Ticker

6/recent/ticker-posts

Ranar Hausa Ta Duniya, 2023 - Gudummawar Dr. Aliyu Tilde Bauchi

Bayanin da Prof. Bunza ya yi a BBC da safe yana kan hanya sosai. Muna gode Allah da yab ba mu Hausa.

Wata uku da suka wuce a wani dandali wasu sun yi ta sukar wannan ranar don wandanda suka kafa ta wai ba asalin Hausawa ba ne. Ina kira ga masu raya ranar da kar su yi kasa a gwiwa. A tarihin duniya, shi harshe in ya bunkasa ba sai dan asalinsa ke raya shi ba. Haka kuma tarihin harshen Hausa shi ma ya nuna. 

Ga kasidata ta bara don taya murna da harshen da ya dinke mu a wannan sashi na Afrika. 

Kafar Intanet Ɗin Da Za Ku Samu Dubbannin Rubuce-Rubuce Game Harshe Da Al'ada Da Adabin Hausawa

—————

HARSHEN HAUSA

1. A yau duniya ke bukin tuna Hausa

Muna gode Allah da yab ba mu Hausa.


2. A harshen bakake gaba dai ka duba

Na farko na biyu za ka kirga da Hausa.


3. Yawan yaduwa haka nan kama baki

Da saukin fadi babu yare ya Hausa.


4. Sa’annan da karbo kalaman wadansu 

Ya sanya a nasa su zamto na Hausa.


5. A gun Larabawa ya karbo kidaya 

Altinin, Laraba, Alhamis ka ji Hausa.


6. A gunmu Fulani ya karbo su Goggo

Da Kawu da Baffa da Yaya a Hausa.


7. Wajen Yoruba nan ya samo su keke

Da kwano, sule, har da sisi a Hausa.


8. A gun Ingilishi ya karbo su mota

Da canji, da tebur da layi a Hausa.


9. Mu gode wa harshen da yat tattaro mu

Ya maishe mu jinsi guda “Onye Hausa”.


10. Da Barno, Filato kaza Adamawa

Idan an gane mu a ce mana “Hausa”.


11. Idan an kira mu Bahaushe mu amsa

Da karfi mu ce musu tushenmu Hausa.


12. Idan dan’arewa kake kar ka musa

A Nijeriya ba ka gata ya Hausa.


13. Gama Hausa ta ba ka harshen kalami 

Da danginka duk masu zance da Hausa.


14. Siyasa, kusanci, zumunci da dina

Gaba daya mun tattare inda Hausa.


15. Fa Hausa zare ne na dinke mutane

Arewa gaba dai fa turkenmu Hausa.


16. Ga mai hankali kuwa ya zama tilas

Ya taso ya caffa ya girmama Hausa.


17. Ya koya ya koyar da harshen kasarmu

Ya ce wa diya: kun ga gatanku Hausa.


18. Ku koye shi haikan ku zam sarrafa shi

Rubutu da wake ku zam yi da Hausa.


19. Ku zurfafa ilmi ku nemo a nesa

Ku kawo ku yada cikin mu da Hausa.


20. Ta’ala Aliyu yana yin du’a’i

Ka karfafa dankon zumunci na Hausa.


21. Ka karo fahimta da so har da yarda

Tsakanin mazauna kasarmu ta Hausa.


22. Ka bunkasa ilmi kaza arzikinta

Talauci ya kaura mu wala a Hausa.


23. Masifar akida, kabila, ta’adda

Ka k’are, mu zauna amana a Hausa.


24. Ga duk wanda ke da’awar raba kanmu

Ka sa ya ji kunya, ka tsarshe mu Hausa.


25. Ka karo salati bisa Annabinmu

Ka sa mu cikin mabiyansa na Hausa.


Dr. Aliyu U. Tilde

Bauchi

26 Agusta 2022

Post a Comment

0 Comments