𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Shin Ya Halatta
Saurayi Da Budurwa Suyi Aure Babu Wanda Ya Sani A cikin Dangin Budurwar Da
Dangin Saurayin, Kuma Suna Garinda Iyayensu Suke.?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
الحمد والصلاة والسلام على رسول الله.
Shidai aure baya inganta saida Abubuwa
guda uku:
1. Sadaki
2. Shaidu biyu
3. Waliyyi (bangaren mace)
Namiji yana iya neman aure sannan
ya biya sadaki harma ya karɓi auren ba tare da ya fadawa kowaba.
Sa'eedu bin musayyib_ ya aurawa
dalibinsa 'yarsa ba tare da dalibin ya zoda kowa daga danginsaba.
Sannan Abdurrahman bin Auf ya yi aure
azamanin Annabi Sallallahu Alaihi wasallam kuma bai sanadda Annabi sallallahu
Alaihi wasallam ba, sai daga baya Annabi Sallallahu Alaihi wasallam yaji labari
sai ya ce: masa ka yi WALIMA ko da DA AKUYAC NE ashe namiji zai iya aure ba tare
da ya sanadda danginsaba.
Amma mace bata Auradda kanta a
shari'ance. Dole ta Samu wani wanda zai zama waliyyinta awajen bayarda aurenta.
Wanda sukafi can-cantar subada
auren mace sune:
1. Uba, Kaka, Yayanta.
2. Ɗah, ɗan Ɗah, ko kanin Ɗah, ko
yayan Ɗah.
3. Makusantanta cikin dangin uba
Yayan mahaifinta ko kanin mahaifinta.
4. Sarki ko wakilinsa, idan babu ɗaya
cikin wadancan ko auren yakai gaban alkali.
Induka mace ta rasa wayannan akan
dawo aduba a cikin dangin mahaifiyarta awakilta wani ya bada aurenta.
In ba a samuba, to sai tasamu
wani namiji ya wakilci bada aurenta.
Malaman fikhu sukace: Idan
mahafin mace yana raye sai taje wani daban ya daura aurenta kuma ba mahaifinne
yabada damaba, to Aure ya ɓaci.~fathul jauwaad-1-150.
Dan haka sunan wannan aure da
sukayi auren mutu'ah auren jin daɗi daholewa kawai zina kenan ma'ana karuwanci.
Shi ne akeyinshi ba shaidu, ba
waliyyai, ba sadaki, saidai ladan aiki.
Shikuma auren mutu'a Annabi
Sallallahu Alaihi wasallam ya haramtashi alokacin da akadawo daga yakin
khaibara.
Dan haka wajibi ne suraba auren
tsakaninsu su samu waliyyai da shaidu asake daura musu aure, idan sun samu Ɗah
ko ciki to ɗansune.
WALLAHU A'ALAMU
Tambaya da Amsa Abisa fahimtar
Magabata Nakwarai.
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan
Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Fb6ƙgYPXfEeHb8CD1SWAkK
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.