Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Zama Da Mijin Da Ba Ya Sallah

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum malam tanbayana shi ne ina da miji yanzu a haka 'ya'yanmu 3 amma baya sallah. Ba yadda banyi ba idan ya fara sai ya bari amma sallar Jumaa ba ya wuce shi yanzu a haka mahaifina ya ce zai yi karar sa ya sake ni tun da baya Sallah to malam in kashe auren ne ko yaya?

𝐀𝐌𝐒𝐀👇

Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Tabbas idan har an yi masa nasiha amma bai ji ba, to bai halatta ki cigaba da zama amatsayin matarsa ba. Domin kuwa akwai sashen Malaman Musulunci da ke ganin cewa ko da sallah guda ce mutum ya barta da gangan to ya kafirta, balle kuma shi Mijin naki wanda ba ya yin dukkan sallolin ma in ban da Juma'a.

Abin lura a nan shi ne tun ranar da aka ɗaura aurenku aka damƙa masa amanar ciyar da ke da tufatar dake, da kuma koyar da ke addini. To Mutumin da shi kansa ba ya yin sallah, ta yaya zai koyar da ke addini?. Ta yaya zai koya ma 'ya'yanku kulawa da muhimmancin sallah? Cigaba da zama da shi awannan halin zai iya kaiwa zuwa ga lalacewar taki tarbiyyar ma. Kuma zai wahala bai lalata tarbiyyar yaran naku ba.

Manzon Allah ya ce: "SALLAH ITA CE GINSHIKIN ADDINI. WANDA YA TSAYAR DA ITA, TO HAKIKA YA TSAYAR DA ADDINI. WANDA KUMA YA RUSHETA TO HAKIKA YA RUSA ADDINI". Kuma ya fa'da a cikin wani hadisin wanda Muslim ya ruwaito: "TSAKANIN MUTUM DA TSAKANIN SHIRKA DA KAFIRCI shi ne BARIN YIN SALLAH".

WALLAHU A'ALAM.

Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/JLojawdOWYsEOeSHZMNdjf

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments