Ticker

6/recent/ticker-posts

Yanayin Tsaro A Garin Gusau

Wannan bincike mai taken "Yanayin Tsaro A Garin Gusau" ya zo da babuka biyar. A babi na ɗaya an yi gabatarwa ne a cikin wannan bincike da manufar bincike da hasashen bincike da farfajiyar bincike tare da kawo matsalolin da aka fuskanta a wannan bincike da muhimmancin da kuma hanyoyin da aka bi wajan gudanar da wannan bincike daga ƙarshe aka zo da naɗewa. Babi na biyu kuwa yana ƙunshe da bitar ayyukan da suka gabata da hujjar cigaba da bincike daga ƙarshe aka zo da naɗewa. A bani NA uku an kawo fashin baƙi a kan ma'anonin kalmomin da suka haɗu suka gina taken bincike waɗanda suka haɗa da ma'anar yanayi da ma'anar tsaro da ire-iren tsaro da ma'anar gari da kuma ma'anar kalmar Gusau daga ƙarshe aka zo da naɗewa. A cikin babi na huɗu kuwa an zo da bayanai a kan gundarin taken bincike, a inda aka kawo bayani game da yanayin Tsaro na gargajiya da tsokaci a kan ganuwar Gusau da ƙofofinta da kuma makaman da ake amfani da su na gargajiya da yanayin tsaro na zamani da irin kayan da ake amfani da su domin, kula da da yanayin tsaro na Gusau da bayani a kan su wa ye 'yanta'adda da ire-iren 'yanta'adda da ayyukan 'yanta'adda an zo da bayani a kan abubuwan da ke haifar da ta'addanci da kalmomin 'yanta'adda da illoli da ayyukan ta'addanci ya haifar a garin Gusau da matsalolin da tsaro yake fuskanta wajen al'umma da jami'an tsaro da rawa da jama'a da hukuma ke takawa wajen kawar da ayyukan ta'addanci daga ƙarshe wannan babi ya zo da muhimmancin tsaro a garin Gusau da naɗewa. Babi na biyar ya ƙunshi sakamakon bincike da ta'arifin wasu kalmomi daga ƙarshe aka zo da da shawarwari da naɗewa. Wannan bincike ya ta'allaƙa ne a kan yadda aka gudanar da "Yanayin Tsaro A Cikin Garin Gusau.

Yana Yin Tsaro A Garin Gusau

NA

MAHADI MUSTAPHA

Yana Yin Tsaro A Garin Gusau

SADAUKARWA

Na sadaukar da wannan aiki mai taken “Yanayin tsaro a garin Gusauga Mahaifana, MalamAlmustapha Abdullahi Ajiya Sallau da Mahaifiyata, Hajiya Zara'u Muhammad Nalado, da Malama Lauratu Usman, waɗanda suka haife ni, sannan suka ba ni tarbiyya da cikakkiyar kulawa domin ganin na zama mutumin ƙwarai dangane da harkokin rayuwata a kodayaushe.

Haka kuma, na sadaukar da shi ga dukkan malamaina, na makarantar Firamare da Sakandare da Difiloma da kumaJami’a.

GODIYA

Ina mai godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki Mai kowa Mai komai Mai rahama Mai jin ƙai zuwa ga bayinSa. Tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad (S.A.W.) da sahabbansa da zuri’arsa da dukkan waɗanda suka bi shi har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka, ina miƙa godiyata da jinjina zuwa ga mahaifina Malam Almustapha Abdullahi Ajiya Sallau, bisa irin jajircewar da ya yi na ganin cewa na samu ilimin addini da kuma na zamani a rayuwata. Kuma ina ƙara gode masa a kan irin addu’o’in da yakan yi mani dare da rana. Ina mai addu’ar Allah (SWT), ya saka masa da mafificiyar aljanna (maɗaukakiya), amin. Haka kuma, ina mai miƙa godiya da jinjina zuwa ga mahaifiyata dangane da irin namijin ƙoƙarin da takan nuna a kaina na ganin cigaban rayuwata har zuwa ranar da rai zai yi halinsa.

Haka kuma, ina miƙa godiya da jinjina ga Malamina, wanda kuma shi ne ya duba wannan aiki nawa, watau Dr. Rabi'u Adamu Bakura, bisa jajircewa da ƙoƙarin ganin ya ɗora ni a kan hanya don samun nasarar kammaluwar wannan aiki nawa. Godiya ta musamman ga Dr. Bakura, Allah Ya biya shi kuma Ya saka masa da Aljanna a ranar gobe ƙiyama, amin.

Bugu da ƙari, ina farin cikin miƙa godiyata ta musamman ga Malamaina waɗanda suka yi mini riƙo na amana da mutuntawa tare da ba ni shawarwari a kan harkokin karatuna domin ganin na samu nasara. Waɗannan malamai sun haɗa da: Farfesa A.M. Bunza, Farfesa M. Tsoho Yakawada, Farfesa Aliyu Musa, Farfesa Balarabe A., Farfesa M. L. Amin, Dr. Malumfashi, Dr. R.M. Tahir, Dr. Nazir I. Abbas, Dr. Musa Fadama, Malam Isa S. Fada, Malam Musa Zaria, Malam Aliyu Rabi’u Ɗangulbi, Malama Halima Kurawa, Malam Abu-Ubaida Sani, Malam M. Arabi da sauransu. Ina roƙon Allah  ya saka masu da mafificin alkhairi, amin.

Har ila yau, ina miƙa godiyata ta musamman zuwa ga yayyena da ƙannena da kuma abokaina, bisa ga irin gudummuwar da sukan ba ni da kuma addu’o’in da sukan yi mani, kamar su; yaya Anas Almustapha Ajiya, Abdul'aziz Almustapha Ajiya, Anty Hafsat Almustapha Ajiya, Anty Nafisa Almustapha, Anty Kafiya Almustapha Ajiya, Anty Samira Almustapha Ajiya, da ma waɗanda ban samu damar ambaton sunayensu ba, kuma da fatan za su yi haƙuri da ni.

Sannan kuma, ina miƙa godiya zuwa ga ƙannena da abokan karatuna kamar su; Saddam Almustapha Ajiya, Gaddafi Almustapha Ajiya, Ibrahim Almustapha Ajiya Usama Almustapha Ajiya, Aliyu Almustapha Ajiya, Abbas Muhammad Hussaini, Sadam Yusuf, Ibrahim Garba Total, Amir Tijjani, Umar Muhammad, Yusuf Muhammad Kwalli, Abdulrashi Bala, Abdulrashid Isma'il, Makiyu Balarabe, Jamilu Officer, Munnir Sani Mai Fulla, Abdulmalik Mai Biredi da sauransu. Haka kuma, ina mai godiya ga abokan zamana Yahaya Sani Deemama, Yasir Sani Moyi, Aminu Aliyu Ɗanmaituwo, Zaidu Tukur Sarkin Rafi Mubarak Hamisu Pepe, Bilyaminu Rabi'u Buzu,  da sauransu. Allah ya saka masu da alkhairi kuma Allah ya albarkaci karatu, amin.

 

 

 

BABI NA ƊAYA

1.0 GABATARWA

A cikin  wannan bincike za mu yi nazari ne a kan yanayin tsaro da ma'anar tsaro a garin Gusau da kuma rabe-raben tsaro, da irin rawar da jami'an tsaro da al'umma suke takawa a kan sha'anin tsaro. Haka kuma wannan bincike zai yi ƙoƙarin kawo ma'anar ta'addanci, da kuma illoli da matakan kawar da su a garin Gusau.

A cikin wannan bincike za a yi nazari ne a kan yanayin tsaro a cikin garin garin Gusau.

Haka kuma za a tsara wannan aiki a kan babi-babi, a babi na ɗaya za a yi bayani a kan manufar bincike da, hasashen bincike da, farfajiyar bincike da matsalolin bincike da, muhimmancin bincike da, hanyoyin gudanar da bincike, daga ƙarshe kuma ya zo da naɗewa.

1.1 MANUFAR BINCIKE

Duk wani abin da ɗan Adam ya ƙuduri ya aiwatar a rayuwarsa, za a tarar cewa, lallai, akwai wata manufa ta musamman da ta wajabta masa aiwatar da wannan abu. Masu iya magana kan ce 'kowane allazi da nasa amanu, idan muka lura da wannan zance za mu fahimci cewa babu wani bincike da za a aiwatar ba tare da manufar gudanar da shi ba. Don haka manufofin gudanar da wannan bincike shi ne domin samun takardar shaidar kammala karatun digirin farko. Haka kuma fito da yadda yanayin tsaro yake a garin Gusau, tare da nuna muhimmancin tsaro musamman a wajen al'umma da kuma wanzar da zaman lafiya a cikin al'ummar garin Gusau, domin su fahimci muhimmancin tsaro, tare da gano irin hikima da fasaha da dabaru da ke ƙunshe a cikin lamurran tsaro.

1.2 HASASHEN BINCIKE

Hasashen da ake yi a cikin wannan bincike sun haɗa da:

1. Tsaro na ɗaya daga cikin abubuwa mafi muhimmanci ga rayuwar al'umma.

2. Tsaro na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatuwar samun zaman lafiya mai ɗorewa a tsakanin al'umma.

1.3 FARFAJIYAR BINCIKE

Kafin a shiga bayanin farfajiyar bincike, yana daga cikin ƙa'ida ta bincike, ɗalibin bincike ya yi nazari a kan abin da yake kusa da shi, wato muhalli ko farfajiyar da yake zaune, domin samun ingantattun bayanai game da abin da yake bincike.

Bari mu ga ma'anar farfajiyar bincike da muhalli:

Wikepedia (2019) an bayyana muhallin bincike da cewa, shi ne wuri na musamman wanda aka gudanar da bincike a kan wani abu da ke da mazauni a wurin, kamar al'umma, abubuwa da sauransu, ta hanyar littattafai, da mukalu, da kuma tarukan kara wa juna sani, domin samun wani sakamako.

Wannan bincike an gudanar da shi ne a garin Gusau babban birnin jihar Zamfara, za a yi nazari a kan yanayin tsaro a cikin garin Gusau, inda za a gana da jami'an tsaron domin jin yadda suke gudanar da aikin su.

1.4 MATSALOLIN BINCIKE

Kamar kowane irin al'amari na rayuwa, a kan iya haɗuwa da wata mastala ko cikas, wannan aiki ya haɗu da barazana ta hanyoyi da dama, kamar haka.

1. Rashin samun wadatattun littafai waɗanda suka yi magana a kan lamarin tsaro, wanda hakan ya tilasta aka shiga neman kundaye, da muƙalu, da kuma hira da ɗaiɗaikun mutane.

2. Bayan haka kuma, akwai matsalar rashin samun haɗin kan wasu al'ummomi da lamarin ya shafa.

3. Daga ƙarshe kuma akwai matsalar da aka fuskanta, ta rashin kuɗi masu gidan rana, domin gudanar da aiki a cikin lokaci.

1.5 MUHIMMANCIN BINCIKE

Bincike shi ne gano wani abu wanda, da ba a sani ba, ko ƙari ga wani abu wanda aka sani domin bayar da gudummuwa ko warware wata matsala da ta zama damuwa ga wata al'umma (Bunza 2017).

Daga wannan za a iya cewa muhimmanci wannan bincike ga rayuwar al'umma baki ɗaya, ya haɗa da abubuwa kamar haka:

1. Kasancewarsa bincike na farko da aka gudunar a kan sha'anin tsaro a garin Gusau wanda zai taimaka wa al'umma da 'yan uwana ɗalibai manazarta domin samun sauƙin fahimtar yadda sha'anin tsaro yake ba tare da shan wata wahala ba.

Wannan zai sa su san irin rawar da za su taka wajen bayar da tasu gudummawa don tabbatar da nasarar samun ingantaccen tsaro a tsakanin al'umma.

2. Wani muhimmanci kuma da wannan bincike zai kawo shi ne ƙara samun haɗin kai ga al'umma, domin samun zaman lafiya a tsakanin al'umma. Domin Hausawa na cewa: Hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinka. Shi kuwa lamarin tsaro abu ne da ke buƙatar haɗin kan kowa da kowa.

3. Wannan aiki zai taimaka wa ɗalibai da manazarta, domin samun damar ɗora nasu bincike a daidai inda na tsaya.

1.6 HANYOYIN GUDANAR DA BINCIKE

Da yake ana nazari ne a kan abin da ya shafi yanayin tsaro, hanyoyin da ake tsammanin sun fi dacewa a bi don cimma ƙudurin wannan bincike sun haɗa da:

1. Da farko an fara tattara bayanai daga littatafan da aka wallafa da waɗanda aka samu a ɗakunan karatu daban-daban.

2. Nazarin kundayen binciken da aka gudanar a makarantu da Jami'o'i daban-daban da kuma muƙalu da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani daban-daban da suka danganci duk wani nazari da aka aiwatar game da yanayin tsaro.

Haka kuma, an yi amfani da babban ɗakin karatu na Jama'ar Tarayya Gusau.

Da kuma ɗakin karatu na Kwalejin horas da malamai na Gwamnatin Tarayya da ke Gusau Jihar Zamfara (F.C.E.T Gusau).

Haka kuma akwai ɗakin karatu na Kwalejin Ilimi da Fasaha (Zacas Gusau). Domin samun nasarar wannan bincike.

Haka kuma za a tattauna da dangogin masu sana'o'i daban-daban da suka haɗa da:

1. Dillalai kamar na: Dabbobi, babura, kekuna, motoci, filaye

2. Kungiyar 'yan kasuwa

3. Kungiyar direbobi

4. Kungiyar maƙera

5. Hukumar jami'an tsaro

6. Kungiyar 'yansakai

7. Kungiyar 'yan banga

8. Kungiyar mahauta

9. Daga ƙarshe kuma za a tattauna da tsofaffin da suka san jiya da yau, da sarakuna, da hakinmai da masu unguwanni, da sauransu.

Haka kuma an tsara zantawa da jami'an tsaro da ke zaune a garin Gusau, domin fahimtar yadda ake aiwatar da aikin tsaro jiya da yau da kuma dalilin da ke haifar da haka.

Bayan wannan za a zanta da 'yan jarida da ke zaune a cikin garin Gusau, da kuma manyan malamai, musamman na cikin wannan gari, domin samun sakamakon bincike mai armashi da gamsarwa.

Bugu da ƙari, an shirya ziyartar wasu manyan jami'an tsaro da ke a cikin garin Gusau, domin samun bayanai yadda suke gudanar da aikin nasu.

Tare da matsalolin da ke addabar su da hanyoyin magance matsalolin, domin samun nasarar tabbatar da tsaro a cikin garin Gusau da jihar mu da ƙasarmu Najeriya baki ɗaya.

1.7 NAƊEWA

Daga ƙarshe kuma wannan babin gabatarwa ce game da wannan aikin binciki, domin haskakawa mai karatu, wanda ya zo da gabatarwa, da manufar bincike, da hasashen bincike, da farfajiyar bincike, da matsalolin da suka kawo tarnaƙi game da bincike, da muhimmancin bincike, da hanyoyin gudanar da bincike, daga ƙarshe kuma wannan babin ya zo da naɗewa.

BABI NA BIYU

BITAR AYYUKAN DA SUKA GABATA

2.0 GABATARWA

Duk da irin yadda ake ganin cewa ba a yi wani abin da ya taka kara ya karya dangane da irin wannan bincike na yanayin tsaro, ba za a rasa wasu abubuwa da suka yi kama da hakan ba, musamman idan aka yi la'akari da irin binciken da masana da ɗalibai suka gabatar a kan lamarin tsaro. Wannan fasali zai waiwayi ɗan abin da ya samu, domin mu ga yadda yanayin ya kasance.

Wannan babi zai yi bayani ne a kan bitar ayyukan da suka gabata, waɗanda suka haɗa da bitar littattafan da aka wallafa, da kundayen bincike, da kuma muƙalu da mujallu, da aka gabatar a wurare daban-daban masu alaƙa da wannan aiki.

2.1 BITAR AYYUKAN DA SUKA GABATA

Masu azancin magana kan ce "Waiwaye adon tafiya." Haka yake, domin masana da dama sun gudanar da bincike mabambanta dangane da sha'anin tsaro, amma ba a taɓa aiwatar da wani bincike mai take irin wannan ba.

Babu shakka ya zama wajibi ga duk wanda zai aiwatar da bincike, ya tsaya ya dubi ayyukan magabata domin samun haske game da yadda suka gabatar da nasu ayyukan. Domin ta yin haka ne za a fahimci inda aka kwana da kuma inda za a tashi.

Wannan ne ya tilasta a waiwayi aikace-aikacen ayyukan da masana suka aiwatar domin samun ƙarin haske. Daga cikin aikace-aikacen da aka gudanar waɗanda aka yi bitar su, sun haɗa da: Bugaggun littattafai, da kuma muƙalu, tare da kundayen bincike, kamar yadda za mu gani ɗaya bayan ɗaya.

2.1.1 WALLAFAFFUN LITTATTAFAI

Masana da dama sun yi rubuce-rubuce, musamman akan harkar tsaro, inda suka tofa albarkacin bakinsu, musamman a kan ma'anar tsaro da rabe-raben tsaro da muhimmancin tsaro ga al'umma, da kuma gudummuwar da al'umma ke bayarwa a kan harkar tsaro, daga cikin waɗannan masana akwai.

Nalado A.M. (Babu shekara). Daga cikin wannan littafi mai suna Kano state jiya da yau an yi (1864-1968) an yi bayanin yadda yaƙin Damagaram ya gudana da dabaru iri-iri domin tabbatar da tsaron al'ummarsa tare da kariyar mutuncinsu.

Haka kuma daga cikin wannan littafi an nuna yadda sarakuna suke shirya dubarun zuwa yaƙi, da yadda suke ƙoƙarin bayar da kariya ga jama'arsu.

Gusau M.B. Da Gusau M.S (2012). A cikin littafinsu mai take: Gusau ta malam Sambo sun kawo bayanin sunan Gusau da kirarinta, da kuma asali da ma'anar kalmar Gusau. Haka kuma an yi bayanin kafuwar Gusau da haɓakar ta wanda ya ƙunshi tarihin garin Gusau da mutanenta na farko da bunƙasarta da tsarin sarauta da mulki, da kuma tarihin rayuwar sarakuna tun daga jiya har zuwa yau. Haka an kawo bayanai game da ganuwar garin Gusau wadda ta kasance wani ginshiƙi na samar da tsaro a da.

Shi kuwa Muhammad Isa Talata Mafara (1999).A cikin littafinsa mai taken: "Daular Usmaniyya" ya bayyana irin hanyoyin da sarakuna ke bi domin kare kansu daga abokan gaba, da yadda suke samar da kayan zuwa yaƙi da kuma na kariyar mutuncinsu; Wannan littafi yana ɗauke da bayani a kan yaƙe-yaƙen da Shehu Usmanu danfodiyo ya yi.

Shi kuwa Aliyu M.Bunza (2006). A cikin littafinsa mai suna "Gadon feɗe al'ada" Ya kawo bayani akan "Tsaro da siyasa" Ya ce daga cikin manufar al'ada a rayuwar masu ita akwai samun tsaron kai da kaya, da gudanar da siyasar rayuwa ba cikin takurawa ba.

Ya kuma bayyana cewa, a can da ƙasar Hausa na fuskantar barazanar maƙiya na ciki da na waje, don haka ne Bahaushe ya ƙirƙiro tsaro ta hanyar tsafe-tsafen tsare kansa, da garinsa, da lafiyarsa, da kuma dukiyarsa.

Shi kuma, Gusau A.R (2014) A cikin littafinsa mai taken "Mai dubun nasara". Ya kawo bayani a kan tarihin Gusau a taƙaice, haka kuma ya kawo bayanin jerin sarakunan Gusau, da kuma bayani a kan rabe-raben tsaro inda ya nuna akwai tsaro irin daban-daban kamar haka:

1. Tsaro na dukiya

2. Tsaro na addini

3. Tsaro na rayuka

4. Tsaro na shuwagabanni

Masanin ya ƙara da cewa, tsaro abu ne da sarakuna ya kamata su kula da shi, su ma talakawa ba za a barsu a baya ba, domin suna taka rawa wajen ba da gudunmawa ga tsaro.

Maryam, M. Na Inna. (Babu shekara). A cikin littafinta mai suna "Tarbiyyar matasa a Musulunci" daga cikin wannan littafi ta yi bayanin abubuwan da ke kawo taɓarɓarewar tarbiyya da kuma hanyoyin samar da zaman lafiya, daga cikin wannan littafi ta kawo wane ne ɗan ta'adda da kuma bayani a kan hanyoyin magance wannan matsala.

Haka kuma. Waya (2000). A cikin littafinta mai suna "Kano da Masarautarta Jiya Da Yau", ta yi bayani akan asalin masarautar Kano da kuma hasashe akan mazaunan farko, da wanzuwar mutane da kafuwar mazauni a Kano, haka kuma ta kawo bayani akan hanyoyin kariyar kai.

2.1.2 KUNDAYEN BINCIKE

Hibbatullahi M. Da wasu (2014). Sun yi nazari ne akan matsalolin da ke haifar da ta'addanci a unguwar Sabon Fegi Gusau wanda suka gabatar a Sashen Hausa Tsangayar Harsuna Kwalejin Ilimi da Ƙere-Ƙere ta Gwamnatin Tarayya da ke Gusau Jihar Zamfara. Sun kawo ma'anar kalmar ta'addanci da kuma waɗanda ke yin ta'addanci da abubuwan da ke haifar da ta'addanci, da matsalolin da ta'addanci yake haifarwa. Haka kuma sun kawo hanyoyin yaƙi da ta'addanci, daga ƙarshe kuma sun zo da bayanin hanyoyin da ya kamata abi a samar da jami'an tsaro donmagance matsalar ta'addanci.

Yusuf Wada Da wasu (2014) a kundin bincikensu mai taken "Yanayin Tsaro A jiya Da Yau A Garin Dandume" Da suka gabatar a sashen Turanci, da Hausa da Islama kwalejin kimiyya da fasaha "Zacas Gusau jihar Zamfara" Domin cike sharaɗin samun Takardar "Diploma" Sun yi bayani akan ma'anar tsaro, ire-iren tsaro da kuma yanayin tsaro a garin Ɗandume, da kayayyakin da ake gudanar da tsaro a garin Dandume, da kuma bayani a kan matsalolin tsaro, da ƙarshe kuma sun kawo bayani akan muhimmancin tsaro a garin Ɗandume.

2.1.3 MUƘALU DA MUJALLU

Muƙalu da mujallu su ne takardu masu ɗauke da bincike na ilimi, mafi akasarin waɗannan ana gabatar da su ne a lokuttan tarurrukan ƙara wa juna sani. Game da harkar tsaro, a matakai daban-daban an gabatar da muƙalun da dama da suka haɗa da:

Shekarau M.I (2007). A cikin wata muƙalarsa da ya gabatar mai taken "Role of Government In Security of Life and Property" a cikin wannan muƙala an yi bayanin cewa a ƙalla akwai dubban mutane da suke yaƙi a tsakanin 'yan ta'adda, haka kuma daga cikin wannan muƙala an kawo bayanin inda Alh. Yusuf Maitama Sule: Ya ce a cikin harkar tsaro akwai rashin ma'ana, ita kuma siyasa an gurɓata ta da cece kuce, shi kuma tattalin arziki an gurɓata shi da cin hanci, haka kuma al'umma an gurɓata su da rashin kyakkyawan ɗabi'u, haka kuma an yi bayanin ta'addanci a cikin lokaci, daga ƙarshe kuma an yi bayanin tsaro a ɓangaren musulunci.

Kadaura journal of Hausa multi disciplinary studies. Vol 1. No 5 September(2019). Department of Nigerian Languages and Linguistics Kaduna State University, Kaduna. A cikin wannan mujallar sun kawo bayani akan ma'anar tsaro da kuma bayani a kan kafuwar tsarin shugabanci na gari-gari, haka kuma sun kawo bayanin yadda za a kare al'umma daga miyagun mutane, da yadda suke samar da kayayyakin yaƙe-yaƙe, da kuma cusa tarbiyya ta hanyar tsaro ga yara, haka kuma daga ƙarshe sun nuna yadda ake samar da jami'an tsaro.

Farfesa M.L. Mayanci (2019) a cikin wata muƙalarsa mai taken: "Converting the Menace of Insecurity in Zamfara State Within 100 days Governor Matawalle". Daga cikin wannan muƙala an yi bayanin mene ne tsaro, inda ya ce tsaro wani babban haƙƙine ga kowace ƙasa baki ɗaya. Ya kuma yi bayanin cewa shi tsaro ya ƙunshi tsaro na mutane da tsaro na dukiya, da tsaro na muhalli, da kuma tsaro na jindaɗin rayuwa. Haka kuma ya bayyana cewa, a cikin kundin tsarin mulki na ƙasa, na shekarar (1999) ya nuna tsaro da walwala ta mutane ya kamata ya zamo mataki na farko da gwamnati za ta yi aiki akai, wato kulawa da shi, domin yawan matsaloli na rashin tsaro da suke faruwa a cikin sassa daban-daban na Najeriya shi ya sa aka kirata da ƙasa marar tsaro, haka kuma an yi yinƙuri daga sassa daban-daban na gwamnati, don a samu a kawar da matsalar rashin tsaro.

1. Tsaron kai

2. Tsaron kaya

3. Tsaron kare martabar gari

4. Tsaro na "Kura rame"

5. Tsaro na ganuwa.

2.2 HUJJAR CIGABA DA BINCIKE

Idan muka yi la'akari da bayanan da suka gabata, a inda muka yi tankaɗe da rairaye a kan nazarce-nazarcen da aka aiwatar a ƙoƙarin muna kwatanta ƙudurin wannan nazari da abin da magabata a fagen nazari suka aiwatar, za a luracewa har zuwa yanzu ba a ci karo dawani bincike da aka gudanar dangane da yanayin tsaro. A garin Gusau ba. Wanda ke da alaƙa da nawa shi ne na Wada (2014). Shima ya karkatane a garin Ɗandume. Kowa ne al'amari a rayuwa yana buƙatar hujja a wajen cigaba da aiwatardashi, wannan binciken da ake kan gudanarwa yana da matukar muhimmanci, domin a iya bincikena ban yi karo da wani bincike ba mai irin wannan taken aikin da nake gudanarwa sai dai mai alaƙa da shi, saboda haka cigaba da wannan binciken zai taimakawa masu sha'awar bincike irin wannan, wajen sauƙin fahimtar yanayin tsaro a garin Gusau.

2.3 NAƊEWA

Wannan babin ya fara ne da gabatarwa tare da bayyana irin ayyukan da aka yi bita a binciken da ya gabata, domin waiwaye kan ayyuka masu ƙarin haske, ko kuma masu shige da irin wannan aiki da suka haɗa da bugaggun littattafai masu alaƙa da wannan aiki, da kuma muƙalu, da mujallu, da kuma kundayen bincike, duk waɗannan ayyuka babu mai take guda da wannan aiki, sai dai alaƙa.

 


BABI NA UKKU

FASHIN BAƘI A KAN MA'ANONI DA SUKA SHAFI TAKEN BINCIKE

GABATARWA

Wannan babi zai yi bayani a kan ma'anar yanayi, da kuma ma'anar tsaro da ire-iren tsaro, da ma'anar gari, haka kuma wannan babi zai kawo ma'anar kalmar Gusau da ƙarshe kuma wannan babin ya zo da naɗewa.

MA'ANAR YANAYI

Bayaro (2006 : 478) ya bayyana yanayi da cewa hali irin wanda ake ciki, kamar na damina ko sanyi, ko zafi. Haka kuma ya ƙara fassara yanayi da cewa hali irin wanda mutum ke ciki, ko a ce yana fushi, ko farin ciki, misali kamar yadda fuskarsa ya nuna wanda ake iya gani a wannan lokaci.

Kamar yadda shi ma Ayuba T Abubakar (2015 : 496) ya bayyana yanayi da cewa, hukuncin iska, ko sanyi, ko ɗumi, ko damina, ko rani, ko da fannin duniya ya shiga ko ya canza daga wani zamani zuwa wani.

 

 

MA'ANAR TSARO

Ayuba T Abubakar (2015: 472) ya bayyana kalmar tsaro da cewa, suna, namiji, wato kare jama'a daga abin da zai cuce su. Ma'aikatan tsaro masu aikin tsare lafiya da dukiyar mutane, haka kuma akwai tsaron ƙasa, kare ƙasa daga illa ko abokan gaba, ko kuma kare kai ko, ƙaddara.

Bunza A M (2006 : 99) ya bayyana tsaro da siyasa na daga cikin manufar al'adar rayuwar masu ita, akwai samun tsaron kai da kaya da gudanar da siyasar rayuwa, ba cikin takurawa ba. A can da, ƙasar Hausa na fuskantar barazanar maƙiya na ciki da waje. Dalili da haka ne Bahaushe ya ƙirƙiro tsafe-tsafen tsare kansa, da garinsa, da lafiyarsa, da dukiyarsa.

Binta Musa Hassan (2019 : 176) ta ce, Kalmar tsaro na nufin yin gadi ko kare ko kula ko kiyaye wani ko wasu muhimman abubuwa daga taɓuwa da za ta kawo illa ga abin. Ko kuma ajiye ko riƙe ko kange ko kulle  wani abu wato dai kariya "CNHN", (2006). Haka kuma kalmar na iya ɗaukar ma'anar kula ko kare duk farfajiyar ƙasa da iyakokinta da arzikinta da kuma kula da lafiyar 'yan ƙasa da iyalinsu da tarbiyyarsu da kuma samar masu da ayyukan yi "kamar sana'o'i" da yi masu jagoranci na gari da tabbatar da zaman lafiya a tsakaninsu . Waɗannan su ne ginshiƙai kuma muhimman abubuwa da tsaro ya ƙunsa. Yayin da rashin jagoranci na gari da rashin ayyukan yi ga jama'a da aikata manyan laifuka da rigingimu a tsakanin al'umma kan haddasa rashin tsaro da rarrabuwar kawunan al'umma.

 Gusau da Gusau (2012 : 188), sun bayyana cewa, tsaro abu ne da kowace al'umma take da buƙata da shi ; Da zarar aka wayi gari rayuka da dukiyoyin mutane suna fuskantar barazana, to abu ne mawuyaci, ko addini su iya gudanarwa yadda ya kamata. Tabbatar da tsaro ga dukiya da addini, da rayuka, da hankali, da zuri'ar mutane, abu ne da alhakinsa ya ɗora a kan shugabanni. Amma kuma, tattare da haka, su ma talakawa akwai rawar da ya kamata su taka a matsayin tasu gudunmawa. Bisa wannan manufa ne sarakuna a kowane lokaci, suke ƙoƙarin faɗakar da talakawansu akan muhimmancin kula da wannan lamari.

 

 

 

 

 

IRE-IREN TSARO

Ana iya kallon lamarin tsaro ta mabanbantan fuskoki da masana suka karkasa shi, ta la'akari da nau'in da.

1. TSARO NA GANUWA

Bunza A.M (2018 : Lecture) ya bayyana cewa, tsaro na ganuwa shi ne tsaron da ake zagaye gari da gina ta laka, haka kuma a kan yi mata ƙofofi domin shige da ficen mutane, a kan yi wannan ganuwa ne domin kare martabar gari, da kuma mutanen gari, da dukiyoyinsu, da lafiyarsu, a kan yi wannan ganuwa ne domin tabbatar da tsaro.

2. TSARON KURA RAMI

Bunza A. M (2018: lecture) ya ƙara da cewa, tsaron kura rami, tsaro ne wanda mutanen gari ke taruwa a bakin gari, suyi rami babba musamman don hana miyagun namun daji shigowa cikin gari.

3.  TSARON KAI

Bunza A. M (2006:99) ya bayyana cewa tsaron kai shi ne dukkanin wani tsaro da zaka samarwa kanka, domin kariya daga wani haɗari ko farmaki wanda zai iya samun rayuwarka a tafiya, ta yau da kullum. Haka kuma tsaron kai na iya ɗaukar dukkanin abin da za ka yi domin samarwa kanka kyakkyawar kulawa da kariya ga duk wani abu da zai cutar da kai.

4.  TSARON ƘASA

Bunza A. M (2018: lecture) ya bayyana mana da cewa, wannan shi ne tsaron da ake bayar da cikakkiyar kulawa da shuwagabanni kan yi wajen kare ƙasarsu ko garurukansu daga masu tayar da zaune tsaye, ko kuma domin hana kwace wani ɓamgare na ƙasarsu. Haka kuma tsaro ƙasa shi ne duk wata gudummuwa da shugaba zai bayar domin tabbatar da kariya da bayar da kulawa ga ƙasa domin gujewa farmaki ga abokan gaba da mahawara da kan iya kawowa daga wani ɓamgare.

5. TSARON DUKIYA

Bunza A. M (2018: lecture) ya bayyana tsaron dukiya da cewa, wannan tsaro shi ne wanda ake yi domin ba da kulawa da kariya ga dukiyoyin al'umma, domin kare dukiya daga 'yan fashi ko ɓarayi, ko kuma masu yiwa dukiyoyin al'umma, ko gwamnati ɓarna. Haka kuma tsaro ne da aka bayar da kulawa mai muhimmanci, domin dukiya ita ce ƙashin bayan duk wata rayuwar al'umma. Bugu da ƙari, tsaron dukiya tsaro ne wanda ke da matuƙar muhimmanci, domin kare al'umma daga rikice-rikice ko faɗace-faɗace.

6. TSARON JAMA'A

Yusuf Wada da wasu (2014) a cikin kundin bincikensu mai taken yanayin tsaro a garin Ɗandume, inda suka bayyana cewa tsaron jama'a shi ne, kasancewar gwamnati ita ce uwar al'umma ta kanyi iya ƙoƙarinta domin ganin ta bayar da kariya da kulawa mai inganci ga jama'a, domin kaucewa rikici ko faɗace-faɗace a cikin gari. Bugu da ƙari, tsaron jama'a shi ne irin kulawar da masu mulki wato shuwagabanni ke bayarwa a kan talakkawansu tare da ƙudurin kawo zaman lafiya a tsakanin al'umma.

7. TSARON SHUWAGABANNI

Yusuf Wada da wasu (2014) a cikin kundin bincikensu mai taken yanayin tsaro a garin Ɗandume, inda suka bayyana cewa tsaron shuwagabanni shi ne tushiya mafarin duk wani tsaro. Wannan shi ne irin tsaron da ake baiwa shuwagabanni tare da cikakkiyar kulawa, da kuma karesu daga mahara. Haka kuma wannan shi ne tsaron da ake ba muhimmanci domin nuna kulawa da bayar da cikkakkiyar kariya ga shuwagabanni domin karesu daga duk wani abu da ke iya cutar da su.

MA'ANAR GARI

Bayaro (2006: 159) ya nuna cewa kalmar "gari" na cikin jerin sunaye na maza, jam'i kuwa garuruwa a wani karin harshen a kan ce garuruka ko garurra. Kalmar na nufin wurin da mutane suka zauna suka yi gidaje.

MA'ANAR KALMAR GUSAU

Bayaro (2006 : 177) ya bayyana cewa, kalmar na cikin jerin kalmomin suna jinsin mace. Ya kuma nuna kalmar na ɗauke da ma'anar : "sunan babban birnin jihar Zamfara.

Gusau da Gusau (2012 : 1) sun bayyana asali da ma'anar kalmar "Gusau" an samo ta ne daga kalmar "gusa" ko "matsa" waɗanda ke nuna gurgusawa ko matsawa daga bagire zuwa wani bagire da ke kusa.

 

NAƊEWA

Kamar yadda muka kammala wannan babin, mun yi bayani a kan ma'anar yanayi, da kuma ma'anar tsaro da ire-iren tsaro, da kuma ma'anar gari, haka kuma mun yi bayani a kan ma'anar kalmar Gusau.


BABI NA HUƊU

YANAYIN TSARO A GARIN GUSAU

4.0 GABATARWA

Wannan babin zai yi bayani a kan taƙaitaccen tarihin Gusau, da bayani a kan yanayin tsaro na gargajiya da na zamani kamar yadda za mu gani a ciki. Haka kuma an kawo bayani a kan 'yan ta'adda da ire-iren 'yan ta'adda, da kuma abubuwan da ke haifar da ta'addanci a garin Gusau, da illolin da ta'addanci ke haifarwa, tare da kawo bayani game da matsalolin da hukuma ke fuskanta. Babin ba zai kammala ba, sai an zo da irin rawar da al'umma da hukuma ke takawa wajen ganin an magance matsalar ta'addanci a cikin garin Gusau, an kawo muhimmancin tsaro a cikin wannan babi, daga ƙarshe kuma ya zo da naɗewa.

Garin Gusau gari ne mai faɗi sosai, da kuma albarkatun ƙasa, da sana'o'i kamar noma da kiwo, da kuma sauran hanyoyin bunƙasa tattalin arziki kamar kasuwanci. Haka kuma gari ne wanda yake da yawan al'umma, sannan ga ingantaccen tsarin mulki na gargajiya da na zamani, hakan ya sanya aka bai wa tsaro muhimmanci jiya da yau. A wannan babin za a yi ƙoƙarin gano ko fito da ma'anar tsaro da rabe-raben tsaro da kuma ma'anar ta'addanci da ire-iren daga ƙarshe kuma ya zo da naɗewa.

4.1 TAƘAITACCEN  TARIHIN GARIN GUSAU

Gusau (2014: 96) an kafa garin Gusau ne a shekara ta 1811 bayan tasowa daga 'Yandoto a shekara ta 1806.

Garin Gusau yana ɗaya daga cikin manyan garuruwan tsohuwar jahar Sakkwato, kafin daga bisani ya zama babban birnin Jahar Zamfara a shekarar 1996. Kundin bayanin tarihin ƙasa na 1920 ya nuna, garin yana bisa kan titin Sakkwato zuwa Zariya ne; kilomita 179 tsakaninsa da Zariya, 210 kuma tsakaninsa da Sakkwato. Daga Gabas, ya yi iyaka da ƙasar Katsina daga Kwatarkwashi. Daga Arewa kuma ya yi da ƙasar Ƙaura. A yayin da ya yi wata iyakar daga Yamma, da Bunguɗu. Ta ɓangaren Kudu kuma ya yi da ƙasar Ɗansadau da Tsafe. (Gusau, 1912:7).

Gusau (2014: 96) ya ƙara cewa, kasancewar almajirin Shehu Usmanu dan Fodiyo, Malam Sambo ɗan Ashafa ya kafa Gusau a shekara ta 1811, wanda yake shi da jama'arsa ba ruwansu da duk harkokin da suka shafi bautar iskoki ko tsafi irin wanda Hausawa ke yi kafin zuwan addinin musulunci. Watau, garin Gusau ba ya da tarihin Jahiliyya. Hakan ta sa duk al'adun Gusawa, al'adu ne irin na Musulunci. Kuma shigowar wasu mutane, wato baƙi a Gusau, ba ta gurɓata waɗannan kyawawan al'adu ba, don kuwa mafi yawan baƙin da ke tahowar Malamai ne na Musulunci da almajirai, Fulani da wasunsu, da kan taho garin don tsira da addininsu, da mutuncinsu, da kuma dukiyarsu.

Gusau (2014 : 97), haka kuma ya nuna cewa, ta ɓangaren fada kuma, duk umarnin da zai fito daga can, zai kasance ne dabara da abin da Musulunci ya yarda da shi na kyawawan ɗabi'u da al'adu. Musamman kuma da yake, kusan duk Sarakunan da aka yi a garin Malamai ne na addinin Muslunci masu taƙawa da tawali'u. Da wannan shimfiɗa ne, al'adun Gusawa ke gudana dabara da koyarwar addinin Musulunci da kyawawan al'adu irin na Fulani da na Hausa, waɗanda ba su ci karo da Shari'a ba. Irin wancan yanayi na kwararowar baƙi da ƙungiyoyin mutane daban-daban musamman a zamanin Sarkin Katsina Gusau Malam Muhammadu Modibbo "1867 M / 1282 H - 1877 M / 1291 H" Ya sa garin ya sami bunƙasa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci.

Gusau (2014: 97), ya nuna cewa, samun sukunin gudanar da harkokin addinin Musulunci, waɗanda suka shafi karatu, da karantarwa da kuma ibada ba tare da wata tsangwama ba. Samun cikakken tsaron rayuka da dukiya sakamakon ganuwa da garin yake da ita. A haka sai aka wayi gari, babu abin da ya sha wa mutanen garin kai, sai harkokin karatu da noma da kuma kasuwanci. Nan take kuwa sai haɗuwar waɗannan ginshiƙai, ya samar da wani kyakkyawan yanayi a garin, kuma ga kyakkyawar nagartattar aƙida, da yalwar arziki da kwanciyar hankali, da suka taimaka wajen bunƙasa wannan gari.

Gusau (2014: 98), ya nuna cewa zuwan Bature da cin ƙasar Hausa da shimfiɗa tsarin ilimin Boko, ya sa wasu al'adu tsiruwa. Ana cikin haka kuma sai ga Shari'ar Muslunci ta sake kunno kai, ta godaben Mujaddadi. Wannan sabon lamari a wannan ƙarni, shi ma ya kawo canje-canje na alhairi a al'dun mutanen garin Gusau a matsayinsa na babban birnin Jiha. Mutane da yawa na halartar masallatai don tafsiri da itikafi fiye da ɗari. Kawo wa yau akwai malamai da dama da suka shahara da gudanar da tafsiri a masallatan Juma'a da wasunsu a garin Gusau.

Gusau (2014:98) A bisa ƙididdiga da taƙaitawa, garin Gusau a daidai lokacin da ake gudanar da wannan aiki, yana da masarauta ɗaya (1); babban sarki ɗaya, uwayen ƙasa goma sha uku (13); 'yan majalisa goma sha takwas (18). Masallatan Juma'a ashirin da uku (23); ƙananan makarantun boko sittin da huɗu (64); matsakaita kuma Arba'in da uku (43). A yayin da ake da manyan makarantu guda huɗu (4).

Gusau (2014:99). Haka kuma akwai manyan kasuwanni guda uku (3); kamfunnan kasuwanci kuma ashirin da bakwai (27). A yayin da ake da manyan Malaman addinin Musulunci tsakanin rayayyu da waɗanda suka riga mu gidan gaskiya. Bankunan kasuwanci kuma da na noma akwai guda ashirin da uku (23), a yayin da ake da attajirai, manya da matsakaita, da ƙanana, da masu tasowa kimanin ɗari da talatin da biyar (135), da sauran abubuwa da dama.

Daga kuma lokacin da aka kafa wannan gari na Gusau, an yi Sarakuna kamar haka:

Malam Muhammadu Sambo (1806-1827)

Malam Abdulƙadir                   (1827-1867)

Malam Muhammadu Modibbo (1867-1876)

Malam Muhammadu Tuburi (1876-1887)

Malam Muhammadu Giɗe (1887-1900)

Malam Muhammadu Murtala (1900-1916)

Malam Muhammadu Ɗangidan (1916-1917)

Waɗanda suka yi sarautar Gusau ba daga gidan Malam Sambo ba.

Malam Ummaru Malam (1917-1929)

Muhammadu Mai akwai (1929-1943)

Usman ɗan Sama'ila (1943-1945)

Ibrahim Marafa (1945-1948)

Muhammadu Sarkin Kudu (1948-1951)

Alhaji Sulaimanu Isah (1951-1984)

  Dawowar sarauta gida:

Alh. Muhammadu Kabir Danbaba (1984-2015)

Alh. Ibrahim Bello (2015-?)

4.1.1 KAFUWAR GUSAU DA BUNƘASARTA

Gusau da Gusau (2012: 26: 27: 28), sun bayyana cewa, Gusau a zama na biyu, duk da matsalolin da suka kewaye Wonaka, sai da Sarkin Katsina Malam Abdulƙadir ya shekara talatin da uku (33) a Wonaka daga 1827 zuwa 1860.

A shekarar 1860, Magajin Korau wato Sarkin Katsina na Maraɗi da Magajin Baciri wato Sarkin Gobir na Tsibiri suka yi niyyar su yi wa garin Wonaka zobe tun da safe, daga nan sai Sarki Abdulƙadir suka sami labari, don haka, suka fita zuwa Birnin Rawayya, Sarkin Katsina Abdulƙadir ya shekara biyu, daga 1860 zuwa 1862 da jama'arsa a Birnin Rawayya kafin su koma tsohon wurin zamansu na Gusau.

Gusau da Gusau (2012: 27:28), sun nuna cewa, a yayin da mutanen Gusau suka sami zama a Rawayya, suka ga sun yi ƙarfi, sai suka shiga tsananta wa mutanen Rawayya, suka hana su shaƙaƙat, har ta kai idan Rashi, hakimin Rawayya, ya sa aka yi shela, sai su koma su yi tasu shelar, su warware abin da Rashin ya umarta. Daga nan, sai mutanen Rawayya suka yi shawarar hanyar da za su bi don su fitar da mutanen Gusau daga garinsu. An wani daga cikinsu ya ce, tun da bamu iya cin su da yaƙi, ba abin da zai sa su bar garin nan sai gori. A bari sai Sarkin yaƙinsu ya fita ƙilisa bayan gari a rufe ƙofofi, in ya yi  magana a mayar masa da baƙar magana. Suka shiryar da haka, kowa ya yarda da wannan shawarar.

Gusau da Gusau (2012:27:28), haka sun ƙara da cewa, bayan wannan shawara, ran nan sai Sarkin Yaƙi Salihu Ɗankambo cikin mutanen Wonaka ya fita ƙilisa da marece. Ko da ya dawo, sai ya tarar an rufe dukkan ƙofofi, ko'ina ya zagaya, sai ya tarar da ita a kulle. Daga nan ya koma ƙofar da Sarkin ƙofa yake a zaune, ya nemi ya buɗe masa ya ƙi, sai Sarkin ƙofa ya ce masa, "Kai gusa ka ba mu wuri na ƙi buɗe maka.  Bayan haka ana nan, sai Sarkin Katsina Abdulƙadir suka fita zuwa idi, sai mutanen Rawayya suka rufe ƙofofinsu. Mutanen Gusau suka nemi a buɗe masu, aka ƙiya, har ma dai suka yi masu gori da su zarce zuwa garinsu na farko. Daga nan Sarkin Yaƙi Salihu Ɗankambo ya ɗaura ƙaya a sirdin dokinsa, ya jawo ta har zuwa tsohon wurinsu, wato 'Yar Gusau, ya buɗe hanya ga mutane, amma sai Ya gurguso gabas kaɗan da 'Yargusau ya zaɓi wuri. Da mutane suka iso aka ci gaba da gyara wuri, aka kafa wa Sarkin Katsina Abdulƙadir bukkokinsa, sai kuma na Malam Muhammadu Modibbo da Ɗangaladima Usamatu da shi kansa Salihu Ɗankambo da Liman Muhammadu Babba da sauransu. Haka dai mutanen Gusau suka dinga tasowa daga Rawayya suna zuwa suna gyara wuraren zama har suka bar Rawayya kwata-kwata. Da suka dawo wannan wuri sai suka kira shi Gusau.

 4.2 YANAYIN TSARO NA GARGAJIYA

Tukur Ibrahim S/Rafi (2021), ya nuna cewa, a lokacin da, yadda ake gudanar da tsaro ya sha bamban da yadda ake gudanar da shi a wannan lokacin, saboda a can da garin Gusau duk wani mulki da cikakken iko da bayar da kariya ga al'ummar garin Gusau duk suna a hannun sarakunan gargajiya ne. Kasancewar akwai ƙauyuka da dama da ke ƙarƙashin kulawar garin Gusau kamar Abarma da Tungar Fulani, da Mareri, da Damba da sauransu. A kowane ƙauye akwai mai Unguwa wanda shi ke da alhakin kula da al'ummar wannan yanki, ta ɓangaren tsaron lafiya da dukiyoyinsu baki ɗaya.

4.2.1 GANUWA DA ƘOFOFIN GUSAU

Abdulmalik A da Murtala I Gusau (2019: 100) Kamar yadda muka samu tarihi an samar da ganuwa ne sanadiyyar yaƙe-yaƙe da hare-haren da ake fuskanta na wancan zamani. An gina wannan ganuwa da ƙofofinta a lokacin Sarkin Katsinan Gusau Malam Abdulƙadir a shekarar 1863 bayan dawowa Gusau a zama na biyu.

Bayan mutanen Gusau sun baro Rawayya a shekarar 1862, sai suka dawo Gusau a karo na biyu kamar yadda masana suka bayyana, haka kuma a wani lokaci cikin shekarar 1863 Malam Abdulƙadir ya kai ziyara ga Sarkin Musulmi Amadu ɗan Atiku kuma suka tattauna matsalolin da Gusau ke fuskanta na rashin tsaro, Sarkin Musulmi ya yi umarni ga Sarkin Fulanin Bunguɗu da Sarkin Ƙauran Namoda da mutanen Rawayya da mutanen Kwatarkwashi, cewa su taimaki Malam Abdulƙadir a kewaye garin Gusau da ganuwa. Wannan aiki shi ya tabbatar da dawowar cibiyar masarautar Gusau da zuwa garin Gusau tare da ba da kariya ga mutanen garin, don tabbatar da tsaro.

Bayan haka kuma a kowace ƙofa da ke a cikin garin Gusau tana da ƙyaure na ƙarfe wanda maƙera na gargajiya suka ƙera a matsayin gambun wannan ƙofa, haka kuma akwai Sarkin ƙofa wato wani mutum da a kan sanya domin kula da wannan ƙofa domin masu shiga da ficen wannan ƙofa.

Abdulmalik A da Murtala I (2019: 101), sun nuna cewa, a kan gina ganuwa a gari ne, domin kare garin da jama'arsa daga hare-hare da suka yi yawa a wancan lokaci, dalili da haka shi ya sa bayan an gina ganuwa a kan ƙarfafa tsaronta ta hanyar gina rami a bayanta. Wannan rami a kan haƙa shi daga bayan gari kimanin ƙafa goma daga jikin ganuwar, kuma ana cika shi da duwatsu da ƙayoyi ta yadda mutum ko doki na zai iya bi ta cikinsa ba. Bayan an kammala ginin ganuwa a gari, an samar da ƙofofi waɗanda ta cikinsu ne kawai ake shigowa cikin gari, dan haka kowace ƙofa da sunan da aka raɗa mata bisa wani dalili ko munasaba. Kusan dukkan tsofaffin birane a ƙasar Hausa waɗanda aka kafa kafin jihadi ko bayan jihadi suna da ganuwa, misalin irin waɗannan garuruwa sun haɗa; garin 'Yan doto, Kano, Katsina, Alkalawa, Bauchi, Birnin Kebbi, Zariya da Daura duk suna da ganuwa.

Abdulmalik A da Murtala I Gusau (2019: 101), sun nuna cewa, ganuwar garin Gusau an yi ta ne bayan jihadi, an gina wannan ganuwa sanadiyyar hare-haren da mayaƙan ƙasar Katsina ke kawowa mutanen Gusau. Ginin ganuwar ya faru ne a lokacin Sarkin Katsinan Gusau Malam Abdulƙadir a zamanin Sarkin Musulmi Amadu ɗan Atiku.

1. ƘOFAR KWATARKWASHI

A binciken da muka yi a kan ƙofar Kwatarkwashi mun samu bayanai daga masana sun tabbatar mana da samuwar wannan ƙofa kuma sun faɗi daidai inda ƙofar take, tana nan wurin tsohuwar MTD kusa da tankin ruwa da ke sabon gari. Ita wannan ƙofa babba ƙofa ce, wadda mutanen Kwatarkwashi ke shigowa zuwa cikin tsakkiyar garin Gusau. A lokacin da aka gina ganuwa, an buɗe wannan ƙofa ne saboda mutanen Kwatarkwashi da ke shigowa Gusau domin, hulɗoɗin kasuwanci da cinikayya da sauran mu'amaloli yau da kullum, haka ya sa aka saka mata suna ƙofar Kwatarkwashi, Bello Aliyu Ɗanmaituwo (2020).

Taswirar Ƙofar Kwatarkwashi

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

2. Ƙofar Katsaura

Ƙofar Katsaura ɗaya ce daga cikin ƙofofin Gusau, mazaunin wannan ƙofa yana nan cikin Unguwar Toka a yanzu. Mun tuntubi mutane mazauna wurin da dama game da wannan ƙofa, a inda muka samu ra'ayoyi mabanbanta a kan asalin sunan wannan ƙofar. Da farko mun yi hira da Alhaji Shehu Ɗan Moriki mai shekaru saba'in da huɗu (74) ya tabbatar mana da cewa ƙofar tana nan a Unguwar Toka daidai kusa da gidan Baba Ɗan kantoma. Ya bayyana mana cewa asalin kalmar Katsaura sunan wani bawan Allah ne mai suna Katsaura mutumin Nahuce ne. Shehu Ɗan Moriki (2020).

                       Taswirar Ƙofar Katsaura

3. ƘOFAR RAWAYYA

Ƙofar Rawayya kamar ƙofar Kwatarkwashi take an kafa ta ne saboda mutanen Rawayya, su ke shigowa ta wannan ƙofa idan sun zo kasuwanci Gusau, haka mutanen Gusau idan zasu tafi Rawayya ta wannan ƙofa suke bi. Bisa ga abin da muka ji daga bakin Garba mai gudu: Ya ce wannan ƙofa tana nan a bakin tsohuwar kasuwa wurin gidan Alhaji Goga kusa da gidan maƙera a hanyar zuwa gidan Sarki kanwuri Gusau. Malam Hassan Mai keke (2021)

                    

Taswirar Ƙofar Rawayya

4. ƘOFAR JANGE

Ƙofar Jange asalin muhallin da ƙofar take mashaya ce wato wuri ne da yake magudanar ruwa mutane na ɗibar ruwa a wurin kuma suna shayar da dabbobinsu. Jange sunan wani mutum ne mayaƙi, Jarumi, maharbi da ke zaune a wurin yana farautar namun daji. Kamar yadda muka samu bayani daga bakin Abdulmalik Aminu marubucin littafin (Hasken masarautar Gusau 2019) mai shekaru alba'in da ɗaya (41).

                     

 

    Taswirar Ƙofar Jange

5. ƘOFA MATSATTSA

Ƙofa Matsattsa mazauninta yana nan a Marnar Talikai gaba da injinin niƙa kusa da makarantar Allo ta Malam Sanda. An yi wannan ƙofa ne a sanadiyyar wani mutum da ake kira "Kako" (Kakan su Sanata Hassan Nasiha da Muhammadu Buwai) mutumin Katsina ne ya fito daga 'Yan Tumaki. Mun yi hira da wani mutum mai suna Muhammadu Nakungun mai shekaru ɗari da 'yan kai yana nan zaune a Marnar Talikai, sunan kakansa Muhammadu Ɗan mairi shi ne wanda ya yi tsaron wannan ƙofa ta Matsattsa. Hassan Muhammadu Ɗanmairi (2020).

                   Taswirar Ƙofar Matsattsa

6. ƘOFAR MANI

Abdulmalik A da Murtala I Gusau (2019 : 109) Ƙofar Mani na ɗaya daga cikin ƙofofin Gusau, ta samu sunanta ne daga wani mutum da ake kira Mani, haka kuma an sakawa sunan unguwar ƙofar Mani. Kamar yadda bincike ya nuna, ƙofar Mani tana nan a hanyar zuwa Kanwurin Sarki, idan ka matsa kaɗan zaka cimma Ƙofar Mani daidai  wata kasuwa, a gefe kuma akwai tsohon gidan Mani inda ake sayar da hatsi.

 

 

 

                         Taswirar Ƙofar Mani

7. ƘOFAR TUBANI

Ƙofar Tubani tana dab da gidan Malam Muhammad Noma kusa da injinin niƙa dab da wata ƙaramar gada da kuma makarantar Islamiyya da  Gangaren Na Dumau. Haka kuma akwai tsohon gidan Dumau yana nan kusa da ƙofar, amma a wancan lokacin gidan yana cikin baici ne. Asalin sunan ƙofar an samo shi ne daga wani mutum da ake kira da suna Tubani, shi manomi ne, sai dai zuwa wannan lokaci babu sauran birbishin zuri'arsa. A halin yanzu, mun samu waɗansu bayanai ne daga wani dattijo mai suna Sani Madugu mai shekaru tamanin da biyar (85), da kuma wani mutum mai suna Sani Ɗankwamma mai kimanin shekaru saba'in da biyar (75).

 

 

 

                     Taswirar Ƙofar Tubani

8. ƘOFAR DOKAU

Abdulmalik A da Murtala I Gusau (2019 : 111) Ƙofar Dokau ko Dogo? An sami saɓani dangane da sunan wannan ƙofa. A ruwayar wasu marubuta da suka wallafa littatafai da ke ɗauke da tarihin Gusau sun kawo cewa sunan ƙofar ita ce, ƙofar Dogo ba Dokau ba. Kamar yadda muka ba da bayanai ana raɗa wa ƙofa suna ne a sanadiyyar wata a salsala ko munasaba, idan muka duba tsofaffin garuruwa dukkan ƙofofinsu suna da wata munasaba da ta sa aka raɗa masu suna. Haka abun yake anan garin Gusau ƙofofin namu sun samu ne sanadiyyar wasu dalilai. Dalilin da yasa ake kiranta da wannan suna Ƙofar Dokau saboda samun wani gari da ake kira Dokau shiyasa ake kiranta da wannan suna Ƙofar Dokau.

 

                    

             

Taswirar Ƙofar Dokau

9. ƘOFAR GOJE

Abdulmalik da Gusau (2019: 113), kamar yadda muka yi wannan bincike akwai wannan ƙofa ta Goje, amma cikin binciken da muka yi ba mu samu tabbacin inda wannan ƙofa take ba. Bayan haka kuma duk mutanen da muka tuntuɓa suna faɗa mana cewa Gusau tana da ƙofofi har guda tara (9) amma ba su san inda muhallin wannan ƙofa take ba, saboda haka wannan ƙofa mutanen mu saboda sakaci da riƙon sakainar kashi tarihin wannan ƙofa ya kucce masu. Dan haka a iya binciken da muka yi bamu samu tabbacin inda wannan ƙofa take.

Dukkan waɗannan ƙofofi an yi su ne domin tabbatar da tsaro a garin Gusau. Haka kuma dangane da kulawa da ake yi daga mahara akwai wata hasumiya da ake amfani da ita domin hango mahara, wasu kuwa suna tsaron ƙofofin idan na saman hasumiyar suka hango ayari ko runduna tafe, musamman mayaƙa, sai su buga ƙugen yaƙi domin sanar da sauran jama'a, su kuwa 'yan dakon da suke a bakin ƙofa suke da alhakin buɗewa ko rufewa ga duk wani baƙo da zai shigo a cikin garin, domin kare barazanar 'yan samame da mahara. Haka kuma duk wanda almuru ta yi masa a wajen bakin ƙofa to ba zai shiga garin ba sai gari ya waye.

Kafin zuwan Turawan mulkin mallaka sarakuna sune gaba wajen yin ayuka, kai tsaye a matsayin shuwagabanni a masarautunsu. Don haka suke da hakkin tabbatar da tsaro, ke nan su ne wuƙa su ne nama a wannan ɓamgaren. Haka su ke ba da muƙamai kamar Dakarai ko Jarumai da ke ƙarƙashinsu domin su ba da kulawa da kuma kariya ga al'umma, da dukiyoyinsu, dama gari baki ɗaya.

Irin waɗannan mutane da ke aiwatar da tsaro su ne kamar haka:

1- Mayaƙa / Dakarai

2- Sarkin Dogarai

3- Sarkin Yaƙin Dogarai

4- Galadiman Dogarai

5- Madawakin Dogarai

6- Ciroman Dogarai

Yusuf Wada da wasu (2014 : 17), sun bayyana cewa, duk waɗannan dogarai da aka zayyana babban aikin su, shi ne bayar da cikakkiyar kariya da tsaron lafiyar sarki, da wani abu ya samu sarki gara su rasa rayuwarsu, haka kuma waɗannan mutane suna da asiri iri daban-daban saboda ƙoƙarin kulawa da sarki, sannan sauran dogarai sukan zagaya a cikin gari domin kula da irin abubuwan da ke faruwa a cikin gari, ma'ana suna kwantar da duk wata hayaniya, da sasanta tsakanin talakawa, da kuma kawo rahoto ga sarki, a kan irin abubuwan da su ke faruwa a cikin gari.

 

 

 

 

4.2.2 MAKAMAN DA AKE AMFANI DA SU

Dangane da kayayyakin da ake amfani da su a garin Gusau, a wancan lokaci, akwai kayayyaki da dama da ake amfani da su, domin tabbatar da samun zaman lafiya a cikin al'umma da dukiyoyinsu, da kuma kare martabar gari.

Daga cikin irin waɗannan kaya sun haɗa da:

1- Mashi

2- Gariyo

3- Tsikata

4- Majaujawa

5- Kibiya

6- Baka

7- Kwari

8- Adda

9- Takobi

10- Gora

11- Sanda

12- Kulki

13- Garkuwa

14- Sulke

15- Kwalkwali

Waɗannan su ne kayan da ake amfani da su domin kare martabar gari, haka kuma dogarai kan yi amfani da bulala a wajen ayukansu na yau da kullum a cikin garin Gusau.

   Adda                                                               Takobi

 

 

     

Gora                                                          Tsikata

 

 

    Kwari                                                             Baka

 

 

 

 

 

 

             Kibiya                                                       Mashi

        

 

 

 

 

 

 

 

 

4.3 YANAYIN TSARO NA ZAMANI

Yusuf Wada da wasu (2014:19), a cikin kundin bincikensu mai taken "yanayin tsaro jiya da yau a garin Ɗandume. Sun bayyana cewa, a yau (wato wannan zamani) yadda ake gudanar da tsaro ya sha bamban da yadda ake gudanar da shi a da, saboda tsaro a yau ya ta'allaƙa ne kacokan a hannun gwamnati (ma'ana a irin mulki na zamani) domin a yau gwamnati ita ce ke da wuƙa da nama a wajen gudanar da aikin tsaro.

Kamar yadda muka sani cewa ana gudanar da tsaro ta amfani da ma'aikatan tsaro da gwamnati kan ɗaukar aiki, musamman don haka. Irin waɗannan ma'aikata sun haɗa da 'yan sanda da sojoji da sauran ma'aikatan tsaro. Su ne waɗanda gwamnati kan ɗauka kuma take biyansu albashi, domin su tabbatar da bin doka da kuma tabbatar da tsaro a garin Gusau.

Haka kuma ana gudanar da tsaro ta hanyar amfani da sarakunan gargajiya. Haka kuma dogarai amfaninsu ya tsaya ne ga tsaron sarakunan gargajiya. Su kansu sarakunan ana amfani da su domin tsawata wa mutanensu idan buƙatar hakan ta taso domin kuwa har yanzu ana girmama sarakuna a garin Gusau. Haka kuma ƙungiyoyin 'yansakai suna taka muhimmiyar rawa ta fuskar tsaro a yau. Irin waɗannan ƙungiyoyin sun haɗa da 'yanbanga (Vigilante) da masu gadi. Haka kuma masu kuɗi kan taimaka, wa irin waɗannan ƙungiyoyin na 'yansakai da kayan aiki kamar su takalma da fitilu da kayan saƙi (Uniform) da sauran abubuwan da suke buƙata.

Kasancewar gwamnati ke da wuƙa da nama a harkar tsaro a yau, takan yi ƙoƙarin samar da kayan aiki irin na zamani tare da kulawa da jami'an tsaro don tabbatar da cikakken tsaro ga al'umma da dukiyoyinsu, ta kuma samar da duk wani abin da jami'an tsaro ke buƙata ta fuskar aikinsu tare da kulawa da jindaɗinsu domin su samar da cikakkiyar kariya ga al'umma daga duk wata barazana da ka iya tusgowa ta fuskar tsaron lafiya da dukiyoyi.

A yanzu akwai tsaron iyakar garin Gusau wanda wasu nau'o'in jami'an tsaro ke gudanarwa. Aikinsu shi ne kula da masu shiga da fice (Immigration Service), kamar yadda aikin Sarkin ƙofa yake a da. Sannan akwai kuma masu kula da shige da ficen kaya (Custom) domin hana miyagun kaya shigowa kamar ƙwayoyi a cikin garin Gusau. Bayan haka kuma gwamnati kan raba ayyukan tsaro zuwa sassa daban daban don sauƙaƙa aikin tsaro, kamar turasu a Unguwanni daban-daban da ke a cikin garin Gusau.

A garin Gusau a wannan zamani akwai masu gudanar da aikin tabbatar da zaman lafiya iri daban-daban da suka haɗa da jami'an tsaro na gwamnati, da kuma na 'yansakai, da suke aikin tabbatar da tsaro ga rayuka, da dukiyoyin al'umma, da shuwagabanni baki ɗaya.

Misalin irin waɗannan jami'an tsaro sun haɗa da:

1- Yansanda

2- Yanbanga

3- Masu gadi

4- Sojoji

5- Hukumar kula da haɗura

6- Dogarai

7- Hukumar hana shigowa da miyagin ƙwayoyi da fataucinsu

8- Masu kula da shige da ficen kaya

9- Masu kula da shige da ficen mutane

10. Hukumar (Civil defence)

11. 'Yan ƙato da gora.

Da sauransu.

4.3.1 KAYAN DA AKE AMFANI DA SU.

 A yau kayan aikin da ake amfani da su, a sha'anin tsaro sun sha bamban da waɗanda ake amfani da su a lokacin da, wannan kuwa ya faru ne saboda irin cigaban da ake samu a Duniya ta fuskar kimiya da fasaha. Kayan da ake amfani da su a yau suna da yawa, amma ga kaɗan daga cikin su.

1- Motoci

2- Babura

3- Bindigoge

4- Barkonon tsohuwa

5- Ankwa

6- Wayar tangaraho

7- Dabbobi (Irin su karnuka da dawaki)

8- Makami mai linzami.

Da sauransu.

4.4 SU WA YE 'YAN TA'ADDA?

Hibbatullahi da wasu (2014 : 27), a cikin kundin bincikensu mai taken "Nazari a kan matsalolin da ke haifar da ta'addanci a unguwar Sabon Fegi Gusau. Sun yi bayanin cewa 'yan ta'adda su ne waɗanda ke tayar da zaune tsaye, ta hanyar tashe-tashen hankulla a cikin al'umma, wato ta hanyar yin faɗace-faɗace ko kawo rikici a cikin al'umma. Su waɗannan 'yan 'ta'adda, sukan iya tayar da tashin hankali ne haka kawai ko kuma kawo rikici na siyasa a cikin al'umma da sauransu.

4.4.1 IRE-IREN 'YAN TA'ADDA

1. Akwai 'yan sara suka

2. Akwai 'yan bindiga daɗi

3. Akwai 'yan fashi da makami

4. Akwai masu yaɗa kayan shaye-shaye

5. Akwai ɓarayi masu ƙwace

6. Akwai masu garkuwa da mutane

Da sauransu.

4.4.2 AYYUKAN 'YAN TA'ADDA

Ba za a rasa wasu ayyuka da 'yan ta'adda ke yi ba, musamman ayyuka marassa kan gado wato ayyuka marassa kyau a harkokinsu na yau da kullum a cikin al'umma. Misali: idan 'yanta'adda suna jin yunwa sukan fito farauta a cikin gari lungu da saƙo, haka kuma, duk wanda suka samu yaro ko babba za su ƙwace abin da ke hannunsa, misali abinci ne ko kuɗi ko kuma wayar hannu.

Misalin ayyukansu sun haɗa da:

1. Sace-sace

2. Sare-sare

3. Buge-buge

4. Shaye-shaye

5. Da kuma aikata fyaɗe ga mata.

Da sauransu.

4.4.3 ABUBUWAN DA KE HAIFAR DA TA'ADDANCI

 1. Rashin kyakkyawar tarbiyya

Yusuf Umar Auta (2021). Wannan kusan ana iya cewa yana ɗaya daga cikin dalilan da suka hardasa wannan baƙar ɗabi'a shi ne babban dalili da ke saka matasa a cikin sha'anin harkar ta'addanci. Sau da yawa yaro zai taso a gaban iyayensa sai su saka masa ido ba su kula da tarbiyyarsa ko don gudun ɓacin ransa ko don nuna soyayya ga yaran. Wannan lamari na rashin kula da tarbiyya yara shi ke sa idan yara suka girma suka zama matasa ba su tsoro ko shakkun kowa, kuma sai su aikata abin da suka ga dama.

Irin wannan lamari iyaye ne suke yin ko - oho ga lamarin kula da yaransu, wato ba su kai su makarantu kamar na addini da na zamani kuma ba su tsawatawa idan yaran suka aikata abin da ba daidai ba. Idan kuwa iyaye ba su tsawata na yaro ba, saboda lalacewar tarbiyyar yaro zaka tarar baya ganin girman iyayensa ban lantana yaga girman kowa idan suka tashi aikata wani abu ko da ba mai kyau ba ne. Saboda haka da wannan lamari na rashin tarbiyya yana daga cikin dalilan da suke hardasa wannan lamari na ta'addanci.

2. Jahilci

Hussaini Muhammad (2020). Dalilin da yasa nace jahilci shi ke kawo ta'addanci a cikin al'umma, saboda duk inda aka ce al'umma ta rasa ilimi to tabbas wannan al'ummar ta gurɓata. Ba wani jindaɗi da zai wanzu a cikin wannan al'ummar saboda bata da ilimin da zata yi amfani da shi don gyara al'umma a kan tafarki mai kyau, jahilci yana da illolin da dama da suke zama barazana a wajen al'umma baki ɗaya tun daga matasa dattawa da sauran al'umma baki ɗaya.

3. Shaye - shayen miyagun ƙwayoyi

Alkali Bashir Mahe (2020). Shaye-shayen miyagun ƙwayoyi yana daga cikin dalilan da suke hardasa ta'addanci. Saboda idan muka lura za mu ga cewa, ba kowa ne zai iya aikata wani aiki na ta'addanci a bainar jama'a ba, ba tare da ya kawar da hankalinsa ba. Sheye - shaye wani lamari ne na shan kayan barasa (maye) don kawar da hankalin wanda yasha. Haka kuma shaye-shaye yana iya zama wani yanayi na shan ƙwayoyi ko sinadari da zai kawar da hankalinsa ɗan wani lokaci, wannan yanayi na shan kayan maye domin kawar da hankali da aikata wani abu mararsa kyau galibi matasa ne ke yinsa, kuma sukan sha kayan mayen ne idan za su aikata wani lamari na ta'addanci kamar sare - sare ko zage - zage ko tashin hankalin jama'a. Matasa kan sha kayan maye da suka haɗa da:

Giya

Sholisho

Ƙwaya

Babba juji

Tabar wiwi

Bidar ibilis

Roci

4. Rashin adalci

Hamisu Halliru (2021). Rashin adalci, idan muka diba za mu ga cewa, hukuma ita kanta tana daga cikin manyan dalilan da suka sanya matasa cikin lamarin ta'addanci. Hukuma ta bayar da gagarumar gudummawa wajen samar wa ta'addanci gindin zama a cikin al'umma, saboda gazawa wajen samar wa matasa aikin yi da kuma yi masu hukuncin da ya dace a lokacin da suka aikata aikin ta'addanci. Rashin adalcin da hukuma ke yi wajen hukunta wanda ya aikata ta'addanci sai a sake shi da zaran aka ba su kuɗi. Wani lokaci kuma sai a gaya ma jami'an tsaro cewa yaron manya ne, su sa ke shi ko a raba su da aikinsu. Wannan duk sakacin hukuma ne da take da shi wajen hukunta mai laifi, kuma wannan yana ƙara wa yaran ƙwarin guiwar sake aikata mummunan ta'addanci.

4.4.4 KALMOMIN ‘YAN TA'ADDA

'Yanta'adda Kamar yadda muka sani cewa ba za a rasa wasu kalmomi da suke amfani da su ba, a matsayin ɓad da sau. Su na amfani da salon magana ko, karin magana ko, kuma zaurance haka kuma idan muka duba yadda ilimin ma'ana ya ke zuwa da kalmomi masu sarƙaƙƙiya ta yadda dole sai an walwala ma'anar wannan kalma.

Misalin irin wannan kalmomin da suke amfani da su, sun haɗa da:

1- (An kar - an kar) ana nufin a kiyaye.

2- (Ga lakwaye na tafe) idan aka ga jami'an tsaro tafe.

3- (Ayya dai - ayya dai) idan aka ga wayar hannu ko kuɗi ga wani.

4- (Hanya ba kyau) idan an fita nema ba a samo ba.

5- (Tir - tir) idan an fizge  abun wanda aka sani.

6- (Hanya dai kaɗo) idan an hango wani baƙo tafe.

7- (Ba gashi ba) idan ana son a canza labari.

4.4.5 ILLOLI DA AYYUKAN TA'ADDANCI YA HAIFAR A GARIN GUSAU

Malam Rabi'u Aliyu Dangulbi (2021). Ayyukan 'yan ta'adda sun haifar da illoli da dama a cikin garin Gusau, musamman babbar illa ita ce: muna ji muna gani akwai unguwanni da yawa a cikin garin Gusau wanda illar ta'addancin da ake yi ya haifar da sa tsoro a cikin zukatan al'umma, al'umma ba su shiga irin waɗannan unguwanni muddun suna da abu ga hannun su.

Misalin irin waɗannan unguwanni.

1- Tudun Wada Awala

2- Yar mangorora

3- Bulunku

4- Tulluƙawa

5- Sabon fegi

6- Tudun Faila

7- Shiyar Kongo

8- Hira da Kwaɗɗi

9. Sinami

10. Yar Ɗorayi

Misali:

Nura Mu'azu (2020). Unguwar Tudun Wada Alwala; irin wannan Unguwa matsalar ta'addanci ya haifar da sa tsoro da fargaba a cikin zukatan al'umma, irin wannan Unguwa, baka da ikon shiga daddare, saboda irin yadda 'yanta'adda suke ƙwace wayar hannu da kuɗi ga hunnan al'umma.

Haka idan muka diba Shiyar Bulunku da ke a cikin garin Gusau, irin wannan al'umma ba sa son mu'amala a cikin wannan Unguwa, illar ta'addanci yasa al'umma cikin fargaba da sanya tsoro a cikin zukatan al'umma, wannan Unguwa mutane ba sa son shigarta musamman da daddare, domin ana tare mutane ana ansar kuɗi da wayar hannu da kuma garkuwa da mutane.

Haka idan muka diba illar ta'addanci ya haifar da sa tsoro da fargabar aje abin hawa wato mashin

Ibrahim Mahe (2020). Rashin tsaro a cikin garin Gusau, ya haifar da taɓarɓarewar kasuwanci a cikin garin Gusau, za a tarar da shagona a rufe da ƙananan Kasuwanni a rufe, a kan matsalar da ke faruwa ta, ta'addanci a cikin wannan gari na Gusau.

Haka kuma, illar ta'addanci ya haifar da durƙushewar ilimi a cikin garin Gusau, musamman irin yadda aka rufe makarantun sakandare da Furamare, yara su na zaune a gida su na zaman banza zaman kashe wando, muna roƙon Allah ya kawo muna zaman lafiya mai ɗorawa.

4.5 MATSALOLIN DA TSARO YAKE FUSKANTA WAJEN AL'UMMA DA JAMI'AN TSARO

  Ba za a rasa samun wasu matsaloli ba, da ke tasowa idan ana so a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali

 Misali

Abdulrazak Bello Kaura (2020). Cin hanci da rashawa; irin wannan matsala kan daƙushe harkar tsaro harma yakai ya kasa cimma gurinsa, cin hanci kan haifar da matsaloli da dama, ta fuskar aikin yansanada da sauran jama'an tsaro da suka karɓi kuɗi don ƙyale masu laifi suci karansu babu babbaka.

Yusuf Wada (2014 : 26). Rashin bayar da kyakkyawar kulawa ga wanda ya jikita ko ya rasa rayuwarsa a wajen aikinsa; mafi akasari gwamnati nayi da kaine idan kana da lafiya da zarar an ce ka naƙasa to shi ke nan sai ajefar da kai, an riga anci muriyar ganga, haka ga iyalan wanda ya rasa rayuwarsa a wajen gudanar da aikinsa da zarar aka ba su kuɗin sallama shi ke nan babu wani tallafi da za a sake ba su.

Matsalar rashin muhalli. Wani lokaci aikin kantaso da za a nemi ma'aikaci da gaugawa, amma saboda inda yake zaune ba kusa da wajen aikinsa bane zai yi wuya a samu damar haɗa ma'aikata fiye da goma a cikin ɗan ƙan ƙanin lokaci. Haka kuma akwai

4.6 RAWA DA JAMA'A KE TAKAWA WAJEN KAWAR DA AYYUKAN TA'ADDANCI

Al'umma na iya ƙoƙarinsu na wajen ganin al'ummar garin nan ta gyaru, musamman idan muka diba ƙoƙarin da iyaye keyi wajen tabbatar da al'umma sun samu kyakkyawar tarbiya.

1. Kai rahoto ga jami'an tsaro a lokacin da abun yake faruwa

2. Iyaye sukan kira ɗiyansu domin ba su shawarwari tare da yi masu nasiha

3. Haka kuma a kan samar masu da aikin yi kamar turasu a gona da samar masu sana'a domin hana su zaman banza.

4. Haka kuma malamai sukan taka rawa wajen ganin an samu nagar tacciyar al'umma.

5. Haka kuma akwai Hakimi da mai Unguwa da dattawan Unguwa, da limamai su kan taka rawa wajen ganin al'umma sun samu kyakkyawar tarbiyya.

6. Daga ƙarshe kuma akwai hukuma mai zaman kanta domin kawar da ɓata gari a cikin garin Gusau. Kamar hukumar Hizba.

4.6.1 RAWA DA HUKUMA KE TAKAWA WAJEN KAWAR DA AYYUKAN TA'ADDANCI

Hukuma ta kan bi hanyoyi da dama wajen ganin ta ɗauki mataki ga ayyukan 'yan ta'adda domin tabbatar da samun zaman lafiya a cikin gari Gusau. Da farko dai hukuma ta kan bi hanyoyin samar da kayan aiki ga ma'aikatan tsaro, domin su gudanar da aikin su yadda ya kamata, haka kuma hukuma ta kan ɗauki matakin hana kai ma 'yan'ta'adda miyagun ƙwayoyi irin na shaye-shaye, da kuma ɗaukar matakin duk wanda aka kama da makami a hannun shi za a kamashi, bayan haka hukuma ta kan bi hanyoyin tura jami'an tsaro a cikin gari, domin tabbatar samun kwanciyar hankali, tare da tura 'yan leƙen asiri a cikin unguwanni daban-daban, domin su sanya ido ga al'umma, haka kuma hukuma ta kan ɗauki matakin duk wanda zai shigo cikin garin Gusau, sai an bincike shi, ina ya fito kuma ina zaya tafi, sannan kuma suna binciken kayan da aka ɗauko a cikin mota. Hukuma ta kanbi hanyoyi da dama, domin ganin an tabbatar da samun tsaro a cikin garin Gusau, daga ƙarshe kuma hukuma ta kan taka rawa wajen bayar da shawarwari ga matasa da kuma al'umma baki ɗaya.

4.7 MUHIMMANCIN TSORO A GARIN GUSAU

Tsaro shi ne ginshiƙin duk wani cigaba, domin kuwa babu wani cigaba da za'a iya samu idan har akwai fargaba a zukatan 'yan gari. Haka kuma ta hanyar tsaro ne gwamnati ta ke tabbatar da abin doka ga 'yan gari, sannan yana daga cikin ma'aunin da ake auna cigaban gwamnati da ta samu ko akasin haka, ta hanyar tsaro ne a yau ake kare lafiyar 'yan gari, ta hanyar hanasu shaye-shaye na miyagun ƙwayoyi. Haka kuma ana kula da irin kayan da ake shigowa da su a cikin gari, ta haka gwamnati kan samu kuɗaɗen shiga ta hanyar tsaro, domin akwai harajin da ake sanyawa, a wasu daga cikin sana'o'in kayan da ake shigowa da su, sannan daga baya a baka izinin shiga gari.

Haka nan ma yakan kawo haɗin kai ga ma'aikatan tsaro, domin kuwa sukan zama tsintsiya maɗaurinki ɗaya a kowa ne lokaci don tabbatar da aikin su. Haka nan ta hanyar tsaro,  jama'a da dama sun sami aikin yi, domin kuwa a yanzu a kan bayar da albashi ne ga dukkan ma'aikatan tsaro, wanda hakan ya taimaka wajen hana zaman banza a cikin al'umma.

 

4.8 NAƊEWA

Kamar yadda muka kammala wannan babin, ya fara ne da gabatarwa tare da bayani a kan yanayin tsaro na gargajiya da na zamani, haka kuma an kawo  ire-iren 'yan ta'adda da kuma abubuwan da ke haifar da ta'addanci, da kuma irin kalmomin da 'yan ta'adda ke amfani da su, domin sakaya zancen su na yau da kullum, da illolin da ayyukan ta'addanci yake haifarwa, haka kuma an bayyana irin matsalolin da tsaroyake fuskanta da, kuma bayani a kan irin rawar da al'umma da hukuma ke takawa wajen ganin an magance matsalar ta'addanci a garin Gusau daga ƙarshe kuma an kawo muhimmancin tsaro a garin Gusau.


BABI NA BIYAR

SAKAMAKON BINCIKE:

5.0 GABATARWA

A wannan babi na biyar, mai taken sakamakon bincike, za a duba muhimman abubuwa kamar haka: Sakamakon bincike, Ta’arifin wasu kalmomi na (Rataye), da shawarwarin da za a kawo da suka shafi wannan bincike.

5.1 SAKAMAKON BINCIKE

A wannan babi za a yi bayani ne a kan sakamakon da aka samu a wannan bincike da aka gudanar. Sakamako yana nufin abun da aka gano sanadiyar wani bincike da ake gudanarwa ko gwaji (Asibiti ko makaranta). Sakamakon bincike a fagen ilimi yana nufin abun da wani malami ko ɗalibi ya gano ko masana suka gano wajan wani bincike da suke gudanarwa. Wannan bincike da aka gudanar an gano abubuwa  muhimmai kamar haka:

1. A cikin wannan bincike da aka gudanar an gano cewa yanayin tsaro ya samo asali ne daga sarakunan gargajiya, tun a lokacin da.

2. Wannan bincike ya gano cewa a da, sarakuna su ke da alhakin samar da tsaro ga al'ummarsu.

3. Haka kuma a yayin gudanar da wannan bincike an zaƙulo wasu keɓaɓɓun kalmomi da yan ta'adda ke amfani da su domin kawar tunanin jami'an tsaro ko jama'a.

4. Bugu da ƙari wannan bincike ya gano wasu tsofaffin ƙofofin garin Gusau, waɗanda ake amfani da su a da wajen tsare garin.

5. Haka kuma binciken ya bayyana irin matakan da al'umma ke bi wujen ganin an magance yaduwar ayyukan ta'addanci.

6. Duba da kutsen zamani kuwa, binciken ya gano cewa a yanzu yanayin samar da tsaro ya koma a hannun jami'an tsaro da wasu hukomi.

7. Har ila yau binciken ya bayyana irin yadda jami'an tsaro su ke jajircewa wajen ganin an kawar da yaɗuwar ayyukan ta'addanci, tare da samar da tsaro ga al'umma.

8. Haka kuma wannan bincike ya gano garin Gusau, a lokacin da tana da ƙofofi har guda tara, amma saboda rikon sakainar kashi da kuma sakaci da sukayi wa ƙofa guda (1), ta ɓace ba a san inda mazaunin wannan ƙofa take ba.

5.2 RATAYE

A wannan ɓangaren za a kawo ta’arifin wasu kalmomi na rataye, keɓaɓɓun kalmomi na nufin wasu kalmomi ko alamomin magana da wasu ƙungiyoyi ko mutane ke amfani da su wajen gudanar da harkokin su na yau da kullum.

1. Tsikata; wato gitta wata abu ce mai kamar gatari, sai dai ita tsikata tana da tsini daga bayanta, a gabanta kuma tana da faɗi, ita ma ana amfani da ita wajen sara ko suka.

2. Gariyo; ƙarfe ne mai kama da lauje yana da lankwasa a gaba kuma yana da kaifi daga waje, shima ana amfani da shi waje sara ko jan wuyan abokan gaba.

3. Majaujawa; wata igiya ce da ake sakawa takaba ana ƙullata cikin hikima sai ayi mata gurbi da za a iya sanya dutsi domin yin jefa mai nisa.

4. Baka ; wato kibau, wani abu ne mai lankwasa wanda ake ɗaurawa igiya mai ƙwari, ana amfani da shi wajen harba kibiya.

5. Garkuwa; wani makari ne da ake yi da fata ko kuma baƙin ƙarfe wanda ake amfani da shi domin kare sara ko suka, musamman a harbin kibiya, ko sukar mashi, ko sarar takobi.

6. Sulke; wata riga ce, ta saƙa a kan sanyata a jiki, domin tare sara ko sukar jikin mutum.

7. Gora; wani icce ne da ake shukawa yana da ƙullutu a ƙasansa, ana amfani da shi wajen yin duka.

8. Takobi; wani dogon ƙarfe ne mai kama wuƙa, sai dai shi yafi wuƙa tsawo, yana da kaifi ciki da waje, mafi akasari ana yin sa ne da farin ƙarfe.

9. Mashi; wani ƙarfe ne dogo mai tsini daga saman sa, ana amfani da shi wajen suka ga abokan gaba, a fagen yaƙi.

 

 

5.3 SHAWARWARI

Shawara ba a fagen bincike kaɗai take ba ko a harkokin mu na yau da kullum tana da mutuƙar muhimmanci ɗari bisa ɗari. Wannan ne muka ga yakamata a matsayin mu, na ɗalibai da muke gudanar da wannan bincike na yanayin tsaro a garin Gusau, domin mu isar da shawarwarin mu ga masana da ɗalibai, da malamai, da gwamnati, da ƙungiyoyin tsaro, da manazarta al'ummomi da ke gudanar da aikin tsaro.

1. Yakamata hukumar jami'an tsaro ta ƙara ƙyami wajen sa ido ga jami'anta domin ganin sun gudanar da ayyukansu yadda yakamata.

2. Haka kuma iyaye su bada kyakkawar kulawa ga ƴaƴansu, tare da basu tarbiya da ilimin addani da na boko.

3. Har ila yau gwamnati yakamata ta samar da ayyukan yi ga matasa, domin magance zaman kashe wando wanda shi ne ummul aba isin ayyukan asha.

4. Iyayenmu sarakuna na da rawar da su ke iya takawa wajen ganin a magance yaduwar ayyukan ta'addanci ta hanyar amfani da wasu daga cikin sarautu na gargajiya kamar: sarkin samari, sarkin baki, da ƴan rahoto/ ƙamshin gari.

5. A karshe yakamata gwamnati ta yi amfani da yan banga da duk wani wanda yake iya taka rawar a zo a gani wurin ganin an magance ayyukan ta'addanci, ta hanyar yi masu ihisani.

5.4 NAƊEWA

A taƙaice wannan babi ne na kammalawa yana ɗauke da abubuwa kamar haka, gabatarwa, da sakamakon binciken wannan aiki da aka gudanar, da wasu keɓaɓɓun kalmomi na (Rataye) da shawarwarin da suka dace da wannan aiki.


MANAZARTA

Aminu, A da Gusau, M. I (2019) "Hasken Masarauta: Rayuwa

        da zamanin Mai Martaba Sarkin Katsinan Gusau na Tara (9)" Kano:

        Century Research and Publishing Limited.

 

Abubakar, A. T. (2015)"Ƙamusun Harshen Hausa"Zaria: NNPC LTD.

 

Bunza, A.M (2006) Gadon Feɗe Al’ada. Lagos: Surulere Tiwal Nigeria Ltd.

Bunza, A.M. (2017) DABARUN BINCIKE (A Nazarin Harshe Da Adabi Da

Al’adun Hausawa) Zaria: Ahmadu Bello University Press Limited.  CNHN (2006)"Ƙamusun Hausa "Kano: Jami'ar Bayaro

 

Gusau, A. R (2014) "Mai Dubun Nasara: Rayuwa Halaye

          Saƙonni: da Jawabin Mai Martaba." Gusau:  Al-Hudah Ventures.

 

Gusau, B.M, Gusau S.M (2012),Gusau ta malam Sambo Benchmark Publishers. Limited KanoNigeria.

 

Hassan, M. B  (2019) Kadaura: Journal of Hausa Multi Disciplinary Studies.

         Vol. 1, No. 5 September, 2019.

 

Hibbatullahi, dawasu (2014).Nazari AKan Matsalolin Dake Haifar Da

Ta'addanci: ASashen Hausa, Tsangayar Harsuna, Kwalejin Ilimi Da Ƙere Ƙere, Ta Gwamnatin Tarayya, Gusau Jihar, Zamfara.

 

 Nalado, A.M (b.she) Kano State Jiya Da Yau AD.999. 1864 - 1968; Zaria:

        Gaskiya Cooperation.

Yusuf, Wada, da wasu (2014). Nazari a kan Yanayin Tsaro Jiya Da Yau

         A Garin Ɗandume. Sashen Hausa Kwalejin Kimiyya da Fasaha:

         Zacas, Gusau Jihar Zamfara.

 

Shekarau, M.I (2007) Role of Government in Security of Life and property;

         Presented at Ladi Kwalli Hall, Sheraton Hotel & Towards, Abuja.

MUTANEN DA AKA YI HIRA DA SU

1. Abbas Mu'alleɗi, lauyan gwamnati mai shekaru 43, hirar da  anka yi da

           shi ranar 03/03/2020, a gidansa da ke Gada Biyu Gusau, da misalin

           ƙarfe 10:00am.

 

2. Abdulrazak Bello Kaura shugaban 'yan jarida na jihar Zamfara, mai

            shekaru 42, hirar da anka yi da shi ranar 13/03/2020, a wurin aikinsa

            da ke "FM Radiyo Gusau". Da misalin ƙarfe 11:30am.

3. Abdulmajid Umar Galadima, mai shekaru 41, hirar da anka yi da shi ranar

            15/03/2020, a wurin zaman shi da ke Kanwuri Gusau, da misalin

             karfe 5:15pm

 

4. Aliyu Rufa'i Gusau, hirar da anka yi da shi ranar (20/03/2020), a

        mazaunin shi da ke Kanwuri Gusau, da misalin ƙarfe 9:20am

5. Abdulhamid A Baba mai shekaru 61, hirar da anka yi da shi ranar

           23/03/2020, a mazaunin shi da ke Unguwar Toka Gusau, da misalin

           ƙarfe 6:00pm.

 

6. Abdulrahman Abdullahi, mai shekaru 35, hirar da anka yi da shi ranar

           17/04/2020, a wurin aikinsa da ke Tudun Wada Gusau, da misalin

           ƙarfe 4:30pm.

 

7. Aminu Aliyu, mai shekaru 39, hirar da anka yi da shi ranar 19/04/2020, a

           gidansa da ke Sabuwar Gusau, da misalin ƙarfe 10:00am.

 

8. Aminu Shehu, mai shekaru 35, hirar da anka yi da shi ranar 23/05/2020, a

          wurin zaman shi da ke 'Yar Mangorora Gusau, da misalin ƙarfe

          9:30am.

 

 9. Alkali Bashiru Mahe, mai shekaru 51, hirar da anka yi da shi ranar

10/07/2020, a mazauninshi da ke Unguwar Dallatu Gusau, da misalin

            ƙarfe 8:30pm.

10. Bawa Makau, mai shekaru 67, hirar da anka yi da ranar 26/08/2020, a

              gidan sa da ke Tsohuwar kasuwa Gusau 5:43pm.

11. Bello Adamu Dinawa, babban jami'in tsaro na 'yan sanda, mai shekaru

           46, hirar da anka yi da shi ranar 28/08/2020, a wurin aikinsa da ke

"Central Police Gusau", da misalin ƙarfe 10:20am.

 

12. Bello Aliyu Ɗanmaituwo, mai shekaru 73, hirar da anka yi da shi ranar

           05/09/2020, a mazauninshi da ke Tsohuwar Kasuwa Gusau, da

           misalin ƙarfe 2:14pm.

 

13. Dauda Muhammad, mai shekaru 43, hirar da anka yi da shi ranar

              07/09/2020, a wurin gudanar da aikinsa da ke "Headquarter Gusau",

              da misalin ƙarfe 10:23am.

 

14. Faruk Umaru Auta, mai shekaru 68, hirar da anka yi da shi ranar

             18/09/2020, a mazauninshi da ke Tsohuwar kasuwa Gusau,

              da misalin ƙarfe 10:35am.

 

15. Garba Abdullahi Aliyu, mai shekaru 71, hirar da anka yi da shi ranar

             25/09/2020, a gidansa da ke Tsohuwar Kwata Gusau, da misalin

             ƙarfe 8:20pm.

 

16. Hassan Muhammadu Ɗanmairi, mai shekaru 68, hirar da anka yi da shi

              ranar 13/10/2020, a gidansa da ke 'Yar shararra Gusau, da misalin

              ƙarfe 5:10pm.

 

17. Hussaini Muhammad, babban jami'in tsaro na 'yan sanda, mai shekaru

              43, hirar da anka yi da shi ranar 26/10/2020, a wurin gudanar da

              aikinsa da ke "C.I.D Office Gusau", da misalin ƙarfe 2:23pm.

 

18. Ibrahim Mahe, mai shekaru 45, hirar da anka yi da shi ranar

           24/11/2020, a gidansa da ke Sabuwar Gusau, da misalin ƙarfe

           8:00pm.

17. Ibrahim Gali Tayi, mai shekaru 31, hirar da anka yi da shi ranar

           18/12/2020, a mazaunin shi da ke Ƙofar Jange Gusau, da misalin

           ƙarfe 6:34pm.

 

18. Jabir Yusuf Auta, mai shekaru 44, hirar da anka yi da shi ranar

             23/0/12/2020, a wurin aikinsa da ke "Headquarter Gusau",

             da misalin ƙarfe 2:20pm.

 

19. Nura Mu'azu S.P, mai shekaru 43, hirar da anka yi da shi ranar

27/02/2020, a unguwar su da ke Bakin Tsohuwar Kasuwa

          Gusau, da misalin ƙarfe 5:17pm.

 

20. Namadi Sulaiman Muhammad, mai shekaru 76, hirar da anka yi da shi

               ranar 13/01/2021, a mazaunin sa da ke Bakin Tsohuwar Kasuwa

               Gusau, da misalin ƙarfe 5:00pm.

 

21. Mu'azzam Sulaiman, mai shekaru 32, hirar da anka yi da shi ranar

              27/01/2021, a wurin zamanshi da ke Gangaren Kwata Gusau,

              da misalin ƙarfe 5:30pm.

 

22. Munnir Abdullahi, wakilin layauka sadarwa na jihar Zamfara mai

shekaru 41, hirar da anka yi da shi ranar 19/03/2021, a

          mazauninshi da ke Bakin Tsohuwar Kasuwa Gusau, da misalin

          ƙarfe 2:43pm.

 

23. Muhammadu Kabir Sarki, mai shekaru 58, hirar da anka yi da shi ranar

              23/03/2021, a mazauninshi da ke Tudun Wada Gusau, da misalin

              ƙarfe 7:23pm.

 

24. Malam Rabi'u Aliyu Ɗangulbi, hirar da anka yi da shi ranar 16/04/2021,

             a gidansa da ke Gidan Dawa Gusau, da misalin ƙarfe 5:15pm.

 

25. Sani Muh'd babban jami'in tsaro na 'yan sanda mai shekaru 38, hirar da

             anka yi da shi ranar 27/04/2021, a wurin da gudanar da aikinsa, da

             ke Central Police Gusau, da misalin ƙarfe 12:11pm.

26. Sani Madugu, mai shekaru 74, hirar da anka yi da shi ranar 14/05/2021,

             a gidansa da ke Zawiyya Gusau, da misalin ƙarfe 5:30pm.

 

27. Sani Ɗankwamma, mai shekaru 69, hirar da anka yi da shi ranar

            14/05/2021, a Unguwar su da ke Zawiyya Gusau, da misalin ƙarfe

            5:30pm.

28. Sani Muhammad babban jami'in tsaro na 'yan sanda, mai shekaru 38,

             hirar da anka yi da shi ranar 16/06/2021, a wurin aikinsa da ke

             Central Police Station Gusau, da misalin ƙarfe 3:35pm.

 

29. Surajo Yalwa Sarki, mai shekaru 43, hirar da anka yi da shi ranar

             23/06/2021, a gidansa da ke Bello Bara'u Gusau, da misalin ƙarfe

             5:12pm.

 

30. Tsalha Musa Bashiru, mai shekaru 67, hirar da anka yi da shi ranar

             18/07/2021, a gidansa da ke Sabon Fegi Gusau, da misalin ƙarfe

              4:30pm.

 

31. Tukur Ibrahim Rahi, mai shekaru 68, hirar da anka yi da shi ranar

             16/08/2021, a gidan sa da ke Unguwar Dallatu Gusau, da misalin

             ƙarfe 9:00am.

 

32. Yusuf Ummaru Auta Gusau, mai shekaru 78, hirar da anka yi da shi

             ranar 20/08/2021, a gidansa da ke Bakin Tsohuwar Kasuwa Gusau,

             da misalin ƙarfe 3:35pm.

Post a Comment

0 Comments