𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mijine yasaki matarsa tana shayarda yaron, data
yayeshi sai babansa ya ce tabashi ɗansa,
ita kuma tace musulunci ya ce uwa keda hakkin rike ɗanta natsawon shekara bakwai, inason karin
bayani dangane da hakan.?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد لله.
Abun da malamai suka haɗu akansa shi ne uwa ita ce take da hakkin
rainon yaro matukar baikai shekarun tamyiziba (shekara bakwai zuwa goma) saboda
yaro acikin waɗannan
shekaru yana da bukatar jinkai da rahma da tausayi da wani nau'i na kulawa
wanda uwace zata iya yimasa uba ba zai iyaba.
Saidai wannan hakki yana faɗuwa a kan mace dazarar tayi aure, domin
hidimar yaron zata shagaltar da ita daka yiwa mijinta hidima, za a samu cinkaro
wajan maslahar yaron datake raino da maslahar mjinta, ibnu munzir yaruwaito
ijma'i a kan faɗuwar
hakkin kulada yaro ga mace idan tai aure, Duba Alkafi Na ibnu Abdul barri (
1/296) da Mugny Na ibnu qudama (8/ 194)
Hadisin Abdullahi bin Amru Allah yakara musu yarda
yana nuni dahakan, wata mata tace ya manzan Allah sallallahu Alaihi
wasallam wannan ɗan nawa cikinane Abuncinsa, nono nane Abun
shansa, dakina shi ne inda yake kai komo acikinsa, Babansa yasakeni kuma yazo
yanaso yakwaceshi daka wajena Sai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce da
ita, ( Kece kika can-canti kiriqe ɗanki
matukar bakiyi Aureba) Ahmad yaruwaitoshi ( 6707) da Abu dauda ( 2276) Albani
ya ingantashi acikin Sahihu Abu dauda, Ibnu kaseer ya ingantashi acikin
Irshadul faqeeh (2/250)
Abu Nagaba shi ne ciyarda yaro wajibine a kan uba
koda sun rabu da uwarsa, Mahaifiyar yaron mai wadatace ko talakace ubansa keda
hakkin ciyarda shi.
Idan Uwa tana shayarda da ɗanta bayan sun rabu da babansa zata nemi
yabiyata abun da take kashewa yaron.
Ciyarda yaro kuma yahaɗa wajan kwanciya da Abun kwanciyar da
tufafi da magani da subulun wanka da wanki, da kuɗin makaranta, da duk Abun da datake bukata
wajan kulada yaron, taimasa lissafi dakyautatawa takiyaye hakkin mijin wajan
bayyana masa abun da take bukata wajan kulawa dayaronsu.
Saboda fadin Allah madaukakin Sarki:
ﻟِﻴُﻨْﻔِﻖْ ﺫُﻭﺳَﻌَﺔٍ ﻣِﻦْ ﺳَﻌَﺘِﻪِ ﻭَﻣَﻦْ ﻗُﺪِﺭَ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﺭِﺯْﻗُﻪُ ﻓَﻠْﻴُﻨْﻔِﻖْ ﻣِﻤَّﺎ ﺁﺗَﺎﻩُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻟَﺎ ﻳُﻜَﻠِّﻒُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻧَﻔْﺴًﺎ ﺇِﻟَّﺎ ﻣَﺎ ﺁﺗَﺎﻫَﺎ ﺳَﻴَﺠْﻌَﻞُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺑَﻌْﺪَ ﻋُﺴْﺮٍ ﻳُﺴْﺮًﺍ ٧
Mai wadata yaciyar gwar-gwadon wadatarsa, wanda
aka tsuke masa arzikinsa yaciyar daka iya Abun da Allah yabashi, Allah baya
dorawa rai wani abu sai wanda zata iya, Tabbas bayan kunci Allah yana kawo
sauqi. (Suratul Talaq : 7)
Idan uban yaro mawadacine ciyarwa zata kasance
gwar-gwadon wadatarsa, talaka ko wanda yake tsaka tsakiya gwar-gwadon halin
arzikinsa zai ciyar, idan iyayen yaron sukai yarjejeniya a kan wani abu
nadukiya cewa duk sati zai bata kaza naciyarwa yaron wannan al'amari yana
wajansu, amma idan suna jayayya alkali shi ne zai raba wannan rigima.
Ya halatta mace tanemi mijinta daya saketa yabata
ladan shayarda yaron datake kula da tarbiyyarsa a ittifaqin malamai, kamar
yanda ibnu qudama ya bayyana cikin Almguny ( 11/430) da (11/431) da shaikul
Islam ibnu taimiyyah acikin fatawa Kubrah ( 3/347)
Idan uba yaki ciyarda yaron ya aikata saɓo hakkinsa na rainon yaro ya faɗi akansa.
Kamar yanda yazo acikin Rauzatul dhalibeen ( 9/98)
da Rauzul murbi'i ( 3/251) da Almugny (8/190) da Zadul Ma'ããd na Ibnul qayyeem
( 5/424) da fatawa Sa'adiyyah na Shaeik Assa'ady shafi na (535)
Abun nufi dai shi ne idan uba yaki ciyarda ɗansa hakkinsa nakulada yaro ya faɗi, koda yaki ciyarda ɗan ne danya cutar da uwar ne, Wannan yana
nuna shi bawanda za a amincewa bane, a kan maslahar 'ya'yansa, uwar yaron zata
nemi hakkin ciyarda 'ya'yanta awajansa akotu gurin alkali.
Saboda haka babu kuskure cikin zancenki kece kike
da hakkin kulada da ɗanki
matukar bakiyi aureba, karin bayani kuma shi ne za ki iya neman hakkin ciyarda
yaron awajansa koda akotune gurin alkali.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/CfDLSdXaGD00Wpxdfy2ofp
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.