Ticker

6/recent/ticker-posts

Shin Saina Gayawa Mijina Cewa Nayi Zina Kafin Allah Ya Karɓi Tubana?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Yar uwatace ta yi zina da aurenta don neman kuɗin da matsanancin talauci ya jefata a ciki, sai daga baya ta yi nadama taketa tuba da istigfari tare da neman yafiya a gurin mijinta.

Tambayarta ita ce shin lallai sai ta tona asirin kanta ga mijinta sannan yafiyarsa gareta zata karɓu ga Ubangiji?? Sannan ya matsayin tubanta a gurin Ubangiji da kuma hukuncinta???

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Toh batun matsayin tubanta a wajen Ubangiji wannan ta karɓu In shã Allahu matuƙar dai ta yi nadama ta yi Allah wadarai kuma ta zargi kanta gameda wannan abinda ta aikata sannan kuma ya zama ta yi tuban ne tsakaninta da Allah bawai damar sake yin zinan ta nema tarasa ba shi ne ya sa ta tuba, A'a ta tubane saboda jin tsoron Allah sannan ta yi nadama to in sha Allah Allah ya karɓi tubanta.

 Batun mijinta kuma wannan akwai wata ƙa'ida ta Fiƙhu sukace wai Tunkude ɓarna shi ake gabatarwa memakon a janyo maslaha, DAR'UL MAFSADA MUƘADDAMUN ALA JALBUL MASLAHA kin ga anan gayawa mijin naki cewa kinyi zina yayafe miki wannan babu shakka maslaha ne, to amma kuma bakida tabbacin cewa mijin zai hakura yayafe miki kuma yaci gaba da zama dake bayan kin gaya masa, kekanki zaki riƙa tunanin infa kika gayamai kinyi zina ze iya cewa ya sake ki, wanda sakin shikuma ɓarna ce, bayan sakin kuma waɗanda basu san kinyi wannan zinan ba duk sesun sani musamman iyayenki kuma hakan ba zai musu daɗi ba kema kuma mutuncinki zai zube kin ga wannan duk ɓarna ce, sannan kuma kin tonama kanki asiri bayan Allah ya rufa miki wannan shima duk ɓarna ne

Dan haka malamai sukace wacce tasamu kanta a cikin irin wannan halin to kawai taroƙi mijin yayafe mata dukkan laifukan da ta yi masa waɗanda ta sani da wanda bata sani ba, amma karta kuskura ta gaya mishi cewa ga abinda ta yi saboda karta buɗe ƙofar wadancan ɓarnace ɓarnacenda za su iya biyo baya.

Allah ta'ala ya sa mudace.

Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Fc3hX6HoDt65aKhhKOiDpX

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments