Ticker

6/recent/ticker-posts

Ƙayyade Haihuwa (Family Planning)

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As Salaamu Alaikum. Miji ne ba ya bai wa matarsa haƙƙinta na zamantakewa, kamar sakin fuska da hira da bayar da abinci da ɗinka sutura da sauran kayan masarufi irin yadda yake bai wa kishiyarta, wai dole sai ta amince da abin da yake so, wai sai ta yarda a riƙa yi mata allurar rage haihuwa! Meye hukuncin wannan a sharia?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh

[1] Da farko ya kamata duk mu san cewa: Haihuwa baiwa ce kuma kyauta ce daga Allaah Mabuwayin Sarki, yana bayar da ita ga wanda yake so, a sadda, da inda, kuma ta yadda yake so, kamar yadda ya faɗa a cikin Suratu Shuura:

لِلَّهِ مُلْكُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ يَخْلُقُ مَا يَشَآءُ ، يَهَبُ لِمَنْ يَشَآءُ إِنَاثًا وَيَهَبُ لِمَنْ يَشَآءُ الذُّكُورَ ، أَوْ يُزَوِّجُهُمْ ذُكْرَانًا وَإِنَاثًا ، وَيَجْعَلُ مَنْ يَشَآءُ عَقِيمًا ، إِنَّهُ عَلِيمٌ قَدِير

Mulkin sammai da ƙasa na Allaah ne kaɗai, yana halitta duk abin da ya ga dama, yana yin baiwar ’ya’ya mata ga wanda ya ga dama, kuma yana yin baiwar ’ya’ya maza ga wanda ya ga dama, ko kuma ya gauraya su maza da mata (ga wanda ya ga dama), kuma yana ƙyale wanda ya ga dama a matsayin bakarare, haƙiƙa shi mai ɗimbin sani ne, mai cikakken iko.

A yau kuwa muna ji da ganin yadda ma’aurata da yawa suke neman haihuwar maza da mata a haɗe, ko irin nau’in da bai ba su ba amma kuma ba su samu ba, kamar kuma yadda muka sha ji da ganin waɗanda suke ta ƙoƙari rani da damina, ba-dare ba-rana don samun ko da haihuwar sau ɗaya ma, amma dayake Mai Yin Baiwar bai bayar ba, dole suka yi haƙuri suka dangana. Sannan kuma a kullum mana ji da ganin yadda maaurata suke murna da farin ciki a duk lokacin da Mabuwayin Sarki Mai Yawan Baiwa ya albarkace su da samun haihuwa. Waɗannan abubuwa ne sanannu tabbatattu a cikin musulmi da kafirai da dukkan al’ummomin duniya.

[2] Ni’imomin da Ubangiji Ta’aala ya yi wa bayinsa a koyaushe suna da yawan gaske, kamar yadda ya faɗa a cikin Suratun Nahl:

وَإِنْ تَعُدُّوا نِعْمَةَ اللَّهِ لَا تُحْصُوهَا إِنَّ اللَّهَ لَغَفُورٌ رَحِيمٌ

Kuma in da za ku lissafe ni’imomin Allaah a gare ku, ba za ku iya ƙididdige su ba, lallai Allaah tabbas! Mai Yawan Gafara ne, Mai Yawan Rahama ne.

Sai dai kuma duk da hakan ba mu taɓa ko jin labarin wani mutum guda ɗaya mai hankali da tunani ba ya taɓa ƙyamatar ko da mafi ƙanƙantar baiwa guda daga cikin ɗimbin ni’imomin Ubangiji Ta’aala ba a gare shi. Babu wanda ya taɓa ƙyama ko jin haushi idan itatuwan mangwaro ko lemu ko ayaba a gonarsa suka fitar da yaya masu yawan da bai taɓa ganin irinsu ba. Haka kuma ba wanda ya taɓa nuna baƙin cikinsa ko ɓacin ransa a lokacin da shanunsa ko tumakinsa da awakinsa ko talo-talo ko agwagi da kajin da yake kiwo suka samu yawan albarkar ’ya’ya! Sannan kuma a iya saninmu da tarihin rayuwar al’ummomin duniya, ba a taɓa samun waɗansu mahankalta da suka nuna ƙyamatar yawan haihuwar ’ya’ya a cikin jama’arsu ba!

Sai a waɗannan ’yan shekarun na ƙarshen zamani ne da gaskiyar imani da sakankancewar mutane da Allaah ta yi kaɗan, tawakkalinsu ga Mahaliccinsu Ubangijin Halittu ya yi rauni, shi ne muke jin labarin yadda waɗansu shugabanni kamar na ƙasar Sin sun gwada kafa wa mutanensu dokar hana haihuwa bayan ɗa na farko! Amma tun kafin a yi nisa sai su da kansu suka fahimci mummunar ta’asa da ɓarnar da bin wannan dokar za ta jawo musu: Na yawaitan tsofaffi da ƙarancin yara matasa, da kuma yawaitan maza da ƙarancin mata a cikinsu! Don haka, nan da nan suka janye wannan shuumar doka, suka zauna lafiya!

To, me ya sa mu kuma a yau muke ta ƙoƙarin yin aiki da abin da waɗansu suka gwada suka ga rashin alfanunsa? Alhali kuma ya ci karo da koyarwar sahihin addininmu da kyawawan al’adunmu?!

[3] Mu musulmi mun riga mun yi imani cewa: Kowane ɗa arzikinsa a hannun Allaah Ta’aala ya ke, kamar yadda ya nuna a cikin Suratul An’aam:

وَلَا تَقْتُلُوا أَوْلَادَكُمْ مِنْ إِمْلَاقٍ نَحْنُ نَرْزُقُكُمْ وَإِيَّاهُم

Kuma kar ku kashe ’ya’yanku saboda talaucin da kuke ciki, mu muke azurta ku, da su kansu ’ya’yan.

Sannan kuma a cikin Suratul Israa’i, ya ce:

وَلَا تَقْتُلُوا أَوْلَادَكُمْ خَشْيَةَ إِمْلَاقٍ نَحْنُ نَرْزُقُهُمْ وَإِيَّاكُم

Kuma kar ku kashe ’ya’yanku don tsoron aukuwar talauci, mu muke azurta su ’ya’yan, da ku kanku.

Waɗannan ayoyi, in ji Malamai sun nuna haramcin kashe ’ya’ya saboda talaucin da iyaye suke fama da shi a yanzu, ko kuma don tsoron aukuwar talaucin a nan gaba idan suka ƙyale yayan a raye! Dayake a ayar farko iyayen suna cikin talaucin ne sai ya fara lallashinsu da ambaton arzikinsu da farko kafin na yayansu. Amma a aya ta biyu dayake yayan ne suke ji wa tsoron talaucin sai ya fara ambaton arzikin yayan kafin na iyayen!

A taƙaice dai, babu wata hujja ko wani dalili na ƙyamar haihuwa ko ɗaukar matakan daƙile cigaba da halittar abin da ke cikin ciki tun kafin bayyanarsa a duniya. Allaahumma, sai dai in an tabbatar ko ana kyautata zaton aukuwar wata matsananciyar wahala mai kaiwa, wataƙila ga salwantan rayuwar mai haihuwar ko kuma abin da za a haifa, amma ba talauci ba! Domin a cikin Hadisin Sahabi Abdullah Bn Masud wanda Al-Bukhaariy da Muslim suka fitar Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya tabbatar mana da cewa, tun a lokacin da jaririn yake cikin cikin mahaifiyarsa ne aka gama rubuta arziƙinsa:

ثُمَّ يَبْعَثُ اللَّهُ مَلَكًا فَيُؤْمَرُ بِأَرْبَعِ كَلِمَاتٍ وَيُقَالُ لَهُ اكْتُبْ عَمَلَهُ وَرِزْقَهُ وَأَجَلَهُ وَشَقِيٌّ أَوْ سَعَيدٌ

Sai kuma Allaah ya aika masa da Mala’ika, sai kuma ya umurni da abubuwa huɗu, ya ce da shi: Rubuta irin aikinsa, da arziƙinsa, da ajalinsa, da kuma ko ɗan Wuta ne ko kuma ɗan Aljannah.

Don haka, babu wani dalilin jin tsoron talauci ga jaririn da aka haifa, ko wanda za a haifa a wurin duk wanda ya yi cikakken imani da ƙudura da ikon Allaah Ubangijin Halittu Mabuwayi Mai Girma.

[4] Amma maganar wani cewa, a yau rayuwar ce ta yi tsananin tsada sosai, ta yadda da wahala mutum yake iya ɗaukar nauyin karatun islamiyya da na bokon ’ya’yansa. Ga kuma kuɗaɗen abinci da magani da sutura da na sauran buƙatun yau da kullum!

A gaskiya waɗannan duk abubuwa ne masu sauƙi, kuma ba komai ba ne idan muka tuna abin da muka ambata a baya na yalwa da ƙarfi arziƙin da ke wurin Allaah Subhaanahu Wa Taaala . Amma rashin cikakken dogaro da rashin kyautatawa wurin neman halal ne kawai matsalar. Don haka, maganin abin kawai shi ne: Duk mu samu cikakke kuma kammalallen dogaro da biyayya ga Allaah, sannan mu tashi mu yi da gaske kuma mu kyautata wurin neman halal don amfanin kanmu da zuriyarmu. A cikin Hadisin da Ibn Maajah ya fitar da shi kuma As-Shaikh Al-Albaniy ya sahhaha shi daga riwayar Umar Bn Al-Khattaab, Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

لَوْ أَنَّكُمْ تَوَكَّلْتُمْ عَلَى اللهِ حَقَّ تَوَكُّلِهِ ، لَرَزَقَكُمْ كَمَا يَرْزُقُ الطَّيْرَ ، تَغْدُو خِمَاصًا ، وَتَرُوحُ بِطَانًا

In da za ku dogara ga Allaah haƙiƙanin dogaronsa, to da kuwa ya azurta ku irin yadda yake azurta tsuntsaye: Suna fita da safe a cikin yunwa, kuma su komo da yamma cikin ƙoshi.

Idan har mun yarda yana da ikon warware wannan, ta yaya sauran matsalolin za su gagare shi warwarewa, alhali shi ne Ubangijin Halittu, Mai Rahama Mai Jin Ƙai?!

Daga bayan wannan sai kuma haɗin-kai da taimakon juna. Mu zama tsintsiya ɗaya, kuma Hannun dama da na hagu su riƙa cuccuɗawa suna wanke junansu cikin tausayi da ƙaunar juna.

[5] Kowa ya yi haƙuri kuma ya yi ƙoƙarin ɗaukar nauyin abin da Allaah ya azurta shi na ’ya’ya shi da kansa, kar ya ɗora wa kowa daga cikin dangi da ’yan uwa da abokai ko malaman tsangaya wannan nauyin. Kar kuma ya sake su sakaka suna ta gararamba a tituna da layuka, ba tare da yana ilmantar da su, suna zuwa makaranta inda ake koya musu nagartaccen ilimi da tsabta da sauran kyawawan ɗabi’u da halaye ba.

Idan kuwa ya tabbatar ba zai iya ɗaukar nauyin iyalan da Allaah ya ba shi ba, saboda tsufa ko rashin lafiya da tsananin ƙuncin rayuwa ko dai sauran larurori makamantansu, to a nan ne ya halatta ya ɗauki matakan da suka dace kuma ba su yi hannun-riga da koyarwar addini ba wurin bayar da tazarar haihuwar: Kamar ya daina saduwar kwata-kwata a tsawon lokacin da mace take shayarwa, watau shekaru biyu daidai ga wanda ke son kammala shayarwar, ko kuma ya riƙa yi wa matar azalu da yardarta da amincewarta.

Domin ya tabbata a cikin hadisin Jaabir (Radiyal Laahu Anhumaa) wanda Al-Imaam Muslim ya riwaito: Wani mutum ya taɓa zuwa wurin Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce: Ina da baiwa (kuyanga), ita ce mai yi mana hidima kuma mai yi mana ban-ruwa a gonarmu, ni kuma ina kwanciya da ita, amma kuma ina tsoron kar ta samu ciki? Sai Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

اعْزِلْ عَنْهَا إِنْ شِئْتَ ، فَإِنَّهُ سَيَأْتِيهَا مَا قُدِّرَ لَهَا

Ka yi mata azalu in ka ga dama, amma fa abin da aka ƙaddara mata zai zo mata.

Abin nufi da azalu shi ne: Ya zubar da maniyyinsa a waje maimakon a cikin mahaifarta.

Amma fa wannan ba ya hana aukuwar duk irin abin da Allaah Ta’aala ya ƙaddara halitta shi ga wannan matar.

(Domin ai mun sha jin labarin waɗanda suke ɗaukar matakan bayar da tazarar haihuwar ta bin sababbin hanyoyin da ilimin likitancin zamani ya kawo sau-da-ƙafa, amma daga ƙarshe sai kuma a gwammace da ma ba a ɗauki matakan ba! E, mana! To mace ce ta dakatar da haihuwa na tsawon shekaru biyar, amma lokacin da ta zo haihuwar farko bayan ta gama yin tazarar sai Allaah da ikonsa ya ba ta ’yan uku!!)

Yin watsi da waɗannan hanyoyin da ba su da wata matsala, da komawa ga ɗaukar matakan da ba irin wannan ba, kamar na cushe-cushen wasu robobi a cikin mahaifa, ko na zarƙama wa mata allurai, ko ɗura musu ƙwayoyi iri-iri, waɗanda su kansu ƙwararrun likitoci sun tabbatar cewa suna janyo waɗansu matsaloli masu hatsari ga lafiyar mace da rayuwarta, bai dace ba. Saboda Hadisin Ubaadah Bn As-Saamit da Ibn Abbaas wanda Ibn Maajah ya riwaito cewa, Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

لاَ ضَرَرَ وَلاَ ضِرَار

Babu fara cuta kuma babu rama cuta

Ma’ana: Bai halatta ba, kuma ma haram ne a fili ƙarara, musulmi ya fara buɗe ƙofar cutarwa ga ɗan’uwansa musulmi, ko kuma musulmi su riƙa cutar junansu. Allaah ya kiyaye, Allaah ya tsare mu.

[6] Su kansu ƙungiyoyin da suka yarda da bin wannan hanyar ta dakatarwa ko ƙayyadewa ko bayar da tazarar haihuwa a cikin jamaa sun sanya mata ƙaida ko sharaɗin cewa: Sai an samu amincewar ma’aurata. Watau, sai bakin ma’aurata ya zo ɗaya a kan amincewa da bin wannan hanyar. Amma a samu wasu mazaje, kamar yadda ya zo a cikin wannan tambayar, suna fitina da tilasta wa matan aurensu kan haka, tare da yi musu barazanar hana su haƙƙoƙinsu na kyautata zamantakewa, kamar ta hana su abinci da tufafi da magani da sakin-fuska da rabon-kwana da sauransu, wannan kam cuta ce kuma zalunci ne a fili ƙarara, wanda kuma Allaah Maɗaukaki zai yi sakayya a kansa wataƙila ma tun daga nan duniya kafin zuwa Lahira!

A cikin Al-Musnad, Ahmad ya riwaito Hadisin da Shu’aib Al-Arnaa’uut (Rahimahul Laah) ya sahhaha shi saboda yawan hanyoyinsa, daga Abu-Hurairah daga Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

وَدَعْوَةُ الْمَظْلُومِ تُحْمَلُ عَلَى الْغَمَامِ ، وَتُفْتَحُ لَهَا أَبْوَابُ السَّمَاءِ ، وَيَقُولُ الرَّبُّ عَزَّ وَجَلَّ : وَعِزَّتِي لَأَنْصُرَنَّكَ وَلَوْ بَعْدَ حِينٍ

Kuma addu’ar wanda aka zalunce shi ana ɗaukarta a kan giragizai, kuma ana buɗe mata ƙofofin sama, kuma Ubangiji Mabuwayi Mai Girma yana cewa: Na rantse da Buwayata, lallai zan taimake ka, ko da nan gaba ne!

Sannan wani abin da yawancin mutanenmu ba su cika mayar da hankali gare shi ba game da wannan matsalar shi ne: Me ya sa ba a damu da yaɗa wannan kiraye-kirayen a cikin maƙiyanmu da abokan hamayyanmu ba? Me ya sa ba ma jin hakan a cikin abokan zamanmu da cikin maƙwabtanmu na kusa ko na-nesa? Me ya sa muke jin a wasu wuraren da ƙasashe ma har kyauta ake bayarwa ga iyalan da suka haihu? Don me su suke ƙoƙarin yawaita jamaarsu mu kuma muna ƙoƙarin rage namu?!

Wataƙila wani ya ce, ai tattalin arziƙinmu ne bai yi ƙarfi irin na su ba!

Haba jama’a! Wane irin arziƙi ne a duniya Allaah bai yi mana ba? Ko kuwa dai kuna nufin: Yawan mahandama da masu baba-kere da masu ruf-da-ciki da almubazzarai da maɓarnata da marasa tunani da hangen nesa, kuma marasa kishin ƙasa da kishin jamaarta ne da ba su da shi, waɗanda mu kuma suka yi mana katutu?! In ba haka ba, ai tuni Allaah Ta’aala ya ce:

وَمَا مِنْ دَابَّةٍ فِي الْأَرْضِ إِلَّا عَلَى اللَّهِ رِزْقُهَا

Kuma babu wata dabba a doron ƙasa face arziƙinta yana hanun Allaah ne.

Sannan ita kanta haihuwar ma ba arziƙi ba ce?!

(Akwai gidajen da Allaah ya ba su arzikin ’ya’ya kuma aka yi shaidar cewa talauci ya yi musu katutu, amma daga baya sai ga shi Allaah Mayalwacin Sarki ya azurta su har labarinsu ya yaɗu a ko’ina cewa sun koma gidaje na mawadata!)

Sannan kuma ban da wannan, saboda sakaci da halin ko-oho da muke da shi, a yau akwai hanyoyi da yawa da ake bi domin illata mu da daƙile yawanmu da ƙara raunana mu, kamar ta: Yaɗa muggan makamai a cikin matasanmu, da yawaita shaye-shayen ƙwayoyi da kayan maye masu daskarar da ƙwaƙwalwa a cikinsu, da ƙirƙiran yaƙe-yaƙen babu-gaira babu-dalili a cikin jamaarmu, ga kuma gurɓata kayan abinci da ruwan sha, da lalata tsire-tsire da zurriya, da kiraye-kirayen hana auren-wuri da ƙayyade shekarun aure a tsakanin samari da ’yan mata, da halatta zubar da ciki, da shan magungunan hana ɗaukar cikin, da yi wa yara allurorin da suke cutar da jiki da sunan rigakafi da sauransu. To, don me za mu taimaka wa maƙiyanmu har su samu ikon cin nasara a kanmu?!

[7] A ƙarshe, kar wani miji ya yi tunanin cewa rashin amincewar matarsa ga ɗaukar wani matakin ragewa ko ƙayyadewa ko dakatar da haihuwa wai wannan ya ba shi damar ya danne mata haƙƙoƙinta, ko na abin da ta haifa ko abin da za ta haifa a shimfiɗarsa, kar ya yi tsammani wannan ya isa ya hana shi yi mata adalci a tsakaninta da sauran kishiyoyinta, ko kuma ya ɗauka hakan ba zunubi ko saɓo ba ne! Al-Imaam Abu-Daawud da Ibn Maajah sun riwaito Hadisin da Al-Imaam Al-Albaaniy ya sahhaha shi daga riwayar Abu-Hurairah cewa Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

 مَنْ كَانَتْ لَهُ امْرَأَتَانِ فَمَالَ إِلَى إِحْدَاهُمَا جَاءَ يَوْمَ الْقِيَامَةِ وَشِقُّهُ مَائِلٌ

Duk wanda yake da matan aure guda biyu sai ya karkata zuwa ga ɗayarsu, to zai zo a Ranar Ƙiyama da sashen jikinsa a shanye!

Sanannen abu ne cewa: Abin da ake nufi da karkata a nan ita ce: Dukkan karkata na fili ƙarara, ba ƙaramar karkata ta zuci ba wadda har Annabawa ma ba su da iko a kanta. Kuma wannan ita ce irin karkatar da Allaah ya hana, ya ce:

فَلَا تَمِيلُوا كُلَّ الْمَيْلِ فَتَذَرُوهَا كَالْمُعَلَّقَة

Kar ku karkata dukkan karkata, har ku bar ta kamar wata ratayayya

Wannan kaɗai ya isa wa’azi da gargaɗi ga dukkan mai imani a musulunci, in shã Allãh .

Allaah ya ƙara mana tabbata da kafewa a kan bin Alƙurani da Sunnah Sahihiya kamar yadda magabatanmu na ƙwarai suka fahimta.

WALLAHU A'ALAM

 Wa Sallal Laahu Alaa Nabiyyinaa Wa Aalihi Wa Sahbihi._

Sheikh Muhammad Abdullah Assalafiy

 

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments