Ticker

6/recent/ticker-posts

Ko da so.... (Kashi na Goma Sha Biyar - 15)

In kin Karanta ki yi sharing please

Ruwan da aka tafka jiya da daddare zuwa asubahin yau ya sa kayan da Muktar ya wanke ba su bushe ba, takaici da ɓacin rai duk yabi ya cika shi sam baya son saka ƙananan kaya gashi kaf manyan kayan jiya ya wanke su, cike da ɓacin rai ya buɗe jakar bakkon da ke gefen katifar sa wadda yake sa ƙananan kayan sa shi bama zai iya tuna yaushe ya sanya su ba.

Rai a cinkushe ya shirya ji yake tamkar bai sanya kaya ba, ruwan da aka maka ya sa Inna ta makara batai kosai ba, sai fanke tuni an zuba masa nasa ɗauka ya yi ya musu sallama ya nufi titi.

Sai da ya fara kai abincin sa office ɗin su sannan ya wuce ajin da yake da shi wato SS 2, kamar kullun da yawa sun riga shi zuwa musan man da yake yau ya ɗan so ya makara yana shiga suka sa ihun uncle yau kaine da ƙananan kaya, banza ya musu, ya gaida su suka amsa tare da yin ƙananun maganganu ƙasa ƙasa, girgiza kai kawai ya yi yahau rubutu bisa allo, Khadija da ta doso bakin ƙofar ajin ne ta tsaya turus riƙe da baki tsayawa ya yi da rubutun cikin harshen turanci ya ce "Hajiya kin makara mai makon ki zo ki fara kwafar aiki kin wani tsaya anan"

Ƙarasowa ciki ta yi tana dariya kafin ta ce " class ku faɗamin ba dai dai nake gani ba, anya uncle Muktar ne?," Girgiza kai ya yi Kadija da Fatima ba sa ji sam ya san dama ɗaya cikin su sai ya yi magana. Mustapha ne ya ce ai bari mukai a gama class din mu tambaye shi anya ba twin in uncle Muktar bane.

Fatima da Khadijah ta hango na tawowa ya sa ta leƙawa tare da yi mata alamar ta yi sauri, tana shigowa tasa salati kamar wani babban abu ya faru takaici ya cike Muktar, dakyar ya samu suka zauna, sam bai so yau yake da SS 2 ba gashi dai ya fi son yaran anma sun fi ko wanne aji takura masa, ko dan yanzu ya fara sabawa da ɗabi'un yaran makarantar na rashin hayaniya sam mutsi mutsin surutun ‘yan SS 2 din ya fara damun sa saɓanin da da yake ganin sa ba komai ba.

Yau kusan dai ajin nasa ba su wani gane shi ba dan duk ya ƙare a kan batun kayan da ya sako tamkar wani wanda ya sako kayan da ba su taɓa gani ba, alla alla yake akada ya fice ana kaɗawa ya bar ajin ta taga suka leƙo Allah uncle ka yo kyau " murmushi kawai ya yi tare da yin gaba.

Ko office baije ba ya wuce SS1 su ba su da kula ko damuwa da mai malami yake ciki kamar SS 2 wannan ya sa lafiya ya gama koyar su ya fice lokacin da aka buga break, tana tsaye tana duba wasu takardu da ta amso wurin Abban ta, idanun ta suka wulga caraf suka faɗa kansa tsai ta tsayar da idanun kansa ya yin da wani abu ke yawo a ranta yar take ji da sauri ta ɗauke idanun ta lokacin da ta fahinci ya gane kallon da take masa.

Jiki ba kwari ya ƙaraso dama a tsarge yake ga kuma uban kallo da ta zuba masa duk sai ya kuma tsarguwa daf da ita ya tsaya har yana iya jiyo ƙanshin turaren ta da bai tashi sosai a nutse ta ce "uncle ina kwana?"

Murmushi ya yi " lafiya ƙalau, yau kin rigani fitowa break?"

Itama murnushin ta yi " ina ta kallon ka ko? Yi haƙuri dan Allah kawai gani nayi ka yi kyau?

A ɗan hanzance ya kalle ta yana murmushi haka kawai ya ji kalmomin nata sun masa daɗi, cikin hanzari bayan ta tuna katoɓarar da ta yi ne ta ce cikin rawar murya " kawai yau da nagan ka da kayan da ban saba ganin ka da su bane naga ka yi daban"

Murmushi ya yi " karki damu ai nima na san nayi kyau, duda dai ban kama ƙafar ki ba" ya faɗa tare da yin gaba dan sam kalmomin fun ƙarfin bakin sa sukayi suka fito.

Tsuru ta yi tana kallon sa har ya kule mata samun kan ta ta yi da kasa zuwa kujerar da suka saba ta juya kawai ta yi ajin ta, shiɗin ma kasa fitowa ya yi a office ɗin ya ci fanken sa.

Ko da aka tashi kamar ranar Juma'a yau a bakin gste ta jira shi ya shiga suka tafi yau hirar kusan da Malam Musa sukayi ta dan Hafsa ba ta jin daɗi, gane hakan da Muktar ya yi ne ya sa shi juyowa ya ce "Aunty lafiya dai naga kinyi shiru" tun kan ta yi magana yanayin fuskar ta ya nuna murya kasa kasa ta ce bana jin dadi ne.

Sannu tun da suka tawo yake juyowa lokacin lokaci yana mata yadda ya nuna kulawar sa duk sai ta ji mutuncin sa ya ƙaru wurin ta, a kwanar Dala suka sauke shi ya mata Allah ya sawwake kafin ya tsallaka suka ja mota sukai gaba.

Jiki ba kwari Hafsa ta shiga gidan Gwaggo, Gwaggon na tsakar gida inda Halima ke gefen ta da tana cin abinci da alamu yanzu itama ta shigo dan kayan makarantar ta na school of health technology na jikin ta, sannu da hutawa tama Gwaggo ta shige daɗi, cikin ɗan ɗaga murya Gwaggon ta ce "Bebilo lafiya dai ba haks kika fita ba"

Halima ta ɗan taɓa "ɗan leƙa kiga ko lafiya, turo Halima ta yi kafin ta miƙe ta shiga ɗakin Hafsa ta gani tana ta faman fito da kaya tsayawa ta yi tana kallon ta kafin ta ce Hajiya Hansatu mai kike haka?

Ɗan ɗagowa Hafsa ta yi ta harare ta Allah Aunty Halime banson sunan nan"

"na ji bakya so, mai kike nema haka?" Dafe kai Hafsa ta yi cike da takaici sai yanzu ta tuna a kan drawer ta bari, rai a cinkushe ta ce pad ɗina na mance wallahi," dariya Halima ta yi hardai yau Hansatun nan ba za ta girma shi ne na tashin hankali haka, ina zuwa" ta faɗa tare da fita minti kamar goma sai gata ta shigo da ita.

Amsa ta yi tare da yin ajiyar zuciya dan yanzu da ta fita siyowa gwanda ta tattara ta koma gida.

Zaune suke tana cin abinci Halima na rubutu uncle Zahraddeen ya shigo riƙe da leda, yana ganin ta ya faɗaɗa murmushin sa "kaga manyan ‘yan mata saukar yaushe?"

Dariya ta yi bayan ta ture kwanon yau kwanana uku, ina zuwa kai na fara tambaya ai Gwaggon ta ce baka nan" guri ya samu ya zauna gefen Hafsan bari kawai munje seminar ne yau ɗinma dakyar suka sallame mu."

Bari in zubo ma abinci ta faɗa tare da miƙewa Halima ya kalla, tare da cewa mutun sarkin ƙiwa yanzu da ke ce ko na roka da mita za a zubo"

Dariya ta yi itama na ɗoki ne waye zai ɗauki hidimar ka, kullum kai dai ka ce ayi, harar ta ya yi kafin ya ce in kin gama rubutun ki sarrafa mana kifin nan.

Gwaggo ce ta ce ita da take rubutu Bebilon ta yi dafa mana, a hankali ya ce tab ina Hafsa ina girki kema kinsan Aunty Hadiza ba lallai tana bari Hafsa ta yi komai a gida ba.

Hafsa da ta ƙaraso ce dauke da kwanon abinci da kofin ruwa ta aje masa, tare da ɗaukan ledar kifin aikam na ji ka wato ban iya komai ba kake nufi, ta fada da ɗan tsuke fuska.

Dariya ya yi ah haba "ni na isa ince baki iya ba, kawai banso ki wahala girki a kurfoti ba sauƙi, ki ajiye Halima ta dafa kinji Bebilon Malam," yar harar wasa ta watsa masa "ai fa ba zakamin wayo ba girki na yau dole za ka ci gidan nan"

Gwaggo ce ta sa dariya "Dan Allah ka barta gwamma ta girka yau ɗinnan Malam ya ci ƙarni ya ishe shi ya canja shawara"

Yiri ri! Hafsa ta ɗanyi dariya gami da shewa aikam Gwaggo ki fara haɗa kayan ki dan cewa zai bai sanki ba sabida daɗin girki na" ta faɗa tana shafawa kifin lemon tsamin da ta yanka, ya yin da takaici ya ishi Zahraddeen tunanin asarar kuɗin kifin sa kawai yake ji yake tam kar yaje ya make Halima wadda taƙi zuwa ta amshi kifin hannun Hafsa.

Kiran sallar la'asar da aka yi ya sa shi fita bayan ya yi alwala, tare suka shigo da uncle Mansur yaya ne ga Zahraddeen shi yake bin Umman su Hafsa tuni ya yi aure sai dai baya kwana uku bai zo gidan ba.

Tun daga zaure uncle Mansur ya ce a'ah yau girkin ‘yan gayu ake haka a gidan kamshin da ya daki hancin su ya sa ya faɗi, Hafsa da ke juya miya ta saki murmushi, ai yau girkin nan ko ta fada tare da ɗan yin karamar kwafa.

Gwaggo ce ta ce ai dai abari aci tukunna ba ƙamshin ba ɗan ɗanon suks sa dariya, hira suke sosai kafin Uncle Mansur ya tashi zai tafi dakyar Hafsa ta roƙe shi ya ce zaije ya dawo ya ci.

Kamar yadda al'adar gidan take tabarma suka baje a madai daicin tsakar gidan can gefen taga fitilar ‘yar sola irin wadda yara ke haɗawa suna siyarwa ce ta haske tsakar gidan ya yin da Hafsa ta ɗauko food flasks ɗin da ta juye abincin ta ajiye gaban Gwaggo.

Kallon ta Gwaggon ta yi "mai zan da shi?" Ta tambaya

Murmushi Hafsa ta yi "zubawa"

Halima ta kalla " ki aje wannan karatun kizo ki zuba, dan kin yi sa'a yau an ɗauke miki girkin shi ne wato komai sai dai ayi?"

"Anma Gwaggo nida ba ni na yi aikin ba ai ban san kan sa ba"

Zahraddeen ne cikin kufula ya ce "zaki zuba ko sai na make ki?"

Tana ƙunƙuni tana zubawa ta miƙawa kowa, tun da aka miƙawa Zahraddeen Hafsa ke kallon sa so take ta ji mai zaice, sam bai kula da yadda take kallon sa ba, ya nutsu yana cin abincin sosai ya masa daɗi bai ta ɓa tunanin yarinyar ta iya girka ba bare ts sarrafa kifi ya zama ba ƙarni.

Ganin bazai magana ba ta ce "Uncle baka ce komai ba?

Tsotse ƙayar hannun sa ya yi kafin ya ce " eh to abinci dai gashi nan kamar dusa dusa"

Dariya tasa "ai da dusar ne da farantin nan naka bai zama ba komai kai ba"

Kallon farantin ya yi sai kuma ya sa dariya dan baima san ya cinye ba, Malam ne ya ce ai wannan abincin ko a otel albarka"

Gwaggo da take suɗe hannu ne ta ce "a'ah dai Malam kawai kana tsoron tane" suka sa dariya duka.

Rubutawa

Aeshakhabir

Fadimafayau

Soyayya
Credit: LuckyTD

Post a Comment

0 Comments