𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum inama malan
fatan alkhairi dan Allah shawara nake nema na kasance mace mai karfin sha'awa
tun tasowata gashi iyayena wai sai mun yi karatu me zurfi hartakaiga inasa
hannu a farjina idan nasa nakanji kwanciyar hankali kuma idan nayi istigfari
akan natuba sai nakoma saboda wahalar ciwon da nakeji natuba yafi sau nawa dan
Allah aban shawara nagode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumussalam warahatullah.
To 'Yar uwa wannan matsalar tana
damun matasa maza da mata wato matsalar rashin Aure, kuma wannan sa hannu a
farji, saɓawa ALLAH ta'ala ne, gaskiya kuma shawaran da nake baki anan ita ce.
Na farko kidena zama a Ɗaki ke kaɗai
Sannan ki yawaita Azumin nafila domin Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) yace
yana rage ƙarfin sha'awa.
Sannan ki yawaita karatun Alƙur'ani
shima wannan babban magani ne. Ki yawaita Istigfári, kuma shi ƙofar tubanki
tana nan a buɗe kamar yadda wannan hadisin ya nuna
كل بني ادم خطاء وخير الخطاءين التوابون
"Dukkan 'yan adam masu saɓone,
mafi alherin masu saɓo, sune masu tuba"
Dan haka ki tuba kiyi nadama akan
cewa ba za ki ƙara komawa zuwa ga wannan saɓon ba In shã Allahu, Allah ze yafe
miki.
Anan muke kira ga iyaye wallahil
azeem kuji tsoran ALLAH idan anzo neman Auren 'yayan ku, Ku bayar idan ba haka
ba wallahi zaku haifar da fitina a bayan ƙasa domin a sanadin kaƙi yiwa 'yarka
Aure taje ta fada ZINA !! to lallai kai ne sanadi kuma kanada naka kason Na
zunibi.
Duk Wanda akazo Neman Aure Annabi
(sallallahu alaihi wa sallam) ya ce: Ku kalli addinin sa kawai Ku bashi idan
kunƙi fitina zata haifu a ban ƙasa.
Wallahi saɓawa maganar Annabi
(sallallahu alaihi wa sallam) dedai yake da Saɓawa ALLAH.
ALLAH ta'ala ya tsaremu
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan
Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/CƘ9TMXMrWDx1y7sYye2znU
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.