𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Malam, wai da gaske ne ba a yin
sallah a gaban liman?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.
Malamai sun saɓa wa juna a kan wannan. Amma maganar da ta
fi daidai kamar yadda Shaikhul Islaam Ibn Taimiyah (Rahimahul Laah) ya kawo ita
ce: Sallah a gaban liman tana inganta ne kaɗai idan akwai uzuri. Ma’ana: Idan
masallaci ya cika maƙil da jama’a, shi kuma bai samu wurin da zai tsaya domin yin sallar Jumma’a ko
jana’iza ba sai dai a gaban liman, a nan sai a ce: Yin sallarsa a gaban liman
ya fi ya bar yin sallar gaba-ɗaya.
Wannan ita ce maganar waɗansu daga cikin malamai, kuma ita ce
magana ɗaya
daga cikin mazhabar Ahmad da waninsa daga cikin limamai. Ita ce kuma maganar da
ta fi adalci kuma wacce ta fi rinjaye. (Majmuu’atul Fataawa:23/221).
***
HUKUNCIN YIN SALLAH A GABAN LIMAN
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam mene ne hukuncin yin sallah a gaban liman a wajEn masallaci?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuh.
Asali Sallar jam'i shi ne Mamu ya kasance A bayan liman, Malamai Sun yi Saɓani akan sallar wanda yayita Agaban liman, Mafi ingancin Zancen shi ne ta Inganta idan Akwai uzuri.
Shaikul Islam Ibnu Taimiyyah Rahimahullahu ya ce: Sallah agaban liman akwai zantuka guda uku na Malamai akai..
1. Ta inganta kai Tsaye, duk da sun ce Makaruhi ne, Shi ne zance shaharre a Mazhabar Malikiyya.
2. ba ta Ingantaba, Kamar Mazhabar Hanafiyyah, da Shafi'iyyah, da Ahmad.
3. Ta inganta idan akwai Uzuri, Kamar babu sauran gurin da mutum zai yi Sallar sai gaban liman ɗin, Sai ya zama yin Sallar agaban Liman shi ne ya fi Alkhairi akan ƙin yin Sallar a lokacin.
Wannan shi ne zancen wasu malamai, shi ne Mazhabar Imamu Ahmad da waninsa, shi ne mafi Adalcin zance shi ne ya fi hujjah Mai ƙwari, domin barin shiga gaban liman Maƙurarsa shi ne wajabcin barin hakan, su kuma wajibai suna gushewa idan aka samu uzuri, ko da wajibi ne a asalin sallah, da rasa jam'i gwara rasa wajibi, Saboda haka wajabcin Abin da mutum yakasa yana faduwa a gareshi, na Tsayuwar Sallah, da karatu, da tufafi, da Tsarki, da sauransu. Fatawa Kubra (2 / 331 - 333).
Saboda haka Bai halatta yin Sallah Agaban liman ba, idan Mutum ya yi sallah agaban liman sai ya sake sallah, sai dai idan Akwai uzuri Masallaci babu sauran filin dazaka iya tsaiwa damansa ko hagu ɗinsa. Kamar Yanda Ibnu Usaimeen Ya faɗa a cikin Maj- Mu'u fatawa dinsa (13 / 44).
WALLAHU A'ALAMU.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.