Cite this article as: Lamido, I. & Garba, B. (2023). Makaɗan Hausa A Gombe: Tasirin Makaɗan Fada A Masarautar Buba Yero. Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture, (2)1, 138-144. www.doi.org/10.36349/tjllc.2023.v02i01.017.
Daga
Ibrahim Lamido Ph.D
Sashen Koyar Da Harshe Da Harshe da Kimiyyar Harshe
lamidoibrahim52@gmail.com
lamidoibrahim52@fukashere.edu.ng
07060777144
Da
Bashir Garba
Sashen Koyar da Ilmin Hausa
Kwalejin Ilmi ta Tarayya, Pankshin, Jihar Plateau
sirbash02@gmail.com
08068004477
Tsakure
Hausawa
mutane ne da aka san su da shiga lungu-lungu da saƙo-saƙo na
yankunan maƙwabtansu
na kusa da na nesa. Mutane ne da ke da
sha’awar tafiye-tafiye don neman kyakkyawar matsuguni na samun ɗan abin tasarrufi na sa wa a bakin
salati. A duk inda suka ya da zango sukan yi wa al’ummar da suka taras tasiri
da harshensu da al’adunsu. Wannan takarda ta yi nazarin makaɗa da mawaƙan fada waɗanda suka kwararo jihar
Gombe kuma suke rayuwa suna nishaxantar da masarautar ta Fulani da kaɗe-kadensu da waƙoƙinsu na
fasaha da bushe-bushensu. An kuma kawo dalilai da suka haifar da zuwan Huasawa ƙasar Gombe
da sabubban cuɗanyarsu da
Fulani a Gombe. Takardar ta yi amfani da hanyar hira da masu ba da bayanai da
kuma ajiyayyun takardu don tattara bayanai da suka taimaka wajen taskace
nau’o’in makaɗa da mawaƙan Hausa
da suke masarautar. Daga ciki, an kawo
makaɗan taushi
da na turu da na kotso da na ganga da na ruwa da kuma masu bushe-bushe. An yi
bayanin waɗanda suka
assasa kowane kiɗa a masarautar
da inda suka fito da waɗanda suka
gaje su, da kuma lokutan da suka fi gabatar da waƙoƙin nasu.
Binciken ya gano akwai makaɗan Hausa maza da mata a fadar masarautar da suka shafi dukkan rukuni na
mawaƙan da aka
gabatar a nan sama. An kuma kawo ‘yan misalai na wasu ɗiyan waƙoƙin makaɗan. Binciken ya nuna yadda
‘ya’ya da jikoki da aka haifa a masarautar suka taimaka wajen
gina al’ummar nan da aka fi sani da Hausa/Fulani wato narkewar al’adun al’ummu
guda biyu waje ɗaya.
Kalmomin Fannu:
Makaɗa, Mawaƙa, Tasiri,
Gombe, Fada
1.0 Gabatarwa
Kiɗa da waƙa a ƙasar Hausa wani
ginshiƙin abu ne da ake aiwatarwa don
ilmantarwa ko sadarwa ko nishaɗantarwa ko bayar da wata gudunmawa
ta musamman. Kiɗa ta yi ruwa ta
yi tsaki, ta durmuya sosai a cikin rayuwar Bahaushe ta fuskokin zamantakewa da sana’o’i da bukukuwa da lokacin shaƙatawa. Kaɗe-kaɗe da waƙoƙi suna nan cike
fal da wasu ayyanannun mutane waɗanda aka fi sani da suna ‘Makaɗan Baka’.
Wannan rukuni na jama’a sun bambanta da juna dangane da asalinsu da yanayin waƙoƙin da suke aiwatarwa da kayan kiɗan da suke
amfani da su (Gusau 2005 p. vii). Makaɗan baka na
Hausa mutane da aka san su da sana’ar yawace-yawace zuwa yankunan maƙwabta na nesa da na kusa suna taɓa sana’arsu ta
kiɗa da waƙa (Lamido 2012 p. 14). Wannan bincike
ya duba yadda ɗaya daga cikin nau’o’in makaɗan baka na
Hausa suka yi tasiri a masarautar Fulani na Gombe wato makaɗan fada, waɗanda aka san su
da shirya wa sarakuna da sarautun gargajiya kiɗa da waƙa suna yabon su da kakanninsu da ƙwarzanta su (Gusau 2003 p. 22). Wannan bincike yana da
muhimmanci domin ya daɗa ƙarin haske a kan irin shaƙuwar Hausawa da Fulani musamman na Gombe da binciken
ya shafa. Hakanan ya nuna yadda makaɗan Hausa suka
zama kanwa uwar gami a al’adu da shagulgula na masarautar Bubayero a Gombe.
2.0 Taƙaitaccen tarihin masarautar Gombe
Masarautar Gombe ta samo asali ne
daga jihadin jaddada musulunci da kafa shi da Shehu Usman Ɗanfodiyo ya ƙaddamar a ƙasar Hausa da maƙwabta ciki har
da Gombe. Bubayero ɗan Usman ɗan Arxo Aliyu ɗan Arɗo Mamuda shi ya
jagoranci jihadin a ƙasar Gombe da Jalingo Muri. Shi ne kuma ya kafa masarautar Gombe bayan
jihadi. Jihadin wanda Bubayero ya ƙaddamar ya faro
ne a shekara 1806 kuma ya ƙare ne a
shekara ta 1841. Kodayake ‘yayansa biyu da suka gaje shi sun ci gaba da jihadin
a yankin kudancin Gombe. Bubayero ya zauna a wurare da dama a lokacin jihadi
kafin ya zarce zuwa yamma da Dukku da ke ƙaramar hukumar Dukku ta yanzu ya kafa
cibiyar masarautarsa a wani wuri da ya raɗa wa suna Gombe kuma aka dawo ana kiran sa da suna Gombe Abba[1]
bayan rasuwarsa (Abba 2004 p. 7-9). Bincike ya nuna tun a wannan cibiya ta
masarautar wato Gombe Abba aka soma samun makaɗan Huasa daga
Kano waɗanda suka soma kwararowa zuwa wannan sabuwar masarauta
(Tukur 2003 p. 14).
A shekara ta 1913 zamanin Sarki
Umaru, Turawan mulkin mallaka suka ɗage cibiyar daga Gombe Abba zuwa
Nafaɗa a arewa maso gabas da Gombe Abba. Shekara shida
bayan nan Turawa suka sake bai wa sarki Umaru Kwairanga umurnin sake ƙaura zuwa Gombe Doma cibiyar masarautr ta yanzu kenan.
A nan ne aka gina wa sarki gida
da masallaci da kotu da kurkuku da ofishin Mulki. Aka samar da kasuwa da
makaranta. Wannan wuri da aka gyara asalinsa jejin al’ummar Fulanin Akko da Gona.
Wannan wuri shi ya zama cibiyar masarautar Gombe a yau (Abubakar 2009 p. 14). Masarautar
Gombe masarauta ce ta Fulani kasancewar Bubayero Bafulatani kuma masu riƙe da muƙaman sarauta
galibinsu Fulani ne waɗanda tun a lokacin jihadi suka taho
Gombe ƙungiya-ƙungiya suka taimaki Bubayero jihadi. Masarautar ta ƙunshi Fulanin Kiri Mbororo’en
waɗanda suka fito daga yankin Borno don su taimaki Bubayero.
Sai Fulani Janafula waɗanda ke zaune a duwatsun Lala da
Hona da Ga’anda da Bira a ƙasar ta Gombe
suna kiwo. Daga tsatsonsu ne Bubayero ya fito. Da akwai Fulanin Jada waɗanda ake kira
da Fulɓe Kitaku waɗanda suka ƙaurato daga kudu maso yammacin Borni zuwa Gombe. Sai
Fulani Tera waɗanda ake musu inkiya saboda zama da Terawa asalinsu
daga Tarangara ce ta Marwa a ƙasar Kamaru
daga can suka yiwo ƙaura zuwa Gombe ƙarƙashin jagoransu
Arɗo Kaigama Buba Yele wanda Bubayero ya naɗa madakin Gombe
(Tukur, 2003 p. 25). Saura sun haɗa da Fulanin
Jera ƙarƙashin jagorancin Arɗo Aliyu daga
Jaragol da Kubegasi. Shi ne Bubayero ya naɗa sarkin yaƙin Gombe. Sai Fulani Maga waɗanda suka fito daga
Gulani a yammacin Biu ƙarƙashin jagorancin Arɗo Magi Buba
Kari Banto wanda aka naɗa Kadin Gombe kuma tun daga lokacin
zuriyarsa take riƙe da sarautar sarkin Magin Gombe.
Saura sun haɗa da Fulani Walama waɗanda suka fito
daga Shelleng bayan an kammala jihadi suka zauna tare da Bubayero a Gombe. Sai Fulani
Daɓe waɗanda suka fito daga Dabema kusa da
Shelleng tun a farkon jihadi suka taho Gombe. Sai Fulanin Gona waɗanda suke riƙe da sarautar Galadiman Gombe. Waɗannan bincike
ya nuna suna zaune a Sumbe da Kalshingi tun kafin jihadi (Tukur 2003 p. 8).
Waɗannan su ne
suka haɗu suka zama asalin Gombe kuma waɗanda suka kafa
sarautu daban-daban a masarautar ta Gombe.
3.0 Cuɗanyar Hausawa
da Fulanin Gombe
Lamido (2021 p. 151) ya bayyana cewa
ƙaurace-ƙaurace da aka san al’ummar Hausawa da su zuwa yankunan
maƙwabta na nesa da na kusa su ne silar cuɗanyar Hausawa
da Fulanin Gombe. Hausawa mutane ne da aka san su da tasiri da harshensu da
adabinsu da al’adunsu a kan duk al’ummun da suka tarar a duk inda suka ya da
zango. Bisa ga wannan ɗabi’a Hausawa daga yankunan Kano da
Zariya da Sakkwato da Zamfara da Haɗeja sun daɗe suna mu’amala
da yankuna da dama na arewa maso gabashin Nijeriya waɗanda suka haɗa da Bauci da
Gombe da Maiduguri da Yola da Jalingo Muri.
A Gombe Hausawa sun daɗe suna mu’amala
da ƙabilu mazauna ƙasar Gombe tun a wajajen tsakiyar ƙarni na sha tara lokacin jihadin Bubayero da
‘ya’yansa. Dalilai da dama sun haifar da zuwan Hausawa da cuɗanyarsu da
Fulani a masarautar. Daga ciki da akwai Hausawa waɗanda kasuwanci
da sana’o’in gargajiya suka kawo su ƙasar. Da
Hausawa masu yawon malanta tare da almajiransu suna zama suna ba da karatun Alƙur’ani. Da akwai masu dalilai na sha’awar sauya matsuguni da auratayya. Sai kuma
masu yawon kiɗa da waƙa da masu roƙon baka waɗanda su ne suka shafi wannan
bincike.
4.0 Dabarun gudanar da bincike
An yi amfani da hanyar hira da masu
ba da bayanai waɗanda suka haɗa da masu riƙe da muƙaman gargajiya da
makaɗa. A ciki an yi amfani da mutum 6 wajen tattaro muhimman
bayanai. Baya ga haka an yi amfani da ajiyayyun bayanai a kundayen bincike da
litattafai da kuma faya-fayen sauti da na bidiyo da aka taskace waƙoƙi don samun
bayanai da za su taimaka wajen warware matsalar wannan bincike.
5.0 Kaɗe-Kaɗe da waƙoƙin Hausa a bukukuwan
sarautar Gombe
A ƙarƙashin wannan an
duba kaɗe-kaɗe da waƙoƙi da
bushe-bushe na Hausawa da suka yi naso a shagulgula daban-daban na masarautar
Gombe.
5.1 Kaɗe-Kaɗen Hausawa a bukukuwan
fada na masarautar Gombe
Hausawa suna da kayan kiɗa da dama da
nau’o’in makaɗa suke amfani da su a sana’arsu ta kiɗa da waƙa. Da akwai da dama daga cikin waɗannan nau’o’i
na makaɗan Hausa a masarautar Gombe. Ga fitattu daga ciki:
5.1.1 Kiɗan ganga
Bincike ya nuna da ga cikin fitattun
makaɗa da ake da su, da akwai makaɗan ganga waɗanda suke kiɗan ganga. A kiɗan ganga
bayanai sun nuna sarkin kiɗa Barau Sani shi ya fara kiɗan ganga da waƙa tun a zamanin sarki Haruna Umaru Kwairanga. Daga
bisani ɗansa Adamu Barau ya gaje shi. Tare da su a ƙungiyar tasu da akwai Muhammadu Masi Bateri wanda ke
kaɗa gangar guiwa ya dawo kiɗan ganga. Waɗannan makaɗa suna kida da waƙa a lokacin hirar sarki jaance lamorde da ake yi
a duk daren alhamis. Hakazalika suna kiɗa da waƙa a lokacin shagulgula na salla kumtal julde da na naɗin sarauta lamminki. Ga misalin taken da gangar ke
kaɗawa:
“Ga bajimin
dole ya ƙi garaje,
Jan damisa bai karɓi wasa ba”.
5.1.2 Kiɗan turu
Kiɗan a turu a
masarautar Gombe ya samo asali ne daga Ango da ɗan’uwansa waɗanda suka taho
Gombe a zamanin sarki Abba wato Abubakar Umaru. Daga bisani ɗansa mai suna
Muhammadu Ɗanbawa ya gaje shi da kiɗan kotso har ya
zama Ɗanƙwairon Gombe. Makaɗan turu da
kotso a ranar lahdi da kuma lokacin shagulgula na fada suke tasu nishaɗantarwar (Muhammad 2004 p. 24).
Ga tsakure daga waƙoƙin da suke yi
wa Sarki Abba:
“Sai mu yi
Gombe mu zo mu gano sarki,
In mun gan shi
sa’a ta yi,
Ya ɗau zuriya duka
har da bayi,
Ya ɗauke makafi da
guragu,
Bai bar su da
sha’awar komi ba.”
Amshi: “Abba uban Sule mai sulken daga ɗan Umaru,
Bana mun yi
zama mun sha daɗi,
Mun sami fura
mai nono,
Mun ɗebi tuwo mai nama,
Sai ga fa
hatsina na zaman birni,
Goron da ake
kai wa maroƙa,
Ɗan Umaru Habu yab bayar,
Tilas ake gode
wa sarki,
Bai bar mu da
sha’awar komi ba….”
(Hira da Makaɗa Ahmadu).
5.1.3 Kiɗan kotso
Fitaccen makaɗin kotso shi ne
Muhammadu Mai Lili da jama’arsa waɗanda suka fito daga wani ƙauye mai suna Dole a ƙasar Zamfara. Bayanai sun nuna dalilin zuwansa ziyara
ce ya kawo dutsen Bima wanda ke da tarihi matuƙa. A wannan ziyara tasa ce ya yi wa sarki Abba waƙa. Daga nan ne mai martaba sarki ya ba shi masauki
tsawon wata shida bai sallame shi ba. A lokacin ne ya yi wata waƙa da ya yi wa laƙabi ‘baƙo raɓa’ waƙar da ta ba shi damar komawa garinsu bayan sun yi yarjejeniya da sarki a kan zai dawo
Gombe. Bayan ya koma gida ne ya sake shiri tsaf ya dawo Gombe shi da iyalansa
inda ya zauna ƙarƙashin sarki yana kiɗa da waƙa. Ga misalan waƙoƙinsa:
Jagora: “Halin Umaru na nan ba mu san
magani ba,
Amshi: Yana gaba da maza ko can Habu gobe
shiri nai yai.
Jagora: Yana gaba da maza ko can, Habu goma
shiri nai yai,
Halin Umaru na
na nan gurin Abba bai ya da sakewa ba.
Audu kyauta
ikon Allah.
Amshi: Alhaji kyauta sai jabbaru, Allah
kyauta sai Garba,
Sa mutum yai
magana shi ɗai.
Jagora: mu ɗau kunkuru mu
ba shi horo,
Amshi: Mutum in ya datta sai dai ka ji wai
wai.”
Ban da sarki
Abba Mailili ya yi wa Sarki Shehu waƙoƙi. Ga misali:
“Sarki Shehu
kasuwa tai ta cika,
Runhuna suna
hushin banza,
Yau zai ba ka
gobe zai ba ka.
Rakiya/Amshi: kai wanga mai hushin
ba ka yin komai,
Kai wanga mai
hushi ba ka yin komai,
In ka tuna
amshi dai ya fi”.
(Waƙoƙin Mailili a Faifan CD).
Daga bisani Makaɗa Mailili ya ƙaura ya koma fadar Yariman Gombe hakimin Funakaye bisa
umurnin sarki Abba inda ya ci gaba da kiɗa da waƙa. Ga misali daga wata waƙarsa ga Yarima:
Jagora: “Dogon munafuki da gajere,
Ba su aikata
alheri sai sharri,
Ga su zamne ga
fili,
Sai ko ukkunsu
ga shi bahili,
Tun ga duniya
Allah ya nuna ba ya tare da kowa.
Amshi: Ya gyara duniya ɗan Mamman
Ɗan Abba maza jiran wasu maza”
(Hira da Ndotti Yayari).
5.1.4 Kiɗan taushi
Wanda ya fara kiɗan taushi a
masarautar Gombe shi ne Ɗandabu mai
taushi. Yana kiɗa tare da yaransa yana yi wa sarki kiɗa da waƙa a duk daren Lahdi da kuma lokacin biki da shagulgula
na fada. Ga misali daga waƙoƙinsa:
Jagora: “Idan sarki yai ɗamara haka kowa
sai ya yi tunziri.
Amshi: saboda ƙarfin Allah aka zama mai gayyar doki,
Na Umaru ba ka
taruwa mai gayyar doki.
Jagora: ga can sarki ya fito.
Amshi: Abba hauni nai ba ka taruwa mai
gayyar doki na Umaru gurin daga ba ka taruwa.
Jagora: Abba ba a yi ma reni.
Amshi: Ga ka mutum na san ba shi yiwa mai gayyar doki.
(Waƙoƙin Ɗandabu a Faifan Audio
CD)
A fadar Yariman Gombe da ke Bajoga
Gundumar Funakaye kuwa, da akwai Mai Damma mai taushi wanda ke yi wa Yariman
Gombe kiɗa da waƙa a duk daren
jumma’a. Ga misali daga waƙoƙinsa:
Jagora: “Mamman ka wuce hasada,
Ba yalwa jikan
kasaƙi,
Ingarma ya fi ƙuru ga komai,
In ga karaga a ɗauke gado,
In ga taliya ba ya cin wake,
In ga sulei,
ahu ba ta kar na yi ba…”
(Hira da Jaɓɓo Dawaki)
5.1.5 Kiɗan jauje
Kiɗan Jauje ya
samo asali ne tun a lokacin jihadin Bubayero. Wanda ya fara kawo kiɗan jauje
masarautar Gombe shi ne sarkin jauje
Bawa. Daga shi sai sarkin jauje Adamu wanda ya taho Gombe zamanin sarki Haruna
Umaru, ɗansa Muhammadu ya gaje shi ynna da masu masa amshi
kamar Tijani Garba da Bala Isa da sauransu. Makaɗan jauje suna
kiɗansu a duk daren Jumma’a a fada. Ban da waɗannan da akwai
makaɗa Adamu wanda masarautar ke tare da shi tun a Gombe
Abba. Da shi aka yi ƙaura zuwa Nafaɗa zuwa Gombe
Doma. Ɗansa Ibrahim shi ne ya gaje shi a
yanzu a matsayin Tamburan sarrkin Gombe yana da masu masa amshi mutum tara waɗanda suka haɗa da: Alkalin
Tambari da sanƙiran tambari da wazirin tambari da
Muhammadu madakin marafan tambari. Su ma suna tasu hirar sarki duk daren
alhamis suna kiɗa da waƙa suna yabon
sarki.
Shi ma Sarkin Jauje Salihu yana yi
wa Yariman Gombe Muhammadu Mazadu kiɗa da waƙa yana yabon sa. Ga misali:
“Mamman a kau
da kara, a kau da kararuwa,
Guma-gumai sun
kama wuta,
Yarima kai ne
ba su ne ba,
A gidan na Abdu
ke duniya,
Kowa ya zo ya
sha”
(Hira da Ndotti Yayari)
5.1.6 Kiɗan tambari a fadar Mai Martaba
Sarkin Gombe
Kiɗan tambari kiɗa ne wanda ake
yi tun daga jajiberin sallah ƙarama. Zuwa washegari
ranar salla. Akwai makaɗan tambura waɗanda suke kaɗe-kaɗe tun daren
salla har a washegari a je idi a dawo da kuma lokacin karɓar gaisuwar
salla da sarki yake a fadarsa. Al’adar masarautar Gombe ce da washegarin salla,
hakimai da masu riƙe da muƙaman fada da zuriya-zuriya na masarautar sukan zo su
yi wa sarki gaisuwar salla. To, a wannan lokaci fada takan cika da makaɗa irir-iri
daban-daban waɗanda suke gocewa da kiɗa da waƙa. Masu tambura ma wannnn shi ne lokacinsu. Sukan yi
ta kaɗe-kaɗe suna yabon
sarki da kaknninsa da irin bajintar da suka yi a tarihin masarautar. Daga cikin
fitattun makaɗan tambura da akwai: Tambari Kawu na Sani wanda
shi ne makaɗi na farko da ya yi zamani da Sarki Umaru Kwairanga da
‘ya’yansa Sarki Haruna da sarki Abba. Sai Tambari Babagana wanda ya yi zamani
da Sarki Abubakar. ‘ya’yansa daga baya suka ɗauka suna kaɗa tambarin
musamman lokacin shagulgulan salla babba da ƙarama. Kiɗan tambari ya fantsama har a fadar
mai martaba Yeriman Gombe hakimin Funakaye[2].
Makaɗa Audu Tambari shi ya fara kaɗa tambari a
fadar Yerima da ke Bajoga daga baya ‘yan’yan ‘yan’uwansa suka karɓa suka ci gaba
da yi. Ga kaɗan daga cikin waƙar Sarki Shehu
da Ibrahim tamburan sarki ya masa:
“Dole a bi ka
Gombawa Shehu mai raba kaya
Shehu uban
sarakuna dodo
Babban barde
shehu mai raba kaya
Giwa duk naka
ne mahe
Gabasawa naka
ne dodo.”
(Hira da Ardo Chindo Abubakar)
5.1.7 Makaɗan Ruwa
Waɗannan su ne
makaɗa masu amfani da ƙwarya da ruwa a matsayin kayan kiɗa da shi suke
gamawa su samar da kiɗa a waƙoƙinsu. Daga
ciki da akwai Hajiya Fatsuma zabiyar sarki ‘yar Alin Kano. Iyayenta suna kiɗan kotso, amma
ita garwa take amfani da shi da kiɗan ruwa. Tana da ‘yan amshi kuma masu mata kiɗa da suka haɗa da Fanta da
Yarima da Mama da Gambo da Lami da Iya Falmata. Ga kaɗan daga cikin
waƙoƙin da take yi wa sarki Shehu a lokacin bikin salla:
“Ya yi halin
girma ya bi da maza ɗan Garba,
Gagarau ka daɗe makayen gidan
Kwairanga,
Ya yi halin girma
ya buwayi maza ɗan Garba,
Ɗan Garba mai rabo da yawa makayen
gidan Kwairanga,
Giwa lafiya ka
wanye da lafiya raba kaya,
Giwa ɗan Hassan na
Haruna ka wanye lafiya uban Baraya,
Komi girman
barewa watarana a hannun mai dawa za ta kwana”
(GLGIU, Video Cassette Record).
Ban da Hajiya Fatsuma, da akwai
Hajiya Amina Yebe Bafulatana wadda ta fara waƙa kimanin shekara talatin da suka wuce. Tana da ‘yan amshi da
makaɗa da suka haxa da: ‘Yar Kwando da Jummai da Kaltume.
Ga kaɗan daga cikin waƙoƙinta:
“Ya fi tantama
raba musu sa maza ladaf Baba,
Mai sulke da
bindiga ka gama lafiya da Turawa,
Ai ba don
kuwaraba bana sai mun gama da Turawa
Baba uban aku,
uban jimin har da dawaki ba gaba.”
(GLGIU, Video Cassette Record).
Akwai Hajiya Intabe wada ta taho
Gombe ta hannun Garkuwa. Tana yi wasa sarki kiɗa da waƙa tare da ‘yan amshinta a lokacin bukukuwan salla da
wasu shagulgula na fada. Ga kaɗan daga cikin waƙoƙinta da take yi
wa Yeriman Gombe Abdulƙadir Abubakar:
“Damo sarkin haƙuri,
Hankaka mai da ɗan wani naka,
Abdulƙadir mai Gombawa,
Na Shehu mai
Gombawa,
Ɗan Abubakar da Haruna,
Hadari malafar
duniya,
Zauna gari na
Shehu,
Zamaninka ban
ga talauci ba,
Allah ya ja
kwana……”
(Hira da Ɗantima).
5.2 Bushe-Bushen Hausawa a masarautar
Gombe
Ban da kaɗe-kaɗe da akwai bushe-bushe
waɗanda ke amfani da kayan busa na Hausawa a fadar mai martaba
sarki. Daga ciki da akwai:
5.2.1 Masu busa kakaki
Masu kakaki su ne waɗanda suke nishaxantar
da sarki a duk daren Jumma’a da busar
kakaki. Malam Abubakar Adamu shi ne ya fara busa kakaki a masarautar a shekara
ta 1930 zamanin sarki Haruna. Yana busa kakaki da shi da ‘ya’yansa. Ga kaɗan daga cikin
taken da yake busawa:
“Allah babban
sarki,
Sarki magajin
sarki,
Kakanka ma
sarki
Ina maka fata
ka daɗe a duniya
Cikin sarari
babban baƙo
Ga bajimin
sarki
Wasa da dariya
ta fi dukiya
Don dukiya
takan ƙare
Zakin sarakuna
Kada ka sake da
duniya
Kada ka sake da
lahira
Daɗa haƙuri kan haƙuri
Mai haƙuri yana tare da Allah”
(GLGIU, Video Cassette Record).
5.2.2 Masu busa algaita
Waxanda suke a sahun farko cikin
masu busa algaita shi ne Adamu sarkiin algaita. Bayanai sun nuna shi ne ya fara
zuwa da algaita a zamanin Sarki Haruna. ‘Ya’yansa Haruna Baƙoji da Sule suka gaje shi suna busa algaita a fada a
ranar jumma’a. Busar tana tafiya da kiɗa, in busa ta canja, sai kiƙa ma ta canja. Ga misali daga taken da suke busawa:
“Ga bajimin
dole,
Amma ya ƙi garaje
Ga shi a
sarari,
Hattara cigarin
raba kaya”.
(Hira da Arɗo Chindo
Abubakar).
6.0 Sakamakon bincike
Wannan bincike ya nuna yadda aka
samu malalar makaɗan Hausa a ƙasar Gombe
musamman ma makaɗan sarauta. Bincike ya nuna yadda aka samu nau’i na
makaɗan Hausa da suka haɗa da makaɗan ganga da na
kotso da na tabshi da na turu da na ruwa. Ban da waɗannan an ga
masu bushe-bushe waɗanda suka darara a masarautar da
nasu kayan bushe-bushen da suka haɗa da kakaki da algaita. Akwai alamu
da ke nuna Fulani ba su san waɗannan nau’o’in kaɗe-kaɗe ba sai da
suka haɗu da makaɗan Hausa. Kafin zamanin Muhammadu
Kwairanga, masarautar Gombe
ba ta san waɗannan kaɗe-kaɗe ba, sai a
lokacin da su makaɗan suka riƙa kwararowa daga yankunan ƙasar Hausa zuwa Gombe. Binciken ya nuna yawancin waɗannan makaɗa Huasawa sun
fito ne daga ƙasar Kano Zamfara da Katsina.
Hakazalika makaɗa ne da suka ƙunshi maza da
mata waɗanda suka taho Gombe a mabambantan lokuta. Wasu ma
daga cikinsu a nan iyaye suka haife su suka tashi suka gaji kiɗa da waƙa a hannun iyayen nasu. Su waɗannan ba su san
ko’ina ba ban da Gombe. Wannan na nuna yadda makaɗan Hausa suka
malala a ƙasar Gombe kuma suka yi shuhura da
sana’arsu ta kiɗa da waƙa. A yau da
makaɗa da dama da ke ganin Gombe gida ne saboda nan suka
tashi kuma suke ci gaba da raya gadon gidajensu da suka samu daga iyaye da kakanninsu.
Kuma da su ne ake daɗa samun yalwar al’ummar nan da aka
fi sani da suna Hausa/Fulani.
7.0 Kammalawa
Wannan bincike ya yi nazarin makaɗa da mawaƙa da suke warwatse a ƙasar Gombe msuamman makaɗan fada. An
kawo nau’o’in makaɗa da aka yi bayaninsu dangane da
irin kayan kiɗan da suke amfani da su a waƙoƙinsu. Daga ciki,
an yi bayanin makaɗa da masu bushe-bushe. An kuma kawo
‘yan misalai waɗanda suka ƙunshi tsakure
daga waƙoƙin nasu. Binciken har wa yau ya yi bayani a taƙaice wuraren da suka fito da silar zuwansu Gombe da
yadda suka tare suna kiɗa da waƙa a Gombe. Hakazalika an ga yadda wasu daga cikin makaɗan ‘ya’ya ne da
jikoki na makaɗan farko da suka taho waɗanda Gombe ta
zama musu gida kuma suke rayuwa suna kiɗa da waƙa. Waɗannan makaɗa saboda
auratayya da Fulani da suka yi yanzu sun narke sun zama al’ummar na da ake kira
da Hausa/Fulani.
Manazarta
1.
Abdullahi, A. (2019). “Nazarin Waƙoƙin Malam Muhammadu Mailili na Marigayi Sarkin Gombe
Alhaji Shehu Usman Abubakar”. Kundin Digiri na Ɗaya Wanda Aka Gabatar a Sashen Koyar da Harsuna,
Jami’ar Tarayya ta Kashere, Jihar Gombe.
2.
Gombe Local Government Information Unit. Gombe Eid El
Fitr Celebration Record (1990). VHS Cassette.
3.
Gombe Local Government Information Unit. Gombe Eid El
Fitr Celebration Record. (1994). VHS Cassette.
4.
Gombe Local Government Information Unit. Gombe Eid El
Fitr Celebration Record. (1996). VHS Cassette.
5.
Lamido, I. (2012). “Tasirin Adabin Hausa a Al’adun Fulanin Gombe”.
Kundin Digiri na Biyu Wanda Aka Gabatar a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Bayero, Kano.
6.
Muhammad, Y.J. (2004). “Nazarin Waƙoƙin Ɗanbawa Ɗanqwairon Gombe”. Kundin Digiri na Ɗaya Wanda Aka Gabatar a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato.
7.
Tukur, A. (2003). “History of Gombe”. Unpublished History of Gombe
Emirate. Waƙoƙin Wasu Makaɗan Fada a
faya-fayen Audio CD.
[1] Bubayero ya raɗa
wa wannan wuri suna Gombe daga sunan wata bishiya da Bolawa mazauna ƙauyukan kewaye suke kira da yarensu ‘Gombe Memosiri’.
Amma wasu sun ce suna Gombe daga sunan asalin garin da kakanninsa suka taso a ƙasar Mali ne, wato Dagombe. An ci gaba da kiran wurin
da suna Gombe Abba bayan rasuwarsa wato Gomben Abba. Abba taƙaitaccen suna ne da ke nufin
Abubakar wanda shi ne cikakken
sunan Bubayero. Wato Gomben da Abba ya kafa.
[2] Yeriman Gombe
Muhammadu Kwairanga ya zama sarkin yanka bayan da aka xaga gundumar Funakaye ta
koma masarauta a shekara ta 2001.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.