Ticker

6/recent/ticker-posts

Matsayi Da Darajar Ubangida A Wakokin Baka Na Hausa

Takarda Wadda Aka Gabatar Domin Tunasarwa Da Ba Da Shawara Ga Makaɗan Baka Na Hausa A Shiryawa Da Tsara Matanonin Waƙoƙinsu Bisa Dacewa Tare Da Zaɓo Ingantattun Kalmomi Kafin Su Rera, Su Kuma Sadar Da Su. Lahadi, Mayu 07,2023/SHAWAL 17,1444

SA’IDU MUHAMMAD GUSAU,

SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA,

JAMI’AR BAYERO, KANO.

 

1.0          Gabatarwa

A wasu rubuce-rubucen da na aiwatar[1] na tattaɓa nazari a kan dabarun aiwatarwa da rerawa da sadarwar waƙoƙin baka na Hausa. Haka kuma na kalli yanayin harshen waƙar baka da furuci a Zubin waƙoƙin baka da kuma yadda Sarakuna na al’ummar Hausawa suka fara zama masu ɗaukar nauye-nauye na wasu makaɗan baka. An kuma duba wasu waƙoƙin makaɗan baka da suka waƙe wasu mabambantan Ubangida a matsayinsu na jagororin al’ummar Hausawa ko gwarzaye ko masu ilimi ko masu hikimomi ko masu fasahohi ko masana falsafofi. Har wa yau kuma Makaɗan baka bisa turbobinsu fitattu su ne waɗanda suke shirya waƙoƙinsu a kan kyawawan al’adun Hausawa da na addinin Musulunci.

Waƙoƙin baka na Hausa sun jima a tsakanin Hausawa waɗanda aka fara gudanar da su tun ran gini, ran zane. Waƙoƙi ne da suka danganci zamantakewar Hausawa har zuwa yau da suke ta bunƙasa, lokaci bayan lokaci.

Su waƙoƙin baka, waƙoƙi ne waɗanda ake shiryawa da aiwatarwa da rerawa da sadarwa da amo na murya a haɗe da amo na kiɗa. Hausawa sun soma wanzar da amo na kiɗa a waƙar baka ta amfani da wasu abubuwa da ba an yi su ne kawai domin a haɗa su da waƙar baka ba[2]. Daga nan kuma Hausawa suka sami fasaha da azanci na ƙirƙiro kaya na musamman domin a buga ko a kaɗa su, su ba da amo ko sauti na kiɗa, sannan a haɗa murya da amon su tayar da rauji na waƙar baka ta Hausa[3]. A hulɗoɗin Hausawa da baƙin al’ummu sun sami ƙari na wasu kayan kiɗa da ake ambata kayan kiɗa na baƙin al’ummu[4].

Kamar yadda aka soma yin bayani a baya, a zangon da Hausawa suka ɓullo da tsari na makaɗan baka ne aka fara shirya kayan kiɗa da za a iya haɗa amonsu ko sautinsu da furucin baki (murya) a samar da rauji wanda yake hawa ko sauka ko faɗuwa a madirar kalmomi na ƙarshen layuka ko saɗaru a ɗa ko ɗiya na zubin matanoni na waƙar baka Bahaushiya.

Ta fuskar haliyyar waƙoƙin baka na Hausa, makaɗan Hausa sukan shirya waƙoƙi masu turaku ko saƙonni manya game da hidimomin da Hausawa suke gudanarwa a zamantakewarsu a bisa doron ƙasa. Ciki kuwa har gami da halaye da nauye-nauye da suka ɗoru a wuyayen Sarakuna da sauran manyan rukunoni na masu Sarauta da shugabanci.

Idan aka yi la’akari da ire-iren waƙoƙin baka na Hausa za a iya rarraba su zuwa:

i)                Waƙoƙin makaɗa a Turke da Sarakuna (Turkakkun Makaɗan Sarauta): Makaɗan baka turkakku sukan jingina waƙoƙinsu kawai zuwa ga Sarakuna da sauran masu Sarautu. Daga cikinsu akwai Muhammadu Dodo Maitabshi, Sakkwato, Gwadabawa da Buda Ɗantanoma, Argungu da Ibrahim Narambaɗa, Tubali, Isa da Salihu Jankiɗi, Gusau, Sakkwato da Abubakar Akwara, Sabon Birni da Abdu Kurna, Maradun da Sa’idu Faru, Sakkwato da Sa’idu Maidaji Rambaɗawa, Sabon Birnin Gobir da Aliyu, Sarkin Kotson Kano[5] da sauransu da yawa.

ii)              Waƙoƙin Makaɗan Sarakuna a Sake: Su ne waƙoƙi waɗanda makaɗa suke yi wa kowane Sarki. Misalan makaɗa na wannan kaso su ne Aliyu Ɗandawo, Shuni, Argungu, Yawuri da ɗansa Sani Aliyu Ɗan’dawo Yawuri da Hussaini Sarkin Makaɗan Gusau da Makamantansu.

iii)            Waƙoƙin Makaɗan Sarakuna da Game-Gari: Su ne kamar Musa Ɗanƙwairo Maradun da Musa Ɗanba’u da Dr. Aminu Ladan Abubakar, Alan Waƙa, Sarkin Ɗiyan Gobir da Imamu Sunusi Ɗanƙwairon Katsina da ire-irensu.

iv)            Waƙoƙin Makaɗan Siyasa a Turke: Ire-iren Makaɗan siyasa a turke sun haɗa da Tijjani Gandu (NNPP) da Kabiru Muhammad Birnin Magaji (PDP) da Shamsu Huwarich (PDP) da Musa Ɗanba’u (PDP) da makamantansu.

v)               Makaɗan Siyasa a Sake: kamar Dauda Kahuta Rarara (PDP, APC, NNPP) da Sanusi Aliyu Gadanga, Gusau da sauransu.

vi)            Waƙoƙi na Makaɗa Game-Gari wato Makaɗa na Kowa da Komai: Misali Dr. Mamman Shata Katsina da Dr. Adamu Ɗanmaraya Jos da Aliyu Gadanga, Gusau da Babangida Kakadawa, Gusau, Sakkwato da Naziru Muhammad Ahmad, Sarkin Waƙa, Kano da Prince Adam A. Zango, Kaduna da S. Fada, Kano da Muftahu Umar Muhammad, Kano da Aliyu Rijiyar Zaki, Kano (Chairman) da Sarfilu Sarkin Waƙa da Nazifi Asnanic da ire-irensu.

vii)          Waƙoƙin Makaɗan Bege: Su ne waƙoƙin da wasu makaɗa suke yi wa Manzon Allah, sallallahu alaihi wa sallama, da dukkan ahalinsa da sauran Manzanni da Annabawa da Mujaddadai. Makaɗan nan sun ƙunshi Hafizu Abdullahi, Kano da Fadar Bege, Kano da Ahmad Muhammad Sabi’u (Shehi) Kano da Bashir Ɗandago da Sadi Sidi Sharifai, Kano da Rabi’u Usman Baba, Kano da Bashir Ɗanmusa da Halifa Sanusi Gyaranya da Kawu Dogarai da Rabi’atu da Shamsu mai Rangaɗaɗau da Kabiru Classic, Gusau da sauransu da yawa.

viii)        Waƙoƙin Makaɗan Soyayya a Turke: Kamar na Umar M. Sharif, Kano da Hamisu Sa’id Breaker, Kano da Abdul D. I. da Auta Waziri da Auta M. J. Boy da Sani Ahmed da Sadiƙ Sale da Husaini Danko da Adamu Hassan Nagudu da sauransu.

A dunƙule, waɗannan nau’o’in makaɗan baka na Hausa da ma waɗanda ba a jero sunayensu a nan ba, an daɗa karkasa su zuwa:

-                   Makaɗan Bege

-                   Makaɗan Sarakuna

-                   Makaɗa Game-Gari

(Gusau, S. M. (2002) sh. 161-162)

Ƙananan batutuwa su a wannan takarda sun ƙunshi:

º                  Ma’ana da Tarihin Shigar Ubangida a Waƙar Baka Bahaushiya

º                  Daidaita Tunani da Tsinkaya a Waƙoƙin Baka na Hausa

º                  Ubangida a Ɗiya ko a Waƙoƙin Makaɗan Baka na Hausa

º                  Zambo da Habaici a Waƙoƙin Ubangida

º                  Tsakure a Misalce na Wasu Ɗiya ko Waƙoƙi da Wasu Makaɗan Baka Suka yi wa Ubangida

 

2.0          Ma’ana da Tarihin Shigar Ubangida a Waƙar Baka Bahaushiya

 

2.1          Ma’anar Kalmar Ubangida

Kalmar Ubangida tana da tsagi biyu Uba + n gida, an haɗa kalmomin biyu da alamar (-n ) mai nuna wata dangantaka. An kuma ɗauki kalmomin su zama ɗaya a wata ƙa’ida ta rubutu na daidaitacciyar Hausa (Galadanci, M. K. M. (1976).

Uba kalma ce ta suna wato Mahaifi ko Shugaba ko Jagora. -n gida kuwa wani haɗi ne mai nuna dangantaka (CNHN, 2006, Sh: 461).

Ma’anar Kalmar Ubangida ta fuskar fannin ilimi ko isɗilahi wato bisa ganowa ko kiyasin Malamai ko masana ko manazarta ita ce:

Shugaba ko Sarki ko wani jami’i ko attajiri ko masani ko ma’aikaci ko soja ko ɗansiyasa ko sauransu, manya, masu kamala, masu matsayi ko wata daraja, waɗanda kuma makaɗin baka ya yi wa wata waƙar baka ta Hausa bisa daidaitaccen shiri da rauji da rerawa da sadarwa (Gusau, S. M. 2008, sh. 459).

2.2          Tarihin Shigar Ubangida a Waƙar Baka Bahaushiya

Hausawa sun ɗauki lokaci mai tsayin gaske suna shiryawa da rerawa bisa rauji mai gamsarwa tare da isar da wani saƙo dangane da wasu fannonin rayuwa daban-daban.

Wani tsari da ya shigo cikin waƙoƙin baka na Hausa, shi ne a sami wani makaɗi na baka ya nace wa wani Sarki ɗaya a yi masa waƙoƙin baka. A haka makaɗin zai turke kansa a da’ira ta Sarki ɗaya.

Domin haka, tun daga daidai lokaci ne, wasu makaɗan baka, suka mayar da hankula wajen yi wa Sarakuna[6] waƙoƙi, suka kuma ɗauke su a matsayi da muƙami na iyayen gidajensu. Ta wannan wasiɗa sai Sarakunan suka kasance masu jiɓintar hidimomi da ɗaukar nauye-nauye na muhimman al’amura na waɗannan makaɗa.

A kwana a tashi, musamman da tafiyar Hausawa ta tsala a cikin hada-hadar amincewa da sauraron waƙoƙin baka, sai a wasu zanguna, tun ma na mulkin farar hula wato ‘yansiyasa da mulki na masu kakin Soja wato Sojoji ba, makaɗan baka sun daɗa buɗa matsayi na Ubangida har ya ƙunshi:

·            Sarakuna, manya da ƙanana, da iyayen ƙasa da hakimai da dagatai da masu unguwanni da sauran masu riƙe da muƙaman Sarautu;

·            Jami’an Gwamnati tun daga Shugabannin Ƙasa da Gwamnoni a Jihohi da Ministoci da Kwamishinoni da Ciyamomi da Sakatarori da sauran jami’ai madangantansu;

·            Attajirai, masu kuɗi ko tarkoki ko kamfanoni ko masu gudanar da harkoki madanganta kasuwanci da saye da sayarwa;

·            Manya da hamshaƙan mutane masu tafiyar da sauran al’amura na sana’o’i;

·            Mashahuran Malamai na addinin Musulunci ko na sauran fannonin ilimi;

·            Mutane masu darajoji a sauran rukunoni da kadadu na tarayyar Hausawa da a dukkan al’ummu waɗanda Hausawa suke yin hulɗoɗi da su a duniya.

 

3.0          Daidaita Tunani da Tsinkaya a Waƙoƙin Baka na Hausa

Nagarta da kwarjini na waƙoƙin baka sun ta’allaƙa ne ta fuskar aiwatar da su cikin jeranta tunani da zaɓo kalmomi a kowane matani na waƙar baka da za a shirya, a rera, a sadar da shi. Ashe ke nan ya zama wajibi ga masu yin waƙoƙin baka su zama masu tsinkaya, masu hararowa, masu hango baya da gaba, tare da yin lura da taka-tsantsan da neman dacewa bisa furuci na waƙar baka da za su dinga farfaɗa. Har wa yau kuma makaɗan za su dinga tantance yanayi da nauyin daraja na waɗanda suke yi wa waƙoƙin baka, musamman dangane da lokaci da zanguna mabambanta na tattakinsu (Gusau, S. M. (2008) Sh: 463).

Makaɗa na waƙoƙin baka, hakazalika, ya dace su dinga tsayawa kan hauji da haddi dangane da nau’o’in kalamansu a waƙa, ba tare da shige gona da iri ko zarce iyaka ba[7].

Akwai alfanu matuƙa makaɗi ya jeranta tunaninsa a waƙa, ya kuma lura Hausawa suna ƙarfafa halaye da abubuwa kyawawa kuma nagartattu. Kada furuci ko kalamai na waƙoƙin makaɗa ko mawaƙa su kasance sanadai na haƙa ramin mugunta ko su ba da wata kafa wadda za ta iya sabbaba ce-ce-ku-ce ko tsagewar bango. Ashe ke nan wajibin makaɗi ne ya dinga furuci mai kan gado[8].

Sannan mai yin waƙar baka, ya sani cikin haƙiƙancewa, shi mutum ne mai gyara rayuwar al’ummarsa ta Hausa da tarsashi na jinsuna madanganta hulɗoɗin Hausawa. Makaɗin baka alƙalami na al’ummarsa ne, mai sarrafa takobi, mai kaifi, da garkuwa da kiyayewa da tabbatar da alfarma da muhibba na waɗanda yake yi wa waƙoƙi, ba tare da kuma yana gaya musu furuci na kowace irin fallasa ba[9].

Haka zalika, shi Ubangida a ma’anarsa ta fannin ilimi, sananne ne, mai ƙima, wanda kuma za a raga masa bisa wata maslaha kai ko ma don dole. Ubangida, a tunanin wasu a yau, ya shiga sahun da Hausawa suke nunawa, ‘Ana jin kunya tasa ko don dole’. Akan ba shi haƙƙoƙinsa da suka ta’allaƙa da shi. Allahu ne mai shiryarwa![10]

Wata shahararriyar dabi’a ta makaɗi mai Ubangida, a zamantakewar Hausawa, a da ko a yau, yakan riƙa Ubangida[11] da ƙima, ya dinga girmama shi, ya tsare yi masa biyayya, ya dinga zaɓen kalmomi na jamala yana gaya masa. Shi kuma Ubangida yakan amince da makaɗi, ya zama sirrinsa, ya dinga kulawa da shi, ya kuma karkatu a yi masa hidimomi gwargwadon iko domin amana da zaman tare.

 

4.0          Ubangida a Ɗiya ko a Waƙoƙin Makaɗan Baka na Hausa

Makaɗan baka sun ci gaba da shiryawa Ubangida waƙoƙi masu turaku na kansu ko waɗanda suke saka su a cikin ɗiya na wasu waƙoƙi a matsayin ƙananan saƙonni. Ke nan makaɗi yakan iya ƙulla babban saƙo wato turke a waƙa sukutum ko ya jefa ƙaramin saƙo a tsari na tubali a ɗa ko ɗiya na wata waƙa da zai danganta su da Ubangidansa.

Yana daga cikin kulawar makaɗi, ya aiwatar, tare da sadar da waƙoƙi ga Ubangidansa domin ya bayyana ƙauna da soyayya da zumunci da hulɗoɗi ƙwarara da suke a tsakaninsa da shi (Ubangidansa).

Makaɗi zai dinga gaya wa Ubangidansa kalamai na zubin waƙoƙin baka ta rauji mai garɗi cikin sadar da zaɓaɓɓun kalmomi masu nagarta, masu fitowa da mutunci da muhibba da kwarjini da taimako nasa. Ya dace, zubin nan ya zama mai jan hankali, mai sakawa da samar da nustuwa, a yawancin lokuta ma, zubin ya kasance mai ɗaga zuciya, mai sa mata farin ciki da kawar mata da kowace irin damuwa. Haka kuma zubin ya danganci cicciɓawa da kwarzontawa gwargwadon matsayi na Ubangida.

Makaɗi kuma ya zamana ya kauce wa kowaɗanne irin kalmomi ko ƙananan matanoni na batsa ko zage-zage ko cin fuska ko sukar muruwa ko faɗar da mutunci ko muhibba ko kuma kowace hasla wadda take da muni ko take taɓa alfarma da mutuntaka ta maigida ko Ubangida[12].

 

Makaɗan baka na Hausa sukan jingina waƙoƙin da suke yi wa iyayen gidajensu bisa waɗannan turaku ko tubalai:

·             Bege

·             Yabo

·             Soyayya

·             Karimci

·             Kyauta

·             Baiwa

·             da sauransu da yawa

 

Haka kuma sukan zuba wa matanoni na waƙoƙi na mabambantan Ubangida dabaru na adon harshe da jan hankali da daɗa tabbatar da daraja da ƙima da jamala. Ga wasu daga cikin dabaru na hikimomi da azance-azancen maganganu:

·             Kamantawa

·             Siffantawa

·             Alamtarwa

·             Kinintawa

·             Alkunyantawa

·             Barkwantawa[13]

·             da sauransu

 

Wasu turaku ko tubalai ko dabarun adon harshe cikin zaɓaɓɓun kalmomi da makaɗan baka suke furta wa Ubangida, wasunsu ne a jadawali kamar haka:

Waƙoƙin Hausa



A siga ta yi wa Ubangida ado ko yi masa kwalliya ko yi masa tajmili ko shela ko jan hankulan mutane a kan halayensa ko ɗabi’unsa ko tallafinsa ko taimakonsa ko nauyi na tausayinsa, makaɗan baka sukan kwatanta shi da:

·             Dabbobi masu kwarjini, masu buwaya, masu taƙama masu wobuwa, masu shaja’a ko jaruntaka ko nauyi na iko da mulki a tsakanin sauran dabbobi a Gandun Daji.

·             Tsuntsaye masu halaye da ɗabi’u na jamala da kwarjini, ba masu yawan surutu irin suda ba. Duk da yake Makaɗa Sa’idu Faru ya kwatanta Ubangidansa, Sarkin Musulmi Alhaji Muhammadu Macciɗo a yayin da yake riƙe da Sarautar Sarkin Kudan Sakkwato da Suda wadda ta yi wani ɗan waƙa ta bayyana muhibba ta Macciɗo da Sa’idu Faru. Haka kuma Abubakar Imam ya yi amfani da Aku, ya ɗora shi a matsayi na Wazirin Sarki a Magana Jar ice.

·             Itatuwa da bishiyoyi da ƙwari na tudu da na ruwa da gulabe da fadama da saiwoyi da tsirrai da makamantan waɗannan abubuwa ko halittu a duniya.

 

5.0          Zambo da Habaici a Waƙoƙin Ubangida

Zambo da habaici da baƙar magana da shaguɓe da ba’a da arashi da gatse da gugar zana da dungu, kai hatta ma da tumasanci, suna daga cikin maganganun hikima ko azancin magana da wasu Hausawa suke shiryawa ta furucin baki. Hausawa sukan ƙirƙiri maganganun hikima a hulɗoɗin rayuwa a zamantakewa ta dare da ta rana domin hannunka-mai-sanda da yin gargaɗi da jan hankali da tunasarwa da faɗakarwa da neman a yi taka-tsantsan da sauransu (Gusau, S. M. (2011) sh: 14-15).

Kamar yadda bincike ya tsinkayo, zambo da habaici da baƙar magana da ba’a da barkwanci, azance-azance ne na hikima da sukan tusgo ko kutso ko ratso zubi na wasu matanoni na waƙoƙin baka na Hausa domin hannunka-mai-sanda ko nuni cikin waƙa ko faɗakar da al’umma ko jan kunne ko madangantan waɗannan halaye.

Alal-Misali, Budan Zakka, Makaɗa Buda Ɗantanoma, Argungu ya furta wani ɗa na waƙa inda ya faɗi:

Jagora: Sama ba yaro ba,

: Ba aboki nai ba,

 Y/Amshi: Ba warin yaro barwa,

Jagora: Ba matsuwa, sa tuba,

 Y/Amshi: Ba sake faɗin an yi,

Jagora: Mamman mai wada yas so,

 Y/Amshi: Sarkin ɗibah haushi,

: Gagara Ƙarya Sadauki,

: Jangwarzon Alƙali.

(Waƙan Buda Ɗantanoma ta Sarkin Kabin Argungu

 Muhammadun Sama (Gusau, S. M. 2008, Sh; 234)

 

A wannan ɗa na waƙa, Buda Ɗantanoma, ya baza himma wajen ayyana wasu fitattun halaye na ƙima da daraja da ƙwato wa jama’a haƙƙoƙinsu da tsayuwa kan gaskiya wofintu daga yin ƙarya na Ubangidansa, Sarkin Kabin Argungu Muhammadu Sama.

Ƙari a haka kuma, akwai wasu makaɗan baka da sukan kare ko daɗa bunƙasa mutunci da muruwa na Ubangida ta fuskar shirya wa wasu zambo ko habaici domin nuni cikin waƙa.

Dubi wata magana ta hikima cikin ishara da makaɗa Ibrahin Naranbaɗa Isa yake gaya wa Sarkin Gobir na Isa, Alhaji Amadu Bawa I wani zance da wasu suka yi maras tushe. Ga kalmomin da ya yi masa nuni da su cikin waƙa:

Jagora: Baban Maiwurno bar su can su yi zancen banza,

 Y/Amshi: Mai ga-noma bai yi ƙwazon mai gona ba.

 

Jagora: Ka ji wai mai roƙo hura ya sha ya shige danga ta,

 Y/Amshi: Sai ka ji ya raina mai dame arba don ƙarya,

: Ka san tabbatar tsiya ga matsaci an nan,

: Gwarzon Shamaki na Malam toron giwa,

: Baban Doda ba a tam ma da batun banza.

(Waƙar ‘Gwarzon Shamaki’ ta Ibrahim Narambaɗa wadda ya yi wa Sarkin Gobir na Isa Amadu Bawa I (Gusau, S. M. 2008, Sh; 255-256)

 

A yayin zaman tare, a wasu lokuta, akan sami gilmayya da faruwa na wasu abubuwa kamar damuwa da nuna ƙiyayya ko wata jayayya ko cin dudduge ko wasu ayyuka na wuce gona da iri da ire-irensu. A aukuwar ire-iren waɗannan halaye, makaɗan baka sukan shirya kalmomi a cikin ƙananan saƙonni domin su kiyaye mutunci da baiwoyi na Ubangida ko su yi masa garkuwa ta katangar dutsi ko ta kalmomin ƙarfe irin na kandiri ko kwangiri.

Ga wani misali daga wani ɗan waƙa ta ‘Gagara Ƙarya, ta Buda Ɗantanoma Argungu shi ne:

Jagora: Kanta Ubanzagi, Jibo as Sarki,

 Y/Amshi: Ba Sarkin ƙaƙe ba,

: Gagara ƙarya sadauki,

: Jangwarzon Alƙali.

 

A wannan ɗa Buda Ɗantanoma yana yi wa wasu habaici ne masu yawo da wata ƙaramar magana suna nuna Ubangidansa, Muhammadun Sama Argungu, wai ba jarumin Sarki ne ba.

A wani ɗan waƙa kuma makaɗa Buda Ɗantanoma Argungu yana kare kansa da kansa inda yake faɗin:

Jagora: Mai nuƙura da Buda Sarkin Turu,

 Y/Amshi: Bai san Allah na ba,

: Gagara Ƙarya Sadauki,

: Jangwarzon Alƙali.

(Gusau, S. M. 2008, Sh; 243-247)

 

Makaɗa Sa’idu Faru ya mutunta wasu tsuntsaye, suda da burtu, ya mayar da su mutane ko makaɗa, kuma suna ta rera wa Sarkin Kudun Sakkwato, Alhaji Muhammadu Macciɗo[14] wani ɗan waƙa na kwarzanta shi da bayyana darajojinsa. Hatta Larabawa ma sun shiga yi wa Sarkin Kudu Macciɗo (Sarkin Musulmi) waƙoƙi masu mutunta shi da fito da darajojin da Allahu ya yi masa. Ga kalmomi na wannan dogon ɗa na waƙa kamar haka:

 Jagora (Ɗani[15]) : Nic ce suda waƙa akai,

: Tac ce lallai waƙa nikai,

: Waƙam Muhamman Sarkin Kudu,

: Waƙan nan da Ɗan’umma yai mashi,

: Baicin uwat tsuntsaye nike,

: In da kamam Mulki na nikai,

: Da nai mai wasiƙa yai min kiɗi,

: Dannan ni ko sai niw wuce,

: Can nat taɓa yat tafiya kaɗan,

: Sai ni ishe burtu na kiwo,

: Shina ta waƙar Sarkin Kudu,

: Ala Sabbinani ɗan Amadu,

: Allah shi ƙara mai nasara,

: Nic ce burtu waƙa akai,

: Yac ce lallai waƙa nikai,

: Waƙam Muhamman Sarkin Kudu,

: In na yi ta za ni wurin kiwo,

: In na zo abinci sai na rage,

: Sai ni ko sai niw wuce,

: Can na taɓa yat tafiya kaɗan,

: Nik kai bakin bahar Maliya,

: Sai ni ishe Larabawa wurin,

: Suna ta waƙas Sarkin Kudu,

: Rainai ya daɗe Sarkin Kudu,

: Ala Sabbinani ɗan Amadu,

: Allah shi ƙara ma nasara,

: Ɗan mai daraja Sarkin Kudu,

: Jikan mai daraja ɗan Amadu,

: Sannan mai daraja shi yay yi shi,

: Shina gida zanne a Sakkwato,

: In ya yi salla yai tazbaha,

 ‘Y/Amshi: Hasken nashi han nan kallo mukai,

: Kana shirye Baban ‘Yan’ruwa,

: Na Bello Jikan Ɗanfodiyo.

(Waƙar Sa’idu Faru ta Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo (Sarkin Kudun Sakkwato a da) Gusau, S. M. (2009) Sh: 155-156)

 

Wasu maganganun hikima da ake tsattsarmawa a wasu waƙoƙin baka na Hausa, musamman na Ubangida, su zama ƙananan saƙonni, a taƙaice sun haɗa da:

-                   Zambo

-                   Habaici

-                   Gargaɗi

-                   Faɗakarwa

-                   Tunasarwa

-                   Nuni Cikin Waƙa

-                   Taka-Tsantsan

-                   Ƙima

-                   Muhibba

-                   Ayyana Daraja

-                   Ɗaukaka Daraja

-                   Tsaron Mutunci

-                   Bunƙasa Mutunci

-                   Bayyana Mutunci

-                   Inganta Rayuwa

-                   Kyautata Rayuwa

-                   Bunƙasa Muruwa

-                   Girmama Muruwa

-                   Kariya

-                   Kangiya

-                   Garkuwa

-                   Dakushe Azarɓaɓiya

-                   Hana cin Dudduge

-                   Hannunka-mai-Sanda

-                   Ingiza mai Kantu Ruwa

-                   da Sauransu

 

 

6.0          Tsakure a Misalce na Wasu Ɗiyan Waƙoƙi da Wasu

Makaɗan Baka Suka yi wa Ubangida

Kamar yadda aka kawo bayani a baya, akwai misalai na wasu ɗiyan waƙoƙin Hausa waɗanda makaɗan baka suka sassaka kalmomi masu fitowa tare da ɗaga darajoji da kwarjini da ɗaukaka da muhibba da taimako da buwaya da tsayuwa a kan duga-dugi da sauransu waɗanda suka danganta su da Ubangida daban-daban.

A wannan fage za a kawo misalai ƙalilan kamar haka:

6.1          Ibrahim Gurso Mafara, yanzu Jihar Zamfara, ya gaya wa Ubangidansa, Sarkin Musulmi Abubakar III, a yayin da yake riƙe da Sarautar Uban Ƙasa ta Sardaunan Sakkwato a Talata Mafara a 1938, dab da zai zama Sarkin Musulmi, ya haye halifa ta Shaihu Usmanu Ɗanfodiyo a zama na Sakkwato:

Jagora: Iro ni na dace,

: In Sarki yas so ka,

: Ka hi gonat taki,

: Ka hi hwataucin Gwanja,

 Y/Amshi: Tun da Allah yab ba ka,

: Ƙara godiya mukai,

: Gagarau ɗan Shaihu,

: Garba Rura gwarzon Atiku,

: Sa maza ladab.

(Ibrahim Gurso a waƙar Sardaunan Sakkwato, Alhaji Abubakar III, dab da zai zama Sarkin Musulmi a 1938 (Gusau, S. M. 1988: Juzu’i na Biyu).

 

6.2          Alhaji Salihu Jankiɗi, Sarkin Taushin Sarkin ya shirya wa kansa wasu kalmomi na sanin kima da zalaƙar waƙar taushi ta Ubangida. Ya furta ɗan ne a cikin da ya yi wa Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar III (1938-1988). Ga ɗan waƙar kamar haka:

Jagora: Jumurin kwaram a kwana ana tahiya,

: Sai goga, jaki bai kai nan ba,

 Y/Amshi: ‘Yan yara masu kurin waƙa, ku bar wargi,

: Ma’ana ba ta zama ɗai ba,

: Ni ba ni yin kiɗin iska sai ga Sarkina,

: Ɗibgau bajinin dole,

: Abubakar na Amadu ya gyara Masallaci.

(Salihu Jankiɗi a waƙar Sarkin Musulmi, Abubakar III, ‘Ɗibgau bajinin dole’ (Gusau,. S. M. 2002. Sh: 95-96).

 

6.3          A wani ɗan waƙa, Mamman Sanƙira ɗan Makaɗa Idi Ɗangiwa Zuru ya bayyana ƙaramin saƙo ko tubali na ginin waƙa dangane da zaman mahaifinsa Sarkin Taushin Zuru, Alhaji Idi Ɗangiwa Zuru a Masarautar Sarkin Zuru. Ga ɗan waƙar kamar haka:

Jagora: Mamman na jiya tun hwarko,

: Wannan ya zamo tarihi,

: Ɗangiwa da yaz zaka Zuru,

: Mamman Sani yak kawo shi,

: Sannan Garba Sami ka iko,

 ‘Y/Amshi: Shi kau yar riƙe mu da kyawo,

: Yanzu ko Shehu Danga ka iko,

: Shi kuma ya riƙi mu da kyawo,

: Alhaji Sa’idu ɗauki abinka,

: Don kak ka ban ni ga daji,

 G/Waƙa: Koma shirin maza ɗan Mamman,

: Alhaji ba a kai ma raini.

(Waƙar Mamman Ɗangiwa Zuru ta Alƙali Sa’idu. Gusau, S. M. 1988: Juzu’i na Biyu).

 

Jagora: In dai kag ga matag gado,

: Ita in ta taho ga mijinta,

 Y/Amshi: To, shi ko, shi riƙe ta amana,

: Don dai kas shi bat ta ga hanya,

: Koma shirin maza ɗan Mamman,

: Alhaji ba a kai ma raini.

(Waƙar Mamman Ɗangiwa Zuru ta Alƙali Sa’idu. Gusau, S. M. 1988: Juzu’i na Ɗaya: 226 & Juzu’i na Biyu).

 

6.4          Makaɗa Sa’idu Faru, Makaɗin Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo ɗan Sarkin Musulmi Abubakar III, shi kuma ga abin da yake faɗa:

Jagora: Alhaji Baba Muhammadu Macciɗo,

 Y/Amshi: Baba barka da hayewa Maliya,

Jagora: Waƙag ga da nim maka Muhammadu,

: Na ji daɗinta Mamman Sarkin Kudu,

: Tun da Kabi hak Kano ham Masar,

: Hab birnin Legas hab Bichi,

 Y/Amshi: Kowa ya ji waƙar Sarkin Kudu,

 G/Waƙa: Kana shire Baban ‘Yanruwa,

: Na Bello jikan Ɗanfodiyo.

 

Jagora (Ɗani/Mu’azu): Maganag ga da za ni faɗa maka,

: Gagarau ɗan Aliyu kai man gafara,

: Wada duk aka gadon ƙasura,

: Wada duk aka gadon ɗaukaka,

: Wada duk aka gadon ci gaba,

: Mamman ka gaji Abubakar,

: Ko da sayen halin nan a kai,

 Y/Amshi: Baba halin da ka kai kuɗɗi shikai,

 G/Waƙa: Kana shire Baban ‘Yanruwa,

: Na Bello jikan Ɗanfodiyo.

 

Jagora: Ko da ni makaɗin Ubanzagi,

: Na gaji ka ba mu dawakuna,

: Na gaji ka ba mu jukunkuna,

: Na gaji ka ba mu garuruwa,

 Y/Amshi: Muhammadu in Allah yai nuhi,

: Ba mu gari da mutanenai duka,

Jagora: Na gode riƙon Baban Zagi,

 Y/Amshi: Allah shi yi ma babban rabo,[16]

: Albarkar Shehu da Bello,

: Had da Atiku zuwa Sarki Hassan,

 G/Waƙa: Kana shire Baban ‘Yanruwa,

: Na Bello jikan Ɗanfodiyo.

 

(Sa’idu Faru a Waƙar Sarkin Kudu Macciɗo kafin ya zama Sarkin Musulmi. Gusau, S. M. 2009. Sh: 152-154)

 

6.5          Alhaji Muhammadu Bawa Ɗan’anace a Waƙarsa ta Ɗanduwa ya kwarzonta shi, yana faɗin:

 

Jagora: Maza ga giwa ma sha dahi,

: Zaki mai ƙashi guda,

 Y/Amshi: Gwanki mai kiyon ɓata,

 G/Waƙa: Ba tsoro garai ba,

: Ɗandunawa maƙi gudu.

 

Jagora: Da in ɗauki bugunka Duna,

 Y/Amshi: Gwamma a halban da bindiga,

Jagora: Bindiga in kashi takai,

 Y/Amshi: Ko hannu kashi yakai,

 G/Waƙa: Ba tsoro garai ba,

: Ɗandunawa maƙi gudu.

 

(Waƙar Ɗan’anace ta Ɗandunawa. Gusau, S. M. 2014. Sh: 95-96)

 

 

7.0           Kammalawa

Kamar yadda aka nuna tun a tsakure da gabatarwa, wannan takarda ta yi Nazari ne kan matsayi da darajar Ubangida a Waƙoƙin Baka na Hausa’.

Muhimman kalaman da aka kawo su a rubutun nan bisa taƙaitawa, sun fuskanci bayani kan Ubangida da fasalolin shigar Ubangida a cikin zubi na matanonin waƙoƙin baka na Hausa. Daga nan kuma aka ɗora nazari a kan wasu yanaye-yanaye da suka cancanta makaɗan baka su dinga saisaitawa da daidaita tunane-tunanensu da tsinkayoyinsu a manya da ƙananan saƙonni wato turke da tubalan ginin turke na Zubin waƙoƙinsu.

Haka kuma an kawo wasu sigogi da matakai waɗanda makaɗan waƙar baka Bahaushiya suke bayyana Ubangida a kansu, misali ta fito da asalinsa da nasabarsa da zuriyyarsa da kwarjininsa da ɗaukakokinsa da himmominsa da tallafe-tallafensa da karimcinsa da baiwoyinsa, musamman da ya samu daga Allah, mai yadda ya so bisa ikonsa da rahamominsa.

A wasu lokuta, sukan yi adontawa tare da yi wa Ubangida kwalliya da kwatanta shi da wasu halittu kyawawa, masu jamala, masu ƙarfi ko shaja’a ko waibuwa ko siddabaru ko makamantan waɗannan abubuwa.

Makaɗan Ubangida kuma an nuna sukan tsarma wasu maganganun hikima ko azanci ta yi wa al’umma hannunka-mai-sanda ko tunasarwa ko faɗakarwa ko taka-tsantsan ko gargaɗi, a wasu lokuta kuma har da yi musu ingiza-mai-kantu-ruwa, duka a furuci da rauji na waƙoƙin baka na Hausa.

Takardar nan ta ayyana, makaɗan baka, sukan jefo zambo ko habaici ko baƙar magana ko ba’a ko arashi ko gugar zana da sauransu don yin kariya da garkuwa ga Ubangida da sauran waɗanda suke yi wa waƙoƙi.

Daga nan ne aka kawo wasu misalai a dunƙule na ɗiya da makaɗan baka suke yi wa Ubangida ko wani wanda suke yi wa gayaunar waƙa.

Kamar yadda aka yi bayani a binciken nan, an yi tunasarwa ne da bayar da shawarwari ga makaɗan baka na Hausa, tun ma na yanzu da kuma masu tasowa ba, kan su dinga tattaunawa da shirya zaɓaɓɓun kalmomi masu dacewa da matanonin waƙoƙin da suke aiwatarwa da sadarwa ga al’umma.

Ya kamata kalmomin da makaɗa suke zaɓowa suna jefawa a cikin waƙoƙinsu su dinga kasancewa suna kallon shekaru ko muruwa ko tattaki ko ƙima na mutane waɗanda suke yi wa su.

Idan kuma aka daɗa waiwayar nahiya ta sakamakon wannan bincike, za a nuna, akwai bukatar a yi wa makaɗan baka tunasarwa da faɗakarwa a kan su dinga yin naciya da mayar da hankali a wajen zaɓo maganganu ƙanana da manya, masu ma’ana da daidaito, masu kalami na ƙarfafa kafaɗu na al’ummar Hausawa. Kada su dinga amfani da kalmomi na ɓatanci ko kalmomi waɗanda za su tarwatsa Hausawa da Ƙasar Hausa da Arewa da Nijeriya baki ɗaya.

Haƙiƙa, wajibi ne al’umma ta mayar da hankali ta fuskar ba wa waƙoƙin baka da makaɗan baka matsayai da ƙimominsu domin suna daga cikin masu riƙe da mutunci da samar da hanyoyi na nagartacciyar rayuwa. Haka kuma akwai bukatar al’ummar ta dinga kauce wa biyar gwadabu na masu sakin baki ko surutai barkatai babu na zaɓi. Daɗa makaɗan baka ne ko masu yaɗa jita-jita.

Musulmi su dinga tuna akwai sakamako da hukunci a bayan rayuwar nan ta duniya, a yayin da aka mutu, aka tafi Barzahu da rayuwar ta lahira.

Dukkan waƙoƙin baka na Hausa, ana son su zama nagartattu ba ballagazazzu ba, masu kwarjini da ƙima da amfani ga al’ummar da ake yi su da ma sauran al’ummun duniya. Ta haka ne ya dace cikin armasawa a dinga shiryawa da aiwatarwa da sadarwar waƙoƙin Hausa bisa suluki da turba miƙaƙƙu. Daga nan kuma a tsare tare da kiyaye mutunci na ɗaiɗaikun mutane, tun ma ba dattawa da tsofaffi da masu shekaru da auki ba, da kuma jumlatanin jama’ar Hausawa da dukkan masu hulɗoɗi da su.

Makaɗan baka na Hausa tun ma ba a yau ba, su lazimci sadar da waƙoƙinsu bisa muhallansu da munasabobinsu na rukunonin jama’a mabambanta wato yara da matasa da matsakaita da manya da tsofaffi da dattawa. Sannan da masu muƙamai da darajoji na ilimi da na mulki da na dukiya ko na attajirci ko na sauransu. Har way au kuma su dinga ɗora waƙoƙin nasu ta kallon jinsunan maza ko mata tare kuma da tantance nahiyoyi ƙimomi ko mutuncin kowannensu.

A wata mahanga ta wannan takarda kuma an lura makaɗan baka na Hausa ba su yi wa Ubangida tsoho ko sabo, ko wanda suke yi wa waƙa ko da kuwa ta gayauna ce, zambo ko habaici ko baƙar magana ko shaguɓe, ko arashi ko gugar zana ko sauransu domin amana da fahimtar juna da mutunci da suke a tsakaninsu[17].

Ya kamata iyayen gida, manya da ƙanana, su daɗa fahimtar waɗannan hasloli kyakkyawa, waɗanda makaɗan baka na dauri a al’ummar Hausawa suke biye da su, sannan su kwaɗaitu da aiki da su a kowane hali da daɗi ko ba daɗi.

Alhamdu Lillahi Rabbil-Alamina, was-salatu was-salamu ala Sayyidina Muhammadu, khatimul-ambiya’i wal-mursalina, allazi ballagar-Risalata wa addal’amanata, sallallahu alaihi wa sallama.

Muna yin addu’a ga Allahu, tabaraka wa ta’ala, ya daɗa fahimtar da makaɗan baka na Hausa, su kasance masu inganta tunaninsu da furucinsu na waƙa.

Muna roƙon Allah ya fahimtar da mu kyawawan kalami da suke isarwa a gare mu, ya daɗa ɗaukaka harshen Hausa, ya tsare shi, ya kiyaye shi daga kowane irin ɓata-gari.

Muna kuma ɗaga hannuwanmu a sama, muna roƙon Allahu ya daidaita zukatanmu a yi masa ibada, ya kuma daɗa mana ƙauna da so da bege ga Manzon Allah, cikamakin Manzanni da Annabawa, ya kuma sanya mu a cetonsa a Ranar Mahshar. Ya Nabiyyul-lahi, Khatimil-Mursalina, Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.

 

Alhamdu Lillahi.

MANAZARTA

 

Adamu, M. T. (2015) Haihuwa da Suna a Bahaushiyar Al’ada. Kano: Salma-A’aref Publishers.

Adamu, M. T. (2018) Aure da Biki a Ƙasar Hausa. Kano: Ɗan Sarkin Kura Publishers Limited.

Al-Buhari, A. A. M. I. B. (?) Sahihul-Buhari.

Al-Nawawi, M. Y. I. S. (1418AH) Hadisai Arba’in da Sharhinsu da Harshen Hausa(Al-Arba’una Al-Nawawiyah), Riyadh: Al-Hamramaini Islamic Foundation

An-Nawawi, A. Z. Y. S. (?) Arba’una Hadisan. Cairo: Maɗaba’ar Shu’unil-islamiyya.

Galadanci, M. K. M. (1972) The Structure and Syntactic Function of Comound Noun in Hausa in Anthropological Lingiustics no 14.4.

Galadanci, M. K. M. (1976) An Introduction to Hausa Grammer. Lagos: Longman igeria.

Gora, Y. C. (1989) Camfi a Al’ummar Hausawa. Kundin Digiri na Biyu: Kano: Sashen Koyar da Harsunan NIjeriya, Jami’ar Bayero.

Gusau, S. M. (1980/2002) Sarkin Taushi Salihu Jankiɗi. Kaduna: Baraka Press and Publishers Limited.

Gusau, S. M. (1988) Waƙoƙin Makaɗan Fada: Sigoginsu da Yanayinsu, Musamman a Ƙasar Sakkwato: Juzu’i na Ɗaya. Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Gusau, S. M. (1993-2003) Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Kano: Benchmark Publishers Limited.

Gusau, S. M. (2008) Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa. Kano: Benchmark Publishers Limited.

Gusau, S. M. (2009) Diwanin Waƙoƙin Baka. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M. (2011&2013) Adabin Hausa a Sauƙaƙe. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M. (2014) Diwanin Waƙoƙin Baka, Juzu’i na Biyu. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M. (2014) Waƙar Baka Bahaushiya. Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Gusau, S. M. (2015) Abdu Karen Gusau. Kano: Century Research and Publishing Limited.

Gusau, S. M. (2022) Bugaggun Littattafai da Wasu Maƙalu. Takardar da ya Gabatar. Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Gusau, S. M. (2022) Diwanin Waƙoƙin Baka, Juzu’i na Shida. Kano: Commercial Printing and Publishing.

Haɗejia, M. S. . (2007) Hausawa da Al’adunsu. Kano: Gidan Dabino Publishers.

Lawan, U. M. (2021) Tsakure Cikin Al’adun Hausawa da Adabin Gargajiya. Kano: Gidan Dabino Publishers.

Mu’assasar Al-Balagh (1993). Haƙƙu Zawil Ƙurba. Iran: Islamic Republic of Iran.

Rufa’i, M. K. (?) Aƙlul Muslim.

Sha’arawi, M. M. (?) Manhajar Tarbiyya fil Islam. Masar, Cairo: Al-Ittihad al-Alim Liɗalibi, Jamhuriyati Misra al-Arabiyya.

Tahir, R. M. (2012) Ajamin Hausa don Ƙananan Makarantu. Kaduna: Yahaya Ɓentures, General Printers and Publishers.

Yahya, A. B., Ainu, H. A., Idris, Y. (2015) Sai Alu: Sharhi kan Waƙoƙin da aka yi wa Dr. Aliyu Magatakarda Wamakko (Sarkin Yamman Sakkwato). Kaduna: Ahmadu Bello University Press Limited.

Yahya, I. Y. (1971) Tatsuniya da Wasanni, Littafi na Biyar. Ibadan: Oɗford University Press.

Yahya, I. Y. (1971) Tatsuniya da Wasanni, Littafi na Ɗaya. Ibadan: Oɗford University Press.

Yaro, A. (1994) Waiwaye a Al’adun Hausawa a kan Fulanin Yola. Kundin Digiri na Biyu: Kano: Sashen Koyar da Harsunan NIjeriya, Jami’ar Bayero.

 

RATAYE

HOTUNA NA WASU MAKAƊAN HAUSA

NA DA DA NA YAU


 

Hotunan Mawaƙan Hausa

Hotunan Mawaƙan Hausa


Hotunan Mawaƙan Hausa

Hotunan Mawaƙan Hausa

 

Hotunan Mawaƙan Hausa

Hotunan Mawaƙan Hausa

Hotunan Mawaƙan Hausa

Hotunan Mawaƙan Hausa

Hotunan Mawaƙan Hausa

Hotunan Mawaƙan Hausa

Hotunan Mawaƙan Hausa



[1] Daga cikin ayyuka na S. M. Gusau, akwai Gusau, S. M. (2002) da (2013a&b) da (2014) da (2017) da (2018a&b) da (2021) bisa misalai. Akwai bukatar a sami dama a nazarci waɗannan ayyuka domin su zama masu yin tuni da tunasarwa dangane da usuli da bunƙasar waƙoƙin baka na Hausa.

[2] Ire-iren waɗannan abubuwa na samar da amo ko sauti su ne ake ambata da kaya waɗanda ake yi ba don kiɗa ba, sai dai akan gwama su da furuci na waƙar baka. Su ne kamar Tafunan Hannuwa ko ɗuwawu da ake girgizawa su bayar da amo ko ƙirji da ake dokawa ko ƙafa ko ƙwarya ko shantu ko duma ko tasa ko sauransu.

[3] Su ne ake kira kayan asali na kiɗa da makaɗa suke rera waƙar baka ta Hausa. Sannan ba a yin wani abu ko wani aiki da su sai kiɗa kawai. Su ne kamar kalangu ko ganga ko kuwaru ko kurya ko tambari ko turu ko kanzagi ko sauransu.

[4] Kamar kotsaye na Fulani ko fiyano da jita da kayan kiɗa na ɗakin sitidiyo da kayan kiɗa na band da sauransu. Hausawa sun yi wa waɗannan kayan kiɗa halin hankaka mai mayar da ƙwan wani nata.

[5] Amma duk da haka, wani Sarki ko Sarakuna sukan nemi izini a wajen aminansu Sarakuna waɗanda wasu makaɗa suke turke a wajensu domin su yi musu waƙoƙi a matsayi na gayauna.

[6] Zuwa wannan lokaci Hausawa sun raya Masarautu a garuruwa da birane tare da nannaɗa musu Sarakuna masu shugabantar gudanar da harkoki na zamantakewarsu.

[7] Daga nan ne kuwa makaɗan za su waiwayi al’adun al’ummar Hausawa nagartattu, musamman waɗanda suke a cakuɗe da hukunce-hukuncen addinin Musulunci. Kai tsaye kuma za su kula da matakan tarbiyya da na kunya da alkunya, ba kuma tare da yaɗa fitsara ko batsa ko alfasha ba. Su zamana masu faɗar gaskiya, masu kwatance na daidaito ba na kashi ba domin su cim ma aƙiba kyakkyawa da sauka lafiya.

[8] Ko asaberi ko tabarma ko tsintsiya ko kuma kitso da mata suke yi wa kawunansu.

[9] Waɗanda ake yi wa waƙa masu alfarma ne ga makaɗan baka a kowane irin lokaci, kuma su mutunta ne makaɗan ne. Wani hadisi yana nuna:’Musulmi ɗan’uwan Musulmi ne, kada ya ƙi shi ko ya hantare shi’. Akwai kuma: ‘Musulmi ya so wa ɗan’uwansa abin da yake so wa kansa’ (Al-Nawawi, M. Y. I. S. (1418H) Hadisi na 35 da Hadisi na 13).

[10] Abu ne mai matuƙar alfanu, a kintsa furuci, a ajiye kwaɗayi ko roƙo a gefe. Wani abin waiwaye da ma waɗannan abubuwa ba su cikin hasloli ko al’adu na Hausawa, kyawawa ko managarta. Sannan ba su hau turbobi na addinin Musulunci ba.

[11] Ubangidan nan kuwa yana tare da shi makaɗin alif-da-alif ko kuwa makaɗin ya daɗa samun wani Ubangida sabo dal.

[12] Manzon Rahama, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ƙarfafa faɗar: Al-mumin Lil-mumin yashuddu ba’adhu ba’adhan. Hadisi na 6026. Al-Buhari, A. A. M. I. B. (Sahihul-Buhari)

[13] Dubi wasu matanoni na diya na barkwanci da yawa a waƙar ‘Gwarzon Shamaki na Malam toron giwa’ ta Makaɗa Ibrahim Narambaɗa.

[14] Sa’idu Faru ya yi wa Alhaji Muhammadu Macciɗo wannan waƙa yana a riƙe da Sarautar Sarkin Kudun Sakkwato kafin ya zama Sarkin Musulmi.

[15] Wato Mu’azu ƙanen Sa’idu Faru kuma Wazirin Kiɗa, Daudun Kiɗan Kotso na Sa’idu Faru.

[16]Sa’idu Faru yana yi wa Sarkin Kudu Macciɗo addu’a ya sami Sarautar Sarkin Musulmi, ya zama Amiral-Muminuna na Nahiyar Nijeriya.

[17] Amma duk da haka, a wasu lokuta makaɗan baka sukan yi furuci na ingiza-mai-kantu-ruwa, idan sun haƙƙaƙe ko sun tabbatar Ubangida ba zai kintsu ba. Tare kuma da kyawawan maganganu na tarbiyya da suke gaya masa.

Post a Comment

0 Comments