta Saba ba...

Ta iso daidai kofar dakin zatayi moppin har tasa tsumma saita ga baya goguwa sossai..

Hakan ya sa tasa hannun ta ta murda handle kofar ahankali zata bude...

Ita Ko Fulani Jin ana kokarin bude kofar ya sa ta make da bangon lungu tare da toshe hancin ta....dan kada ta ji numfashin ta...

Cigaba da moppin dînta tashiga yi tana yi tana fadin wash Allah yau dai naga takaina Yarima haka yake babu tausayi....

 Rahama ce ta iso wajen nata cikin tsananin mamakin uban aikin da take yi ta ce haba ƙanwata dakin barshi nayi.

kokarin amsar moppan take hannun khadija...

Ita Ko khadija sai Fadi take Ah Ah wallahi kibarshi zanyi da kaina kada yaya ya fito yagan mu....

Yarima daya fito Daga dakin nasa cikin shigar sa na lauyoyi tare da hulan lauya akansa kallon time ya yi yana tafiya hakan ya sa ya leka dakin Rahama ganin ba ta nan ya ce Hubby hubby hubby kina ina ne m'y Wife...

Jin babu Alamun ta ita da khadija ya sa ya yi hanyar fita Daga dakin nasa..

Yaci karo da Rahama da khadija suna moppin tare...

Kallon Rahama yake babu Ko kiftawa soyake ya wuni da ita dan yanuna mata zallan so da kaunar da yake mata...

Wuyar rigar sa ya gyara tare da yin gyaran murya...

Hakan ya sa khadija ta dukar da kanta akasa ta ce yaya ina kwana..

Lafiya lau baby na yabata amsa atakaice...

Tare da maida kallon sa a kan Rahama da Idanun su suka tsarke cikin juna wani kallo yake binta da shi masu manufofi da dayawa..

Cikin yin kasa da murya ya ce hubby zan tafi Kotu ki kulamun da kanki kinji Ko..

Kada masa kai ta yi ganin Khadija ya sa duk tasa bashi wata Amsa...

Cike da ladabi ta ce Amjad daman ina son inje gun mamy da Anty inkaban dama....

Kallon ta yake ya ce Ah haba to kibari zan kira Karima ta yi miki j'agora har dakin su 'Fulani har wajen Mama karama zaki je ki gaishe su idan na dawo zan sameki acen sashin Mamy amma kada Khadija tabiki ta zauna daki..

Rahma cikin yin kasa da murya Alamun roko ta ce pls Dan Allah ka barta mu je tare kafana kafar ta ta mairairaice fuska...

OK ya furta yana kokarin sa kai zefi ce..

Ita Ko Fulani zazzare idanu tasoma Jin takun tafiyar Yarima...

Cike da nutsuwa Rahama ta take masa baya..

Daidai saitin da Fulani take nan Rahama ta tsaya hakan ya sashi waigowa ya ce hubby harkin iya rakon miji Ko uhmm nasan Asiya ta koyamiki

Rau Rau da idanu take kallon sa ta ce Asiya kuma wacce Ko auren ba ta dashi..

Murmushi ya yi ya ce nasani mana amma ai tafiki wayewa

..hannayen sa ya sa tare da tallafota suna Jin numfashin juna '' kiss dîn ta ya shiga yi yana fadin uhmm kamar dai mu koma cikin daki my hubby...

Murmushi ta sakar masa cikin cool voice din ta ta ce Amjad dîna Allah yakaika lafiya yatsare hanyar ka '' ta tafiya da ta dawowa gida..

Allah yarabaka da sharrin Karfe '' ameen ya furta tare da manna mata kiss a goshi...

Ita Ko Fulani sai kallon su take tana zazzare idanu gashi ta toshe bakin ta da hancin ta...

Sakin hannun Rahama ya yi ya ce wife zanturo miki Karima kedai ki shirya saina dawo yafada yana kokarin barin wajen...

Ita Ko Rahama juyawa ta yi dan komawa cikin dakin ta...

Cikin hanzarin sa ya sakai zefi ce haryakai bakin kofar Fita yaga Bayi masu tsaron Sashin sa..

Cike da ladabi suke gaishe shi Barka da fitowa ranka yadade Allah ya ja zamanin ka dan Sarki jikan Sarki...

Yarima kallon su yake yana kada kai ya ce nagan ku kamar bakwa cikin hayyacin ku...

Daya Daga cikin su ya ce babu komai Ranka yadade '' gimbiya Fulani ciki zata zauna ne harsai kadawo ne dan zamuje cin abinci yakarashe zancen cikin ladabi...

Yarima cikin tsananin mamaki ya ce Fulani ba ta ciki ai waya ce muku ta shigo..

Ranka yadade tana ciki kila tana sashin Gimbiya Rahama ne...

Yarima beko tsaya bin takansu ba kai tsaye yajuya zuwa ciki sai dube dube yake yana tafiya cikin hanzari da zafin nama.....

Ya shiga har dakin Rahama ya duba Sam bega Fulani ba ya duba sashin nasa nan ma be ganta ba...

Rahama cikin mamaki ta ce wai Amjad me kake nema ne..

Shiru ya yi yana kallon ta ya ce Fulani ba ta shigo ba kada kai ta yi Alamun A'a...

**************************

Karfin iko yana shigar da Karima gidan Yarin '' ya rinƙa dukan ta da bulala ba kakkautawa '' wani razananne kara ta saki tana fadin wayyo Allah na Ya Allah ka cece ni ya Allah ka kawo mun dauki..

Karfin Iko dake tsaye a kan ta dako riga babu a jikin sa..

Duk kirjin sa ya tattashi Saboda azabar wahalar da yake ba Karima....

Yana cigaba da dukan ta har sai da kayan jikin nata suka yayyage dukan jikin ta jini tsiyaya yake....

Cilla ta ya yi da kafa ta fadi kasa wargas...

Wani kofi ya je ya dauko mai dauke da ruwan gishiri..

Tana kallon sa da Idanun ta da suka kafe babu digon hawaye ta ce InshAllah abun da kayi mun sai Allah ya yi maka wanda ya Ninka nawa....

Dariya ya bushe da shi ya ce shegiya bakin ki be mutu ba Ko..

To. Yanzu zan murje bakin naki...

Ruwan gishiri dake hannun sa yadauko tare da nufar ta cikin wannan Jinin dake tsiya a jikin ta da raunuka ya zuba mata shi yana murzawa da karfin sa..

Wani razananne kara ta saki wanda amon muryan ta saide ya je kunne iya firdausi da take dakin nata tana kukan Abun da akewa Yar ta..

Jin bazata iya jurewa ba ya sa ta fito cikin hanzarin ta zatayi sashin Yarima Samad...

Bayi masu tsaron kofar suka ce bazata wuce ba '' saide tajira kamar fita zeyi yanzu zata ganshi......

Shiko Yarima fitowa ya yi Daga dakin nasa adu'oi yatsaya karantawa dan yama mance kwata kwata beyi ba.

Ita Ko Fulani gajiyar da ta yi awajen aboye ga zafi ya sata sakin tari me karfi..

Yayi daidai da karasowan Yarima daidai wajen..

Wayar sa ya kunna tochla din sa '' tare da haskawa dan ganin meye awajen..

Caraf Idanun su suka tsarke cikin juna shida Fulani cikin.....

Ta ku har kullum kyauta Daga Allah7️4️

09069080725

Shida Fulani cikin tsananin Mamaki ya ce Mama Fulani mekike anan lungun ya tsura mata dararan Idanun sa '' masu kwarjini..

Fulani gyara Tsayuwar ta yi tana saki tarin dayazo mata lokaci daya '' cikin Rawar murya ta ce daman nazo inma ka wasan April koka mance yau ne first....

 Cike da kallon tuhuma da yake bin ta da shi ya ce inaga nidake ba abokan wasa bane inma haka ne din ma '' 'meye zaki shigo lungu acikin lungun nake ne Ko a daki acen zaki sameni Ko.

Gayamin me kike nema a lungun nan' 'hannun ta yake kallo ganin makullai dakin nasu cikin tsananin mamaki ya ce mama Fulani wayannan makullan fa ina kika same su..

Cikin Rawar murya ta ce makullai kuma ban san ya'akayi sukazo hannuna ba..

Mika mata hannun sa ya yi ya ce miko min ingani yana karba ya tsurawa makullan idanu ganin SD a jikin makullan ya tabbatar masa nasa ne ba zargi bane..

 Nan da nan annurin dake kwance saman fuskar sa ya ba ce bat ya murtuke fuska cikin rashin mutunci irin nasa..

Ya ce Hajiya Salamatu kike Ko Fulani ni Sam bana iya tuna ainihin sunan naki...

Cikin tsawa ya ce zaki gayamin abun da makullan dakina suke yi a hannun ba tare da da izinina ba...

Koko so kike mu je gaban Sarki acen zakiyi min bayani...

Cikin Daga murya yake mata magana wanda ya sata gigicewa cikin tsananin tsoron yanda ya canza launin sa..

Ta ce pls dan Allah katsaya zan maka bayani Karima taban makullan ta ce bazata samu damar bude mun dakin naka ba...

Gashi ina son naje naga surukata insan ya ta tashi..

Kasaitaccen Murmushi ya sakar mata cike da takaici ya ce uhmm wasa farin girki yaushe kika fara damuwa da iyalina ban sani ba...

Karki damu lafiya lau ta '' ta tashi.

 mu je Ko yana nuna mata hanyar fita Daga sashin sa

..

Sum Sum ta fito cike da kunya tana gaba yana bin ta abaya yana Girgiza kai cike da mamakin me yakawo ta..

Cikin hanzari da saurin ta tafita sashin Yarima '' kofar fita ta iske Iya Firdausi tsaye tana kuka hawaye shar shar...

Cike da tsananin mamakin meya kawo ta '' cikin zare idanu ta ce iya Firdausi mekike yi anan gashi tana tsoron Yarima yaritsa da ita tsaye anan wajen hakan ya sa ba ta jira amsar da iya firdausi zata ba ta ba.

Tasakai tawuce cikin sauri sauri..

Daidai da fitowar Yarima da mamaki yake kallon saurin da Fulani ke zubawa.

Dawo da kallon ya yi a kan iya Firdausi dake kuka ya ce Mama cike da girmamawa me kikeyi anan wajen ya tsareta da idanu gashi time na tafiya dan baya Jin zeje gun Mamy..

 

Tsagaita kukan ta ta yi ganin Yarima na shirin tafiya dan yama manta ya ce a kira masa Karima taje ta taho da Rahama cikin masarautar...

Tsintar Murya Iya Firdausi ya yi tana fadin.

Dan Allah Yarima katsaya Karima ce tana hannun Karfin iko dan Allah kataimaka kada ya yi mata illa takarashe zancen cikin tsananin kuka mai tsuma rai..

Cak yatsaya tare da waigowa Arazane ya ce Karima !! Karima !! take hannun Karfin Iko..

Be jira amsar iya Firdausi ba kai tsaye ya yi ɓangaren gidan Yarin zuciyar sa tana harbawa da karfi

 idanuwan sa sun rufe baya ganin gaban sa sai duhu...

Tun daga Nesa Karfin Iko ya hango Yarima zuwa hakan ya sa ya yi maza ya sa Rigar sa tare da barin inda Karima take ya dawo da zaman sa kan kujera kan sa aduke...

Yarima kamar anjefo shi Daga Sama haka ya karaso wajen yana bin Karfin iko muguwar kallo ya ce kai dan iska ina Karima take bakin sa na Rawa...

Karfin iko cikin farga ya ce tana ciki ranka yadade...

Wani tsawa Yarima ya daka masa ya ce shege dan iska shiga ka fito mun da ita za ka gayamin uban daya daure maka gindi A'cikin masarautar nan..

Karfin Iko cike azzama da tsoro ya je kiran Karima ganin kamar ba ta numfashi.

Yasa shi ruɗewa yasoma jijjiga ta cikin tsananin mamaki ya ce Karima bude Idanun ki '' ga Yarima nan..

Takun tafiyar Yarima yaji ya shigo ciki cike da mamaki yake kallon Karfin iko da Karima dake kwance kamar sumammiya' '..

Karfin Iko cikin tsoron Abun da zeje yadawo ya ce InshAllah Yarima zata farka bekarasa fadin abun da zefada ba Yarima ya daka masa tsawar daya gigita shi..

Cikin gigita yake kallon Yarima' ɗuk yabi yagama tsoracewa hakan ya sa cikin hanzari ya samo ruwa tare da dawowa gun Karima ya yayyafa mata...

Amma still dai shiru ba ta motsa ba.......

Wayar Yarima ce tasoma ring yana dubawa yaga Kiran Faruk ne..

Babu ba ta lokaci yakara wayar a kunnen sa cike da damuwa kwance a kan fuskar sa amma Idanun sa nakan Karima dake kwance..

Ya ce Faruk dafatan dai lafiya kuwa..

Daga can ɓangaren ya ce kai kadai ake jira kai ka san Alkali badan shar'iar ka ba ce wlh ba zai saurare ka ba..

Dan kawuce time amma nace su fara gudanar da wani shari'an kafun naka..

Yarima cikin gamsuwa da bayanan Faruk ya ce godiya nake yanzu babu ba ta lokaci InshAllah zantaho nima wani uzurin ne ya rike dafatan kuna Tare da Aminu Ko..

Faruk ya ce eh gashi cen zaune yana chat.

Daga haka suka yi sallama...

Shiko Yarima dawo da kallon sa ya yi a kan Karfin iko dake ta faman yayyafa wa Karima ruwa...

Bangaje karfin Iko ya yi sai gashi yafadi akasa wargas yana nishi kamar wanda ya yi wasan tsere...

Yarima durkushewa ya yi gaban Karima yana kallon fuska ta yanda take walwali Idanun ta arufe gam...

Hannun ta ya ɗaga tare da soma dan buga a hankali '' still dai shiru kake ji..

 Hakan ya sa da kansa yadauki wannan Kofin ruwan da karfin iko ya ajiye agefen nasa...

Ya dauka yana kallon ruwan yanda duk datti yataru acikin sa...

Cikin Daga murya ya ce kai Karfin iko kake Ko Iko nima Sam bana gane sunayen ku kaida wasu agidan nan..

Banza dakiki maza je ka dauko mun ruwan Swan afirij din yan yari...

Shiru Karfin iko ya yi yana kif kif da idanu cikin Rawar murya ya ce Ranka ya dade ai jikan Sarkin Marwan ya hana asa ruwa a firij din sai dai na rijiya.....

Wani mugun kallo Yarima kebinsa da shi tare da tashi tsaye ya ce what waye ya isa ya canza dokar da nasaka babu izinina...

Na fada maka babu wanda ze shiga gidan Yarima sai inhar ankama shi da laifi da shaidu..

Inada labarin baku daina azabtar da bayi ba bisa zalunci kai har ka manta ni ne silan zaman ka anan da innaso sai inbar ka a cigaba da azabtar da kai... Ba wannan ba..

Miko min wannan ruwan hakanan ya Amshi ruwan hannun sa tare da karanto bismillah ya watsa mata a fuska sau uku...

Numfashi ta ja da karfi hade da sheshekar kuka sai fadi take dan Allah Karfin Iko ka kyaleni wayyo kar ka kashe ni..

Jin muryan Yarima ta yi yana Fadin Karima..

Bude Idanun ki Abdul Samad ne agaban ki...

Ahankali tasoma bude Idanun nata tasauke su a kan shugaban ta...

Ganin sa ya sa sabon kuka ya kwace mata...

Cikin kukan sai Fadi take ya shugabana kayi hakuri na take dokar ka ba tare da na iya hanawa an amshi makullan kofar naka ba..

Wallahi fin karfina akayi....

Rau Rau da idanu yake kallon ta cike da tausayawa cikin cool voice dinsa da Idanun sa da suka kawo ruwa ya ce uhmm Karima suwaye suka amshi makullan da karfin tsiya a hannun ki...

Dago kai ta yi tana kallon Karfin iko shima kallon ta yake yana Girgiza mata kai Alamun karta ce shi ne...

Kasa da kanta ta yi ta ce Karfin Iko shi ne ya amshe a hannun na...

Kallon kallo Yarima da Karfin iko sukewa juna ajiyar zuciya Samad ya sauke yana kallon Karfin iko dayaga Alamun tsoro ya bayyana a fuskar sa...

Ya ce kai dan uban ka waya ba ka izinin amsar makullan sirrina...

Karfin iko dake markakata bakin sa na rawa ya ce Yarima umarni na samu Daga Gimbiya Fulani da Jikan Sarki Marwan...yakarashe zancen yana dukar da kan sa Alamun neman afuwa...

Yarima Samad kallon sa yake yana nazartan kalaman da yanayin sa''' kauda kai ya yi Daga kallon sa yadawo da kallon sa a kan Karima dake kokarin tashi tazauna nauyin da jikin ta ya yi mata ya sa ta kasa....

Cikin takaici ya ce wannan mugun dukan da kayiwa Karima ka faffasa mata jiki duk jikin ta jini ne..

Wallahi saina fanshe shi kabari inje indawo amma kafun nan zanturo gangami ya kulle ka a dakin yari lamba uku inda yake kusa da masai nan za ka zauna tsawon wata daya tare da horo yunwa '' sau daya za ka ringa ci arana''' bulala kullum za ka ringa shan guda hamsin har tsawon wata daya wannan hukunci yana Daga cikin Adalci na....

Nan da nan Karfin iko yarikice ya san abun da Yarima Samad yafada babu me canzashi..

Karima Da ƙyar tamike cikin kuka ta ce shugaba na Da ƙyar inzan iya tafiya cike da tausayawa ya ce wai gayamin abun da ya faru mana....

Nan ta shiga bashi labarin abun da ya faru..

Jikin Yarima ya yi mugun daukan zafi tana kai karshen labarin...

Cikin yin kasa da murya ya ce zauna nan zanturo iya firdausi tazo ta tafi dake cen sashin ta zata kula dake har indawo InshAllah '' 'inada aiki a gabana yafada tare da barin gidan Yarin cikin saurin sa...

Cin karo da iya firdausi ya yi da take kuka cikin saurin da yake yi yana kallon agogon dake daure a tsintsiyar hannun sa..

Ya ce yawwa gwamma ɗana hadu dake Iya firdausi ina son kije gidan Yari ki dauko Karima ki ciccibe ta dan Allah ba ta iya tafiya..

Ki kira likitan masarautar mu ɗuk abun da yake yi yabari ya je yaduba karima kice injini

 yakarashe zancen tare da barin wajen ba tare da yajira amsar iya firdausi ba.....

Ita Ko Iya Firdausi cikin hanzarin ta '' tawuce wajen Karima zuwa ta yi ta ciccibe ta ta yi dakin nata da ita tare da kiran likitan masarauta dan yaduba ta....

Yarima daidai fita Daga cikin masauratar ya yi Horn mai gadi yana kokarin bude masa gâte..

Ya hango gangami cikin shigar su na masu kula da yan gidan Yari..

Ihu kiran sunan sa yyi hakan ya sa Gangami yakaraso cikin hanzarin sa..

Yarima cikin ba da umarni ya ce ina son kaje ka hukunta mun karfin Iko kaida yaran ka..

Sannan horo har tsawo wata daya har da na yunwa.....

Maida glass din motar sa ya yi ya rufe tare da ficewa cikin tsauri yabar masarautar cikin hanzarin sa..

Sam ya mance da batun Rahama tana son fitowa

Labarin abun da ya faru ya je kunnen Mamy dan kuskus akaitayi acikin masarautar..

Cikin tashin hankalin daya bayyana a fuskar mamy '' barin dakin ta ta yi tare da fitowa nan falo '' ta iske Ahmad zaune yana kallon video a tiktok sai washe baki yake musamman wata big baby da taketa tikan rawa cikin wakar turanci tana sanye cikin riga da mini siket ga karin gashi cike a kan ta '' tazubo shi '' Ko' 'ina sassan jikin ta motsawa yake..

Cibiyar ta yatsurawa idanu' '' yana Murmushi ''

Sam hankalin sa ya yi nisa besan da fitowar Mamy ba...

Sai ji ya yi ta wabce wayar Daga hannun sa''cikin fada ta ce baba na yaushe ka zama hkne kai ba za ka bar rayuwar yahudu da nasara ba da rayuwar Arna ba' 'meye ribar wannan video da kake kallon' 'cikin Daga murya take fada sossai Ahmad ya tsorace yau Mamy da kanta take hawar shi da fada haka.

Cilla masa wayar sa ta yi a kan kafar sa..

Ta ce maza kashe wayar nan biyo ni kaji abun da Ya faru da Karima baiwar Samad..

Cikin tsananin Mamaki ya ce Ah Ah meya same ta cikin gigita yake magana dan Sam baya Jin ze iya yafewa wanda ya taba Karima..

Tashi ya yi yakama hannun mamy cikin damuwa ya ce mu je Ko Mamy..

Yayi daidai da fitowar Hassana Daga kitchen Ahmad na ganin ta yadaure fuska cike da takaicin Mamy na wajen ya ce mata ina kwana..

Lafiya lau ta ba shi amsa.

Kallon Mamy take ta ce na ji kuna maganar Karima Allah ya sa lafiya Ko...

Nan Mamy tashiga ba ta labarin abun da ya faru '' '.

Ahmad bejira yaji karshen labarin ba..

Cikin zafin nama da saurin sa kai tsaye dakin iya firdausi ya tafi...

Hassana cikin tausayawa Karima ta ce gaskiya ba a kyauta mata ba..

Cikin yin kasa da murya ta ce yawwa mamy yau nakeson inje babban kasuwar kwatano Tokpa zanje indan yi siyayya kin san gobe tafiya ta..

Mamy cikin rashin son Rabuwa da hassana dan sun Saba ta ce haba hassana yanzu baki Daga tafiyar ba...

Hassana Murmushi ta sakar mata ta ce Mamy tun da nazo banga mijin naki ba '' daman ya rasu ne '' ko baya zama garine...

Mamy cikin tsananin mamaki take juya kalaman hassana Girgiza kai '' ta yi ta ce Ah Ah be mutu ba..

Idanu ta tsurawa hassana ta ce nayarda dake zanbaki labarina '' amma da sharadi...

Hassana cikin Jin dadin saukin kan Mamy ta ce meye sharadin InshAllah zan yi...

 Mamy gyara Tsayuwar ta yi tana fuskantar Hassana ta ce saikin gayamin abun da yakawo ki '' masarautar mu''

Kina gayamin gaskiya nima zakiji gaskiya abun da kika tambaya...

Hassana sossai ta yi mamakin Jin furucin Mamy..

Cikin tsananin kaduwa ta ce kibari mu je mu duba Karima' 'mu dawo Ko..

Ahmad koda ya isa dakin iya Firdausi iske Karima ya yi tana barci ga bandeji fari duk an nannade mata kai...

Hannun ta dauke da kalula ana mata karin ruwa..

Iya firdausi cikin kasa da murya ta ce Ah Yarima Ahmad kaine..

Eh nine yabata Amsa atakaice ina zuwa kawai ya furta '' be tsaya ba ta lokaci ba kai tsaye ya yi Sashin Fulani cikin azzama..

Yayi daidai da fitowar Mamy da hassana cike da mamaki suke kallon inda Ahmad din yashiga...

Mamy cikin gigita ta ce Yaron nan yanda yake tafiya ba lafiya bane '' mu take masa baya....

Ahmad da kafafun ya bankada kofar Fulani ya bude '' maida kofar ya yi yarufe tare da danna mata key...

Fulani zaune take tana yagan cinyan kaza...

Bata Ankara ba '' sai ji ta yi anbuga mata uban naushi abaki '' kashin kazar...........

Muje zuwa.

Ta ku har kullum kyauta Daga Allah7️5️

09069080725

Kashin kazar dake hannun ta faduwa ya yi ka san carfet '' cikin gigita ta dago kai take kallon Ahmad dake shirin kai mata wani dukan '' kaucewa ta yi cikin neman hanyar guduwa ta ce Ahmad haukar naka ya tashi ne daman ba ka samu lafiya ba..

Wani wawan rikon da ya yi mata ya sa cikin zazzare idanu ta ce Ahmad ka mance Koni wacece nifa matar kanin uban ka ce...

Me nayi maka ne '' da har za ka saka hannun a jikina takarashe zancen cikin kukan da yazo mata...

Ahmad dake huci sama sama cikin dagawa ya ce uban me Karima ta yi miki kika sabanta mata rayuwa zan babbalaki nima duk hukunci da za a dauka akaina adauka na yarda zanjure '' cigaba da bugun Fulani yake ta '' ta Ko ina sai ihu take tana neman ceto..

Mamy da Hassana suna ta bubbuga kofar cikin ihu take magana tana fadin Ahmad kabude kofar nan bakajina ne..

Ina bemasan tanayiba '' ihun Fulani ya karade dukan Masarautar.

Labari ya je kunnen Mai Martaba da Abban Marwan ga Ahmad nan yanata bugun Fulani '' bugun bana wasa ba.....

Hakan ya sa Sarki ya tura waziri ya je a balla kofar koda suka je kokarin su na balla kofar '' Mamy ta ce karku balla kamar ya tsai gaita da bugun nata '' 'cikin ihu ta ce babana dan Allah bude kofar nan' 'cikin tashin hankali take magana dan sossai Ranta yake aba ce...

Daga cikin dakin yana Jin muryan Mamy yakara damkar Fulani tare da kai mata naushi a bakin ta nan da nan bakin ya rinƙa tsiyaya da jini..

Razannannen kara ta saki' Kuka mai cike da tsoro Idanun ta sun canza launi zuwa ja' '' hannun tasa ta taba bakin nata taga jini yabi hannun ta cike da ruɗewa take kallon Jinin tana kallon Ahmad dake tsaye yana kallon ta '' hannun ya yi mata alamu cikin Daga Murya ya ce Inkika kuskura kikayi tari anan wajen saina taka ki..

Hannayen tasa ta toshe bakin nata tana zazzare idanu..

Jin karar buga kofar yaki karewa ya sa ya nufi inda kofar yake..

Cikin hanzarin sa ya bude kofar caraf Idanun sa ya tsarke cikin juna shida Mamy cikin bacin rai Mamy ta Daga hannun zata mare shi..

Hassana tarike mata hannun cikin magiya ta ce dan Allah karki mare shi Mamy ''

Waziri da bayi da hadimai da kuyangu harda Abban Marwan cikin hanzarin su suka Shiga dakin...

Ita Ko Mamy kallon Ahmad take cikin tsawa ta ce dan rainin hankali kashige ciki kajira ni ina zuwa make kafada ya yi Alamun oho Ko a jikin sa '' tun da ya yi abun da ran sa yake so beki duk wani hukunci da za ai masa ba....

Ahmad nawuce wa '' 'Mamy ta ja hannun Hassana suka yi cikin dakin Fulani koda suka Shiga iske fulani suka yi ana ta jero mata Sannu..

Abban Marwan rike da roban ruwan dumi yana gasa mata bakin nata...

Sai Wash take fadi tana ciza labban ta..

Cikin kidima Mamy ke kallon yanda Fulani takoma cike da rudani ta karaso gaban Fulani cikin muryan ban hakuri ta ce dan Allah Mama Fulani kiyi hakuri '' wallahi tallahi ban san ya akayi yaron nan Bejin magana ta ba...

Harara Fulani take watsawa Mamy cikin dauriya ta ce uhmm daman kin turo shi ne ya karasa ni ko''' bayan kinsa dan naki yana da mental problèm ba daidai yake ba..

Abban Marwan dake cikin Jin haushin Mamy cikin Daga Murya ya ce kinzo kiga Ko mata ta ba ta karasa bane Ko..

To wlh kujira kiga abun da zebiyo baya inban da rashin hankali Mata ta ze buga '' yaro mara Tarbiyya irin uban sa...

Ran Mamy yakai kololuwa wajen baci ta ce uhmm Ai mijina shi kuwa keda Tarbiyya ka san ance Albasa batayi halin ruwa ba..

Ahmad danka ne duk zagin da zakayi masa a kan ku ze koma amma InshAllah shi Allah ze wanke sa''bana goyon bayan sa dan kowa bewuce kuskure ba...

Takarashe zancen tare da kama hannun hassana dake shirin magana ta katse ta ta hanyar Jan ta suka fice...

Waziri cikin tsananin mamaki ya ce Ah Ah Fulani kinga ikon Allah ashe haka Yarima Ahmad ya yi miki mugun ta'asa...

Barin su ya yi dan zuwa sanarwa Sarki yanda abun ya ka sance....

Sarki na zaune cikin jama'ar sa yana sauraron dawowar Waziri...

Isowar Waziri ya sa Fadawa suka bashi hanya ya iso gaban Sarki cike da za kuwa ya rinƙa bashi labarin yanda sukaga Fulani...

Salati Sarki ya yi cikin tsananin damuwa ya ce Amma dai Ahmad wuyan sa ya isa yanka tome dalilin daya sa ya mata wannan dibar haukan...

Gangami ya nemi ayi masa iso '' 'babu ba ta lokaci Sarki ya ce ashigo dashi....

Cike da girmamawa ya shiga jerowa Sarki kirari..

Allah yataimaki Sarki Yarima Samad yabada umarni ahukunta Karfin iko' Kuma harna aiwatar Saboda sanin dokokin masarautar nan..

Bisa laifin dukan Karima da ya yi cikin umarnin Fulani a kan ta hana ta makullan sashin Yarima' 'shi ne Marwan ya ce ahukunta Karima yana kai karshen labarin.

Gabadaya wajen suka dau Salati..

Sarki cikin gyaran murya ya ce da dai ba Karima ba ce wata baiwar ce zan iya magana' '' iya firdausi da Karima '' yarima ne ya Fanshe su Daga masarautar zaria Nigeria dan haka banda ikon shiga wannan zancen...

Duk abun da Ahmad ya yi wa Fulani abu daya zan iya shi ne in hana shi kada ya sake amma adokar masarautar nan babu hukunci a kan wanda yadauki hukunci a kan antaba baiwar sa.....

Iya Firdausi itama baiwar Yarima Samad ce ban san yanda abun ya juye takoma sashin Fulani ba....

Gangami ya ce Allah yataimaki Sarki zankoma daman dukan zancen kenan daya kawoni Daga haka ya fi ce...

.........................................

Yarima Samad '' cikin murnan Nasaran daya samu a kotu kan wannan matar da Aka ɗAnnewa hakkin ta...

Takardun ta da komai ya mika mata..

Cikin kuka mai tsuma zuciya ta ce Yarima nagode Allah ya saka maka da Alkhairi yanda ka taimakeni InshAllah zan taimaka maka...

Cike da mamaki Faruk da Aminu suke kallon ta...

.

Yarima ya ce bangane zaki taimaka mun ba..

Hajiya zulai '' cikin ɗAnne kukan dayazo mata '' ta ce ina masaniya a kan wannan baiwar da kake nema shekara da shekaru ɗana...

Cikin zazzare idanu Yarima ke kallon ta cike da nazartan kalaman ta ya ce wace baiwar kenan kike magana a kan ta..

Hajiya zulai cikin yarda da kan ta ta ce Saratu mana baiwar Mahaifiyar ka habiba ''...

Yarima Samad cikin hada rai ya ce kin san inda Saratu take kika kasa gayamin '' to ya akayi ma kika san ina neman ta

ina da ayar tambaya a kan ki....

Faruk da Aminu dake tsaye wajen suna sauraron su''suka ce kwarai kuwa zancen ka haka yake Yarima....

Zatayi magana wayar Yarima tasoma ring' 'yana duba wayar yaga Mamy ce hakanan yaji faduwar gaba cikin dauriya ya Daga wayar ta...

Daga can ɓangaren ta ce inafatan ka gama abun da kake ina son ganin ka yanzu gidan nan ba ta jira cewar shi ba ta katse wayar...

Rike da kugun sa yake kallon Su Faruk ya ce muna iya tafiya na so inje gidan Su Faruk ingaida iyayen nasa kaima Aminu mu biya naku gidan '' Daga baya zankai Rahama ta gaishe su...

Faruk ya ce Ah kar ka damu wani uzurin yana gaban wani naga kamar Mamy ke neman ka mu je dukan mu.

Ko zuwa gobe saikaje gidajen namu aiba bakon waje bane a wajen ka...

Yarima ya ce godiya nake Abokaina dawo.da kallon sa kan Hajiya zulai ya yi ya ce wannan sirrin da kike da shi kina tabbaacin zaki sanar mun komai kowani zaki gayan ki boye wani...

Hajiya zulai cikin tsananin mamaki yanda yake zaro zance.

da ya yi magana inyayi shiru za ka ce bashi bane ya yi kalamin ba...

Ta ce Yarima wannan hakkin da Aka kwace mun ka karbo mun wlh hadda hakkin daure wa karya gindi shi ne Allah ya nuna mun ishara ina nufin Nina boye Saratu agida na watan uku Sannan ta bar kasar ''...

Cikin razana suke kallon ta dukan su''yarima innaliahi kawai yake ta maimaitawa acikin zuciyar sa..

Ya ce hajiya zulai maganar mu dake mai tsawo ne...

Tun da nasan gidan naki nan da kwana uku innagama uzurin gabana zamu zo nida Abokaina harda Mata ta...

Sossai ta ji dadin furucin sa Daga haka suka yi sallama...

Faruk motar Samad ya shiga '' Shiko Aminu ya ja tasu motar da suka zo da ita kotun....

Ahanyar su Yarima Samad ya ce ka ga yanda Allah yake ikon sa Ko...

Wannan matar ta yi AlKawarin zata gayamana inda Saratu take InshAllah mun kusa kawo rabin matsalar gidan mu...

Faruk ya ce gaskiya kam haka ne.....

**************************

Kano

.

Mama ita da Aminiyar ta zaune gaban wani tsohon malami yana jan carbi dago kai ya yi yana kallon su..

Ya ce Aishatu gaskiya wannan matar saita haihu kuma tagwaye ne acikin nata mace da namiji...

Abu daya zakiyi shi ne kisa mata guba acikin abinci taci ta mutu..

Koko kisa mata maganin daze barar mata da cikin nata cikin ruwan shan ta...

Amma asiri ba zai kamata ba dan tanada kariya sossai tattare da ita ba ta wasa da karatun Alkur'an..

Sannan adu'oi koda yaushe cikin su take '' 'mijin naku shima ba a iya samun sa..

Maganar gaskiya yafison wancen matar' Ke kuma yana tausayin ki ne a matsayin matar da mahaifin sa ya yi masa zabi kuma ya haramta masa rabuwa dake....

Sai maganar Diyar ki Salma kuna son akashe wannan auren' 'shi abune me sauki' '' saide mijin nata yanzu da gaske yana son Salman ya tuba a kan laifin sa na baya...

Yakuka. Gani dago kai. ya yi yana. Kallon su....

Aminiyar Mama ajiyar zuciya ta sauke cikin yin kasa da murya ta ce ai kawai araba auren nan...

Akwai wanda zamu hadata da shi wani Alhaji Ibrahim bushasha...

Sossai Malam ya yi mamaki ya ce Alhaji Ibrahim baya kasar nan fa...

Aminiyar Mama ta kwace zancen hannun malam ta ce yana garin mana '' 'har waya muna yi dashi...

Shiko shiru ya yi yana Girgiza kai yaso ya yi magana amma Aminiyar mama ba ta bashi dama ba...

Mama ta ce uhmm ni dai araba auren so muke yazo har gida yabata Takardan saki har uku...

Malam ya ce babu matsala cikin da take dauke da shi ya zaku yi...

Mama ta kalli kawar ta tana jiran amsar ta...

Kawar ta ce kawai Malam a barar da cikin me zatayi da wani ciki Ana neman wani sabon miji........

Malam ya ce uhmm gaskiya ba zan iya lalata cikin ba '' Amma zan iya raba auren Daga haka dai suka yi abun da za su yi.

Ya sallame su...

Ahanyar su ta komawa gida Mama ta ce ni dai ina son Sa'adatu wannan cikin jikin nata ya bare wallahi niban haifi tagwaye ba ita ce zata haifa...

Kawar mama ta ce karki ɗamu kamar jibi za su dawo Ko '' sha kurumin data dawo ki sanar mun...

Cike da Jin dadi suka taba hannun ita da Mama.....

Sheik zaune kofar gidan nasa yana kallon ta inda Mama zata taho dan tafita babu izinin sossai ransa ya baci....

Zaune yake yana nazarin ina take zuwa ne. Kullum tun da yadawo ba ta zauna ba...

Kukan zuci yake ya ce Abbana mahaifina kaine ka hadani da Ayshatu nasan rabon yaya ne ya koka tsakanina da ita...

Amma tun da na aure ta banji dadi ba '' 'ya Allah kashirya min Aisha ta''' adua yake sossai A'cikn zuciyar sa...

Hango ta Daga nesa ita kadai tana tahowa ya sa shi maida kallon sa a kan ta...

Cikin. Tsoro da fargaban ganin mijin nata a kofar gidan nasu...

Jiki babu kwari ta karaso, wajen tana kokarin wuce shi...

Taji yana fadin Aysha dakata dan Allah karki dauke ni sakarai mana...

Cak ta tsaya cikin sanyin jiki ta juyo tana kallon sa ''...

Bakin sa na rawa ya ce Daga ina kike kuma da izinin wa kika fita sossai ya hada ransa...

Cike da tsoro ta ce magani naje siye...

Maganin me kike je siye yana kallon ta cikin ido...

Cikin yin kasa da murya ta ce maganin haihuwa mana''' naga tun a kan Salma bankara haihuwa ba...

Saboda tsabar mugun ta shi ne ka nemowa Sa'adatu maganin haihuwa nika kyaleni Saboda ba ka ya yi na..

Cikin kukan Borin kunya ta ce dan niba fara ba ce irin ka shi ya sa ba a sona...

Baka nemana a shimfida sai inhar Nice na nema....

Sake da baki Sheik yake kallon ta har dariya ta subuce masa besaniba.....

So yake ya yi dariya amma ganin ta ya sa yadaure...

Uhmm Ayshatu kenan ya furta cikin Jan sunan ta.

Ya ce me kike so inmiki wanda ban miki ba...

Kinzo kina kawo zancen shirme mara tushe...

Bana kwanciya dake uhmm dukan zancen banza kike yi ayshatu...

Kishin naki ne ya motsa Ko haihuwa ta Allah ce shike ba wanda yaso kuma ya hana wanda yaso...

Keda Allah yaba arzikin yaya wasu suna nan basu haihu ba kuma sun zauna lafiya...

Bâri kiji maganar gaskiya aure zankara kwanan nan InshAllah..

Mama jin kalaman sa ta yi kamar anbuga mata guduma akai...

Cikin zazzare idanu ta ce aure kace fa

..

Cikin yarda da kai ya ce eh mana kona wuce yin aure ne..

Dan haka maganar haihuwa kishirya Inkinada Rabo sai Allah yabaki..

Cike da takaici yawuce ta ya shige cikin gidan nasa yana juya kalaman na baya kwanciya da ita...

Zama. ya yi kan. Kujera yana Girgiza kai. Ya ce oh Allah mata iyayen sharri duk abun da kake musu wataran za su ce ba ka taba tsinana musu komai ba...

Barin wani tunanin ya yi tare da dauko Alkur'an mai girma yasoma karantawa.......

*******************, ***

 Kwatano...

Sossai Mamy take ta yiwa Ahmad fada a kan abun da ya aikata '' '

Koda ya Yarima ya shigo Jin labarin abun da Ahmad ya yi besa yaji haushi ba kuma be masa fada ba...

Zaune yake yana kallon yanda Mamy ta zage. Tana fada iya gaskiyar ta...

Saida yaga tagama ta zauna ya ce Mamy hakuri zakiyi damu fa..

Dan na Ahmad kadan ne a kan nwa yanzu ma dakin Fulanin da marwan zani...

Sallamar Rahama da Khadija ne Asiya da Salma suna biye dasu ya sa kallon sa yakoma kansu...

Ganin Rahama na cikin su ya fara kokarin dawowa hayyacin sa amma ina yariga da yadau zafi hakan ya sa bekara.kallon inda suke ba....

Cike da ladabi Rahama da Asiya da salma suka gaishe da Mamy amsa musu ta yi cikin yin kasa murya ta ce Rahama har kin iso '' 'nuna musu Kujera ta yi da su zauna hakan ya sa suka zazaauna Ko wanne su ya yi shiru..

Ita Ko Rahama satar kallon Yarima Samad take da sam hankalin sa baya kanta....

Mamy cikin son dakatar da shi ta ce bangane na Ahmad kadan bane me kake nufi Abdul Samad ta tsare da idanu...

Ganin ya tashi tsaye hannun sa dauke da katuwar ɗorina ya ce Mamy babu ruwan ki...

Cikin Daga Murya duka waɗanda ke falon saida suka tsorota ganin yanda jikin sa yadau rawa sossai kamar mazari..

Cikin zafin nama yajuya a fusa ce ze wuce kokarin tare shi Mamy take yi..

Ita Rahama cikin hanzarin tabi bayan sa ganin yanda yake zuba uban saurin sai fadi take Amjad Amjad Amjad....

Tsaya dan Allah dan Allah katsaya Nice Rahama..

Cikin.............

Ta ku har kullum KYAUTA Daga Allah7️6️

09069080725

Nice Rahama cikin hanzarin ta da zafin nama amma ina ya yi nisa sai buga sauri yake kafun isowar sa labari ya isa wajen Fulani ga Samad shima zuwa '' Fulani cikin hanzarin ta canza daki tare da kulle kanta ta cewa bayi karsu ga inda take...

Koda Samad ya iso yana ta dube dube '' 'cikin tsawa yake kallon bayin ya ce ina Shugabar ku take....

Bakin su na rawa suka ce ba mu inda ta tafi ba' '' ya yi daidai da karasowan Rahama da Mamy...

Rahama kama hannun sa ta yi cikin takaicin ashe haka ya iya fada '' ta ce haba Amjad dan Allah kayi hakuri duk da ban san mêke faruwa ba.

Ganin Mamy zatayi magana ya fi ce Daga dakin direct dakin Marwan ya shiga..

Marwan kwance yake yana Waya da Yarinyar da yake so ya aura...

Kamar Daga Sama yaji antake masa hannun sa dake rike da wayar da karfi wanda yajawo fashewar wayar a hannun sa''nan da nan hannun ya amsa Alamun gocewa...

Cikin gigita yadago kai ganin Yarima' Samad ne a kan sa Idanun sa '' babu annuri..

Wannan dorinar yake ta lafta masa ta Ko ina yana magana cikin ihu ya ce na rabaka da Karima da ka san wacece ita Sam ba za kayi mugun tunani a kan ta ba...

Karima ba baiwa ba ce '' tsagaita maganar sa '' ya yi yaci gaba da bugun Marwan yana ihu iya karfin sa...

Mamy da Rahama ne suka yi nasaran shigowa dakin '' 'cikin tsawa ta ce daman haka kuke kaida Ahmad bakuda mutunci''' kuma inhar rashin mutunci naku ya motsa bakwajin bari..

Yanzu dan Allah ni me kuka daukeni mara amfani kenan inhar ba ka daina bugun sa ba''' wallahi zanbar muku gidan naku'''.

Cak Yarima ya tsaya kamar an dasa shi '' cike da nadama ya juyo yana kallon yanda Mamy ke '' kuka '' cikin rarrashi ya ce dan Allah Mamy karkiyi fushi damu '' fushin ki '' 'musiba ce a gare mu..

Ban san yanda akayi nakasa iya contrôle din kaina ba....

Shiko Marwan da Allah ya cece shi be jigata ba''' ya fara neman hanyar barin dakin...

Mamy dake kallon sa cikin kalan tausayawa ta ce ɗana Marwan dan Allah kayi hakuri'' Nice Mamy dinka ka san ba zan taba yarda Samad ya zage ka ba..

Bare duka' ina neman Afuwa....

Marwan dake kallon ta''' cikin kuka dayazo masa '' ya ce Karki damu Mamy nasan ba za ki aiko shi dan yabugeni ni sheda ne '' kece ma kika dakatar da abun da yake aikatawa...

Kokarin fita Daga dakin yake '' 'yaji Mamy ta kama hannun sa''' ta rungume sa cikin kuka ta ce Marwan dan Allah kadawo a Marwan dinka na Asali dana sani' '' Nice nan na raineka '' Saboda me za ka juya mun baya '' 'ina tarbiyyan ɗana ba ka sossai take kuka...

Dukan ila irin jikin kowa dake dakin saida ya yi sanyi har shi Samad din..

Sossai yake nadaman daukar wannan dokar a hannun sa''' sai yanzu yake Jin dadin da Allah ya sa bega Fulani ba ''' da ita ce yakama abun ba zaiyi kyau ba...

Marwan cikin tsagaita kukan nasa ya ce Mamy InshAllah zanshigo sashin naki zuwa anjima yanzu zanje aduba mun hannuna ne kamar na goce '' yafada yana kokarin sakin jikin Mamy.....

Mamy Sam taki bashi damar tafiya da kanta tasa Samad yakira wanzam ya duba shi '' Koda wanzam yazo yana duba hannun ya ce gaskiya ya yi mugun gocewa zeji zafi inhar zan gyara'..

Mamy dake kallon Marwan ta ce kabari ya yi maka dan kada abun ya fi haka..

Wanzam ya shiga gyaran hannu Marwan yana ta ihu cikin Jin zafi da radadi da azabar ciwo da yake masa..

Gabadaya dakin kowa ya yi jugum yana kallon Marwan cike da tausayawa...

Sallamar Ahmad ne ya sa hankalin kowa yakoma a kan sa.

Mamy taresa ta yi tana ce shima yazo ya yi na rashin mutunci ne...

Ciki damuwa ta ce kai baba na meya kawo ka...

Ahmad ya ce ah ya ba zan zo ba nida dakin kanina marwan na ji abun da ya faru da shi ne '' shi ne nazo in jajanta masa yakarashe zancen tare da shigowa cikin dakin...

Kallon Asiya yake yanda ta yi shiru tana jinjina Al'amarin '' 'cike da isa ya ce keee baki isa gaisuwa bane....

Kowa ya gaishe ni acen bandake.

Asiya cikin rashin son magana' Kyale shi ta yi ba ta tanka masa ba..

Ransa ba ƙaramin baci ya yi ace kamar shi wai ze mata magana ta' '' amma ta kunya ta shi lallai zata san koshi waye agidan nan....

Nan dai aka gama komai

Mamy ta rinƙa kula da Marwan ba ta bari ya nemi abu yarasa ba..

Yarima Samad da Ahmad fadar Sarki suka nufa..

Inda suka iske Sarki zaune bayi suna masa fifita '' 'shigowar su ya sa ya fadada Murmushin' tare da fadin maraba lale da mazan fama...

Watau baku tsoro ko..

Yarima Samad cikin yin kasa da murya ya ce tsoho mai ran karfe...

Kayi hakuri a kan abun da Ahmad Yayiwa Fulani zan masa fada nan gaba kada yakara..

Ni kuma dai sai Adu'a abun da na yi wa marwan ina son komai yawuce duk wannan abun ya faru ne a kan taba Karima..

Basu San wacece Karima ba'' shi ya sa suke takata son ran su...

. Sarki dake kokarin gyara rawanin sa' 'ya ce bangane basu San wacece Karima ba..

Naga baiwar ka ce..

Yarima Samad ya ce eh mana baiwa ta ce...

Katse firan ya yi da fadin gobe in Allah yakaimu yan uwan Rahama za su wuce..

Sarki ya ce MashaAllah har lokaci ya yi babu matsala kadai shirya masu tafiyar Ko..

Samad ya ce na shirya komai '' rana kawai ake jira yazo..

Suna gama tattauna suka bar fadar Sarki cike da mamaki Sarki ke kallon su yanda suke tafiya komai nasu iri daya......

Anty cikin shigar ta ta atamfa sossai dinki ya zauna mata ajiki tasaka hijab din ta..

Wayar ta na ring cikin hanzari ta duba ganin yayar ta ce Daga can kanon cike da hanzari ta.

Ta Daga wayar Daga can ɓangaren ta ce Sa'adatu ance gobe zaki dawo in ji mijin naki...

Murmushi anty ta yi ta ce amma dai Sheik yacika zumudi shida ya ce mun aure zekara yakamata abawa Amarya hakkin ta Ko...

Daga can ɓangaren ta ce wai kina nufin dagaske auren zeyi ina ya samu matar auren ne...

Anty ta ce a Gabon ya samu kuma ya karba daman a jirace yake..

Amma Sa'adatu kina ganin beyi tsauri ai sheik duka nawa yake dazeyi mata uku ''..

Anty cikin jinjina kalaman ta ce yanzu sheik bekai 50 ba aduniya yaya ta kinga Ko haryanzu da karfin namiji ne fa..

Wallahi ya yi auren sa '' Allah yabamu tagari '' meye matsalar dazai sa kadamu kanka tun da mijin ka yana kula da kai yana kula da cin ka da shan ka lafiyar ka....

Mata dayawa wallahi rashin samun wayannan abubuwan ya sa suke gudun mazan su

Su kara aure ni wlh har gudummuwa zan bashi in auren ya tashi...

Daga can ɓangaren rasa abun cewa ta yi cikin kuka ta ce Sa'adatu ke anya kina da kashi a jikin ki kuwa...

Sossai Anty ta jinjina kalaman ta '' ta ce ban san me kika gani ba ya sa kika fadi haka ba..

Amma sai ince miki babu ɗan Adam dake rayuwa babu kashi a jikin sa...

Nasan kina magana a kan karin auren sheik..

Ba a aure ne '' ni ya aure ni....

Karfa ki manta yana da aure na aure shi..

Inhar nadauki hakan amatsayin laifi ne auren dazeyi kenan nima kuskure na tafka wajen amincewa da auren nasa..

Duk da Aminin sa ne yahada auren...

Numfashi ta fesar tana kokarin daukar jakar ta..

Ni dai Dan Allah mubar zancen auren mijina...

Daga haka suka yi sallama..

Ita Ko Anty tsaf ta fito inda kai tsaye sashin Mamy ta nufa dan kiran Asiya ta rakata kasuwar kwatano...

Tana isa sashin Mamy ta iske su Rahama cike da jin dadi ta rungume Rahama ta ce daughter kina nan..

Rahama ta ce eh antina bark da fitowa..

Cike da girmamawa anty ta gaishe da Mamy ɗasu Samad da Ahmad...

Kallon ta ta dawo da shi a kan Asiya ta ce yawwa Asiya zoki rakani kasuwar kwatano atamfofin garin ance suna kyau sossai...

Ahmad dake sauraren zancen nasu ya ce kwarai kuwa suna da kyau sunfi na Nigeria kyau da kwaliti...

Kasuwar zakije ne yajefo mata tambaya.

Anty ta ce eh nan zamuje nida Asiya..

Jin da Asiya za a je ya ce OK bari zan kaiku.

Salma ta ce nima zanje.

Ahmad cikin sakin fuska ya ce ai babu matsala..

Rahama tana satar kallon Samad da Idanun sa ke kanta yana jiran yaji itama me zata ce.....

Cikin yin kasa da murya ta ce nima......

Kema zaki je Ko be bari takarasa fadin abun da zata ce '' 'uhmm babu inda zakije agidan in gayamiki nima akwai inda zamuje nidake dan haka tashi Muje...

Mamy dake kallon rashin idon Yarima Samad ta ce uhmm ni kadai za a bari agida ne...

Samad ya ce ga khadija nan nabaki aron ta har indawo.

Sossai Khadija ta ji haushin hanata fita da ya yi gashi babu waya '' 'cike da takaici ta kasa boye fushin ta..

Ta ce haba yaya Samaɗ 'bekamata amun haka ba' kabari in raka su Asiya ka ga baki ne suna bukatar taimakon yar gari..

Sossai ya jinjina kalaman babu daman ya ce bazata je ba ganin yanda anty ta tsura masa idanu cikin yarda da zancen khadija...

Kasa da muryan ya yi ya ce to Allah yakaiku lafiya yadawo daku lafiya...

Mamy ta ce ameen babu komai ai hassana tana nan maida kallon ta yi a kan hassana ta ce yawwa taso mu je mu duba lafiyar Karima..

Bayan duk sun watse masu tafiya kasuwa sun wuce '' 'Yarima ya ja Rahama a mota da batasan inda za a kai ta ba........

Ko da Mamy ta isa wajen Karima iske ta ta yi zaune iya firdausi na ba ta ruwan shayi Da ƙyar take amsa...

Ganin Mamy ya sa ta kakaro Murmushi cike da kaunar Mamy tai mata alamu da idanu na Barka dazuwa..

Mamy ta karanci abun da take son fadi ya sa ta nufe ta cike da tausayawa sannu kadai take ta jerowa Karima '' 'iya firdausi na amsawa da yawwa.......

Hassana gyaran murya ta yi tana kallon iya firdausi ta ce amma gaskiya ba ƙaramin illa akayi mata ba' Koda yake ai yarima yadau mataki a kan wannan abun shida Ahmad...

Iya firdausi cike da Jin dadi ta ce wallahi banda abun da zan iya biyan Yarima Samad da Ahmad wallahi sun mun dukan mutunci nida Karima.....

Juyowa ta yi tana fuskantar Mamy ta ce dan Allah Mamy ki Amsheni Daga hannun Fulani akwai bayi dayawa a masarautar nan kuma tanada wasu bayin bayan ni dan Allah ki maidani a matsayina na yar wajen ki....

Sossai Mamy ta tausaya mata ta ce InshAllah zan aikawa Sarki takardan na janye ki Daga hannun Fulani '' 'itama Fulani zan aika mata saita nemi wata a madadin ki....

Saboda tsabar Jin dadi iya firdausi durkushewa kasa ta yi tana jerowa mamy godiya da adu'oi...

Yarima kiran Mamy ya yi yana tambayar irin kayan abincin da ze siyo wa Karima wanda zata ji dadin cin su...

Ganin tana dakin ne ya sa ta yi musu sallama tabar hassana a dakin..

Cikin Jin dadi ta zayyana masa duk abun da yadace da siya mata yakawo gida Daga haka suka yi sallama....

Ahmad koda suka isa kasuwar daidai parking space ya paka motar sa...

Habawa jama'ar wajen suna Ganin jikin lambar motar An rubuta Yarima Ahmad no 6..

Gabadaya wajen aka tattaru da masu son ganin sa basu taba haduwa da shi ba sai a hoto dan ana maganar '' matashi ne me cike da izza da takama........

Ahankali ya fara sauke kafafun sa Daga cikin motar wanda yajawo hankalin dumban jama'a wajen jiran suga fuskar sa.....

Fitowa ya yi gabadaya Daga cikin motar yana sanye cikin boyel fara ba ƙaramin kyau shigar ta yi masa dan ya samu din ki Daga kwararren tela...

Ganin Idanun mutane a kan sa ya sa ya hada rai sossai kamar be taba dariya ba..

Kokarin bude musu kofar yake Albarkacin Anty ya yi daidai da Asiya tana cikiniyar budewa...

Ganin hakan ya sa ya janye hannun sa yana hararan ta '' taka san idanu...

Tsaf tagane abun da yake Ganin su Anty ya sa ta sakar masa Murmushi tare da fadin yaya Ahmad basai ka bude mu ba..

Kawomu ma da kayi shima wani karin girma na samu awajen ka..

Drever dan Allah mu je ka kai mu shagon da zamuyi siyayya duk abun da take fade babu wanda yake Jin abun da take fadi sai shi da yake kusa da ita....

Sossai ran sa yabaci yana nanata kalmar drever''' a zuciyar sai fadi yake wlh saina gyara miki zama Asiya kafun kibar garin nan........

Jama'ar wajen sai kuskus suke ta yi. Suna fadin anya ba matar sa ba ce...

Wasu Daga cikin su suka ce gaskiya beyi aure ba sai dai in ita ce ze aura duba da irin kallon da suke wa juna yakawo cece kuce a kasuwar...

Wata mata acikin shagon ta le kowa ta yi dan kallon su cike da tabe baki ta ce amma wannan kamar matar sa baku ga yanda yake bin ta abaya ba '' yana Girgiza kai...

Ganin Khadija ya sa su Fadin kai yau khadija Turaki nan wlh ba mu taba ganin ta acikin gari ba...

Sai dai a hoto...

Babu ba ta lokaci suka cusa cikin kasuwar inda ya yi musu jagora wani babban shago dan yin siyayya '' ɗuk abun da suke hankalin sa nakan Asiya yana tabe baki aransa sai ayyana yanda ze hukunta ta yake....

**************************

Yarima Samad bayan sun gama siyayya kai tsaye wani babban wuri yakai su wanda sai wanda ya amsa sunan sa yake zuwa wajen....

Isowar Yarima Samad ba ƙaramin matukar bazata ya yi wa mutanen wajen ba..

Karanta sunan wajen nayi naga anrubuta SAMAD...

Cike da Mamaki Rahama take bin wajen da kallo..

Ganin su ya sa duk aka fara fitowa da duk waɗanda ke wajen dan oga yazo ba asan ganin kowa harsai yafita....

Rike da hannun Rahama suke.tafiya. Ma'aikata suna ta yi. Masa welcome

Hannun kawai yake Daga musu '' 'cikin isa da izza yakara rike hannun Rahama gam yana satar kallon ta ya ce kinga nan wajen.

KADA masa kai ta yi ya ce nan wajen na danki ne da zaki haifa mun' Kuma sunan ubansa zeci watau Abdul Samad kin san Saboda me zanyi haka....

Girgiza kai ta yi ta ce A'a saika fada cikin zazzakar muryan ta....

Uhmm wannan wajen...... 7️7️

Uhmm wannan wajen yana Daga cikin wurin da nayi shekara da shekaru ina mafarkin ki...

Rau Rau da idanu take kallon sa cike da tsananin mamaki ta ce bangane ba.

Fahimtar dani..

Ciikin da zakuwa ya ce Rahama yakamata kisan, wanene asalin mijin naki '' dan kisan yanda rayuwar auren namu ze tafi...

Cike da gamsuwa ta ce inajin ka Amjad dîna tare da maida kallon ta agareshi cike da zakuwa son Jin labari abakin sa..

Numfashi ya fesar ya ce Mahaifiya ta Asalin ta Yar garin bohicon ce cikin unguwar zongo...

Rahama cike da rashin Fahimta ta ce inane bohicon Amjad.

Murmushi ya sakar mata cikin sakin Fuska ya ce bohicon itama jaha ce me zaman kanta kamar kwatano '' amma asalin garin kamar kauye ne '' zamani yazo da sauyi hakan ya sa ba za ka taba iya kiran sa da kauye ba '' saide kwatano yana gaba da ita dan ita ce Capital din kasar Benin Republique...

Sossai Rahama ta jinjina uhmm Amjad cigaba da ba ni labari dan nima inba wasu anan gaba...

Murmushi ya yi ya ce wasu kamar wa Kodai yayan da zaki haifa mun su zaki ba labari..

Cike da Murmushi ta ce uhmm yaya kuma ina nagansu ni dai yanzu abar wannan zancen aci gaba da ban labarin baya....

A garin bohicon ne mahaifina Salihu Turaki ya yi karatu wajen mahaifin Mamy wanda ake kira da malam Ahmad sossai wannan malamin ya yi suna awannan garin Daga nisa ɗana kusa ake kawo masa dalibai karatu lokacin da Sarki Turaki ya tura yayan sa guda biyu Salihu da SANI GARIN BOHICON SANI YAKI ZAMA YA CE WAHALA AKE BASU BASU CIN Abinci kan lokaci...

Ya damu shidai ba zai iya zama ba shi kwatano ze zauna har yasoma guduwa Daga Makaranta yana yawon bin abokan banza wannan dalilin ya sa Sarki Turaki yadawo da shi gaban sa..

Yabar Salihu kadai a garin kwatano yanda ake ba mu labarin sa '' babu wanda yataba sanin Dan Sarki ne saboda yana mu'amalar sa kaman dan dabeda gata duba da irin suturar da yake sawa '' 'Malamin da yake koya masa Karatun Malam Ahmaɗ'' duk cikin daliban sa babu me yi masa biyayya kaman Salihu Ko lokacin da Salihu ya je Saudiya ya yi karatun sa ya yi degree acen Daga can ya samu wani babban aiki' '' mahaifin Sa ya ce Sam be yarda ba yana bukatar sa akusa da shi dan yanzu girma yasoma kamashi...

Babu yanda ya iya hakanan yadawo kwatano watan bakwai da dawowa malamin sa ya aika yazo garin bohicon yana son ganin sa....

Koda ya je garin yanata sake sake dalilin kiran gaggawan da ya yi masa bekawo komai aransa ba..

Yatafi garin bohicon '' a lokacin cikin shigar sa na Alfarma yatafi '' ya bakar motar sa jeep '' daidai kofar gidan Malam Ahmad ya paka motar tasa....

Bayan ya isa gidan sun zauna sunyi firan yaushe gamo' '' Sannan Malam Ahmad yazo masa da bukatar yanason ze ba sa daya Daga cikin yayan sa...

Sossai Salihu ya shiga damuwa dan bekawo aure akusa ba...

Malam Ahmad daya karanci damuwa a kan fuskar sa ya ce inhar kana ganin ba ka bukata ba zan matsa maka ba na yi wa yayana sha'awan samun miji irin ka nagartacce...

Jin wannan furucin nasa ya ce ya amince hakan ya sa a kira masa yayan sa mata guda uku '' dan manyan yayan nasa ba sa kasar suna misra..

Koda suka iso.

Farida.

Habiba.

Firdausi...

Salihu yana. Ganin su yarasa wacce ze zaba kawai lissafi ya kunce masa hakan ya sa ya yi amfani da llimin sa '' wajen yi musu tambayoyin da ya shafi Addini Ko wanne su ya ba shi amsa daidai gwargwado '' duk da basu son dalilin turo da akayi wajen Salihu ba '' amma Farida lokaci daya ta ji ta yaba dan batasan hakan yakeda kyau ba duk zaman da ya yi agidan nasu saida hutu yazauna jikin sa sossai...

Ganin yarasa Mafita ya sa shi tunanin inda ze bullowa Al'amarin '' tun da suka shigo dakin Sam Habiba taki Daga kai bare ta kalle sa '' sai dai yaji ta yi magana kanta aduke...

Yana son mace mai Alkunya '' kuma ya san habiba ciki da waje '' duk cikin su ba ta da hayaniya hakan ya sa ya ce ya ce sauran su bashi waje ze gana da Habiba sossai ran Farida yabaci ya za ai tana babba ze fadi haka....

Koda yagama tattauna da Habiba ya nuna mata yanason ta da aure kuma bakowa ne yaturo sa ba daman ya dade da wannan kullin aransa mahaifin ta ne ya ba shi damar yazo ya duba wacce ta yi masa '' 'shikuma yana da muradin sa ita ce...

Sossai ta ji dadin haka duk da ba ta nuna ba'''..

Koda sauran yan uwan nata suka ji labarin aure za a kulla tsakanin habiba da Salihu afili' 'farida ta nuna zallan kiyayyan ta....

Da hassada da bakin ciki ta yi magiya a kan mahaifin nasu ya janye auren da Habiba ayi da ita...

Shikuma ya ce besan da wannan zancen ba...

Amma zehada da wani yaron wani dan kasuwa Alhaji kawu.....

Sossai ta ji bakin cikin hakan duk da bashi taso ba ta amince ne dan shima akwatano za su zauna....

Masarautar gheuzo suka nemi auren Habiba aka basu kamar yanda suka bukata..

Komai ya kankama akayi auren Salihu da Habiba..

Farida da bilyaminu wanda ake. Kira da kawu....

Koda aka kawo Mamy masarautar babu kowa sai ita Abban Marwan beyi aure ''ba...

Sallamar me kawo abinci da kayan drinks su lemuka ne ya sa Yarima yin shiru yana kallon abinci cikin kasaitaccen murmushin sa ya ce Ramatullah ga abun tabawa muci indan mun gama sai aci gaba da labarin Ko...

Hada rai ta yi cikin wasa sossai labarin da yake ba ta ya yi mata dadi kamar wasan kwaikwayo take kallo ganin yanda yake ba ta labari daki daki kamar a gaban sa kayi...

Cikin tsare sa da idanun ta masu kashe masa garkuwan jiki '' ta ce uhmm daman lauyoyi akwai iya ba da labari '' tun da kace sai naci wani abun Sannan zakaban sauran labarin ''..

To kafara ci dan ni wallahi hakanan na ji bana sha'awar wannan abincin tana turo baki gaba..

Kallon ta yake cikin sakin Murmushi ya ce bakyaso Ko..

Gyada masa kai ta yi eh banaso saide Insha lemu...

Waini dan Allah ba ayin dan wake ne yau na tashi da bala'in kwadayin sa...

Kuma inhar banci ba akwai matsala...

Rau rau da idanu yake kallon ta tare da dauko kofi ya tsiyaya lemun yana kokarin kaiwa bakin sa '' 'Ya ce dan wake kuma Hubby meye hadin mu da shi nifa tun da nake sau daya aka taba cin sa agaba na..

Naga Mamy tana yawan cin sa amma saide taban labari..

Pls hubby karki ci ki fadi wani abun daban zan nema miki yana marairace mata fuska kamar ƙaramin yaro...

Hada rai ta yi sossai tasha kunu shi ne karo na farko arayuwar sa daya ganta cikin wannan yanayin cikin sakin kukan shagwaba tana bubbuga kafafun ta akasa ta ce wallahi ban yarda ba..

Ni dai inbanci danwaken nan ba akwai matsala fa...

Ganin hankalin ma'aikatan zedawo kansu ya ce to na ji zomu je cikin zongo na ji acen ake samun masu saida kokuma inkira Ahmad ya nemo miki amma fa wallahi zaki zubar masa da aji wajen siyan dan waken nan yana sakin dariya...

Uhmm babu komi aiba kashi ya je siye ba kawai bawa na bukatan abu ace wai da kunya siyan sa...

Yaji kunya din kila akwai yan matan sa ne a unguwar takarashe zancen tare da daukar wayar nasa ta ba shi...

Kallon wayar yake ya ce kash sarkin mayata wai Ahmad din ne zan kira yana kasuwa fa...

Ganin zata fara bubbuga kafarta ya sa shi fadin yi hakuri gashi na danna masa kira....

Ahmad dake kokarin saka kayan da anty ta yi siyayya yana zubawa a boots din motar sa...

Yaji karar wayar sa yana dubawa yaga Samad cikin hanzari ya ɗaga...

Daga can ɓangaren yana Murmushi ya ce uhmm kanina na kaina kana ina ne...

Ahmad najin wannan kirarin ya san aike ne wanda ba zai masa dadin zuwa ba...

Turo baki ya yi gaba ya ce yaya kenan fadi me zan maka...

Yarima cikin ba da umarni ya ce yawwa mata ta ce take son dan wake duk inda ake saida shi kaje yanzu ka nemo mata. Kamar a zongo ba a rasawa...

Ahmad cikin razana ya ce what banji da kyau ba yaya danwake fa kace...

Daga can ɓangaren ya ce eh shinake nufi yanzu nakeso fa '' 'mata ta ke bukata...

Cikin tsananin bacin rai ya ce kamar...........

Ta ku har kullum kyauta Daga Allah

Ta ku. Har kullum kyauta Daga Allah7️8️

09069080725

Ya ce danwake fa kanbuhu lallai '' cikin yin kasa da murya ya ce to yanzu de muna kasuwa sai na koma gida nakoma nasiyo mata dutsen...

Samad dake murmushin kalamin Ahmad ya ce na ji Ko Arfa ce ni dai kaje kuma ta ce asa yaji sossai Ko kuma kabiya super market kasiyo mata haddaden yaji...

. Cikin Kosawa da zancen Ahmad ya ce na ji bejira cewar Samad ba ya katse wayar maida kallon sa ya yi a kan Asiya dake kokarin zuba kayan nasu cikin mota ba '' suna gama zubawa yarufe..

Anty tashige gidan baya '' ita da Salma da khadija '' 'Asiya zata shiga Ahmad ya ce' Kai Asiya kunyi yawa abaya ke dan zo gabana mana ki zauna...

Cike da takaicin kalaman sa tasan da wata manufa akasa...

Hakanan taje kujerar gaba ta zauna ya juya ta dayan ɓangaren motar ta sa tare da zama mazaunin drever' '' kokarin tada motar yake..

Ganin sansanin yan kasuwa da yan shigo na fito '' duk suka jeru ana kallon sa wasu har selfie suke daukan sa Daga nesa ganin haka ne ya sa shi tada motar tare da tada kura awajen wanda ya yi sanadin wasu na fadin wai Allah ze kashe mana idanu..

Wata ta ce ba gulma bane yakai ku ba aiyana sane wlh maganin sa'idawa yayi..

Tuki yake yanata cin fada shikadai ya ce haba mutum beda ikon ya je wani wurin asirrince sai dandazon mutane sun cika a kan sa wannan dalilin ya sa duk son yawo na Inde ba ɗare bane to bancika yin sa ba...

Asiya hararar sa take ta gefen idanu' 'cikin yin kasa da murya ta ce in banda shirme irin na mutane me za su kalla a tattare da kai nagadai ba kyau kafisu ba..

Ko wani abu.ba..

Salma dake kujerar baya tabe baki ta yi ta ce haba Asiya wallahi Yarima. AHMAD aikuwa abun kallo dan yana kyau fiye da misali dan ya fi mijin Rahama ehee....

KADA kai Ahmad ya yi cikin takaici ya ce Salma kedai barta '' banda lokacin ta.....

Khadija da Anty dariya suke yi inda anty ta ce yi hakuri Ahmad '' Asiya haka take da wasa take....

Asiya ta karbi zancen ta ce haba anty wlh ba wasa nake ba..

Ke kuma Salma da kike cewa ya fi Yarima Samad kyau lallai na yarda bakisan me ake kira natural kyau ba wlh..

Habawa mijin kawata' 'hadadden namiji ne' ga kyau ga iya taku''' ga respect ga ilimi duk inda ake son namiji yakai kedai Salma bar zancen kawai Rahama ta dace.....

Ahmad sossai kalaman ya doki zuciyar sa sai sake sake yake yi a kan yanda ze gyara mata zama' '' murmushi ya yi ya ce Asiya bakiyi karya ba '' Ance yabon gwani yazama dole...

Shiru ne ya ratsa acikin motar '' babu wanda ke magana banda wakar dake tashi acikin motar da anty duk ta takura bude volume din ya yi duk yacika motar da wakar Hamisu break..

Wanda yake fadin

Ashe da rai nakeson sahiba ba da zuciya ta ba...

Komai ruwa da iska a kan ba zana daina kewa...........

Sossai khadija da Salma suke bin wakar.......

*****************

Rahama tana gama shan lemun kwalin exotic dake gaban ta '' cike da zakuwa ta ce yawwa Amjad ba ni labarin Da kake ba ni dazun nan..

Tsagaita abun da yake yi ya yi ya ce uhmm labari yasha ruwa inhar kina son inbaki full labari saide yau kimun AlKawari zakiban Zuman ki indan latsa...

Ta gane abun da yake nufi sai ta wayance masa ta ce bangane Zuma na ba..

In Zuma kake so akwai su anty tazo dasu roba nawa kake so...ehee

Kasaitaccen murmushi ya sakar mata

 cike da kaunar ta Ya ce uhmm Rahama idan munje gidan zan nuna miki inda Zuman take sai kibani...

OK ta furta tanajin faduwar gaba dan ya ambato mata abun da bataso '' 'cikin dauriya ta ce wani irin mafarki kakeyi akaina dakace anan muke haduwa...ina sauraron ka...

Naki wayau naki Rahama nafa gayamiki wal ba ni wal hanani wal keme me...

Yanda ya ja zancen ba ƙaramin dariya yabata ba...

Tsare shi da idanu tayi.

Gira ya Daga mata ya ce ya ce yes haka nake nufi gwanati ta hana aikin banza...

Tabe baki ta yi ta ce na ji shi ne harda latsamin Zuma abaki Ko dan ka ga na matsu shi ne za ka fake da abun da ban san mene ne shi ba da kake so...

Samad yin kasa da muryan sa yayi. Ya ce kema ai Zuman kika latsamin kika hanani kara latsa kinga munyi anko kenan...

Dan haka tashi mu je super market zamuyi wa Karima shopping kinsa mara lafiya saida kulawa...

Da ƙyar ta tashi Daga zaunen tana kokarin daukar jakar ta''' Ya ce Ah Ah bari nizan daukar miki Hubby na...

Yana gaba tana biye da shi abaya....

Ma'aikatan ganin basu wani dade ba '' cikin hanzari suka nufo su '' Daya.daga cikin su ya ce shugaba har za ka wuce ne...

Gyada masa kai yayi. Ya ce eh zan tafi ne in akwai abun da kuke bukata manager ya nemi ni...

Dan waje ne na shakatawa wajen wasan yara da manya sossai Park din yahadu hade da decoration dake WAJEN Samad aka. Rubuta '' Komai samad...

Uniforme din dake jikin ma'aikatan sa sanye suke da rigunan polo fari da Aka rubuta Samad Park da manyan baki....

Rahama sake da baki take kallon yanda jama'ar da suka zo shakatawa wasu da matan su' '' wasu da yan matan su'Wasu da yaran su da dai sauran su...

Duk akayi waje dasu Saboda zuwan su...

Ganin sun fito ne Idanun mutane yana kansu suna fadin wannan ai me waje da kansa ne yazo amma kunata fadin wani me kudi ne yasiye wajen...

Dan ya shakata da matar sa...

Sossai suka shagala da firan su' '' duk abun da suke fade Rahama tana Jin su..

Cikin su wata ta tsurawa Samad idanu kamar zata cinye shi...

Ganin kallon ya yi yawa ya sa Rahama kama hannun sa da yake kokarin bude motar sa...

Dawo da kallon ya yi a kan ta Daga mata gira ya yi ya ce wife ya akayi ne Ko mu koma ciki ne baki gaji ba.

Kada masa kai ta yi ta ce A'a kawai naga wata mayya tanason ta cinye mun kai adu'a zanmaka Allah ya kareka da sharrin idanu..

Ganin Rahama tarike hannun Samad '' suna face din juna ita dashi...

Sossai wajen suka dauki tabi harda masu daukan hoto da video suka dauke su ba tare da sun sani ba...

Wacce ta kurawa Samad idanu ganin Rahama na hararan ta taka san idanu ya sa tasha Jinin jikin ta...

Tana gama masa adu'a suka shige motar har suka bar wajen..

Maganar su ake '' nan da nan aka ringa daura hotunan su kan Facebook '' WhatsApp '' Twitter '' harda video da suka yi masu ba tare da da sanin su ba suka daura kan tik tok da sauran su....

Sheik zaune yana duba Facebook dan daura waazi yaci karo da wannan hoton Rahama da Samad saide Rahama sanye take da hijab hakan ya sa bacin ran nasa beyi zafi ba....

Daukar wayar ya yi yakira anty wacce yanzu ne suka isa gidan masarautar.

Tambayar Rahama yake ta ce basanan sun fita da mijin nata...

Cikin hanzari ya nemi ta turo masa nombar Rahama..

Anty ta ce kash ai inaga ba ta da layin kasar nan tun da tazo '' amma bara innemi na mijin nata tun da suna tare sai yahadaka da ita...

Babu ba ta lokaci tasamo lambar Samad gun Ahmad ta turawa sheik...

Sheik yana ganin sakon texte babu ba ta lokaci ya nemi Samad saida wayar takusa tsinkewa ya Daga ka sancewa yaga suna ya fito da baya Daga bakuwar lamba....

Cike da girmamawa ya ce Sheik imam bark da warhaka bayan sun gaisa Sheik ya ce haba Samad ya za ka bari a dauki hoton matar aure ana yadashi a social media '' wannan ba wayewa ba ce '' kamar kuna kyakwayon halin turawa ne....

Samad dake tuki parking Daga gefen titi ya yi ya ce sheik nifa ban san a kan wani hoto kake magana ba..

Ni banda taba daura hoton Rahama a kan social media ba' nasan illah haka amma kayi hakuri '' katura mun hoton da kake magana akai ban san an yi ba....

Sossai jikin Sheik ya yi sanyi ya ce kar ka damu ɗana dan naga kamar rungume kuke da juna da simple hoto ne ''na kamala ba zance komi ba...

Ka san yanda duniya tasan ni kuma tasan ka' Kuskure kadan ake jira afara cece ku ce....

Samad ya ce haka ne Sheik Imam zan kiyaye Daga haka suka yi sallama...

Mika wa Rahama wayar ya yi cike da shagwaba ta ce Abby kayi hakuri kaida Mama har yanzu bankira ku ba' '' bansamu layi bane '' 'amma na ji ance yau za a samo min...

Sheik ya ce UHMM RAHAMA INDE KINA LAFIYA NI BA DAMUWA TA BA CE SANNAN NA MANCE BAN GAYA MIKI ZANCEN AURE NA BA...

cike da zare idanu Rahama ta ce aure kuma Abby..

Eh aure mana yabata amsa''' amma matar da zan aura din bazawara ce'' Inkin samu layi zan miki bayani daughta Daga haka ya katse wayar...

Jikin ta ya yi mugun sanyi sossai Jin batun auren nan.. Maida kallon ta ta yi a kan Samad

 ta ce inajin abun da kuke fade kaida Abby uhmm mutane sai Aslow' Jin karar message acikin wayar sa ya sa ya bude whsap dinsa ganin hoton da video ba ƙaramin Girgiza shi ya yi ba...

Har yana nunawa Rahama itama mamaki ta yi ta ce uhmm yaushe muka rungumi juna kai wallahi wannan sharrin mutane ne.....

Murmushi takaici ya yi ya ce dadin abun ba kamani suka yi da kwartuwa ba '' 'mata ta ce dasauki ai....

Murmushi Rahama ta yi

Ta ce uhmm kaide Ko..

Ni dai me Ko karya nayi ne wife..

Girgiza kai ta yi Alamun a' a

Cigaba da tukin nasa ya yi babu ba ta lokaci suka iso gida...

Koda ya iso sun iske Ahmad baya gidan ya tafi neman danwaken jaraba...shida Asiya ya ce tun da kawar ta ce wlh ita zata je siye bashi ba...

Ahmad sharara uban gudu yaketa yi cike da tsoro Asiya ke kallon sa ta ce haba Yarima kar ka jefa mu a rami irin wannan gudun haka...

Ko kallon inda take beyi ba bare tasa ran ze tanka mata '' ganin abun nasa gaba yake yi duk inda ya gifta da motar sa sai ya tada kura '' ganin lambar motar ya sa har jami'an tsaro suka kasa tsaida su suna tsoron su tsaida shi su jawa kansu Wahala....

Gabadaya Asiya ta tsorace da lamarin sa babu damar ta yi fada gashi taga babu annuri a fuskar sa cike yake da takaicin wannan danwaken daze ba ta time din sa wajen siyen sa...

Koda suka iso Daga cen nesa ya yi parking din motar inda babu idanun kowa...

Shiru ne yaratsa acikin motar cikin ba da umarni ya cewa Asiya tabude motar tafita '' taje neman inda ake saida danwake inta samu tasiyo tazo nan yana jiran ta....

Asiya cikin tsoron ta yi magana ya huce haushin a kan ta '' tamika masa hannun Alamun yabata kudi...

Drower gaban motar ya bude tare da zaro jaka goma kudin kwatano yamika mata ya ce duk yanda yakama kawai ayi...

Cikin sanyin jiki tafita tana waige waige cike da tsoron unguwar daya kawo ta '' koda tasamu inda wasu mata suke zuwa ta yi ta tambayesu...

Taci Sa'a aka raka ta har gurin saida danwaken

Katuwar Wamer dake hannun ta saida suka cika mata' ta biya su' '' cike da jin dadin ta yi musu ciniki suka ce baiwar Allah amma wannan kular taki ta yi kyau sossai kamar ta zinare..

Murmushi ta yi ta ce nagode cikin azzama takoma inda tabar shi...

Cike da mamaki take kallon wajen ganin ba ta ga motar sa ba...

Daidai saitin inda motar ya tsaya.

Ta tsaya sai waige waige take babu Ahmad babu labarin sa..

Gashi ba ta zo da waya ba..

Daura hannun ta yi a kan ta cikin tsananin fargaba ta ce wannan Ahmad din meyake nufi dani ne...

Sake sake take awajen ita kadai atsaye......

*****************************************

Rahama da Samad kai tsaye dakin Karima suka nufa cike da godiya suke bin Yarima dashi...

Iya Firdausi ta ce gaskiya nagode bisa kokarin da Mamy ta yi wajen janye ni Daga ɓangaren Fulani...

Yarima cike da Jin dadin kalaman ta..

Ya ce babu komai iya Firdausi..

Maida kallon sa ya yi a kan Karima da ita shidin take kallo ganin ya tsura mata idanu ne ya sa ya sa ta sauke nata a kasa...

Cike da ladabi ta ce ya shugaba na nagode da wannan kulawar da kayayyakkin nan daka ba ni Allah ya saka maka da Alkhairi...

Rahama cike da tausayawa take kallon Karima ta ce inbabu damuwa zan so ingana dake Karima.......

Iya Firdausi najin haka ta ce Ah babu matsala bara in tashi inbaku waje...

Babu ba ta lokaci tafita dakin tare da nufar sashin Mamy.....

Shiko Samad kallon Rahama yake ganin yanda ta canza babu wasa a tattare da ita...

Cikin muryan ta me kama da wacce take cikin takaici ta ce Karima...

Karima dago kanta ta yi tana kallon Rahama cikin ido kasa jure kallon nata ta yi hakan ya sa ta yi kasa da Idanun ta

Rahama tashi tsaye ta yi ta rungume hannayen duka biyun a kirjin ta...

Ta ce Karima kinada Amsar tambaya ta..

Ina son ki gayamin meye tsakanin Fulani da Mamy '' da Maman Maryam '' da Maryam '' Abban marwan '' da Sarki '' 'a karshe ina son ki gayamin ina uban mijina yake kuma meye ya sa tun da nazo gidan ban ganshi ba....

Maida kallon ta ta yi a kan Samad da ya yi shiru yana sauraren ta bayajin ze iya dakatar da ita dan bega wasa a Idanun ta ba....

***********************

 Asiya daura hannun akai ta yi tana salati tare da ajiye Wamer din danwaken akasa....

Jin Horn a bayan ta hakan ya sa tawaiga taga uban waye a kan ta....

Ganin Motar Ahmad ne cike da takama ya fito Daga motar ya ce yar rainin hankali daura hannun da kikayi akai mutuwa akai miki ne..

Bata kula shi ba ta rinƙa sauke ajiyar zuciya akai akai dan tagama tsoracewa...

Cikin hanzarin ta tabude murfin motar tashiga hade da Wamer dake hannun ta....

Babu wanda ya yi ma wani magana har ya tada motar yana tuki yana kira'a tare da bin karatun Sudais......

Ita Ko kallon sa take ganin yanda ya nuna kamar besan da zaman ta a motar ba...

Koda suka isa masarautar '' yana parking din motar kai tsaye fadar Sarki ya nufa...

Ita Ko Asiya ta yi cikin gida...

Bakin sa dauke da Sallama ya shiga fadar Sarki....

Waziri da bayi masu yiwa Sarki fifita ganin Yarima yashigo be nemi ayi masa iso ba....

Dukan su sun sa babban magana ce tazo dashi...

Hakan ya sa dukan su suka watse bisa Al'ada in haka tazo fita suke yi abar Sarki da jikan sa....

Suna fita Ahmad yazauna tare da nannade kafafun zuciyar sa na kuna....

Sarki ya ce Ahmad Allah ya sa ba laifi akai maka ba..

Ko wani ne ya taba ka...

Ko Ko kanada wani bukata ne fadi Ko mene ne zan maka inma banda shi zan siya inbaka...

Kai nake sauraro...

Cikin tsaita nutsuwar sa ya dawo da kallon sa a kan Sarki cike da yarda da kai da shawaran da abokan sa suka basa

Ya ce Allah ya taimaki Sarki aure nakeso...

Sarki fadada murmushin sa ya yi ya ce wacece wannan yarinyar mai sa'a da zata mallaki wanna gwarzon na miji

Bakin sa na rawa ya ce bakowa ba ce illa..........

Masu karatu wakuke tunani Ahmad ze furta saina ji ra'ayoyin ku...

Ta ku har kullum kyauta Daga AllahƘANWATA

LITTAFIN NAN KUDI NE INKIN GANSHI A WAJEN GROUP DÎNA NA SATA NE

09069080725

7️9️

Bakowa ba ce illah Asiya..

Sarki ya ce wacece Asiya yar Gidan wacece agarin kwatanon nan....

 Cikin yin kasa da murya ya ce tana cikin bakin da suka rako matar yaya Samad kawa ce agun matar sa...

Murmushi mai cike da daddatako Sarki ya yi ya ce MashaAllah Abu ya yi har kun daidai da yarinyar Ko...

A'a ni basai mun daidai ta ba '' Kawai de ina son a aura mun ita ta zauna kar kashin iko na..

Dariya sossai Sarki ya yi ya ce ikon Allah duk ikon da kake yi a gidan nan da wajen gidan nan be ishe ka ba...

To daman inkana auren ta dole kayi iko da ita kar ka damu tun da kace a nema maka zance yakare zanyi magana da Sheik Abdurrazak nasan ya san iyayen ta ba zai gagara ba..

Cikin yin kasa da murya ya ce Sarki nifa ba na son auren yadau lokaci a sati daya kacal..

Sarki cike da izza ya ce Ah Ah haba Yarima Samad Ko kaza ce za ka dauko aika shirya bare ɗan Adam.

Auren Yayan naka ai daga sama aka dauro shi '' babu yakawo zeyi aure awannan garin '' duba da natsara Ko yana so Ko baya so Maryam ze aura awancen lokacin...

Kaga Allah ya yi hikimar sa tun da na masa aure babu izinin sa...

Shi ya sa na janye zancen Maryam din...

Kaikuma da kanka kazo da bukatar ka ga ina bukatar shiri sossai '' dan tare zan aurar daku kaida Marwan harda yar autar ku...

Gaskiya zuwa nan da wata daya zan gama shirina Daga nan azo asanya ranar aure...

Babu yanda ya iya cikin tabe baki da ba haka yaso ba ya ce uhmm ni dai baza a hada aure na ɗana kowa ba..

Maganar gaskiya sonake asan babu wani daurin aure sai nawa...

Maganar Marwan da Khadija saida kabar nasu bikin zuwa bayan an yi nawa '' ita khadija ta tsaida mijin aure ne....

Murmushi mai kayatarwa Sarki ya yi yana kallon Ahmad ya ce kwarai kuwa na dade da bayar da khadija uwar ta tasani tun da kace haka '' 'naji korafi ya karbu....

Sossai Ahmed yaji dadin Amincewar da Sarki ya yi hakan ya sa suka karasa fadin abun da yake so ayi masa sannan yabar Fadar yanajin saukin damuwar sa ta ragu....

Anty tabude kayayyakin da suka siya Mamy na dubawa daya bayan daya..

Cike da Jin dadi ta ce amma fa kun iya zabe sossai murmushi anty ta yi ta ce Ahmad ne ya yi mana zaben kin san ya san kan gari....

Asiya ta ce aikuwa dai Mamy ya iya zaben kaya kamar mace..

Yayi daidai da karasowar sa''falon caraf kalaman ta suka fada a kan kunnen sa...

Cike da isa ya iso falon ya ce aini nafi karfin kiyi misali na da mace...

Mamy cike da mamaki suke kallon sa ita da Anty da Salma da khadija yanda yake cika yana basewa...

Murmushi Mamy ta yi ta ce uhmm Babana maida wukan yabon ka take waika iya zaben kaya...

Cikin takaici ya ce shi ne zatayi misali na da mace banaso fa kigayamata ta fita idanuna....

Asiya ganin Mamy awajen ta ce Ayya yi hakuri bankarawa '' Wayar ta ce tafara ring tana dubawa taga kiran mamar ta ce hakan ya sa ta ce ni zan fita Daga waje ana dan Amsa waya.....

Ahmad bin ta da kallo yake har tabar dakin yana Ayyana kardai ace Farruk ne ya lalata masa shiri dan yaci Alwashin sai ya gyara mata zama duk da bawani abun zeyi da ita ba Daga baya ya sakar wa Faruk ya aura.....

Cike da zargi yabi bayan ta...

Mamy ta ce kai Babana ina za ka je ne kazo ina son ganin ka...

Cak ya tsaya tare da dawowa cikin dakin ya zauna....

Sallamar bayi ne hannun su riki riki da kaya wanda ya fito Daga Fada...

Cike da nutsuwa suka karaso falon tare da sauke kayan...

Daya Daga cikin su kanta aduke tana fuskantar Mamy ta ce ya shugaba ta.

Wannan kayan sako ne Daga Fadar Sarki..

Paper dake hannun ta '' tamika wa Mamy tare da dawowa gefe tazauna...

Mamy bude sakon ta yi tasoma karantawa kamar haka...

Kyautuka ne Daga Sarki..

Mama Karama..

Sani

Fulani..

Munce abawa bakin mu dazasu koma gobe dafatan Allah yakai su kasar su lafiya....

Sossai Mamy ta ɗara dan farin ciki ta ce ah basai na bude kayan nan ba..

Da kansu sun bude abunsu..

Kuma da kuka kawo sakon nan zan aiko khadija da tukwici ta kawo muku...

Cike da jin dadin Albishir da Mamy ta musu suka koma bakin aikin su...

Mamy kallon Ahmad ta yi dake zaune yana latsa wayar sa ta ce ka ga wannan kayan na bakin nan ne Sarki da su Fulani da Abban Marwan suka bayar a basu..

Anty dake sauraren ta ita da salma sossai ta ji dadin haka Itako Salma tsabar bakin ciki kasa zama dakin ta yi hakan ya sa ta ce bara taje tadawo ta zura hijabin ta tafita...

Anty godiya ta rinƙayi sossai tare da musu fatan Alkhairi...

Mamy shiga ta yi ta fito da nata kyautan ɗana Samad da kudin da ya bayar a basu...

Cike da Jin dadi mamy ta ce wannan gatan ta yi yawa..

Mamy ta ce ina gatan yake wanda kuka mana ya fi namu...

Kunbamu hasken gidan nan watau Rahama kun gama mana komai wallahi saide mu biku da adu'a...

Sossai anty ta yaba da hali irin na mutuntaka na Mamy...

Mamy ta ce kash banji dadi ba akwai yar autar mu tana kasar misra acen suke zaune da mijin nata ta ce jibi zata zo dan yi mana murna auren Samad ba ta samu zuwa a kan lokaci ba na so ku hadu...

Anty ta ce Ayya Allah Sarki karki damu wataran zamu hade ne InshAllah....

Mamy cike da Jin dadi ta dauko wayar ta ta dannawa yayyen ta maza guda biyun da suke saudiya kira babu ba ta lokaci suka Daga...

Daga can ɓangaren me suna Auwal ya ce Habiba yau da kanki kika kirani...

Murmushi mamy ta yi ta ce afuwan yaya Auwal ka san dai ina neman ka wani lokacin bana samun ku ne...

Daga can ɓangaren ya ce karki damu nasan da hakan yakike ya taro ya tashi kiyi hakuri nida Sani a satin nan zamu zo InshAllah nasan Abban mu yana bukatar ganin mu '' ga dan namu ya yi aure kinga yakamata muga surukar tamu....

Mamy ta ce eh wallahi yakamata ku ganta shima Abban namu Nina hanashi zuwa bikin Samad shida maman mu' to yanzu gida babu kowa Ka san masarautar nan ba zaune kalau ake ba..

Ba na son suzo suga abun da be musu ba' '' ka san kuma har gobe basu San mijina baya garin ba '' suna sani akwai matsala...

Auwal ya ce kai Habiba kina nufin haryanzu Abban besan da zancen ba

Ta ce eh besaniba...

Kaima dan Allah karku gayamasa na rokeku kaida Sani...

Karki damu Habiba ba zai ji ba InshAllah...

Tashi ta yi Daga inda take zaune ta tabo kusa da anty ta ce ga Yayana Daga Saudiya zaku gaisa...

Mikawa anty wayar ta yi cike da mutuntawa suka gaisa da Auwal din...

Auwal ya yi masu godiya sossai a kan halarci da suka yi wajen bawa dansa Samad mata...

Sossai anty ta ji dadin mutuntaka irin na yan uwan mamy Daga haka suka yi sallama...

Ita Ko Asiya waya take da mamar ta sun shagala sossai suna hira '' ta ji an wabce wayar Daga hannun ta da mamakin ta juyo dan ganin wanene ya yi mata wannan rashin mutunci...

Ganin Ahmad a kan ta hakan ya sa ta yi tsaki..

Kashe wayar ya yi gabadaya yadawo da kallon ta a kan ta...

Cike da isa ya ce nan fa ba gidan ku bane..

Zaki zo kiyi ta fira da kattai babu aji babu girma..

Wai kina kallon kanki a madubi kuwa...

Cike da mamaki take juyawa kalaman sa tahada rai ta ce bangane wai ina kallon kaina a madubi ba...

Eh mana idan bakya yi tokiyi ke bakiga yanda matar yaya Samad take bane amma kike kiran kanki da kawar ta...

Wallahi tunwuri ki nemi daidai ke dan wannan matar yayar tamu tawuce ajin ki''..

Tafiki kyau ilimi wayewa tafiki Asali ke intakaita miki babu wanda ze kalli Rahama ya kalleki ya ce kun hada hanya......

Sossai Asiya Ranta yabaci cike dajin haushin zagin nata da ya yi ta mika masa hannun ta ce ba ni waya ta..

Idan ban baki ba akwai abun da zakiyi ne..

Girgiza kai ta yi ta ce A'a kawai kabani wayata banson fitina...

Kin ba ta wayar ya yi hakan ya sa yawuce yabar ta atsaye...

Cike da mamaki take kallon sa harya ba ce mata da gani..

Cikin hanzarin ta tawuce masaukin su tare da fadawa kan gadon nasu...

Kuka take sossai mai tsuma rai tana da na sanin zuwa kwatano...

Tana kukan tana tuna Adamu da basu gama chat ba ta amsa kiran mamar ta....

Tashi ta yi taje gaban madubi tana ta kallon kanta Daga kasa har sama ta ce yabon kai jahilci dasai ince banga wani makusa afuska ta da jikina ba..

Cigaba da kallon madubi take cike da takaicin kanta ta ce kila ma gaskiya yafada din banida kyau......

Tana kallon madubin hawaye shar a Idanun ta sossai suka canza launi zuwa ja.......

******, *************

Karima cikin karfin hali take kallon Rahama ta ce matar shugaba na..

Kin cancanci in gayamiki komai koda kuwa shugaban yahana dole in sanar miki da abun da nasani...

Amma ina rokon ki Alfarma kibari zuwa nan da gobe yanzu haka Da ƙyar nake iya magana....

Rahama dake mata kallon tausayi ta ce karki damu Karima InshAllah zan saurare ki zuwa goben tashi ta yi tsaye ta ce mu zamu wuce '' shima Samad tashi ya yi yarike hannun Rahama ya ce Karima mun tafi Allah yabaki lafiya...

Sossai ta yi farin cikin ganin yanda Rahama take manne wa Samad tasan karshen zaluncine yazo karshe....

. Kai tsaye sashin Mamy suka nufa...

Koda suka je iske Anty suka yi tana shirin tafiya masaukin su...

Rahama cike da shagwaaba ta ce Ah anty ina zakije ne kizo muci danwake nasan ankawo shi nan....

Anty sake da baki take kallon Rahama ta ce danwake kuma..

Ko shi ne nagani a babban Wamer din da Asiya ta shigo dashi....

Mamy dake fitowa Daga dakin ta hannun ta dauke da Wamer din ta ce ga danwaken nan Rahama kwantar da hankalin....

Kan danwaken nan baba na kamar zeyi kuka dazeja Asiya suje siyen sa...

Sossai Samad yadara ya ce Amma Ahmad dan rainin hankali ne watau ba zaije siyen danwake shikadai ba shi ne ya ja Asiya..

Mamy ta ce to ka san dan gayu ne ya za ai agan shi riike da Wamer zuwa siyen danwake daka gayamin da da kaina zan mata taci iya cin ta....

Rahama banda dariya ba abun da take cike da Jin kunya ta ce Ah mamy gobe ma zanci InshAllah da kaina zanyi dandai ina tunanin kafun ayi danwaken zan jigata shi ya sa nace ina son na siyarwan....

Mamy ta ce babu komai yanzu de zauna kici....

Kallon Anty ta yi da take shirin fita ta ce Maman Rahama dawo kuci tare...

Anty ta ce Ah Ah ankai mana Abinci taci kayan ta lafiya kasai ta yi tafi ce...

Yarima Samad kallon Rahama yake yanda take cin danwake tanaci ba ta fuska...

Kallon ta yake da mamaki ya ce yadai Ko akaro yaji ne...

Cike da ba ta rai ta ce ni dai danwaken na ya isheni haka kada ya sani amai..

Samad danne dariyar ya yi ya ce Mamy kinajin abun da take fade Ko...

Murmushi Mamy ta yi ta ce inajin ta..kyaleta tahuta eheee banson takura..

Kallon Rahama ta yi cike da so da kauna ta ce gayamin abun da kike so zansa Hassana ta dafa miki....

Fitowar hassana Daga kitchen waya hannun ta cike da mamaki take karanta sakon whsap din ta...

Mahaifin ta ne ya yi mata sako hakan tadawo hakanan duk da besan me taje yi a kwatanon ba....

Ya mata miji har ansa rana auren nata nan da wata daya....

Sossai zufa ya keto mata

Mamy da Samad da Rahama kallon ta suke suka hada baki wajen fadin lafiya kuwa....

Muryan ta na rawa ta ce mahaifina na ne ya ce indawo gida Sannan ya sama mun mijin aure har ansa rana...

Mamy cike da Jin dadi ta ce meye abun ba ta rai ke fa ba yarinya ba ce kiyi adua Allah ya sa shi ne mafi Alkhairi...

Kasa magana Hassana ta yi hakan ya sa tazauna shargab akasa tana maida numfashi...

Rahama barin danwaken ta yi ita da Mamy suke nufi inda take zaune cike da jinjina Al'amarin ace bazawara ce za a fitar mata da miji ai an yi son kai...

Mamy ta ce karki damu kila ya hango Alkhairi ne shi ya sa yake son hada wannan auren.....

Salma tana fita masarautar kai tsaye wani babban pharmacie ta nufa...

Ta ce su ba ta maganin bera....

Ma'aikaciyar ta ce nan babu maganin bera sai dai kije kasuwa...

Salma cike da sake sake tana ciza labban ta '' ta ce uhmm to kuban poison

Ta ku har kullum kyauta Daga AllahƘANWATA

LITTAFIN NAN KUDI NE INKIN GANSHI A WAJEN GROUP DÎNA NA SATA NE

INKINA BUKATA GA NOMBA

09069080725

8️0️

Tokuban poison '' ma'aikaciyar ta ce me zakiyi da poison ne hajiya ya tsurawa Salma idanu...

Salma cikin kasa da murya ta ce beraye ne suka takura mun babu daman in kwanta sai suzo suyi ta cizo na dan Allah ki taimaka ki siyar mun very important nake bukata...

Jinjina kai Ma'aikaciyar ta yi tare da danna computer dake gaban ta '' ta ce..hajiya kudin ki jaka daya...

Salma ta ce babu matsala zanbiya..

Ma'aikaciyar nuna mata wajen da ake biyan kudin tayi' 'itako Salma cikin Rawar jiki taje tabiya ta amshi poison din hannun ta''' na rawa cike da murna......babu ba ta lokaci ta yi hanyar gidan Masarautar...

Mai gadi da securite dake kofar gidan kallon ta suke yanda taketa kif kif da idanu Alamun rashin gaskiya...

Securite stop ya ce mata hakan ya sa ta wai go tana kallon sa...

Tsura mata idanu ya yi '' yaga ta hada rai ta ce kakosan koni wacece kuwa..

Securite ya ce ban san koke wacece ba''amma kabar bakuwa ce' yi hakuri kina iya shiga na dauka bakuwar fuska ce...

Ajiyar zuciya tasauke cike da murnan Allah ya taimake ta be caje ta ba....

Cikin hanzarinta kai tsaye sashin Mamy ta nufa ta iske Rahama har tabar dakin...

Kallon Wamer din danwaken da Asiya ta kawo take cike da rawar murya take kallon Mamy ta ce wai Anty Rahama ta shigo nan ne...

Mamy ta ce eh sunshigo mana ita da Samad yanzunnan suka wuce sashin nasu...

Cikin kunan rai ta ce Ayya amma takoci danwaken nata kuwa...

Mamy ta ce taci gashi nan tabar shi inkinaso ki tafi dashi...

Salma ta ce Ah ah nakoshi nadai tambaya ne zankoma masaukin namu naga magrib ta karato...

Hartakai kofar fita ta ji muryan Mamy na fadin Salma Inkin je ki turo mun Asiya '' da an yi Sallah tazo takai Abinci sashin Samad...

Salma cike da Jin dadi ta ce to meze hana ni inkai mata Mamy ai duk daya ne...

Mamy ta ce haka ne '' to kije in an yi Sallah isha'i kinzo ki dauka '' dakin je kiwa securite sashin nasa magana kice Nina turaki za su barki ki wuce..

Salma ta ce babu Matsala Mamy saina dawo Daga haka ta fice tabar dakin...

Koda ta isa dakin iske Anty ta yi ita da Asiya suna kokarin tada Sallah hakan ya sa itama tafada bandaki domin yin Alwala..

Koda ta fito Daga bandakin iske anty da Asiya harsun idar da Sallah..

Wayar Anty ne ke ruri cikin hanzari ta duba taga bakuwar lamba ce..

Daga wayar ta yi tare da yin shiru Daga can ɓangaren ya ce anty ina wuni dafatan kina lafiya

Al'amin mijin Salma ne...

Anty fadada murmushin ta ta yi ta ce ah surukina sai yau za ka neme mu lallai m'a...

Daga can ɓangaren ya ce wlh anty banzaune ne '' aiki nasamu saida naga komai ya daidai ta shi ne nasamu nutsuwa dan Allah kihadani da Salma Ko kiban number ta inbakya tare....

Anty maida kallon ga Salma dake sallah ta yi ta ce muna tare sai dai Sallah take yi '' 'Al'amin ya ce Tom anty zan sake kira ganin Salma ta sallame ya sa ta fadin tsaya kamar ta idar da sallah...

Daga can ɓangaren dadi yaji sossai hakan ya sa ya ce to anty kibata wayar....

Salma ganin. Anty tamika mata wayar ta karba dan duk firan da suke tana Jin su....

Tashi kusa dasu anty ta yi takoma cikin daki....

Cikin Isa da rashin kunya ta ce Al'amin kenan wai meye dalili kira dan a ba ka ni....

Daga can ɓangaren murmushi ya yi ya ce babu laifi miji dan ya nemi matar sa...

Salma kiyi hakuri mu dawo da rayuwar mu irin ta da kafun muyi aure...

Salma ina son ki a yanzu sona hakika nayi kuskure ɗana dauki auren ki amatsayin wulakancin bayan na manta ke yar wacece kuma na mance irin kawaicin da mahaifin ki ya nuna mun..

Yatsine fuska Salma ta yi tabuga uban tsaki ta ce Al'amin kayi sake dan zaki ya girma yanzu babu ni babu kai wallahi ka sake ni ba zan iya zaman aure da kai ba...

Kana matsiyaci ana batun daula wake maganar gidan bukka...

Wallahi ni sai dan Attajiri Ko attajirin Ko Jinin Sarauta kar kai tunanin zan zauna gidan masu saida waina a kan titi ka makaro '' wallahi Ko Ada danake kula ka kuruciya ne da dangin hauka ya sa na mance ni matar manyan mutane ce ba irin ka me tsaron shago ba...

Sossai Al'amin ya nutsu yana sauraren ta tare da juya kalaman ta yanajin kuna acikin zuciyar sa...

Danne fushin sa ya yi ya ce Salma ba zan iya sakin ki ba..

Yanzu haka na kama muna gida mekyau plat babu kowa ciki dagani saike sai yayan da zamu haifa har Allah ya horemun in yi gidan kaina.....

Sossai Ranta ya ba ce ta ce ni Salma Abdurrazak Nice zan zauna gidan haya kam buhu lallai kanka ya kwance Al'amin

Maza ka nemo shi in saita maka shi.....

Nusarin namiji kawai Alfarma daya zan maka '' tsinannen cikin ka dake jikina nakeson ɗana dawo ka kaini acire mun shi dan wallahi ba zan haifi dan Masu saida waina ba.....

Al'amin cikin takaici ya ce aikuwa tun da ba shege bane saikin haifi dan masu wainar..

Zankai kararki wajen mahaifin ki danshi ba mutumin banza bane...

Salma Jin zeyiwa sheik magana ya sa ta fadin kaima ba ka san wasa ba...

Ai gobe zan dawo kabari inna dawo mun karasa ko

Cikin takaici Al'amin ya katse wayar..

Sai safa da marwa yake ta yi cikin dakin...

Mahaifiyar sa me waina ce ta shigo bakin ta dauke da Sallama ta ce Al'amin matar nan taka '' Nina rasa wani irin aure ne wannan duka kwanan ta uku agidan ka...

.

Kuma ace haryanzu ba ta koma ba...

Al'amin cike da takaicin Salma yake kallon mamarsa ya ce Inna Salma Albasa ce batayi halin ruwa ba...

Duba kigani fa ya za ai ta ce wai zata barar da cikin dake jikin ta '' kasa gayawa mamar sa abun da Salma din tafada ya yi dan kar abun ya yi tsauri...

Mamar Al'amin cike da mamaki ta ce ciki gare ta kuma takeson ta zubar dan uban ta mara tarbiyya astagafirullah na mance iyayen ta mutanen Arziki ne dasai ince Daga gida tadauko mugun hali...

Al'amin dake kallon uwar tasa yana tabe baki ya ce ai Daga gidan ta dauko mana a nono tasha uwar ta wlh ba yar arziki ba ce...

Maman Al'amin cike da mamaki take kallon dan nata ta ce Ah Ah Al'amin karmuyi haka da kai laifin wani baya shafar wani dan yarinya ta yi ma rashin Arziki kar ka hada da uwar ta nasan Ayshatu ban san ta da mugun hali ba...

Kaima harda naka laifin Ko gun auren yarinyar nan wani rashin mutunci ne ba ka shuka ba har daurin auren Da ƙyar ka tafi aka ba ka yarinya kayi mata diban Albarka dan dai uban ta sarkin hakuri baya nuna fushin a kan abu da wanine da kaine zakayi jinyar ta.....

Kila wannan ta duba shi ya sa take maka haka..

Takarashe zancen tana kwance kudin wainar dake daure jikin Zanin jikin ta dan kirgawa....

Al'amin cike da takaici yake kallon yanda take kirga kudin ya ce ni dai Daga yau banson ki kara saida waina..

Dago kai ta yi tana kallon sa ta ce Yau na ji iskanci inace da kudin wainar kabiya sa dakin auren ka...

Oho dai ni dai na gayamiki banaso wlh haba kina jamin zagi agari inna yakamata ki daina fa ehee yana huci sama sama...

Sakaka da baki take kallon sa ta ce to inbada abun ka da iskancin naka daya motsa wani sana'ar zanyi ne ka ga dai mahaifin naku beda karfi yanzu da wannan sana'ar muka dogara....

Ku barshi nace Inna zandau nauyin komai agidan nan Daga yau Daga cinku har sha..

Duka abun da kuke bukata ku sanar mun...

Inna dariya ta yi ta ce ikon Allah Alhmdulilah ɗana yasoma hankali Allah ya sa dagaske kake inhar haka ne nima wlh zan dena sai innemi sana'ar gida Ko sare sare ne ina iringa taba kasuwanci...

Al'amin cike da Jin dadin zehuta da gorin Salma yaciro bandir din kudi dubu dari ya mikawa inna cike da isa ya ce wannan gashi kija jari kuma kiyi cefane duk abun da babu agidan nan ki siye mugani kafun su kare zankaro miki wasu...

Cikin Jin dadi ta girka kudi hade dayin guda sossai baki na rawa ta ce Alhmdulilah Al'amin Allah ya sa kafi haka..

Ameen ya Amsa tare da barin ta a dakin tana murnan samun da tayi....

Ita Ko Salma suna gama wayar ajiye wayar gefe ta yi tafara tunanin yanda zata kai karshen Rahama

Wata muguwar Tsanarta takeji A'cikin Ranta..

Tun suna yara kullum ita ce Asama duk abun da tasa agaba saide ya je kasa '' 'cikin jin haushin ta take Ayyana yanda za ai jana'izzar Rahama a masarautar..

Kuma InshAllah Nice zan maye gurbin ta awajen Samad inma ban aure shi ba...

To kowa yara sa Amma tabbas Rahama barin duniyar zakiyi kin isa ki kwace komai ke kadai waike ta Allah zamu gani ne...

Tashi Daga kwance ta yi tare da nufar falon ta iske Asiya tafita Faruk ya aika a kira ta....

Ganin Anty kadaice zaune cike da murmushin dole ta ce Anty ga wayar taki mun gaisa da shi ya ce yana gaishe da kowa da kowa..

Sossai anty ta ji dadin hakan ta ce yauwa koke fa Salma ina son ki nutsu ki kama mijin naki sossai wallahi yanzu maza wuya suke...

Kinmaci sa'a ke kin san Al'amin kafun aure '' nida wlh ina kuka ina fadin ba na son auren da za ai mun mahaifana suka yi ta rarrashina indau kaddara InshAllah ba zanyi ɗana sani ba...

Yanzu fa duba kigani zamana da baban ki sai Sam Barka wallahi daidai da. Rana.daya be taba yimun abu da. Gangan ba dan raina yabaci ba '' duk da Adam agizi ne....

Nima kuma bêta kamani da nayi masa laifi ba..

Ina kikaye wa duk da a lokacin bawai son shi nake ba...

Amma Daga baya fa uhmm Kullum adua nakewa iyayena dan sun mun zabi nagari dan haka ina son ki rike irin nawa Salma...

Ƙaramin misali duba fa yayar ki Rahama aure aka daura mata batasan mijin ba shima besan matar ba kuma suka rungumi kaddara...

Dan Allah Salma ki nutsu ina son kizama wayayya InshAllah ba zakiyi da na sani ba inkika dauki shawara ta ba....

Salma jikin nata ya yi mugun sanyi kamar wacce tadau nasihan Anty amma azuciyar sai fadi take uhmm ai baku isa ba Daga ke har Rahama zaku gane....

Afili cikin sanyin murya ta ce Anty nagode da shwarar ki....

INSHALLAH NADAUKA...

Asiya samun wuri suka yi ita da Faruk suna fira cikin nishadi ''...

Cike da Jin dadi ta ce ka ga Daga gobe shi ke nan zan bar kasar taku '' sai kuma mun dawo suna in Allah ya sa ta haihu...

Faruk dake Murmushi ya ce kina nufin cike gare ta ne Rahama...

A'a ba haka nake nufi ba wai in Allah yakawo Ko '' dole inzo mata suna...

Kamar ita Rahama na ji Samad na. Fadin nan da wata daya za su tafi kano...

Faruk ya ce kwarai kuwa kanon za su je '' kamar akwai abun da yake nema a kanon har yanzu Burin nasa be cika ba dole yakoma....

Uhmm Allah yakaimu gwamma inringa ganin kawata wlh banson ina nesa da ita sai dole...

Wai in tambayeka

Faruk ya ce inajin ki fadi......

Dan Allah gayamin gaskiya kar ka ga dan gaban idanuna ne...

Uhmm inajin ki fadi mana....

Wai dan Allah Faruk da. Gaske ni mummuna ce Ko kyakkyawa ba na son ka boye mun dan girman Allah....

Dariya mai sauti Faruk ya yi ya ce inhar mafarki kike TOKI FARKA

Babu wanda ze kalleki ya kushe ki wallahi saide hassada..

Son kowa kike kin wanda ya rasa..

Asiya ke kyakkyawa ce ajin farko banson in cika ki da surutu ɗana bude miki file din kyaun surar da Allah ya yi miki...

Wallahi kinada kyau iya kyau gaki fara ga tsini hanci mai daukar hankali...

Asiya ke ta musamman ce..

Gayamin waya ce miki ba ki da kyau...

Cike da Jin dadin kalaman sa ta ce uhmm babu wanda ya ce haka kawai na tambaya ne dan insan yanda nake in daina Rawar kai...

Faruk cike da yarda da kai ya ce Asiya ina son magana dake serios..

Inajin Faruk din Samad...

Uhmm ba Faruk din Asiya ba...

Taya kazama na Asiya rufamin Asiri...

Ni dai inajin ka...

Asiya ina son ingaya miki kalmar da ban taɓa. Furtawa wata ya mace ba

Asiya ina son ki '' ina son ki ina sonnnnn kaiiii ya ja kalmar da wani irin voice me kashe garkuwan jikin wanda ke sauraron sa....

Asiya dago kai ta yi Idanun ta cike da hawaye ta ce Faruk kana sona kace uhmm mikewa tsaye tayi...

Faruk shima tashi ya yi ya ce haba Asiya ina zaki je muna magana..

Kasa Tsayuwa ta yi ta ce Faruk ka makara kayi hakuri na yi wa Adamu AlKawarin zan aure shi kuma har nayi shawara da Rahama..

Bankika ba Faruk ka kai duk inda ake tunani kai gwarzon namiji ne tun farko kayi nauyin baki...

Gashi Adamu yazo da Gadan Gadan ba zan ki shi ba...

Cikin hanzarin ta tabar wajen nasa tana sheshekar kuka...

Shiko Faruk Mutuwar tsaye ya yi yakoma kamar wani matacce '' sossai jikin sa yadau rawa.....

Kuka yake yana fadin Asiya karkimun haka...

Yayi daidai da fitowar Samad Daga Sashin nasa yana sauri zeje sallah insha'i....

Cike da mamaki sukaci karo shida Faruk dake kuka...

Samad ya ce............

Ta ku har kullum kyauta Daga AllahƘANWATA

LITTAFIN NAN KUDI NE INKIN GANSHI A WAJEN GROUP DÎNA NA SATA NE

09069080725

Page biyu ne nan na hada zaku ga ya yi tsawo '' na safe ɗana ɗare ne..

Nagode masu mun uzuri..

Love you All my Fans...

Jinjina gareku yan kungiya ta Jarumai writ associat..

8️1️ ___8️2️

SAMAD ya ce kai lafiya kake kuka meya faru ne '' fuskar dauke da damuwa....

Faruk cikin saita nutsuwar sa ya ce Ah babu komai mu je muyi sallah in mun fito zan maka bayani.....

Kai tsaye masallacin suka nufa...

Ita Ko Asiya zama kusa da Anty ta yi tana ba ta labari Anty ta ce da bakiyi saurin dakatar da shi ba....

Matar mutum kabarin shima wanda kike takama a kan sa ba lallai bane inshi ne zaki aura ba.

Uhmmm haka ne Anty banson ya sa ran zan aure shi inzo ban aure shi ba ya yi tunanin naci Amanar shi...

Adamun danace masa shi zan aura '' shima Adamun haryanzu ban bashi baki ba..

A tsakiya nake Anty..

Cike da Jin dadi anty ta yaba hikima irin ta Asiya ta ce kai Amma Asiya kina wayau da hikima yanda ki ka san babba haka kike abun ki kina burgeni wallahi..

Sossai Asiya ta ɗara ta ce uhmm aidole anty na namiji kar ka nuna masa wai Daga shi babu wani kuma kar ka nuna masa kana mugun son sa nan ze samu damar juyaka yanda yake so...

Sossai Anty ta ɗara cike da Jin dadin kalaman Asiya ''

 tadauko Alkur'an zata karanta kenan Idanun ta ya sauka a kan Salma dake shirin fita

Asiya ta ce Salma ina zuwa ne babu magana...

Cikin takaici ta ce dole inzan fita saina sanar miki ne '' zanje sashin Mamy ne abinci zankai sashin Rahama..

Asiya ta ce Ah kice zaki je gun yayar ki Allah yakai ki lafiya saikin dawo...

Anty dake kallon Salma cikin yin kasa murya ta ce amma fa karki dade idan kinje..

Salma ta ce Ah Ah inazuwa ba zan zauna ba Daga haka ta fice Daga dakin...

'' Yarima Samad tare da Faruk suka fito Daga masallacin inda suka samu gefe daya suka zauna...

Cike da nutsuwa Faruk keyiwa Samad bayanin son da yakewa Asiya kuma ga Amsar data bashi...

Samad cike da jinjina Al'amarin ya ce kar ka damu abokina yanda kamin bayani ni naga son ka A'cikin idon Asiya kawai tana ja maka aji ne irin nasu na mata...

InshAllah da kaina zan mata magana '' zanji ta bakin nata'' kaidai sha kurumin ka zamu nema maka auren Asiya InshAllah....

Faruk cike da Jin dadi ya ce gaskiya na ji dadin wannan maganar taka Allah ya sa rabo na ce..

Samad ya ce Ameen kawai mu nemi Zabin Allah...

Tashi mu je sashin Mamy danni yau ba zan dade banshiga Daga ciki ba..

Faruk ya ce Tabe Tabe za a je sana'ar ne...

Yarima hade rai ya yi ya ce uhmm aina ga tabe taben kakeson yi yarinya tana ja maka Aji dan iska katsaya a kan hanya kamar ƙaramin yaro zakai mana kuka da na sani nabar ka saika kukan indau video wanda zansawa suna Tabe Taben iskancin da kuke kirana kaida Aminu....

. Sossai Faruk ya ɗara ya ce na ji koma meye nawa dasauki kaida kake mafarki kana kuka kana ihu kana fadin karki tafi kibarni ni ban ce maka ƙaramin yaro ba '' sai kaine za ka fada mun haka...

Kasaitaccen murmushi Samad ya yi ya ce uhmm ai wannan mafarkin danake yi ka san ta bude Idanun nata a karshe kuwa...

Faruk ya ce Au haba dagaske..

Wallahi dagaske nake maka kuma fuskar mata ta ce ta bayyana...

Cike da mamaki Faruk ya ce ni dai tun lokacin nan na dade ina zargin kamar Rahama ce wannan zanen nasan ba za ka fahimce mu ba..

Shi ya sa mukayi shiru..

Alhmdulilah tun da ka gano mafarkin ka saura Abban mu da Saratu...

Samad ya ce uhmm sune kadai yanzu agabana Amma Allah zeyi jagora...

Faruk kallon Agogon dake daure a tsintsiyar hannun sa ya yi ya ce Ah ba zan shiga ba akwai inda zanje saina biya gidan su Aminu...

OK.babu damuwa cewar Samad sallama suka yi Daga haka Faruk yafice shikuwa Samad kai tsaye sashin Mamy ya nufa...

Wayar sa ce tasoma ring yana dubawa yaga number wannan matar daya taimakawa a kotu....

Kukan ta ya sashi fadin subuhannalah bayan ya Daga wayar....

Cike da mamaki ya ce lafiya kuwa mêke Faruwa...

Daga can ɓangaren ta ce yanzu haka nagudu nabar gidan mu '' zan tafi kauye farautar rayuwa ta ake yi kuma Daga cikin masarautar ku ne..

Ansamu labarin kamar zan bayyana maka inda Saratu take..

Ita kanta Saratu labari ya je mata a kan zan tona mata Asiri...

Yanzu haka tana shirin barin kasar akace...

Ko ta jirgi Ko ta mota..

Samad cikin tashin hankali ya ce wani gari take ne..

Matar ta ce kano sossai yaji zancen nata kamar saukan aradu..

Yanzu ya tabbatar lallai ita ce wannan matar dayagani a super market....

Karki damu yanzu kisan yanda zakiyi ki boye kanki ita din kibar ta tagudu '' ni Samad inna tashi kamata wallahi a sati daya yamin kadan kawai wuyan ban san kaina Gadan Gadan bane a neman ta...

Kibar ta duk inda zata je a fadin duniyar nan zan iya sawa a kamo min ita tahanyar yada hotunan ta kuma kin san kamar ni innace ina son abu anamun shi saide in mutuwa ta yi shi ne kadai ze raba ta dani...

Sossai Matar da yarda da zancen Samad ta ce Allah ya taimakeka yabaka Sa'a AMEEEN ya furta Daga hakan suka yi sallama.......

Maida wayar nasa ya yi a Aljihun sa kai tsaye yawuce yiwa Mamy sallama tare da kiran wata baiwa cikin bayin sa..data biyo ta daukar musu abinci zuwa sashin nasa...

Cike da naam take bin shugaban ta abaya...

Bakin sa dauke da sallama ya shiga ya iske Mamy na. Zuba abinci cikin Wamer tashirya komai '' Kokarin mikawa Salma take yi Samad ya kunno kai cikin hanzarin sa ya ce Mamy zanshige barci nakeji na tara gajiya...

Abincin namu tare nake da lantana abata abinci..

Salma cikin takaici ta ce ni zan kai muku basai taje ba...

Samad kallon ta yake ya ce ok to saita tayaki rikewa Ko...

Cikin. Jin haushin haka ta ce babu matsala Muje...

Kai tsaye gaba ya yi suna biye da shi abaya '' nan da nan securite suka buda musu hanya ganin shugaba na gaba....

Koda suka yi isa Samad nuna wa lanta dinner table ya yi ta jera abinci cike da nutsuwa har na hannun Salma saida ta karba ta gyara komai tsaf..

Kan ta aduke ta ce ya shugaba na nagama zankoma...

Gyada mata kai ya yi hakan ya sa ta fice babu ba ta lokaci.....

Ita Ko Salma tsaye ta yi tana kallon yanda ya zauna gindin abinci yaki tashi...

Sai chat yake a wayar sa yana kallon ta.

Ta ka san idanu tabe baki yake ya ce uhmm ban san meyasa wannan kanwar tamu Sam ba ta burgeni ba...

Sake sake yake ganin ta yi kikau a tsaye a sanyaye ya dago kai yana kallon ta..

Cikin voice din sa mai daukar hankalin ta... Ya ce kina son ganin Rahama ne..??

Kada masa kai ta yi ta ce uhmm ina son ganin ta mana ka san gobe zan wuce Ko...

Murmushi ya yi mai nuna zallan kyawun sa ya ce ok bismillah Amma karki dade dan dawuri zan kwanta...

Cike da hanzarin ta tashige ciki iske Rahama ta yi da khadija zaune Rahama tana koya mata karatun Alkur'an sossai khadija take ganewa cike da Jin dadi ta ce Anty Rahama na iya nan Ko..

Gyada mata kai ta yi ta ce eh kin iya saura hadda...

.

Shigowar Salma ya sa suka katse karatun nasu '' 'cike da fara' a Rahama ta ce kai ƙanwata kece adaren nan...

Uhmm Nice abinci nazo da shi shi ya sa...

Zoki zauna mu taba karatu cewar Rahama...

Tabe baki Salma ta yi ta ce Ah ah mijin naki na ji yana fadin za a rufe sashin naku kinga zama be kamani ba

Rahama ta ce Ayya Amjad kenan shidai.becika son ana yawan zuwa nan sashin ba..

Barin wani tunani ta yi taje tadauko wannan milyoyin da Samad yadaura a kan lefen nata...

Kama hannun Salma ta yi ta ce wannan kudin gashi kiba Anty In kunje cen zata bawa Abby..

Wannan kudin kowa na ba acikin yan gidan namu harda Asiya za a cire mata nata...

Khadija ta ce gaskiya Anty Rahama kinyi kokari toke ina. Naki..

Kallon khadija ta yi ta ce Ah ah ni bana bukata mezan dasu..

Nasan kila wasu Daga cikin su suna da bukatan hakan.. Yan uwana ne banajin shayin basu koda kuwa suna da shi ina son surike amatsayin kyauta Daga gareni...

Khadija cikin fara'a take kallon Salma dake murmushin dole ta ce kai amma Salma kunji dadi ni ina yaya Samad Ko yaya Ahmad suka taba ba ni kudi uhmm ai saide su siye abu subani ba kudin ba...

Rahama murmushin ta yi ta ce my khady mu ma agidan iyayen mu bama rike kudi to me zakayi dasu bayan komai kace ana maka...

Tabe baki khadija ta yi ta ce haka ne..

Salma dake rike da kudin a hannun ta cikin gajiyawa ta ce uhmm nizan koma m'a sauki saide mun hadu....

Rahama tashi ta yi dan take mata baya....

Salma ta ce Ah Ah kiyi zaman ki nagode antina...

Murmushi Rahama ta yi ta ce kin tabbatar..

Salma ta ce eh wlh babu komai..

Cike da Jin dadi Rahama takoma ciki dan cigaba da karatun nasu....

Koda Salma ta fito iske Samad harya tashi bayanan wajen hakan ya sa ta '' taho a hankali tana kokarin bude Wamer din abinci dan yanzu sotake Daga Rahama har Samad din su mutu......

Cikin hanzarin ta tabude wamer din '' tana kokarin fiddo poison din '' ta tsinkayo muryan Samad dake karasowa falon sanye cikin kayan barci...

. Ah Ah Salma daman baki ci Abinci bane...

Cikin Rawar baki da tsoro daya kamata ta ce uhmm ban koshi bane...

Juya kalaman ta yake yana nazarin ta uhmm Salmatitinaaa ya ja sunan da wani irin husk voice..

Dararan Idanun sa ya sauke a kan ta cike da iya takun sa ya ce to bara in zuba miki kin san ke kanwar mu ce....

Kokarin dauko plate yake sai ga Rahama da khadija sun fito cike da mamaki suke kallon Salma ashe ba ta wuce ba...

Rahama cikin sakin Fuska ta ce my kanwaty kina nan keda yayan ki...

Murmushi Samad ya yi ya ce eh muna nan nida Salmatiti na ya kika gan mu...

Murmushi Rahama ta yi ta ce naganku normal Amjad...

Dauko wayar ya yi ya ce yawwa Salmatitina zo nan mu ɗau hoto mana..

Keda khadija..

Cikin hanzari khadija ta isa kusa da shi Salma cikin sanyin jiki taje tana tunanin anya wannan mutumin be gano ta ba...

Hotuna yadauke su shida khadija da Salma yana tsakiyar su ya dafa su..

Kasaitaccen murmushi ya yi tare da mikawa Rahama wayar ta dauke su...

Babu musu cikin Jin dadi ta dauke su hotunan ba ƙaramin kyau suka yi ba...

Samad ya ce yawwa tun da nayi daku kuban waje nida Amaryata mu dauka...

Khadija da Salma gefe daya suka koma suna kallon yanda yake ta daukar su zafafan hotuna masu zafi Ko wanne yana manne da ita....

Akarshe ya ce to duk suzo ayi tare harda Rahama..

Hoto me kyau yadauke su...

Murmushi ya yi ya ce Salmatitinaaa yawwa zomuje in rakaki har wajen fita banson securite suna miki wani kallo zan gaya musu ke din ta daban ce...

Sossai Rahama ta ji dadin yanda yake kula da kanwar ta.....

Suna fita Daga dakin '' ya ce kash na mance baki ci abinci ba...

Salma ta ce Ah Ah abarshi akwai tsaura a dakin namu zanci...

OK to ya furta yana kallon cikin ido cike da iya taku ya ce Salma dan ba ni maganin dake hannun ki mana kin san na dade ina neman irin sa bansamu....

Wani magani kenan tafurta tana zazzare idanu....

Gashi nan mana tare da saka hannun sa cikin nata sossai taushin hannun sa ya saukar mata da kasala hakan ya sa ta saki roban poison din akasa ba tare da ta Ankara ba...

Durkushewa ya yi yadauka ya Daga robar sama yana duddubawa da kyau kada kai ya yi yana jinjina Al'amarin...

Salma kallon sa take bataga ya canza yanayin sa ba...

Cikin sassaita murya ya ce aro nayi gobe inzaki wuce zan baki abun ki...

KADA kai ta yi cike da tsoro da Fargaba da kuma Jin kunya...

Kai tsaye barin sashin Nasu tayi....

Shima ciki yakoma bayan sun gama cin abinci khadija ta ce Anty Rahama mubar karatun nan saida Asuba barci nakeji tashi ta yi tabar Samad da Amaryar sa....

Ganin Khadija tawuce ya sa yakama hannun ta tana ja cikin muryan shagwaba ta ce wai me zan maka ne..

Wanka zamu yi tare yabata Amsa ''

Haba Amjad wani irin wanka zamuyi za ka fara halin naka Ko...

Uhmm mu je dai banson musu....

.

Tanaji tana gani ya ja ta har bandaki tana nokewa haka ya matsa a la dole wanka yake mata..

Sossai take ta kare kirjin ta...

Shiko dariya ta ba shi ya ce uhmm kiyi kigama kin san zakisiye labari na Ko..

Nace sai kin biyani Sannan inbaki....

Oya tashi mu je tun da munyi wankar......

Yana makale da ita har suka fito Daga bandakin..

Daga nan wasa ya canza salo Samad kara rikicewa ya yi ganin yanda komai nata ya cicciko cike da kwarewa ya ringa sarrafa ta iya son ransa tun tana nokewa harta saki jikin nata....

Kokarin ratsata yake tuna abun da ya faru na farko ya sa tafara hawaye ta ce wayyo Allah Amjad kar ka illatani na tuba....

Beko tsaya sauraren ta tanaji tana gani ya ratsa ta ji zafin sossai amma bekai na ranar farko ba..

. Hakanan ta jure ta daure..

 Yarima Samad ranar beze da wasa ba '' sai kusan karfe hudu na Asuba ya tsarara mata....

Da ƙyar ta tashi ta yi wanka tana jinjina jaraba irin na Samad....

Shima wankar ya yi yadawo tare da makalkale ta kamar wacce zata gudu '' babu wuya barci ya yi awon gaba dasu '' itako Rahama barci take tana mafarkan ban tsoro gameda mijin nata firgit ta tashi ta zauna '' tana shafa kan sa tare da karanto wasu adu'oi ya yi daidai da bokan jeji yana zaune tsakiyar dajin Allah yana ta gurnani...

Ganin Guban daya tura be isa jikin Samad ba..

Mamaki yakama shi'' daya hango Rahama zaune a tsakiyar dakin hannun dauke da da carbi....

Razana ya yi sossai cikin Jin takaici ya shegiya har kin wanke najasar jikin naki...

Shi ya sa kike kokarin hana mu aikin mu...

Caraf kalamin nasa ya doki dodon kunnen Rahama kamar Daga Sama take Jin muryan tasa......

 Tabe baki ta yi da bushe da dariya ban san kome ta karanta ba '' sai gani nayi gabadaya ba a ganin gadon da Samad ke kwance akai......

Cikin Daga Murya ta ce uhmm na wanke najasan '' saura kai ka wanke naka.....zunubin..

Kuma da dukan Alamu Nice zan kawo karshen wannan ta'adancin naka...

Kallon gefen ta ta yi taga bakin Aljanin da Aka turo....

Umarni aka bashi a kan ya kashe Samad sannan yahada da Ahmad cikin wannan daren.....

Be Ankara ba besan Rahama tana ganin sa ba...

Sai ji ya yi ta watsa masa wannan ruwan adu'ar dake hannun ta...

Wani razananne kara ya saki mai hade gurnani daya cika dakin gabadaya banda ita babu wanda yakeji....

Doso ta ya yi cikin zafin nama cike da bacin rai kan yakaraso '' takara wasa masa wannan ruwan '' nan da nan ya fara ja da baya baya yana ihu ya ce wallahi Rahamatullah baki isa ba...

Zan dawo gareki..

Kokarin barin dakin yake yaji Muryan Rahama tana fadin ina za ka ne..

Babu inda za ka je ingayamaka anan wajen nida kai zamu gwada muga wanda zeyi nasara..

Ba a sanin gwani sai angwada....

Kokarin barin dakin yake yaga duk wata kofofin daze sa ya ba ce duk sun rufe....

Cike da tsoro cikin gigita yake kallon Rahama ya ce kee me kike nufi ne....

Kika toshe mun hanya ta....

Murmushi ta yi cike da isa nan da nan ta daure fuska kamar ba ita ce ta yi murmushin ba...

Kace za ka dawo ka nuna mun kokai wanene...

Ni kuma yanzu nakeson in gwada maka matsayina yanda zakaba wasu labari n irin shirin da za su yi su cini da yaki...

Doso shi take cikin azzama Shiko ja da baya yake yana Girgiza kai cikin gajiyawa ya ce Rahama dan Allah ki bari mu sasan ta....

Babu sasanci tsakanina da kai saimun cire rainin....

Aljanin ganin Rahama abun nata Azimun ne ya sa jikin sa yadau rawa...

. Duk abun da suke boka yana cen yana kallon su '' Idanun sa sun kada jajir yana tambayar kansa wannan wace irin yarinya ce dudu ba ta wuce 18 ba aduniya amma take wannan iskanci....

Rahama nan da nan tafara karanta suratul Ar Rahama '' tana gamawa ta dauko bakara tanayi tana wasa masa ruwan adua..

Ihu yake kamar ran sa zefi ta yana sosa jikin sa da hannayen sa...

Cikin tsananin Azabar da yake fuskan ta....

Ya ce Rahama dan zatin ubangiji ki kyaleni haka dan Allah narokeki wallahi ba zan kara ba kuma zan hana wasu aikatawa saide insunyi taurin kai ne za su tunkare ki....

Rahama tsagaita karatun nata ta yi cikin Daga murya ta ce suwaye suka turo ka...

Bokan jeji ne yaturoni azo a kashe Samad da Ahmad a kan wulakancin da suka yiwa Fulani.....

Rahama cikin dauriya zuciyar ta na harbawa ta ce kune kuka rayawa ? ?

Kune kuke kashewa

Girgiza kai ya yi ya ce A'a Allah shike rayawa yake kashewa....

Ka san da hakan kazo shiga hurumin ubangiji...

Cikin Rawar murya ya ce tuba nake....

Wallahi Fulani ce da aiko mu da Farida.....

Rahama ta ce wacece Farida kuma...

Cikin kasa da murya Aljanin ya ce yayar Habiba ce matar gidan nan....

Kasaita cenn murmushi ta yi ta ce in kamun karya wallahi saina wulakanta '' Rantsuwa ya shiga yi ya ce wallahi da gaske nake Inkina tantama kije gidan Farida dakin saman sif din' '' ki duba zaki ga laya....

Rahama cike da daurin kai wannan Al'amarin ta ce layan na mene ne.

Layan shi ne wanda muka daure bakin mai Martaba Sarki Turaki.....

Cikin zazzare idanu '' Rahama ta ce kamar ya kun ɗaure bakin nasa...

Eh mun ɗaure bakin nasa ne a kan dan sa Salihu dan kada yaga Farin sa....

Akwai wani kanin Nasa Sani shikuma layan da muka hada yana dakin Fulani na yanda ze tsani da uwan nasa '' kuma duk abun da Fulani ta ce ba zai mata gardama ba...

Tun farkon zuwan Fulani gidan ya nuna mata Inde tanason zaman ta dole tabi dan uwan sa Salihu....

Da kuma Matar sa...

Ita Ko Fulani yar Asiri ce da Asirin ta yi nasaran auren Sanin duk a lokacin ba ita yake so ba...

 Mulkin da Salihu yake zaune akai sossai ya dame ta hakan ya sa suka yi kokarin Rabawa shi da wannan kujerar harda taimakon Sani amma ba cikin hayyacin sa ba...

Sarki ya Karbi zancen ba cikin hayyacin sa ba...

Rahama cike da Girgiza da labarin ta ce wani sharri ne akayiwa Sarki Salihu...

Aljani cikin gajiyawa ya ce dan girman Allah ki kyaleni in tafi namiki AlKawari zan miki takarda cike da sirrin komai da sani nan da kwana uku zan ajiye miki a gadon naki yanzu wallahi bana cikin hayyacina....

Ajiyar zuciya tasauke adua tafara yi nan da nan hanya tabude masa ya ba ce bat Daga dakin.....

Shiko Boka wani ihu ya yi harda Girgiza ya ce wannan tsinanniyar ta ji sirrin mu...

Kuma wannan Aljanin inyayi AlKawari yana ci kawa harda cewa ze mata takardan komai...

Ina ba zaiyu ba zansa yanda zanyi in dakatar da shi ze tona mana Asiri hanyar cin Abincina ze rufe......

Ita Ko Rahama ganin babu kowa a dakin hakan ya sa tafara adu'oi sossai kusan minti goma sai ga gadon da Samad ke kwance akai ya bayyana a inda yake...

Bakin gadon ta zauna '' tare da sauke ajiyar zuciya akai akai juyawa ta yi tana kallon Samad yanda yake barcin sa hankali kwance rungume da pillow......

Agongo dake makale jikin bango ta kalla taga karfe biyar na Asuba...

Hakan ya sa tafada bandaki domin yin Alwala...

Bayan ta yi nafila tadauko Alkur'an mai girma tasoma karantawa cike da nutsuwa..

Zazzakar muryan ta ya doki dodon kunnen sa.....

Hakan ya sa ya bude Idanun sa dake cike da barci tare da sauke su a kan ta....

Mika yasoma ganin haka cikin sanyi murya take kallon sa ta ce kayi adu'a tashi Daga barci Ko...

Girgiza kai ya yi ya ce afuwan bara in yi koda ya yi kai tsaye bandaki yafada babu ba ta lokaci ya yi fitowa sanye da jallabiyar sa maroon..

Farar hular sa ta saka ya saka a kan sa''' '..

Kallon ta yake tana kokarin tada Sallah' '' Ya ce hubby na...

Yanzu kika tashi ne..

Murmushi ta yi ta ce uhmm ni dai saika dawo....

Daga haka ta fuskan ci Alkibla Shiko kai tsaye ya nufi massalaci babu ba ta lokaci aka tada Sallah

Kusan Karfe bakwai saida gari ya yi haske Sannan suka nufo cikin gida shida Ahmad dake kokarin wucewa sashin sa...

Yarima Samad kallon sa yake ya ce dakata nan Sarki ya aiko yana son ganin mu nida kai..

Cak Ahmad yatsaya tare da waigowa cikin Idanun wanda ke Jin barci ya ce Amma tsohon nan sai ya bari gari ya waye Ko...

Inmunje saika fadamai shiga gaba muje..

Dan tsabar rainin wayau dan waken daka siyo wa Rahma ba a sa mata ya ji yaji ba...

Uhmm aisai ta yi yajin da kanta har danwaken nifa adaina mun zancen wani danwake raina baci yake..

Samad dake kallon sa ya ce Ah to yaya na gama min fada sannan Muje...

Kama kunnen Ahmad ya yi ya murza da dan karfi saida ya saki kara..

Yana sosa kunnen cikin ba ta fuska yaturo baki gaba wai Yaya menayi maka ne tun sanyin safiyar nan...

Zaka wuce mu je Ko sai....

Ganin zekara cikin hanzari suka yi sashin Mai martaba...

Iske shi suka yi zaune bayan sun gaisa...

Cike da fara'a yana Jan carbi ya ce uhmm ku zauna yan Albarka...

Zama suka yi suna sauraren abun da ze ce...

Daman nakira ku ne a kan maganar auren Ahmad...

Yarima Samad dake mamakin furucin Sarki ya ce aure kuma..

Yaushe ya samu matar aure...

Ahmad yasoma sosa keya ya ce uhmm damar Asiya ce nakeso kuma za a nema mun auren ta....

Yarima Samad cikin tsananin damuwa ya ce wace Asiyar ?

Badai kawar mata ta ba..

Ahmad ya ce ita nake nufi mana...

ZUMBUR YA MIKE TSAYE..

Me Martaba da Ahmad da mamaki suke kallon sa Sarki ya ce lafiya kuwa yarima...

Goge Zufa yasoma yi ya ce inafa lafiya yarinyar nan abokina Faruk yake son ta...

Ya za ai ya ce a bashi wannan zancen banza ne...

Sarki ya ce haba Samad kanin ka ne fa ya fi Faruk matsayi awajen ka...

Yarima Samad zama ya yi cikin sanyin murya ya ce Sarki babu soyayya tsakanin Ahmad da Asiya....

Sarki numfasawa ya yi yana kallon yanda Samad yazubawa Idanun sa toka a kan lamarin..

Ya ce inaga kaima da akai maka auren aiba soyayya ta hada ba amma kuma yanzu fa na ji labarin yanda zaman ku yake.....

Turo baki gaba Samad ya yi yana surutai kasa kasa ya ce shi ke nan nayi shiru an nuna mun ban isa inhana laifi afkuwa ba...

Ahmad kallon Samad yake ta gefen idanu ganin lallai da gaske yake beson lamarin....

Sarki gyaran Murya ya yi ya ce ai aikin gama ya gama da ce gaban ka yazo da zancen ka hana toya hanu '' 'nikam harna yi magana da Sheik Abdurrazak ya ce yau zeyi magana da baban yarinya...

Yarima kayi hakuri adua' zakayi kaba abokin naka hakuri...

Yarima tabe baki ya yi tare da yin tsaki ya ce ninasan wallahi badan Allah yake son Asiya ba da wata manufa akasa.... Yarinyar nan kwata kwata ba sa shiri shi ne dan zalunci ze ce ze aure ta...

Naji na amince ayi auren amma ya sani wallahi naga rashin daidai a kan Asiya ba zan duba Alakar mu ba.... Zan gyara maka zama...

.Ahmad murmushin dole ya yi ya ce na ji na amince..

Uhmm Allah ya sa Alkhairi cewar Samad tare da tashi tsaye..

Ahmad shima tashi ya yi mai martaba ya ce '' Samad ina son Daga yanzu afara gyara Sashin Ahmad ayi masa komai yanda akayi maka...

Yarima ya ce babu matsala zanje inda kwanta kafun mu je rakiyan baki.....

Kusan tare suka fita shida Ahmad..

Kowa ya yi ɓangaren sa.....

******************

Kusan karfe tara Rahama da Samad suka shirya tsaf a gaggauce suka yi break duba da lokaci na tafiya za su je rakiya...

Sabon layi daya siyo mata ya mika mata..

Ya ce miko wayar insaka miki '' cike da Jin dadi ta ba shi ya saka mata...

Tana sanye cikin doguwar riga Abaya mai adon Stone '' baki sossai kalan kayan yamata kyau ka santuwa ita fara ce....

Shima Samad cikin suite baki da wandon sa baki takalmin sa haf cover ya sanya sossai shigar ta karbe su hakan ya sa ya musu selfie masu kyau yana rungume da ita....

Rada ya yi mata a kunne ya ce Rahama anjima zaki ba ni Ko...

Bata fuska ta yi ta ce uhmm wayyo Allah Abbana Amjad ze cinyeni...

Dariya sossai ya yi ya ce Abby inyaji ban taba cen kwaceki zeyi Daga hannun abun da yakawo ki kiyi kenan...

Uhmm ni dai Abbana yakawo ni dan inringa dafa maka abinci ne....

Kuma in gayamaka babu na ɗare kama shafa wa kanka lafiya ni tunkiya ce zakai ta tumurmusa ta..

Sossai ya dara harda rike ciki itako uhmm take fadi ni dai mu je ka ga khadija ta yi gaba mu ake Jira....

Babu ba ta lokaci suka fito suna kokarin rufe kofar yaga Karima cikin hanzarin ta ta durkusewa kasa tana gaishe su....

Uhmm shugaba ku tafi zan rufe sashin...

OK. Ya furta ya ce ya jikin naki ta ce dasauki...

Rahama ta ce Allah yakara lafiya Karima sai mun dawo...

Daga haka suka sa kai..

Anty da Asiya ɗa Salma tsaf suka shirya suma ɗuk sun fito farfajiyar gidan.....

Mamy da Fulani' 'Abban Marwan harda marwan da Ahmad duk sun hallara wajen rakiyan baki....

Rahama da Samad kadai ake jira ganin su ya sa babu ba ta lokaci' '..

Motoci suka Jeru aka fara shirya kayan su a bayan boots...

Motoci hudu suka fita Daga masarautar dan kai su filin airport...

Koda suka isa airport din sun iske Faruk da Aminu...

Asiya tana ganin Faruk murmushi ta sakar masa hakan ya sa suka koma gefe daya su biyu suna tattaunawa...

Ahmad duk abun da suke Idanun sa na. Kansu....

Mamy cike da farin ciki ta rungumi Anty tare da musu godiya '' 'fulani ma godiya ta yi a kan kawo musu mata...

Nan dai suka yita fira na rabuwa da junan su....

Har lokacin da matukin jirgin Samad personl ya fito ya ce su shiga ya shirya...

Babu ba ta lokaci anty tafara shiga jirgin..

Salma cikin kunan rai ta shiga..

Asiya zata shiga ta wai go tana dagawa su Faruk hannun '' 'harara ta watsama Ahmad tare da yin tsaki...

Sossai ran sa yabaci..

Rahama dake kukan rabuwa dasu ta ce bara tashiga zatayiwa anty magana...

Samad be hana ta ba...

Tana shiga ta iske anty tana adu'oi cikin kuka ta ce yanzu Anty zaki tafi kibarni...

Ita ma Anty kuka take ta ce kiyi hakuri Rahama aikin ba mu lambar ki Ko kuma kin amshi namu ba mu rabu ba banda abun ki ga waya....

Rahama ta ce Anty keda Asiya. Banson tafiyar ku..

Kema salma banson ki tafi...

Anty salma tabaki kudi Ko..

Anty ta ce eh tabani wannan kudin ne nagane su inna isa zamuyi magana...

Asiya rungume Rahama ta yi tana kuka Rahama itama tana kuka..

Yarima Samad ganin ta dade ba ta fito ba..

Hakan ya sa ya shiga ciki Da ƙyar ya fito da ita tana kuka...

Zuwa tayi ta rungumi Mamy...

Itako Mamy rarrrashi tashiga yi...

Suna kallo jirgin su Asiya ya keta azo a sararin samaniya.....

Farruk da kusa da Ahmad ya ce uhmm zanyi miss din masoyiya ta.

Ahmed fuskantar Faruk ya yi ya ce...........

Ina barar adu'ar ku a kan mahaifiya ta yau tacika shekaru 13 da rasuwa 4 march...

Sannan inajiran ruwan comment...

Taku har kullum kyauta Daga AllahƘANWATA

Littafin nan kudi ne Inkin ganshi a wajen group dîna na sata ne

Inkina bukata ga nomba

09069080725

8️3️

Ahmad fuskantar Faruk ya yi ya ce uhmm daman kuna soyayya ne...

Faruk cike da mamaki yake juya kalaman Ahmad ya ce Ko kana so ne ?

Ahmad ya ce eh mana nagani inaso harna yi wa mai martaba maganar a neman mun auren ta....

Wani irin shock Faruk ya shiga nan da nan kansa ya sara yana ganin hajijiya...

Ahmad ganin yana tangal tangal ya ce yadai yaya Faruk lafiya kake kuwa tare da dafa shi....

Faruk cikin aro jarumta tare da saita nutsuwar sa da taki komawa daidai ya ce uhmm Ahmad ai ko rana aka samun da Asiya kace kana sonta wallahi zan janye in barmaka kaifa kanin mu ne..

Ahmad cikin tausayin sa ya ce Ah Ah kabari ni zan janye kafini bukatar Asiya gashi naga zahiri...

Faruk ya ce kanina kenan kaidai na janye Allah ya sa hakan shiyafi zama Alkhairi..

Wallahi babu abun da za ka so '' face nafika son abun kar ka damu kanina Allah yabar kauna...

Ameen Ahmad ya furta Azuciyar sa sai fadi yake uhmm dan ba ka san dalilin daya sa zan aure ta bane da ba ka barmin ba inna koya mata hankali zan sako ta ka aure ta...

Murmushi ya yi yana yiwa Faruk godiya ganin su Samad da Rahama har sun shige mota ne ya sa Yayiwa Faruk sallama '' '.

Faruk wajen Aminu ya je ya zauna cike da damuwa ya ce Aminu shi ke nan na rasa Asiya ban san haka so yake ba..

Soyayya Zuma ce amma tafi madaci muni inka rasa abun sonka..

Shi ke nan tawa ta sameni...

Aminu ya ce tofah waiku bakuda aiki sai kuka a kan mata ne kaida Samad tsaki ya yi ya ce yanzu wai me akayi maka ne...

Faruk cikin tsagaita kukan nasa ya shiga bawa Aminu labari yanda suka yi da Ahmad...

Aminu jinjina Al'amarin ya yi ya ce kar ka damu '' ka ga Rahama ta samu yar uwa akusa da ita in Ahmad ya auro Asiya....

Ka san shawaran da zanbaka kabawa zuciyar ka hakuri maganar mata..

Ka tattara su gefe daya ka ajiye sai nan gaba...

Faruk ya ce InshAllah na ji shawarar gashi kai kana zaune lafiya tun da ba ka harkan mata..

Aminu Murmushi ya yi ya ce Ashe dai ka gane abun da nake nufi kaide ayi sha'ani kawai mata Ko wahala...

**************************

Gabon 🇬🇦

Baba Salihu cikin shigar sa ta Alfarma shida wasu a bokan nasu za su je kai goron sa ranar auren sheik da hassana sossai yakejin kansa a nishadi hadin da ya yi kuma sheik ya karba....

Zama ya yi bakin gado yana tuna irin Alkhairan sheik gashi faran daya ya ba shi mata ya karba ba tare da ya musa....

Dattijo ne ya shigo bakin sa dauke da sallama yana sanye cikin farar shadda..

Kansa aduke ya ce shugaban Adalai Barka da wannan lokacin..

Kai muke jira mu tafi..

Baba Salihu cike da farin ciki yake kallon dattijon ya ce uhmm ka ga wannan Aminin nawa sheik Abdurrazak ban san da wani kalma zan gode masa ba...

Matar da takeso taje har gidan mu tana bincike dan sanin sirrina shi ne naga gaskiya taje tabinciko sirrin namu ba ta aure ni ba nasan yadawa zatayi duk da babu rashin gaskiya a tattare da hakan...

Shi ya sa na zabi in hada ta da sheik in kanta na rawa ne ze sata ahanya..

Kuma na ji mijin nata marigayi mutum kirki ne...

Kuma itama an shede ta shi ya sa banyi kasa a gwiwa ba..

Banson na yi wa Habiba kishiya '' shima sheik dan ya tara biyu ne shi ya sa zankara masa da daya ya iya rikon gida...

Niko fa Inde a kan mamy ne ba zan iya yiwa wata matar Adalci ba...

Sossai Dattijo ya jinjina bayanan baba salihu ya ce shugaba na maganar ka dutse....

Shi aure anayin sa ne inhar mutum zeyi Adalci tun da ka nuna hada mata biyu anan za ka gaza dole ne ka janye...

Uhmm yawwa ka gane nufina tashi ya yi Daga zaunen babu ba ta lokaci suka fito Daga gidan....

Koda suka isa aka kai goron baba Salihu ya ce uhmm Nine zankai Amarya garin kano '' bikin nake jira sanna in tafi...

Sossai suka yaba da halin mutuntaka irin na sarkin adalai.....

Baba Salihu sanarwa sheik labarin yanda akayi komai ya yi sossai sheik yaji dadi tare da masa Albishir tun da Amarya zata tare za su koma sabon gida...

Yanacen anata gyare gyare Daga haka suka yi sallama....

Shiko Sheik cikin hanzarin sa ya sa aka gyarawa anty dakin nata da ya yi kura komai aka gyara mata tsaf har tukwane saida ya sa duk aka wanke mata su....

Mama dake kallon shiga da fitar sa ta ce uhmm mijin ta ce anata hidima gimbiya zata iso....

Cak sheik ya tsaya yana jinjina kalaman ta...

Waigowa ya yi tare da isowa kusa da ita ya ce...

Ai ban girma ne kazama matar ka duk abun da ta ce shi zakayi wannan ba haramun bane dan ance min mijin ta ce....

Dan bakiyi karyaba sai abun da ta ce shinake yi nima sai abun da nace shi take yi kinga ita matar nace take ni kuma mijin ta ce ya kike ganin sunan yada ce ɗamu Ko....

Yar uwar ki zata zo amma kinkasa tsinana mata komai dan bakin hali..

Da kaina zan shiga kitchen indaura masu girkin Ko inkira kanwar Asiya '' tazo ta dafa musu koda taliya ce dadin abun harda yar ki acikin su.....

Kwabe baki Mama ta yi ta ce uhmm yata tana ciki namata girki ita da Asiya wannan bakar Aljanar ka ita ce bazata ci ba..

Alhmdulilah ya furta tun da ita bakar Aljana ce ke kuma bakar zunubi Ko..

Ba girmana bane in tsaya ina biye miki ba...

Amma kisani wallahi Aisha na gaji da halin ki.....

Daga ji shi ya sa nakosa wannan Amaryan da zanyi Sa'adatu tasamu abokiyar shawara da sauran su wacce zasuyi taimakeni in taimakeki bawai zaman dutse irin naki ba....

Ran Mama ya yi mugun baci waini yau Sheik yake fadawa bakaken maganganu...

Wuce ta ya yi domin shirya dan jirgin su Anty na gab da karasowa..

Wayar Mama ce ta soma. Ring tana dubawa taga bakuwar lamba ce kuma ta kwatano shi ya sa ba ta ki dagawa ba.....

Daga can ɓangaren cike da murna harda buga uban tsalle a daki bakin ta awashe ta ce wayyo Mama na '' Rahama ce....

Mama kallon wayar taki da kyau Jin dai ba Mafarki take ba..

Ta ce Rahama yau kece kike kirana dan kinga anty taki ta baro kasar Ko....

Nan da nan jikin Rahama ya yi mugun sanyin cikin kasa da Murya ta ce mahaifiya ta kodaya karkiyi fushi dani wallahi tun da nazo kasar banda layi sai yau nasamu...

Ki tambayi Abby ran nan ma da yake son magana dani kiran Abdul Samad ya yi ya hadashi dani...

Haba Mama kin san in inada waya da layi ba zanki nemar ki ba....

Kece uwa ta karki yi fushi dani dan Allah...

Mama cikin Jin dadin kalaman Rahama ta ce uhmm na zata kin canza uwa ne...

A'a Mama banda kamar ki aduk duniya dagake sai Abby sai Anty na...

Jin ta Ambaci Anty nan da nan hannurin dake kwance kan fuskar mama ya ba ce bat...

Ta ce dan uban ki meye na kawo zancen Sa'adatu agabana...

Rahma sossai takejin haushin Rashin kaunar da mama ke nunawa Anty '' ba a canza uwa ne data canza haka zuciyar ta ke raya mata....

Afili kuma hakuri tashiga bawa Mama ta ce ina yaya Abubakar yake ne tasan inta ce ina Abdul jalil yanzu zancen ze lalace...

Mama ta ce yana lafiya lau nayi kewar ki yata tun ranar da kuka zo Asibiti duba Salma keda mijin naki bankara sanyaki a idanuna ba...

Rahama cike da bukatuwa ganin uwar ta ta ce InshAllah mun kusa zuwa zanzo gida in yi kwanaki Mama na..

Sun taba hira sossai Rahama taba Mama labarin su Mamy sossai Mama ta ji dadin karamci na Mamy ta ce Rahama ta turo mata lambar Mamy ɗana Samad '' 'babu ba ta lokaci Rahama ta tura mata Daga suka yi sallama....

Mama tabe baki ta yi ta ce uhmm yata tana gidan daula' ɗaman ba a son ka fito gidan dadi kaje gidan wahala ba irin na Salma ba dole yau zamu rikita Al'amin......

*************************

 

Shiko Al'amin zaune yake gaban malamin nasa..

Ya ce malam inada mata ta amma nalura sotake ta rabu dani..

Ni kuma ban gama latsar Zuman ta ba..

Malamin ya ce uhmm ai hâr mijin dazata aura sun fitar mata...

Amma mijin dan karya ne suka hada baki da Aminiyar uwar ta dan acuce ta yanda za su samo kudi ta hannun su....

Al'amin jinjina Al'amarin ya yi ya ce uhmm ni dai gaskiya ba zan sake ta...

Badai karyan Arziki takeso ba uhmm kwanan nan zan Faso gari wallahi zatayi mamaki Ko yanzu na fara samun kudi...

Malam ya ce yawwa kayi kokari kabar gidan da kake ciki kasamu miliyan daya kaba uwar ta..

Ita kuma yarinya basai na fada ba...

Kar kayi wasa inhar ka san kana son ta...

Dan inhar ba ka nuna mata kudi masu yawa ba na tashin hankali ba akwai matsala....

Al'amin cike da yarda da shawaran da Aka bashi ya ce InshAllah zangwada

Sai kusan karfe daya jirgin su Asiya ya sauka a babban filin airport na kano....

Sheik da kan sa ya je dauko su Anty tare da drever ka sancewa Abubakar baya zama gida Ayyuka sun masa yawa shike kula da komai na baban sa.....

Cike da jindadi ya tarosu yana ganin sun sauka a jirgi...

Anty sai Washe baki take taga mijin nata shima din murna agun sa baya misaltuwa yau gashi ga sanyin zuciyar shi...

Basu ba ta lokaci ba suka shige mota direct gida suka zarce...

Asiya cike da gajiya ta ce nikam nayi gidan mu..

Sheik ya ce A'a babu inda zakije kin dawo da zama agidan nan bakisan mun bayar da auren ki ba...

Gab gab haka zuciyar Asiya yashiga dukan uku uku....

Dago kai ta yi tana kallon Sheik dake kokarin shigar da kayan su dakin Anty...

Ita Ko Salma dakin mama ta tafi cike da takaicin wannan rashin nasara data samu.......

Ita Ko Asiya Mutuwar tsaye ta yi tana kallon Sheik dake fira da Anty yana bude mata kulolin abincin da Aka aiko Daga gidan Asiya....

Mama

 nunawa ta yi batasan da zaman anty ba bare ta yi mata barka da isowa

Anty tana gama shirya kayan su ta tashi ta nufi dakin mama cike da ladabi ta ce Maman Salma mun dawo...

Mama tabe baki ta yi ta ce uhmm nasan kindawo to Barkan ki.....

Anty ta ce yawwa godiya nake..

Tare da komawa dakin nata.....

*************************

Bayan kwana uku rayuwa nata tafiya yanda akeso...

Al'amin yazo da niyar daukar Salma su tafi '' Mama ta ba ta wani kullin magani da zata shaka miki inhar yazo...

Cike da hanzarin taje ta tarbeshi har tana wani shafa shi '' lura da bayanin da malamin ya yi masa ya sa ya fara ja da baya baya.

Ita Ko tana kokarin ta kamo shi..

Yana zille mata.....

Ganin akwai abu a hannun ta hakan ya sa yakama hannun nata ya murda saida ta saki kara dan Azaba ya ce uhmm wallahi baki isa yau dinnan zaki zo mu je sabon gidan mu...

Yarfe hannayen ta take yi cike da Azaba ta ce ahaka zanbika..

Babu inda zanje ka kama kanka...

Yayi daidai da shigowar Abubakar daidai wajen nasu ya tsaya yana kallon yanda Salma ke rashin kunya....

Cike da mamaki ya daka mata tsawa tare da kai hannu ya wanke ta da mari.. Cikin fada ya ce mijin ki yawuce raini Ko bakisan girman miji bane...

Wannan ba tarbiyyan gidan mu bane..

Kallon sa ya maida a kan Al'amin ya ce kayi hakuri kadawo anjima da an yi lasa'ar kadauki matar ka.

Ku tafi..

Al'amin cike da Jin dadi ya ce yaya Abu nagode Allah ya saka da Alkhairi....

Itako Salma sossai marin da yayan ta ya yi mata ya yi mata zafi..

Yana shiga cikin gidan ya iske Mama da sheik zaune a dakin nasa.

Da Alamun korafi take masa a kan wannan auren da zeyi '' shikuma sai fadi yake mata sunyi yawa dole ayi ta rage su...?

Mama ta ce wai wannan matar a ina take ne..

Ya ce Gabon

Girgiza kai ta yi ta ce wani munafuki ne yahada wannan auren '' dan nasan ba ka zuwa nema '' saide abika dashi....

Kokarin ba ta Amsa yake ganin Abubakar yashigo ya sa shi yin shiru '' dan yanzu soyake ya kora mama makarfi '' tunanin mahaifin nasu yake '' yaki bashi daman ya koya mata hankali ta hanyar tura ta makarfi ta yi koda shekara daya ne...

Abubakar da ransa yake aba ce ya ce Abby wallahi Salma batasan darajan aure ba..

Kaga yanda take zagin mijin ta Shiko yana tsaye yana kallon ta....

Ran sheik yakai kololuwa wajen baci hakan ya sa miki tsaye cikin zafin nama yabar dakin..

Koda ya isa zaunen be iske su Salma ba.....

Cikin gidan yakoma tare da zuwa dakin su Salman iske ta ya yi zaune zata bude data....

Dago kai azabure ta yi ganin yanda...........

Ta ku har kullum kyauta Daga AllahƘANWATA

Littafin nan kudi ne Inkin ganshi a wajen group dîna na sata ne

Inkina bukata ga nomba

09069080725

8️4️

Dago kai Azabure ta yi ganin yanda yake kokarin kai mata mari...

Cikin gigita ta ce Abby lafiya kuwa...

Dan uwar ki mijin naki kike wa rashin kunya abun da kika ga jatimar ki ta nayi shi ne zaki masa to wallahi ba zan lamun ta ba...

Mama dake karasowa ta ce A'a kar ka zage ni inzakayi mata fada kayi mata amma ai wannan zagina kake yi Nice mara kunya Ko...

Sheik cikin Jin haushin Mama ya ce Aishatu wallahi inhar Salma ba ta koma gidan mijin nata a yau dinnan ba a bakin auren ki duka igoyiyon su tsinke....

Azabure Mama da Salma suke kallon Sheik dake kokarin wucewa sashin nasa cikin bacin rai....

Bakin mama na rawa ta ce '' Salma kinji abun da yafada kuma tun da muke betaba mun irin wannan furucin ba....

Salma cikin gigita ta ce mama ni gaskiya ba zan koma ba...

Tass kake ji mama ta wanke ta da mari yau na tabbatar ke banza ce Salma a kan ki igiyar aure na '' 'na neman tsinkewa shi ne zaki ce' '' ba za ki koma ba '' kenan inbar gidan nan kike so...

To wallahi baki isa ba...

Salma rike da kuncinta hawaye shar a Idanun ta ce mama yau da kanki kika sa hannun ki kika mare ni...

Yaya Abubakar ya mareni..

Abby ya mareni..

Kema kin mareni..

Kusan lokaci daya yau na tabbatar ba a kauna ta agidan nan..

Mahaifina na korana ke kuma dan ya miki barazana tome A'ciki Dan ya sake ki din..

Mama batasan sanda ta doki takalmanta ta rinƙa bugawa Salma ba '' tana ihu '' sossai mama ke bugun ta '' ta ko' ina..

Sheik yazo daidai fita yaji yanda take bugun Salma cak ya tsaya ganin Anty ta fito hakan ya sa shi kallon anty cikin bacin rai ya ce Sa'adatu koma daki nace Ko..

Babu musu ta koma tana Girgiza kai...

Shiko Sheik karasowa wajen Mama ya yi cikin Daga Murya ya ce Aishatu ki sakar mun ya....

Dan ke ba ki da hankali saiki buge ta..

Mama cikin takaici ta ce yarinyar nan ta rainani waini take gayawa zancen banza...

Sheik ya ce kwarai kuwa ta gayamiki ai Salma kawar ki ce...

Dan me bazata fadi son Ranta ba ni tafadamun mana wargi waje ya samu...

Daga haka ya sakai yafice Daga gidan yana Girgiza kai...

Ranar mama ba ta bar Salma ba '' kiran Al'amin ta yi ta ce yazo daukan Salma cike da Jin dadi Al'amin yaturo yayar sa Mariya...

Koda Mariya ta iso gidan '' cike da girmamwa ta gaisa da mutan gidan...

Anty ta ce badan ban nemi izini ba '' ɗana raka ku har gidan ki..

InshAllah innasamu dama zamu kawo miki ziyara nida Asiya...

Sossai Salma ke kukan zuci wai yau mama ce ta hada mata kayan ta..

Babu rarrashi babu magana me dadi neman kawai take tabar gidan....

'' 'Mariya' tarar me napep ta yi tare da taimakon Abdul jalil aka saka kayan Salma cikin napep din.....

Kwatance mariya tayiwa me napep din unguwar da za a kai su...

Ita Ko Salma zaune take zuciyar ta na tafasa..

Sam taki kula Mariya data rakota banda hararan ta ba abun da take yi...

Suna isa gidan '' Mamaki ne yakama Salma ganin wani shahararren gida na gani da na fada.

Kamar gidan daya da gidan Samad sai dai nasu bekai nashi haduwa ba..

Mariya dake kokarin kama hannun Salma domin shiga gidan..

Nan da nan taga Annurin a fuskar Salma..

Waigowar da Salma zatayi Al'amin ta hango cikin wata bakar mota Mercedes cike da zallan Mamaki take kallon sa har ya yi parking A gaban su...

Bakin Salma na rawa ta ce.........

Al'amin ina kasamo mota ne...

Murmushi ya sakar mata cike da jin dadin ganin ta '' ya ce Amarya mushiga Daga ciki wannan motar ɗana tuko mallakkin kine nawa yana cikin gidan..

Hannun ya yi musu ya ce mu je Ko..

Ba musu suka bi bayan sa ya yi musu jagora har cikin gidan.....

Mai gadin Barka da zuwa yake ta fadi '' soya ke ya yi magana da Al'amin ya tambaye sa Ko ita ce matar sa '' yana gudun kada ya kwabsa masa......

Hakan ya sa suka yi cikin gidan...

Wani katoton falo '' sossai mai girman gaske..

Anzuba daula a falon '' kujeru yan waje forein '' komai special hatta carpet din dake malale tsakiyar Falon shima abun kallo ne...

Salma tazama kamar wata bakauya badan ba ta taba gani ba saidan mamaki ne yakamata wai nan gidan mijin ta ne....

Ita kanta Mariya cike da mamaki take dan a tunanin gidan haya ne..

Saita ga sabanin haka so take ta zanta da kanin nata amma babu dama ganin Salma na wajen.....

Salma dube dube tafara acikin gidan tana leka lungu da sako na kowani gidan....

Ganin Salma tabar falon ya sa Mariya fuskantar Al'amin ta ce kai ina kasamo wannan gidan '' da kudi da kake ta fantamawa nifa abun ya fara ba ni tsoro.....

Al'amin tabe baki ya yi ya ce kema zakiyi irin abun da baba ya yi ne nacewan ba zai ci kudin ba '' sai yaji kwakwaran sana'a ta...

Toke ba zan boye miki ba kuma dan Allah karki tona min Asirin nashiga kungiyar Asiri na mafiya....

Mariya cikin gigita take kallon sa ta ce haba Al'amin meya kaika ka san hadarin dake cikin wannan kungiyar..

Uhmm Mariya kenan nifa ba zan ba da Jinin kowa ba saina Salma...

Azabure Mariya ke kallon sa ta ce bangane Jinin Salma za ka bayar ba...

Matar ka ce fa...

Murmusawa ya yi ya ce mata ta ce amma batasona dukiya takeso fiye da komai zanbata dukiya taci a karshe inmika ta....

Innaliahi wa'inna ilairajun Mariya take ta maimaitawa ta ce Al'amin kaji tsoron Allah dan Allah kar ka cuce ta '' tana dauke da cikin ka...

Anty Mariya saita haihu zanbada Jinin ta '' kinga tabar tarihi kenan.

Narokeki karki tona mun Asiri yarda ce tasa nabude miki cikina..

Isowar Salma ya sashi yin murmushi ya ce yadai Amarya gidan ya yi miki ko ''

Kada kai ta yi ta ce gaskiya gidan ya yi kabari sai na haihu saika canza mana gida....

Kuma ina bukatar yan aiki...

Mariya cikin dauriya da tausayin da Salma tabata ta ce uhmm.zaki samu yan aiki har ki gaji dasu yar uwa ta...

Nan dai ya nunawa Salma dakin ta..

Da komai yanda suke..

Sossai ta ji dadin hakan...

Tana murna sotake takira mama marin da ta yi mata da duka ya sa ta ce uhmm ba zan kirata ba..

Sai dai ta ji agari ina fantamawa da naira badai ni ta wulakanta ba..

Koda Mariya zata wuce''' Al'amin duba dari yadauko yamika mata amma taki Amsa ta ce kabar shi nagode...

Salma ta yatsine fuska ta ce haba anti ana baki kina kin Amsa..

Murmushi ta yi ta ce aiya ba ni kafun inzo sun isheni haka...

Al'amin ya ce haka ne to anti mariya mu je in raka ki.....

Har bakin gate ya rakata yana kara jaddada mata karfin AlKawari data dauka..

Cike da yarda da kai ta ce Al'amin baza a ji shi a baki na ba..

Komawa ya yi cikin gidan yabarta anan tsaye..

Itako tsaye take tana lissafin anya zata iya barin akashe rai..

Taci Alwashin inhar salma ta haihu zatasan dabarun dazatayi ta ganar da ita gaskiya ba tare da ya sani ba..

Da wannan tunanin tabar kofar gidan....

Kwatano

Fulani cikin tashin hankali take kallon bokan jeji ta ce kana nufin bakin Aljani ya fallasa sirrin mu..

Bokan jeji cike da takaici ya ce baduka bane dan ya kwantar mata da hankali ya ce '' wace ita data San sirrin namu sai dai ta ji na Farida...

Ajiyar zuciya Fulani ta sauke cike da Jin saukin Asirin ta be tonu ba..

Ta ce bokan jeji yakamata mijina a sake masa sabon jiko jiya naga kamar yana fadin '' ina zega Salihu koda sau daya ne........

Bokan jeji ya ce ina ba zai ga Salihu ba''' kuma kisan yanda zakiyi kibashi magunguna yasha '' shikuma yaba baban shi...

.

Kasaitaccen murmushi cike da takama ta ce '' watau abun naka aike aike ne...

Kwarai kuwa cewar bokar jeji..

Sun dade suna tattauna Daga karshe suka yi sallama..

Ta fito cikin ciyayi nan tare da nufar motar ta......

Rahama zaune take tana gyare gyaren dakin '' mijin nata..

Taji wani iska me karfin gaske ya kada '' nan take tafara adu'oi....

Wannan iskan na tsai gaitawa Idanun ta suka sauka akan.....

Takarda dake kan gadon nata.

Cikin Azzama hannun ta na rawa tadau takardan

Koda ta warware takardan ganin rubutun ta yi dan Jan biro aka rubuta shi ta harshen larabci '' hakan ya sa hankalin ta ya yi mugun tashi cike da aro jarumta take son ganin meye A'ciki...

Sallamar Samad ne ya sa ta kokarin boye takardan amma ina yariga da yagani '' kusanto inda take ya yi cikin hanzari yana mata kallon tuhuma

Cikin tsaita nutsuwar sa '' ya ce Hubby me kike boye mun ne bakyason ingani...

Bakin ta na rawa ta ce uhmm kai me ka gani..

. Hannun ta ya kamo ya hade da nashi yana kokarin amsar takardan...

Girgiza kai tasoma ta ce A'a Amjad dan Allah kar ka amshi wannan takardan Idanun ta nan da nan yakawo ruwa''Sam batason yakaranta abun da ze Girgiza shi...

Kallon ta yake yana nazartan ta''' miko mun ya furta cikin kakkausar murya tare da hada rai kamar bashi ba...

Ganin yanda ya canza launin sa' 'yasa ta tsoro ta

Babu musu ta mika masa

Zama ya yi bakin gadon yasoma karantawa''' a fili.

Kamar haka....

Rahamatullah hakika haduwa ta dake bemun dadi ba' 'nasan kinada sirrin adu'a da zaki iya dawo dani cikin dakin ki inhar bancika AlKawari ba.....

Bokan jeji ya kar kade ni kada in sanar miki da komai nace masa naji..

Amma ban dauka ba...

Rahama nafara baki labari to yanzu zanci gaba Daga inda natsaya aranar kin tambayeni laifin mène uban mijin naki yayi...

Abun da ya faru da sa hannuna ni Aljani Sultan..

Sarkin Adalai Sarki ne mai gudanar da mulkin sa a kan ka'ida da dokokin musulunci '' babu yanda Fulani da Farida basuyi ba dan asauke shi ba...

Ita Farida tanason ya sauka ne dan tun farko be aure ta ya auri kanwar ta da Aka bashi zabi '' wannan bakin cikin yana nan aranta...

Ita Ko Fulani ta nemi da Sarkin Adalai da ya yi Alfasha da ita...

Ya nuna mata Sam shi ba zai iya cin Amanar kanin sa ba..

Watarana safiyar wata juma'a Sarkin Adalai ya fito Daga sashin nasa zanshi Fada '' yahadu..........

Ta ku har kullum kyauta Daga AllahƘANWATA

Littafin nan kudi ne Inkin ganshi a wajen group dîna na sata ne

09069080725

8️5️

Yahadu da wata baiwar Fulani mai suna Saratu '' cikin gigita tana ihu ta ce Shugaban Adalai dan Allah ka taimaka mun kwarto ne acikin dakina....

Cikin gigita yake kallon ta ya ce Saratu kwarto a dakin naki kuma...

KADA kai ta yi cikin kuka ta ce wallahi da gaske nake ya shugaban Adalai nasan saukin kan ka ba kamar tsauran sarakuna bane dan Allah kasa wani ya taimaka mun....

Kallon ta yake yana nazartan ta ya ce yanzu na aiki waziri da fadawa wajen duba dabbobin da za a yanka Sadaka..

Kin tabbatar yana cikin dakin mu je ingani sai insa '' akamashi..

Gaba ta nayi yabinta abaya ''hannun sa najan Carbi...

' 'Fulani da maman Maryam suna labe suna kallon yanda Al'amarin ke faruwa' 'hakan ya sa cikin sanda sanda suka ringa binsu abaya....

Dakin ta bude ta shiga''' tsaye bakin kofar ya yi rike da wayar sa a hannun sa yana haska cikin dakin....

Cikin fada ya ce ina kwarton yake ne...

Be Ankara ba sai dai yaji anbuga masa karfe' a kan sa wanda ya sa ya sa ki uban kara nan take yafadi akasa tsumamme...

Fulani data buga masa wannan karfe da taimakon Maman Maryam da saratun suka shigar da shi cikin dakin...

Kaya suka fara cire masa '' saida ya saura Daga sai boxer ''

Saratu itama cire nata kayan ta yi takwanta kasa '' Fulani da Farida suka daura shi saman Baiwa Saratu...

Nan da nan Fulani ta fita taje tadauko wani kwarya mai dauke da Jinin kaza..

Ta shigo dakin dashi...

Abakin Sarkin Adalai ta zuba masa tare da shafe jikin nasa....

Soma bubbuga kafafun sa ta yi tare da shafa masa ruwa a fuska '' ganin numfashin nasa na kokarin dawowa ya sa ta diba aguje tana tsala ihu cikin masarautar.

Ita Ko Farida nan da nan tabar dakin '' ta yi ɓangaren Mamy tare da shiga dakin Khadija dan tsafta ce jikin nata.....

Nan da nan dandazon bayin dake cikin masarautar da jama'ar Sarki da suka shigo da dabbobin daya basu umarni za a yanka na sadaka..

Dukansu cikin gidan masarautar suka nufa Gadan Gadan cikin zafin nama....

Tsohon Sarki Turaki shida uwar gidan sa Mama karama har rige rige suke dan zuwa ganin abun da ke faruwa...

Cikin gigita suka nufo inda Fulani ke tsala ihu suka yi tare da Abban Marwan da shima dakin nasa ya fito..

Cikin Rawar murya suka ce Fulani meyake faruwa ne jibi yanda kika tara mutane amma kin ki bayani sai ihu kike kina salati...

Cikin kuka take kallon su ta ce Sarki Salihu na dade da gayamuku masafi ne baku yarda ba..

Gashi cen yayiwa baiwata fyade hade da zukan Jinin jikinta nima ihun ta najiyo nazo naga abun da yake faruwa...

Cikin gigita tsohon Sarki. Ya ce mu je mugani.

Mamy da Samad kusan a tare suka nufo wajen Ko wanne cikin hanzarin sa..

Koda aka nufi dakin Saratun iske Sarki Salihu akayi yana kokarin tashi Daga kwance da yake '' itakuwa Saratu zaune take gefe tana kuka mai tsuma rai '' tana fadin Sarkin Adalai menayi maka da zakayi lalata dani' Wayyo jinina daka diba mezakai dashi...

Cak Mamy da Samaɗ ɗa Mama karama suka tsaya kamar an buga musu kusa...

Mamy bakin ta na rawa cikin kuka ta ce mezan gani Salihu kaine awannan yanayin tana nuna shi da ya tsaya..

Bakin sa na rawa cike da mamakin yanayin da yake ciki ya ce wallahi tallahi niban sa abun da ake zargina akai ba...

Juyowa ya yi yana kallon Saratu dake kuka ya ce ke Saratu kiyi musu bayanin abun da ya faru mana....

Sauratu bakin ta na rawa ta kasa hada idanu da shi cikin kuka ta ce fyade yamun...

Kuma harda Jinin jiki na ya fara tsotsewa wai kada yarasa mulkin sa..

Samad rintse Idanun sa ya yi Jin kalmar fyade..

Tsawa ya dakawa Saratu yana kokarin shako ta '' keee wallahi karya kike.. Nace karya kike bude mun gaban naki mugani inda ya yi inzali..

Tsohon Sarki da shima duk yagama yarda da Al'amarin ya ce Kai Samad kanka daya kuwa ya kana ganin gaskiya kana takewa.....

Yarima Samad cikin ruwan bala'i dake cin yajuyo kan tsohon Sarki ya ce wallahi karya ne sharri ne '' in gaskiya ta bude gaban nata mugani....

Mamy dasai yanzu hankalin ta yadawo jikin nata ta ce '' wallahi nima ban yarda mijina ze aika haka ba..

Cikin zafin nama taje zata kamo hannun Saratu..

Mama karama tarike ta ta ce Habiba dakata abi komai a hankali..

Baba Salihu da yanzu ya fahimci ashe sharri ne akayi masa kuka ya fara ya ce Saratu '' menayi miki '' wallahi karya take abu daya nasani shi ne ta ce in taimaka mata akwai wani a dakin nata...

Koda nazo banshiga dakin ba Daga waje natsaya daganan bankara sanin abun da ke wakana ba...

Ni Aljani Sultan ni ne na shiga jikin Tsohon Sarki da dan sa Sani.....

Tsohon Sarki da dan sa nan da nan suka ji sauyin yanayi a tattare dasu...

Sani cikin tafasar zuciya da maganin dake cinsa ya ce '' Wallahi Salihu kabani mamaki kana sarkin Adalai.....

Shima Tsohon Sarki ya ce Albasa batayi halin ruwa daman abun da ake fada a kan ka ina karyatawa gaskiya ne...

Samad ya ce A'a Sarki kar ka yarda da zancen nasu Sharri ne nace tabude gaban nata kunki yarda...

Sarki Turaki cikin jin Haushin Samad da Mamy da suka ki yarda da zancen sai Karima dake bayan su''' itama kam taki yarda wannan abun gaskiya ne..

Tsawa ya dakawa yarima da Mamy cikin Daga Murya ya ce inban da iskanci kuna ganin zahiri kuce karya ne...

Maman Maryam cikin shigar ta da ta yi na dogon riga karasowa wajen nasu ta yi '' cikin ɗamuwa take tambayar Mamy wai mêke Faruwa ne..

Mamy shiru ta yi banda kuka ba abun da take...

Maida kallon a kan Fulani ta yi suna kashewa juna idanu ta ce Fulani dan Allah gayamin mêke Faruwa ne..

Fulani cikin tsananin Tashin hankali ta ce '' Sarkin Adalai ne aka kama yayiwa baiwa ta Saratu Fyade....

Harda shan Jinin jikin ta...

Salati Maman Maryam tafara tana tafa hannu sake da baki take kallon Mamy dake kuka ta ce Habiba hakan ya faru '' daman nasha gayamiki mijin ki dan kungiyar Asiri kinki Yarda yau dai gashi gani da Idanun ki...

Marin da Samad ya yi mata ya sa tafara ganin walkiya har tana neman faduwa '' ba ta Ankara ba '' sai ji ta yi ya yi mata muguwar shaka '' wanda yajawo hankalin Mamy '' '

Cikin hanzari taje kwatar yayar ta hannun Samad amma ta kasa...

Saida Abban marwan ya je Da ƙyar ya banbare ta a jikin sa...

Fulani na ganin Abun da akayiwa Farida kama bakin ta ta yi ba ta kara fadin komai ba......

Shiko Sarki Turaki gyaran murya ya yi cike da takaici ya ce '' Likitar masarautar yazo yaduba Saratu '' ya bincika shin dagsk ne ya yi mata fyaden kuma ya duba inda aka dibi Jinin nata....

Sossai hankalin '' Fulani da maman Maryam dake numfashi sama sama '' dan ba ƙaramin shaka Samad ya yi mata ba....

Likitan masarautar yana zuwa ya fara bincike sossai cikin aikin nasa '' ya ce sai nan da Awa biyu result ze fito...

Gabadaya Fadar Sarki aka hallara dan jiran sakamakon wannan Abun da ya faru...

Mamy zaune take ta yi uban tagumi tana jiran yanda za a kaya.....

Sarkin Adalai dake gefe zaune kukan zuci yake yi sossai yana ayyana Abun da ze faru.....

Likitar Masarautar koda yadawo da Result din wajen yi gwaji nine nan Aljani Sultan na canza result din na maida shi positive....

Koda result ya fito yaga Positif sossai hankalin sa ya tashi babu damar ya canza ya ce negatifs ne a je wani Asibitin aka sabanin nashi....

Cikin Rashin kuzari ya mikawa Sarki Turaki result din...

Sarki na budewa yaga positive Salati yasoma ya ce Salihu Allah yatsine maka Albarka Allah ya tarwatsa ka '' 'Allah yahana gaban ka yin kyau ya hadaka da tsautsayi da hasara....

Sarkin Adalai cikin kuka da yazo masa ya ce Nina San sharrine a kamun babu me yarda dani sai mutum uku kacal' 'Mata ta sai ɗana' 'sai baiwar sa...

Ya Abbana ka fahimce ni wallahi ban aikata ba.....

Mama karama dake kuka ta ce nima nasan ba ka aikata ba.

Fulani da suka ji dadin abun ita da mijin nata da maman maryam' 'murmushi suka yi....

Baba Salihu tashi Daga zaunen ya yi ya ce ni Salihu Daga yau na sauka Daga kan karagan mulkin nan..

Kuma na damkashi a hannun Abbana'''..

Yau zan bar Masarautar nan....

Sarki Turaki dake masa kallon Azzalumi cikin Tsawa ya ce za ka iya tafiya amma babu inda za ka je da Mamy dan bazata bika ba.

Yayan ka ma babu wanda ze bika kai kadai za ka tafi kaje kaji da mugun Aikin ka

Mamy cikin kuka zatayi magana Sarki Turaki ya dakatar da ita ya ce Habiba babu inda zakije da wannan mushurikin....

Baba Salihu cikin zafin nama ya yi hanyar dakin sa yana kuka duk wasu abu dayasani masu muhimmanci ne a tattare da shi ɗuk ya dauko su.....

Ta bayan gida ya fi ce dan Sarki Turaki beyi tunanin shin dagaske yake ba a kan zebar gidan ba...

Tura dogarai ya yi a je aduba me yake yi ne a daki dan gidan kurku '' za a kai sa nan zeyi shekaru uku..

Sannan ya fito koda suka dudduba dakin wayam suka gani babu Sarkin Adalai aciki

Labari yajewa Sarki a kan ya gudu Sarki ya ce dan iska ya san mugun aikin da ya aikata ba zai iya hada idanu da Al'umma ba...

Wannan shi ya tabbatar mana ya gujewa hukunci ne...

Labarin Ankama Sarkin Adalai yana yi wa baiwar matar kanin sa Fyade yakara de duka duniyan hausawa harda turawa dan Shugaban Kasa na saudiya saida ya yi magana a kan haka ya ce cin Amana ne ''Sarki ya cutar da nakasa dashi....

Duk cikin kwatanon duk inda ya je maganar sa ake yi gidan TV gidan redio kasa zama kasar yayi' '' tare da tafiya kano gun neman Wani malami Ko ze samu mafaka agidan nasa.........

Tun da Daga wannan Ranar Saratu ta shiga tashin hankali sam ba ta da nutsuwa inta kwanta barci abun tsoro da mugun mafarkai ke hanata barci...

Zuwa ta yi tasamu Fulani ta ce wallahi nayi nadamar abun da na aikata tun daga ranar sainayi Mafarkin Sarkin Adalai yana kuka yana fadin Saratu kin cuce ni...

Yana fadin Saratu zaki girbi abun da kika shuka....

Fulani. Ta ce karta damu zata daina '' amma shiru abun sai gaba yake yi sai tana barci sai ta ji ana kama kafafun ta '' tana ihu tana fadin me nayi muku ne....

Akarshe ta yanke shawaran zata fallasa sirrin su..

Fulani data Samu labari ta aika a kashe Saratu '' labari yazo m'a Saratu a kan kisan da akace ayi mata hakan ya sa tabar gidan taje gidan wata mata tabuya....

Tsawon wata uku...

Rahamatullah anan na kawo karshen labarin abun da nasani ina fatan ba za ki dauki mataki akaina ba.

Bisalam Daga Aljani Sultan....

Sossai wani zufar wahala ya ketowa Samad da Rahama kusan a tare suke kallon juna suna kallon takardan

Yarima Samad tashi tsaye ya yi hannun sa rike da takardan ya ce uhmm Rahama ke Jaruma ce..

Kin jure gwagwarmaya akaina ga wani yanzu kindakko wannan karan tare zamuyi meye mafita Rahamatullah ke nake sauraro..

Tare da dafata '' kallon sa take cikin kunan Rai ta ce Ancuci Sarkin Adalai bazamu kyale su ba..

Dole mu ɗau Fansa..

Yarima ya ce haka ne yanzu lokaci ya yi da za su gane kuren su ina case dayawa agaba na..

Amma case din Saratu shi ne babba ita ce lomar farko...

Rahama ta ce bayan Saratu waye agaban naka...

Bakin sa na rawa ya ce..

Marwan da Salma...

Cikin Rawar Murya ta ce Salma kuma kardai kace ƘANWATA...

Kwarai kuwa kanwar taki yanzu ba lokacin maganar ta bane '' yakatse zancen da neman mafita a kan Saratu.....

Tunani yashigayi sossai '' cikin tabe Baki ya ce nasan wani Soja A buja babban soja ne. Mataimakin shugaban kasa ne...

Rahama ta ce '' ya sunan shi Ko wannan sojan nan mai rikon gaskiya da Amana wanda ya yi fice a kan harkan bincike da bin diddigi '' Yusuf Sani Yaro...

Yarima Samad ya ce kwarai kuwa shi nake nufi '' zan masa magana a kan Saratu '' yana zaune a abujar zeyi komai tun da tana nijeria tazo gidan sauki....

Rahama ta ce gaskiya kasa shi agaba dan wanda yakama mahaifin sa '' a kan laifi to ka ga ba zai yi shayin kamo mana Saratu ba..

Cike da jinjina Al'amarin Ya rungume Rahama yana kuka ya ce Rahamatullah tun ranar danayi tozali da mugun abu a kan mahaifina adaren ranar ne nafara mafarki a kan ki Rahama....

Cike da zare idanu ta ce Amjad kamarya kenan dan fahimtar dani yanda zangane......

Rahma a wannan Ranar nafara ganin ki a mafarki na kina zuwa min fuskar ki dauke da nikabi''' kullum abu daya kike faɗa min shi ne in yi hakuri da jarabawa zanyi nasara...

Kullum faɗa min kike Amjad ina son ka '' ina son ka amma akwai tazara a tsakanin mu...

Niko nace dan Allah meye tazarar sai kika gayamin A mafarkina tazarar b kasa daya muke ba '' idan zan iya inzo kano neman ki '' kuma mahaifina yana cikin garin kanon kusa da wani shahararren malamin Addini..

Koda naje kano duk inda nasan manyan malamai sainaje neman sa. Amma babu nasara...

Ajiyar zuciya Rahama tasauke ta ce Amjad '' Iskar dake tare da kai ita ce take nuna maka hanyoyi acikin mafarkin ki ita ce take zuwa maka da suffa ta dan tasan lallai zamu hadu kuma zamu zama mata da miji tasan tare nida kai zamu kawo karshen duk wani makirci shi ya sa ta yi amfani da wannan damar tun ranar data bude maka idanu a mafarki da fuska ta ka kara ganin ta??

Girgiza kai ya yi ya ce Ah Ah bankara ganin ta ba...

Uhmmm tun da Daga Ranar Burin ta yacika shi ne tabar jikin ka tabar rayuwar ka tadau Alwashin taimaka maka ne bisa zaluncin da taga anshuka muku ta turo ka gareni ne dan mu taimaki Sarkin Adalai....

Yarima Samad jinjina Al'amarin ya yi ya ce nayarda da bayananki hubby na wai ya akayi kike ganin Aljani bayan mu bama gani...

Murmushi ta sakar masa wanda yake sanya ya m'asa zuciya...

Amjad kakana Sheik Kabeer Hizqeel Makarfi shi ne wanda yake ba ni sirrin abubuwa da makaman su' ɗa kariyar su...

Duk sanda zamu hadu sai ya koyae dani abun da mahaifina be koya mun ba...

Ita Salma Sam taki maida hankali''' ka ga nida Abubakar da Abdul jalil mune muke daukan darusan da yake koya mana...

Tun ina gida ake kawo mun irin yaran mata da Aljanu suka aure su..

Da waɗanda iska ke damun su...

Ninan Rahama ana kawo mun mara lafiya daga wata kasa dan neman magani a kan warware sihiri Ko muguwar cuta.....

Ina ba da magani da ayoyin Allah kuma Alhmdulilah ana dacewa dan abun ba dagani bane Daga Allah ne '' kuma Nice sila..

Amjad tun da nataso agidan namu bansamu shakuwa irin ta uwa ba..

Anty ita ce ta zame min uwa ita ce ta zame tamkar uba na.. Duk da mahaifina yana kula dani...

Da karatun mu..

Anty ta koyar dani Addini da koyamin yanda zan mu'amallanci mutane..

Ta koya mun yanda ake zama da miji tun ina karama...

Agidan mu Salma ita ce babban matsalata ina son ta sossai kuma har gobe ina sonta...

Matsalar da Aka samu mahaifiyar mu batason ganin laifin Salma a kan ta zata bugeni '' Salma tana iya fadin abu wajen ma maman mu kuma maganar ta zauna kenan babu wanda ya isa ya ce ba haka bane...

Salma ita ce silan raba aurena da Adamu da za a daura '' wanda yakawo mai Martaba ya karbar maka aurena...

Hakan na dauke shi a matsayin kaddara sai gashi nasamu wanda nafi so game da komai sai yanzu na tabbata Adamu kaunar sa nake a lokacin...

Kaine ainihin wanda nakewa pur love Amjad......

Farkon haduwata da kai tun daga ranar nakasa sukuni '' duk da bawai na gane ainihin me nakeji a tare da kai bane......

Zagin da kai mun na rashin kamun kai shi ne ya hanani barci...

Kayaita ceen murmushi ya yi saida kuncin sa ya lotsa ya ce Rahamatullah '' ranar na ji bakin ciki ganin ki da wannan Adamun hakanan na ji kamar in shake shi...

Nikaina na dauka rashin kamun kai ne ya sa na ji haushin ganin ku...

Saida ga baya nagane ashe kishi nake yi....

Sossai suka ɗara har lakuta mata hanci ya ce Uhmmm shi ne nace mun a airport Ko...

Uhmmm na nace maka koka nace mun harda wani ɗanne fitananne kawai tana murguda baki....

Bawani Fitina kice kinsha dadi '' dariya ta yi sossai saida fararen hakoran ta suka bayyana ta ce uhmm kaida ka afkamun amma ka tashi kanata zuba ruwan masifa harda wani ka fasa tafiya ka san a ranar bama ka isheni kallo ba....

Uhmm inban isheki kallo ba aina ishe Salma Ko...

Tun da suka dauki hoton mu sanda muke kwance a wayar Marwan.....

Cikin zazzare idanu ta ce hoto kuma.........

Post a Comment

0 Comments