Ta yaya karatun littattafan ƙagaggun labarai zai inganta zamantakewar al’umma?
DAGA
BASHAR ABDULLAHI
1.0 GABATARWA
Al’adun al’umma su ne hanyarta da take gudanar da rayuwa a kai. Adabin al’umma kuma shi ke bayyana yadda al’ummar take gudanar da rayuwar. Adabi shi ne hoton rayuwar al’umma. Zamantakewa kuma abu da ya shafi al’adun al’umma. Kuma ya fi ta’allaƙa ne a kan zaman tare, kyautatawa, maƙwabtaka, da sauransu. Wannan jinga ta duba yadda karatun ƙagaggun labarai suke inganta zamantakewar al’umma. Kafin wannan lokaci Hausawa suna amfani da tatsuniyoyi wajen ilimantar da yaransu. Tsofaffi ne ke shirya labarai domin saita tunanin yara daidai da al’adunsu da abin bautar su, da tsarin zamantakewarsu. Da zamani ya zo da hanyar karatu da rubutu kuma wasu masana kamar su Dr. R. M. East da suka yi ƙoƙarin sanya gasa ta ƙagaggun labarai. Wannan gasa ta samar da littattafan karatu da dama, wanda har a yanzu akwai littattafai da ake rubutawa daban-daban. Wasu a rubuta su don jarunta, wasu don faɗakarwa, wasu don nishaɗi, wasu kuma don tsare gaskiya, wasu don zamantakewa, wasu don soyayya da dai makamantan su.
1.1 ƘAGAGGUN
LABARAI
Sanin jama’a ne cewa wasu masana sun yi
tsokaci a kan ƙagaggun labarai
na zube daga cikinsu akwai:
Ahmad Magaji (1982) cewa ya yi, “Zube labari
ne da mutum ya shirya da ka, sannan ya rattaba a zube”
Shi kuma Isah Mukhtar (2002), yana cewa, “Zube
wani irin zance ne wanda aka faɗarsa da baka ko kuma a rubuce, wanda yake bayyana yiwuwar wani al’amari,
wanda zai iya yiwuwa a zahiri, amma bai faru ba ko kuma ba zai taɓa faruwa ba. Irin waɗannan abubuwa ba dole ne a ce sun
faru ba, amma duk da haka sukan sa ɗan Adam ya yi tunanin ya ƙirƙiro waɗansu
halaye masu kyau ko akasin haka.
Wani dalili da ke sa ɗan Adam ya ƙirƙiro wa kansa labarai su ne, ƙoƙarin fito da wasu abubuwa musamman waɗanda suka shige masa duhu. Misali
makeken ruwa kamar kogi, ko rana da wata da taurari, ko waɗansu bishiyoyi masu ban al’ajabi da ban mamaki. Akwai waɗannan abubuwan daban-daban da suke
fitowa a cikin labarai wani lokaci su ne ke zama tuballan gina labarin.
Ire-iren rubutattun labarai na Hausa kan ginu
ne ta hanyoyi daban-daban misali.
- Ana iya samun labaran baka a tattara su a rubuta su.
- Ana kuma samun wasu labarai na wata ƙabila a fassara su a rubuta su.
- Ana iya yin tsokaci dangane da halin da wata al’umma
ta shiga na rayuwa ta zahiri sai a rubuta shi a matsayin labari.
A ɓangaren jigoginsu
kuwa ya ce, ƙagaggun rubutattun labaran Hausa, yawanci adabin Larabci
da na Turanci ya yi tasiri ƙwarai gare su.
Hausawa musamman marubuta na farko sun kwaikwayi rubuce-rubucen adabin
Larabawa da na Turawa suka haɗa su da nasu. Don haka jigon ƙagaggun
rubutattun labaran Hausa, bisa jimla za mu iya cewa sun ƙunshi muhimman abubuwa guda uku.
·
Adabin gargajiya na Hausa
·
Adabin Larabawa da tasirin addinin musulunci
·
Adabin Turawa da na addinin Kirista
Bisa ga
waɗannan bayanai za
mu iya cewa, lallai ne waɗannan
littattafan cike suke da tasirin zamantakewar Hausawa a cikinsu kuma waɗancan dalilai su ne suke ba ɗan Adam damar ƙirƙirar labari.
2.1 ZAMANTAKEWA A LITTAFIN SODANGI
Marubucin
wannan littafi ya yi ƙoƙarin fito da zamantakewa a wannan littafi tun a farkon
littafin, a kashi na ɗaya kuma
fitowa da ɗaya. A
shafi na sha uku (13) a kofar gidan malam Ɗanjuma, inda mai shela yake gabatarawa ga dai abin da yake cewa:
“masu iya Magana
ne cewa wanda jiya bay au ba, wanda yasan darajar goro shi, yak e adana shi a
algarara, har ma ya dinga yayyafa masa ruwa. A yau dai ba abune boyayye ba irin
mawuyacin halin da guguwar zaman ta jefa zumunta musamman a rsakanin makwabta,
ko irin na mai hakan rijiya ya shafi rayuwar arewa rin tad a ?
Haka kuma
zamantakewa a littafin ta ƙara fitowa a
lokacin da su malam Adamu suka sauri a kawo abinci don su ci su je duba mara
lafiya, shi ma zumunci ne ga dai abin da malam Umar ɗin yake cewa.
“A’a maza shiga ka fito mana da shi ko ma yi sauri mu je
gidan malam Iro dubiya (Hafizu na shiga gida) in ce dai an taso daga makarantar
boko, ga dai yadda take cewa:”kwarai! (jinkiri) kai da ka ke wannan batu malam
Adamu in ban da makarantar bokon da ake yi ai mu ba mu kai shekarunsa na
iyayenmu suka yi mana auren ari. (ya jawo kwanon abincin malam Adamu) Allah dai
ya saka wa Malam Iro domin ilimin zamani da ya sanya ‘yayanmu”
Imam ya
ci gaba da bayyana zumunta wadda ita ce ginshiƙin zamantakewa a fitowa ta uku shafi na ashirin da huɗu (24) inda Inna Shekara take ba Hafizu saƙo zuwa ga gyatumarsa ga abun da take cewa:
“Don Allah in ka je gida, ka fada mata cewa gobe zan zo
ta raka ni barkar ‘yar aminiyata Hajiya Mairo da ta haihu shekaranjiya. Kar fa
ka manta (ya amsa) sai da safe. Allah Ya kai mu”
Idan mu
ka lura da maganar Inna Shekara, zamu ga cewa zumuncin da ke tsakaninta da
Hajiya Mairo ya wuce ƙawance ya zama
zumunta kuma ita kanta barka da za su je zumunci ne.
2.2 ZAMANTAKEWA A LITTAFIN ILLAR GATA
NA AMINA ABDULLAHI SHARAƊA
Wannan
littafi ne da aka gina shi a kan zamantakewa, ko da yake dukkan abin da yake
cikin wannan littafin akwai tsura. Amma dai dukkan abin da littafain yake ɗauke da shi rayuwa ce ta aure
tsakanin Ummi da Abdulhakim. Dukkansu suna ƙaunar juna kuma sun yi aure amma ba mai son a ce shi ya fara son wani. Wani
hanzari ba gudu ba, duk suna kula juna kuma suna tsare haƙƙin aure gudun kar wani ya ji ba a yi masa daidai ba. Akwai kuma tsura da
shagwaɓa wanda ita matar
take yi sakamakon ta fito a gidan masu kuɗi. Zamantakewa a wannan littafi ta bayyana inda suka fita sayayya a babban
shagon sayar da kaya misali:
“Ummi ta ci gaye ta saka leshi mai ruwan tsanwa, shi kuma
hakin yana saye da kaftani fari ya saka hula mai ruwan tsanwa. Suna fita mota
sai wasu mata suka fara kallonsa suna cewa “kai wannan ya haɗu, amma kuma ba su dace da wannan
ba. Da zan samu wannan a matsayin miji da babu wadda ta fi ni. Kin ga fa wannan
tana biye da shi zalan-zalan kamar dai baƙauya. Nan
take Ummi ta juyo ta kai mata naushi domin ta ji zafin abin da ta ce”.
Hakim ya juyo ya ɓamɓare Ummi da ƙyar, ya ce “me ya haɗa ku ne?” “zagina ta yi wai har da cewa tana sonka.” Sikiriti da
suke a wajen suka taso da yake shi Hakim dama soja ne sai ya shiga lamarin ya
kashe wannan wutar. Bayan koma gida sai ya shiga yi wa Ummi faɗa cewa daga yau ba zai ƙara fita da ita ba. Ita kuma sai ta ce, “Ka yi haƙuri sharrin shaiɗan ne.” Ya ce to “ke da ba
kya so na ai ba kya hana wata ta so ni ba.” “Ta ce ai
ban hana ta so ka ba, amma meye na zagi na?” Nan ko ba don zaginta ta yi faɗa ba sai saboda wata ta ce tana son
mijinta. Ummi dai tsananin kishin mijinta take yi....
wannan ya nuna zamantakewa aure da ke tsakanin Ummi da Hakim. Wadda kuma
akwai soyayya a tsakani tare da kishinsa da take yi.
SAKAMAKON BINCIKE
A wannan
jinga an gano cewa, ana samun zamantakewa a cikin littattafan ƙagaggun labarai na Hausa. Kuma su marubutan sukan yi
amfani da zamantakewa irin tasu a yayin isar da saƙonsu a cikin littattafana. Marubuci kan iya yin imani da abin da ya karanta
daga cikin littattafan, wannan kuma kan taimaka masa wajen gyara zamantakewarsa
ta yau da kullum. Manyan jigogin da suka gina zamantakewa kamar zumunci, aure,
maƙwabtaka, abotaka da sauransu, idan mai karatu ya lizimci
littattafan da suka yi tsokaci a kan su ya kuma yi imani da abin da ya karanta
wannan na taimaka masa wajen ingata zamantakewarsa da abokan zama.
3.0 KAMMALAWA
Zamantakewa
al’ada ce wadda ta ƙunshi zaman tare
da zumunci da abokantaka da makamantansu. Karatun littattafai kuma yana
taimakawa wajen inganta zamantakewar musamman idan mai karatu ya yi imani da
abin da ya karanta daga litattafan. Akasari masu karatun sukan ɗauki halaye da ɗabi’u na wani
jarumi da yake a cikin littafi. Idan suka saka haƙuri kuma kamar yadda jarumin littafin ya yi, to wannan yana kai su ga
nasara a cikin zamantakewa da abokan zama.
Manazarta
Ibrahim Y.Y (2002) Tarihin Rubuce-Rubuce A Cikin Hausa.
NNPC Zariya.
Imam, K. (2015) Sodangi Wasan
Kwaikwayo. Gidan Dabino Published Kano state Nigeria.
Malumfashi I. (2009). Adabin Abubakar Imam Garkuwa Media
Services, Ltd, Sokoto.
MuKhtar I (2002), Jagoran Nazarin Ƙagaggun Labari, (Tsari Na Biyu), A.J Publishes
Umar B.D (2010) “Matsayin Karin
Magana A Cikin Ƙagaggun Labarin Hausa,
Na
Gasar Farko (1933). Kundin Digirin
Na [aya, Sashen Harsunan Nijeriya, Jama’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Umar J.T. da Wani (1933), Jiki Magayi, NNPC Zariya.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.