𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Shin Ya Halatta
Saurayi Da Budurwa Suyi Aure Babu Wanda Ya Sani A cikin Dangin Budurwar Da
Dangin Saurayin, Kuma Suna Garinda Iyayensu Suke.?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد والصلاة والسلام على رسول الله.
Shidai aure baya inganta saida Abubuwa
guda uku:
1. Sadaki
2. Shaidu biyu
3. Waliyyi (bangaren mace)
Namiji yana iya neman aure sannan
ya biya sadaki harma ya karɓi auren ba tare da ya fadawa kowaba.
Sa'eedu bin musayyib_ ya aurawa
dalibinsa 'yarsa ba tare da dalibin ya zoda kowa daga danginsaba.
Sannan Abdurrahman bin Auf ya yi aure
azamanin Annabi Sallallahu Alaihi wasallam kuma bai sanadda Annabi sallallahu
Alaihi wasallam ba, sai daga baya Annabi Sallallahu Alaihi wasallam yaji labari
sai ya ce: masa ka yi WALIMA ko da DA AKUYAC NE ashe namiji zai iya aure ba tare
da ya sanadda danginsaba.
Amma mace bata Auradda kanta a
shari'ance. Dole ta Samu wani wanda zai zama waliyyinta awajen bayarda aurenta.
Wanda sukafi can-cantar subada
auren mace sune:
1. Uba, Kaka, Yayanta.
2. Ɗah, ɗan Ɗah, ko kanin Ɗah, ko
yayan Ɗah.
3. Makusantanta cikin dangin uba
Yayan mahaifinta ko kanin mahaifinta.
4. Sarki ko wakilinsa, idan babu ɗaya
cikin wadancan ko auren yakai gaban alkali.
Induka mace ta rasa wayannan akan
dawo aduba a cikin dangin mahaifiyarta awakilta wani ya bada aurenta.
In ba a samuba, to sai tasamu
wani namiji ya wakilci bada aurenta.
Malaman fikhu sukace: Idan
mahafin mace yana raye sai taje wani daban ya daura aurenta kuma ba mahaifinne
yabada damaba, to Aure ya ɓaci.~fathul jauwaad-1-150.
Dan haka sunan wannan aure da
sukayi auren mutu'ah auren jin daɗi daholewa kawai zina kenan ma'ana karuwanci.
Shi ne akeyinshi ba shaidu, ba
waliyyai, ba sadaki, saidai ladan aiki.
Shikuma auren mutu'a Annabi
Sallallahu Alaihi wasallam ya haramtashi alokacin da akadawo daga yakin
khaibara.
Dan haka wajibi ne suraba auren
tsakaninsu su samu waliyyai da shaidu asake daura musu aure, idan sun samu Ɗah
ko ciki to ɗansune.
WALLAHU A'ALAMU
Tambaya da Amsa Abisa fahimtar
Magabata Nakwarai.
Hukuncin
Auren Da Saurayi Da Budurwa Suka Yi Atsakaninsu:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Slm malam
ygd . Malam tambayata ita ce miye matsayin Auren da saurayi da budurwa suka yi
atsakaninsu alhalin iyayensu na raye sunyi ne dan kada su aikata alfasha sukayi
siga tsakaninsu yanemi Aurenta Akan wani Sadaki itakuma ta bashi auren ta bisa
amincewarta.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Aure baya
zama Aure Tsakanin mace da Namiji har sai da Abubuwa guda Huɗu.
1. Na farko Shi
ne ya zama Akwai Sigar Aure a Tsakanin Waliyyan Waɗannan Ma'auratan.
Ma'ana Waliyyin Namiji Yace Ina Nemawa Ɗana ko Kane na Ko Jika na ko Abokina
Wane Auren ɗiyarka Wance ko Kanwarki Wance Ko Mahaifiyarka Wance.
Domin Da zai iya Yiwa Mahaifiyarsa Alwalanaci. Kamar Yadda Anas ɗan Malik ya yiwa
Mahaifiyar sa Ummu Sulaimin Alwalanci a Lokacin da Abu Dalhatal Ansariy ya zo Aurenta.
Sannan shi Alwalalin wannan Macen Yace Na Baka. Sai Alwalin Wannan Namijin Ko
Wakilin wannan Namijin Yace Na Karɓa Masa.
2. Abu Na
Biyu Kuma Shi ne Alwalanci. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace MACE
BA TA AURAR DA MACE, SANNAN MACE BA TA AURAR DA KANTA. Sabida haka Kenan.
Wajibi ne a sami wanda zai Aurar da ita, Kuma Wajibi ne ya Wannan da zai Aurar
da ita ɗin ya zama Namiji.
Mutumin da ya fi kowa Chanchanta wajen Aurar da ita, Yimata Alwalanci shi ne
Mahaifinta. Idan babu Mahaifi Sai a Sami wani daga Cikin Dangin Mahaifinta Ya
Aurar da Ita. Idan babu daga dangin Mahaifin ta, sai a sami wani daga dangin
Mahaifiyar ta. Idan babu dangin Uwa sai Shugaba Kamar Sarki ko Hakimi ko Dakaci
ko Bulama ko Mai Unguwa. ya yi Mata Alwalanci.
3. Aure Baya
Yiwuwa sai da Sadaki. Wajibi ne ya zama an san sadakin wannan Matar tin kafin A
zo Maganar Ɗaura Wannan Auren. Sannan Waliyyanta Za a dankawa Wannan
Sadakin Ba Ita ba. Daga baya ne kuma zasu bata kayanta. Amma mace bata karɓar sadaki da
hannunta. Ko da Kuma ta Karɓa da hannunta. za ta kawowa Waliyyanta su gani su sanya
Masa Albarka. Sai Kuma ita wannan Bata Nemi Albarkar iyayenta akan Wannann
sadakin Nata ba. Hatta a Auren Nata ma bata Nemi Iyayenta su Sanya Mata Albarka
ba.
4. Wajibi ne
a sami Shedun da Zasu Bayar da Shaidar Cewar a Gabansu Aka Ɗaura wannan Auren, kuma duk Wani Sharadi na Wannan Auren
an cika Shi. Sannan Ne zasu Ba da Shaida. Wajibi ne Wadannan Shaidun Akalla Su
Zama kamar Mutum Ukku, da zasu tabbatar da Dauruwar Wannan Aure. Idan babu
Shedu Aure bai yiwu ba. Sannan ya zama Wajibi Waɗannan Shedun su
zama Masu Hankali, Adalai.
Sabida haka
kenan. Ta Kowanne Fuska wannan Auren bai yiwu ba. Domin bai Cika Duk wani
Sharadi na Aure ba. Wannan Wasan yara ne. In banda ma Rashin Tarbiyya. Ta yaya
Mace Budurwa za ta Aurar da kanta ga wani Namiji. Ba tare da sanin Iyayenta ba.
Allah ya gyara mana wannan zamanin da Muke Cikinsa.
Allah Shi ne
Masani.
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan
Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Fb6ƙgYPXfEeHb8CD1SWAkK
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.