In kin karanta ki yi sharing please
Juyawa ta yi ta re da yin ƙunƙuni lokacin da ta ji Muryar Momy tana magana daga bakin ƙofa ita dai tasan ba ta rufe ƙofar ba, wannan ya sa ta juyawa tare da jan maya fin rufar ta dan zaton ta mafarki take sai dai jin muryar Momy ta yi a kan ta tana fadin " wai Hafsa ba zaki ta shi ba sai na ɗala miki duka"
A hankali ta
tashi tana miƙa, "Mum bafa mu da lecture yau dubi agogon yanzu fa 7 ta
yi?"
"Kina jin
ta ko" abin da kawai Hafsa ta ji momy É—in
ta ce kafin ta saka mata waya a kunne, muryar yayar ta ji tana faÉ—a "Hajiya ki shirya
kije gidan kakan nin su Kalil ki É—auko
su ki kawo su nan su ƙarasa sati guda ɗin
kan a koma"
Mum ba ta jira
amsar Hafsa ba ta fice tana ci gaba da wayar ta " ai ke kika kyale su
mutane sunbi sun mallake miki yara"
" To Mum
ya kike so in yi Mansur ya nuna dole sai an kai su, yau É—inma tun jiya na dira masa mitar nawa iyaye ne
baya son su dinga shiga shi ne fa ya ce to in É—auko
su siyi sati"
" Ai kuwa
zaiga sati ki haÉ—a ma
Kalil É—in uniform É—in sa in an koma sch din
Usman ya dinga Kai shi ita kuma ki haÉ—omin
kayan ta in ga in yana da kunyar zuwa ya ce in ba shi su"
Dariya Farida
ta sa " thats my Mum" suna gama tattaunawa bayan ta katse wayar
"Hafsa!" Momy ta kuma kwala kira bayan aje waya.
Rai a cinkushe
Hafsa ta fito tana miƙa da hamma, kai tsaye wurin aje abinci ta nufa tasan tun da
Mum ce ta ke son ta fita da wuri ta dafa breakfast, kamar yadda ta za ta ta
kammala komai tea ta haÉ—a
ta É—ebi chips da
soyayyen kwai ta yo falon dan ba ta son cin abinci kan dining table, cak ta
tsaya lokacin da taga Yaya Usman sam ba ta yi tsammanin ganin sa ba a yanzu,
daurewa ta yi ta ce "yaya ina kwana"
Tsaki yaja
"mene wannan?" ya nuna mata kayan jikin ta.
"wai ke
Hafsa Sau nawa kike son in faÉ—a
miki ki daina fitowa falon nan da kayan bacci"
Kallon kanta
ta yi " but yaya mene ne matsalar kayan nan?"
Hannu ya kai zai make ta ta yi saurin kaucewa
tana dariya, É—akin ta
ta koma mintina baifi ashirin ba ta fito tsaf da ita har lokacin Momy na zaune
tana kallo " yawwa Mum ni na wuce Bala ne zai kaini ko?"
"Eh ki
biya ta gidan yayar taki za ta baki kayan su"
"Tom"
kawai ta ce ta fice
A bakin gate
ya parker motar bugu biyu mai gadi ya buÉ—e
ta shiga da Mijin Faridan ta fara cin tozali.
"lah yaya ashe ma kana gida?"
Dariya ya yi
"yau sarkin rikici ce a gidan namu mukan munyi fushi"
Murmushi ta yi
" a'ah dan Allah, in kun fushi dani ai da matsala, sai in shiga ruÉ—ani, Mun ta shi lafiya ta
faÉ—a lokacin da ta É—an risina"
"Lafiya ƙalau Alhamdulillah,
muje ciki ya ce"
"Ai na É—auka fita zakai?"
"Ah ai
sai nayi wa autar Abba rakiya zuwa falo, kafin in fita" dariya ta yi
"woni" suka sa dariya
A falo ta
zauna inda ya shiga ciki, sai dai wanka ya tarar da matar tasa na yi wannan ya
sa shi komowa suka ci gaba da hira da Hafsan suna ta dariya Farida ta fito tana
taku dai dai tamkar amarya kamshin ta ya mamaye falon, cike da fara'a Mansur ya
É—aga ido ya kalli
matar tasa
"eyye sai anci tarar ki wato da a ce Auta
ba ta zo ba duk wannan wankan haka zan missing kike nufi?"
Murmushin da
tasan yana rikita shi ta masa cikin salon tata yaudarar ta ce kaima dai ai sai
kasa ayi tunanin bana ma gayu fisabilillahi mene cikin wannan shigar kofa mai
ban shafa ba" ta faÉ—a
lokacin da taÉ—an juya
idanun ta bayan ta É—an
kalli jikin ta"
Miƙewa ya
yi yana dariya " ke ko Allah in mutin ya biye miki sam ba zai fita ba, ƙanwar
mu agaishe mun da su Abba," dariya ta sa ta bi shi sai ka dawo min tina kaÉ—an ta dawo tana murmushi.
Sun jima suna
hira da Hafsa kafin ta É—auko
mata kayan yaran ta bar gidan zuwa gidan surukan nasu, tamkar wata babba ce ta
zo haka sukai ta nan nan da ita ya yin da Khalil ke ta faman murna da tsalle
tsakanin jikin Hafsa da Gwaggo wato kakar sa.
Khairat Bacci take
Gwaggo da kanta ta saɓata
a kafaÉ—a tasanya ta
cikin mota tana faÉ—in
" Allah dai ya sa ta zauna dan tun da aka kawo ta yayen nan ba ta yadda da
kowa sai ni"
"In taƙi
yadda ba sai a mayar wa da Babar ta ba" Hafsa ta faÉ—a suka sa dariya duka inda suka shiga mota
Khalil na É—agawa
gwaggo hannu aka ja motar.
*****
Duk da cewar
an musu orientation haka kawai tsoro ya cika shi tunanin yadda za ta kasance
masa da da É—aliban ya
sa gaban sa ke ta faman faÉ—uwa,
yau shigar manyan kaya ya yi sosai haibar sa ta fito, nutsuwa da kyansa suka
kuma bayyana, kallo É—aya
za ka masa kasan shi É—in
nutsattse ne.
Inna na bakin
wuta tana mulmula tuwon siyar wa na safe ya fito, É—auke da kwano da alamu na abin cin da ya yi
kari ne, Inna ni zan wuce asamu a addu'a walllahi tun É—azu gaba na ke faÉ—uwa ji nake tamkar bazan iya ba.
ÆŠagowa
ta yi tana murmushi " kaima dai Muntari yo ai in Sha Allah tinda ka samu
damar tsallake É—aukan
aikin za ka iya ne shi ya sa suka É—auke
ka"
Ajiyar zuciya
ya yi " kin san yaran masu kuÉ—i
koyar da su sai anyi haƙuri"
"Ba fa su
da matsala ba ga sunan ko ina muna ganin su ba, in zanma misali da yaran gidan
Alhaji Sani in ka dubi yadda suke da nutsuwa da tarbiya yaran talakawan ma ba
su da ita"
Murmushi ya yi
" wallahi Inna har kin kwantar min da hankali bari in je kar in
makara"
Miƙewa ta
yi har soro ta biyo shi, "Allah ya tsare min kai ya bada sa'a ya sa a fara
a sa'a"
Cike da kwarin
gwiwa ya fice bayan ya ce "amin"
Da kwarin
gwiwa ya tura gate É—in
makarantar ya shiga É—auke
da littattafan da aka ba shi dan zuwa ya yi nazari ya kuma haɗa lesson plan dan David yaƙi
yadda ya bada lesson plan in wurin sa.
Kai tsaye SS 3
ya wuce nan yake da period É—in
farko, sam baiyi tsanmanin ganin ajin da É—alibi
ko guda ba, dan yadda ya sha ji ana faÉ—e
shi ne yaran masu kuÉ—i
makarar su ta yi yawa.
Cike da
girmawa suka gai da shi ya gabatar da kansa matsayin sabon malamin Physics
kafin ya koma kujerar zaman malami ya zauna, ya hau tambayar sunayyen su duk
cikin jiran takwas É—in
ta yi a KaÉ—a
kararrawar fara lesson, kafin takwas É—in
har hankalin sa ya kwanta har son yaran ya shiga ransa sosai suke ɗan taɓa hira ana kaɗa kararrawa duk suka nutsu
suka hau fiddo da littattafan su, tsarin yaran ya birge shi sosai ba yau ya
fara koyarwa ba domin yana voluntary a unguwar su, nan Makarantar ‘yan
mata ayi shiru ma kawai ya ishi malami.
Motion shi ne
topic É—in da aka ce ya
ƙara
yi musu da alamu malamin su na da ya iya koyarwa dan kuwa bai wani sha wahala
ba dan sun gane topic din sosai tun daga yadda suke watso masa tambaya da kumma
ba shi amsar tambayar da ya mu.
Lokacin bada
class work aka kaÉ—a
wannan ya sa shi rubuta tambayoyin sa ya koma ya zauna lokacin lokacin wa su na
masa tambaya.
Rike da
littattafan na su ya fito dan malamar Chemistry tuni ta hallara har ya fita
wani É—alibi ya ce "
Sir pls Mai ka karanta?"
"Juyowa
ya yi yana murmushi abin da ka ce É—azu
kanasonn karanta"
"Wow É—alibin ya ce u mean engineering
no wonder na ji Ina son ka"
Dariya kawai
Muktar ya yi ya bar ajin sai da ya kai takardun nasu office sannan ya dawo zuwa
SS 2, tun a wurin orientation aka faÉ—a
musu ‘yan
SS 2 sai sun yi haƙuri da su, sai dai sam bai ga matsalar ba in ka ɗauke surutu ƙasa ƙasa
wanda shi tun a GGSS Dala ya saba da wanda ya fishi yadda ma ya fahinta sun fi
SS 3 ɗin ƙoƙari...
Rubutawa
Aeshakhabir
Fadimafayau
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.