Ticker

6/recent/ticker-posts

Sarautun Bayi A Kasar Katagum (1814- 2016) – KASHI NA 3

Abstract: The aim of this study focuses on the traditional titles of slaves in Katagum. It is based on this aim that the research was presented in five chapters. The first two chapters focussed on general overview of the work and relevant literatures related to this research. Chapter three has taken broader look at the historical background of slevary in Hausaland. After the historical survey, the research narrowed to the slave-only traditional titles in Katagum. This has seen the research scrutinising indepthly all the issues surrounding slave- only traditional titles in Hausaland even before the emergence of Katagum. Similarly, the research has scrupulously found out the findings of the work. The research found out that some traditional titles have become extinct. Against this backdrop, traditional instutition have been recommended to establish a special traditional titles office that will handle the historical facts of the kingdom/emirate and other traditional title holders.

Tsakure

Ƙudirin wannan aiki tunkarar Sarautun Bayi a ƙasar Katagum. Bisa ga wannan ƙudirin an kasa binciken zuwa babuka biyar. Goshin aikin ya tunkari gabatarwa da bitar ayyukan da suka gabace shi. Kashi na uku na aikin ya yi dogon share fage a kan tarihin bauta a ƙasar Hausa. Bayan an yi wa tarihi turke mai ma’ana sai aka dubi masarautar Katagum da sarautun bayi da ke ciki. Wannan ya nuna an ƙoƙarin kakkeɓe duk wata ƙura a tarihi da al’ada da bautar take ciki a ƙasar Hausa gabanin a yi ƙasar Katagum dubi na nutsuwa. Binciken ya yi kwakkwara da kammalawa wadda ta fito da ɗan sakamakon bincike da aka yi. Tabbas an gano cewa wasu sarautun gargajiya a fada sun soma ɓata. Don haka, tilas a farfaɗo ko ƙirƙiro wata sarauta cikin kowace masarauta a ƙasar Hausa da za ta kiyaye da tarihin sarautun masarautarta.

Sarautun Bayi A Ƙasar Katagum (1814- 2016) – KASHI NA 3 

Muhammad Abubakar Zabi
muhammadabubakarzabi@gmail.com
08136844199

Sarautun Bayi

SADAUKARWA

Na sadaukar da wannan aiki ga mahaifana, Malam Abubakar Wazirin Zabi da Malama Hauwa’u Ahmad. Allah Ya ƙara musu lafiya tare da imani, amin. Allah Ya saka musu da tarbiyar da suka yi mana. Mun gode, Allah Ya biya.

GODIYA

Godiya mafificiya ta tabbata ga Allah maɗaukakin sarki, mamallakin sammai da ƙasai, wanda Ya raya mu Ya kuma ba mu ikon kawowa wannan mataki. Tsira da amincin Allah su ƙara tabbata ga manzon tsira, Annabi Muhammadu (Sallahu Alaihi Wasalam).

Babu shakka, mutane da dama sun ba da gudummawa wajen ganin wannan aiki ya kammala cikin nasara. Sai dai ambaton sunayensu duka ba zai yi wuya ba, ko da kuma an ambata godiyar fatar baki ba za ta gamsar ba. Sai dai addu‘ar Allah Ya saka wa dukkan wanɗanda suka taimaka da alheri.

Godiya ta musamman wadda ba za ta misaltu ba ga Malamina kuma jagoran duba wannan aiki Farfesa Aliyu Muhammadu Bunza, wanda duk da ayyuka masu dama da suke gabansa, amma ya kula ya kuma yi ta taimakawa wajen duba aikin da kuma gyare-gyare ga wannan bincike. Kazalika, ya yi ta ba da shawarwari masu dama tun daga farkon aikin har zuwa ƙarshensa. Ina roƙon Allah Ya saka wa Malam da gidan Aljanna Fiddausi, amin.

Haka kuma, godiya marar misaltuwa ga Malamina kuma jagoran duba wannan aiki na biyu wato Dr. Abdullahi Sarkin Gulbi shi ma ya yi namijin ƙoƙari wajen ganin wannan aiki ya yi nasarar kammaluwa. Ba don haɗin kan da ya bayar ba, da wannan aiki bai tsayu da ƙafafunsa ba. Da fatar Allah Ya saka wa Malam da gidan Aljanna fiddausi, amin.

Ina miƙa godiyata ta musamman ga malamina jagoran duba aikin na uku, Farfesa Y. Y Ibrahim na Sashen Nazarin Addinin Musulunci (Islamic Studies Department), wanda da taimakonsa aikin nan ya samu kai wannan mataki. Ina fatar Allah Ya saka wa Malam da gidan Aljanna Fiddausi, amin.

Bayan haka, ina mai matuƙar bayyana jin daɗina da godiyata ga shugaban Sashen Nazarin Harsunan Najeriya, Jami´ar Usmanu Ɗanfodiyo, Farfesa Atiku Ahmad Dunfawa, ina yi wa Malam fatar Allah Ya saka masa da alheri. Ina godiya ga dukannin Malamaina na Sashen Nazarin Harsunan Najeriya na Jami`ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato. Waɗanda suka haɗa da: Farfesa Ibrahim Makoshy, da Farfesa Abdullahi Bayero Yahya, da Farfesa Haruna Abdullahi Birniwa, da Farfesa Ahmad Halliru Amfani, da Farfesa Salisu Ahmad Yakasai, da Farfesa Abdulhamid Ɗantumbishi, da Dr. Bello Bala Usman, da Dr. Ibrahim Sarkin Sudan, da Dr. Yakubu Aliyu Gobir, da Dr. Abdulbasir Ahmad Atuwo, da Dr.Yahya Idris, da Dr. Umar Aliyu Bunza, da Dr. Nasiru Aminu Kalgo, da Malam Naziru Ibrahim Abbas da Malam Sama’ila Umar da Malam Dano Balarabe Bunza da Malam Mustafa Muhammad da Malam Musa Shehu. Abokanin karatuna ma sun taimaka da shawarwari da addu’a na gode Allah Ya biya. Waɗanda ta hanyar basira da ilmi da kyakkyawar fahimtarsu na samu nasarar kammala wannan karatu.

Ba zan manta da Hakiman ƙasar Katagum ba, musamman Hakimin Itas da Hakimin Gamawa da Hakimin Sakuwa da Hakimin Gaɗau da kuma Hakimin Azare, da iyayen ƙasa na masarautar Katagum da kuma, Majalisar Masarautar Katagum wajen ba ni lokaci na musamman domin tattaunawa da su. Na gode Allah Ya saka da alheri, Amin. Gadiya ta musamman ga Sarkin Garinmu Alhaji Muhammadu Abdulkadir Madakin Zabi wanda ya taimaka wajen ba ni shawarwari da ƙarfafa mun guiwa wajen ganin kammaluwar wannan bincike, shi ma Allah Ya saka masa da alheri. Ina miƙa godiya ga Ma`aikatar ilimin Firamare ta Giyaɗe, Jihar Bauchi da ta taimaka mun wajen ba ni damar tafiya wannan karatu. Allah Ya saka da alheri.

Ba zan manta da abokaina ba, waɗanda suka ba ni shawarwari tare da taimako na ƙara ƙarfin guiwa kan wannan karatu. Musamman irin su Malam Abdullahi Zabi da Muhammad Abubakar (Khalifa) da Umar Barde da Alhaji Muhmood Abba da Abduƙadir Namangi da Ibrahim Ɗanbaba da Ja’afar Bello da sauran Malaman da suke Makarantar Firamare ta Baduware. Duk ina musu fatar Allah Ya saka da alheri.

Bayan haka, godiya ta musamman ga abokan karatuna na wannan jami`a ta Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato. Irin su Ahmad Garba Aliyu da Jibrin Yusuf da Alhaji Musa Abdulrahaman da Malam Imam Abdullahi da Hajiya Zara‘u da Shamsudeen Isma’il da ma sauran waɗanda ban ambaci sunayensu ba. Duk ina musu fatar Allah Ya sa mu haɗa wannan karatu lafiya, Ya sanya mana albarka a cikinsa.

Daga ƙarshe, ina miƙa godiyata ga mahaifana Malam Abubakar Wazirin Zabi da Hauwa’u Ahmad. Sannan da matata Maijidda Bello da ‘Yayana Khadiji Muhammad Jaɓɓello. da Salmanu Muhammad Jaɓɓello da Al’amin Muhammad Jaɓɓello da Ibrahim Muhammad Jaɓɓello duk ina musu fatar Allah Ya saka musu da alheri amin.

BABI NA UKU

BAUTA A ƘASAR HAUSA

3.1 Shimfiɗa

Wannan babin za a kalli bauta a ƙasar Hausa ta yadda za a duba muhimman abubuwa da dama. Masana da manazarta sun yi ta faɗi tashi wajen kawo mene ne ake nufi da bauta. Da kuma ra’ayoyinsu dangane da ma’anar bauta.

Maradun (1992:52). Bauta wata hanya ce da sarakunan ƙasar Hausa suke kamo mutane daga makwabtansu domin su yi musu wata hidima ta daban.

Ita kuma Waya, (2000:27). Cewa ta yi “kalmar Bauta ta samo asali ne daga dalilin kai hari ko kuma ganimar yaƙi, wasusnsu kuma a kan baiwa sarki gaisuwa”.

C.N.H.N (2006:42). Bauta kamar yadda ƙamus na Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya ya kawo, yana nufin hidimar da Bawa ke yi wa ubangidansa.

Khalil (2006:18). Bauta aba ce da Musulunci ya zo ya tarar ana yi bai hana ba. To amma ya yi mata gyare- gyare ya kuma ƙara tsara ta domin ta dace da rayuwar jama’a. Ko da yake sauran addinai su ma suna da bauta, to amma Musulunci ya fayyace hanyar da za a samu bayi da yadda za a ‘yanta su da kuma matsayinsu.

( Http://wiktionary.org ) Kalmar Bauta, cewa mutum ne wanda wani yake mallake da shi yake gudanar masa da hidimomin yau da kullum[1].

Wani lokaci akan danganta bauta da rashin ci gaban ƙasa ko al’umma tare da danne hakki. Kamar yadda Abubakar Ladan ya faɗa a cikin waƙar Afirikiya , ya nuna cewa saboda rashin ‘yanci shi ya hana Afirka bunƙasa, ga yadda ya ce:

                     Niyyar ‘yanci ya ta koka

                     A kudanci nan na Afirka.

 

                     Mai barci yau ka farka

                     Don karɓan ‘yanci ba shakka

 

   Komai ɗauri komai duka

   Afirka, Afirka, Afirkanmu

 

   Da ƙasa da ƙasa komai namu

   Fetur zinari darmammu

   Ga gwal, ƙarfe da kuzarmu

   Da azurfa dudda tagullarmu

   Muke iko da ma’adanmu

 

                                       A Dauloli kowa na murna

   Kyakkyawa mulki ya zauna

Bisa ga yadda masana da manazarta suka ce, za a iya cewa, bauta na nufin wata hanya ce, da mai Sarauta, ko mai ƙarfi a zamanin da, zai je wani gari ko cikin wata al’ummar da ba ta sa ba, ya ɗauko wani, ya mayar da shi bawa. Ko ya mallaki mutum kacokan ta hanyar saye ko kyauta ko yaƙi ko hari domin ya dinga yi masa hidimar yau da kullum; shi kuma ya ɗauke masa ɗawainiyarsa ta duniya baki ɗaya.

3.2 Zuwan Musulunci Ƙasar Hausa

Zuwan Musulunci ƙasar Hausa wani dogon tarihi ne wanda ya samu kulawar masana da manazarta na ciki da wajen ƙasar Hausa. Kasacewar bautar gargajiya ta sami gindin zama a wasu sassan na ƙasar Hausa har zuwa ƙarni na 14, bai hana addinin Musulunci ya sami kutsa kansa a cikin wannan yanki tun da jimawa ba. Tun daga kafuwar addinin Musulunci a ƙarni na bakwai, Musulunci ya ci gaba da yaɗuwa har lokacin da a wajejen ƙarshen ƙarni na sha ɗaya zuwa farkon ƙarni na sha biyu ya iso wasu daga cikin ƙasashen Afirka ta Arewa irin su Algeria, da Tripoli da dai sauransu. ‘Yan kasuwa waɗanda aka fi sani da Wangarawa ne suka shigo da Musulunci yammacin Afirka har zuwa daular Saifawa a Borno lokacin sarki Mai Humai. Musulunci ya zauna a wannan daula sama da shekara ɗari kafin daga bisani a ƙarni na sha uku da sha huɗu ya kutsa ƙasar Hausa a zamanin Sarkin Kano Yaji Ɗantsamiya (1349-1385), sun iske akwai ɓirɓishin addinin Musulunci a wannan nahiya. Yahaya, (1988:33)

Kafin addinin Musulunci ya shigo ƙasar Hausa sai da aka ƙaddamar da shi a nahiyar Hijaz, sannan ya watsu zuwa sassa daban-daban na duniya, gami da ƙasar Hausa. Daga gabas ta tsakiya addinin Musulunci ya ratso zuwa nahiyar Afirka da Turai, musamman sassan Magrib da Andalusiya. Addinin Musulunci ya barbazu a ko’ina, inda sannu a hankali ya zama addinin duniya. Daga Afirka ta arewa ne, Musulunci ya kutso kai zuwa yammacin Afirka ta amfani da aƙalla hanyoyin guda biyu muhimmai. Waɗannan hanyoyi sun amfanar ne ta hanyar hada-hadar ciniki da saye da sayarwa. A irin waɗannan tafiye- tafiyen ne Musulunci ya biyo ‘yan kasuwa zuwa wararen mazauna yammacin Afirka. Kuma duk da cewa ba Musuluntar da jama’a aka zo yi kai tsaye ba, amma sai da Musulunci ya sami wurin zama.

A lokacin da dakarun Al’murabid suka fatattaki Daular Ghana a shekarar (1076) ya jawo faɗuwar Daular aka maye ta da daular Mali. A wani zangon na mulkin Daular Mali, a zamanin hawan karagar Mansa Musa a (1240) ake jin cewa Musulunci ya bazu a kusan duk faɗin yankin Afirka ta yamma, ciki har da yankin da ake kira Nijeriya a yau. Malumfashi (2009:33)

Shigowar Wangarawa daga Mali (Malle) a zamanin Sarkni Kano Yaji (1339-1385) kamar yadda Malumfashi (2009) ya bayyana, cewa Musulunci ya ƙara samun gindin zama a ƙasar Hausa. Wangarawa sun sa hannu cikin harƙoƙin gudanar da mulki ka’in da na’in da kuma inganta ayyukan Musulunci ta fuskar Limanci da Ladanci da Alkalanci da rubuce-rubuce dangane da masallatai don bunƙasa Musulunci a wannan yanki. Malumfashi (2009:33)

A zamanin Sarkin Kano Yakubu (1452-1463) wasu gungun Fulani ɗauke da littattafai suka shigo ƙasar Hausa daga Mali (Malle). Shigowar waɗannan Fulani ya ƙara wa addinin Musulunci martaba da ɗaukaka a idon jama’a. A wannan lokaci ne aka inganta zuwa aikin Hajji, kuma ƙasar Hausa ta sake jaddada dangantakarta da sauran ƙasashen Musulumi da ke a gabas ta tsakiya. Haka abin ya dinga gudana har zamanin zuwan mashahuran Malamai masu wa’azi kamar al’Maghili.

Daga wannan zamani ne Musulunci ya bar fada, ya warwatsu cikin garuruwa da ƙauyuka na ƙasar Hausa. Ta haka ne ko da malamai irin su Al’maghili suka ziyarci garuruwan Katsina da Kano, sun iske ilimin addinin Musulunci ya ginu. Abin da kawai suka yi shi ne, ƙara rubuta littattafan addini, kamar waɗanda suka danganci sha’anin shari’a. Sannu a hankali Musulunci ya zaunu sosai a ƙasar Hausa Malumfashi(2009:34)

3.3 Zuwan Turawa Ƙasar Hausa

Kasancewar Turawa ba su shiga ƙasar Hausa a jahilci ba, domin suna da wata masaniya a kan mutanen wurin da kuma yanayin ƙasar. Tun a ƙarni na goma sha ɗaya ƙungiyoyi daga jinsin Turawa, sun aiko da masana don su binciki yadda ƙasashen Afirka suke da yadda al’adunsu ke gudana da yanayin harshensu da kuma addininsu. Sa’annan kuma su binciko hanyoyin sadarwarsu ta ruwa da ƙasa da kuma matakan da suke amfani da su ta fuskar ciniki da saye da sayarwa. Wannan ƙoƙarin sanin yanayi da al’ummar nahiyar Afirka da Turawa suka yi, ya kawo kakkafa ƙungiyoyin Turawa masu manufofi daban-daban. A Ingila an samar da ƙungiyar Afirka (Malumfashi 2009:36). Wannan ƙungiya ita ta turo da Mungo Park da Clapperton da Barth da Denham da ‘Yanuwa nan guda biyu, wato Landers Brothers, waɗanda suka ziyarci yankunan ƙasar Hausa.

Baya ga waɗannan ƙungiyoyin na neman sanin halayen da ƙasashen Afirka suke ciki, akwai kuma ƙungiyoyin Mishan da Turawa suka turo don bincike, musamman kan al’adu da harsuna da addinan ƙasashen Afirka a tsakanin ƙarni na 18-19 Shahararru daga cikin waɗannan ‘yan Mishan su ne: G.P Bargery, da J.F Schon da C.H. Robinson da Han Vischer da wasu da dama. Miller (1947:18-19). Ta fuskar ayyukan ‘yan leƙan asiri da Mishan ne daga cikin Turawa, labaran ƙasar Hausa da jama’arta suka isa Turai kai tsaye. Su kuwa ‘yan Mishan irin su Robinson da Miller da Richardson da Ryder da Burgin, sun sami isowa ƙasar Hausa kai tsaye bayan sun koyi harshen Hausa a Tripoli Miller (1947:17). Wasunsu sun zauna a sassan ƙasar na wani lokaci, daga baya suka koma gida suka bayyana abubuwa da suka gano, wasu kuma sun ci gaba da rayuwa a ƙasar suna ayyukan yaɗa addini.

A lokacin da Turawan Mulki suka zo ƙasar nan, sun karɓi mulki a tsakanin (1900-03). Turawa sun kafa mulkinsu, amma ba su kashe tsarin Sarauta da suka tarar ana gudunarwa ba. Ko da yake sun ɗan yi waɗansu sauye- sauye. Domin kasancewarsu ba ‘yan ƙasa ba; kuma mutane masu dabara don jin daɗin tafiyar da mulkinsu sai suka dinga gudanar da mulkin mutane ta amfani da sarakunansu, domin gudun tawaye da ƙoƙarin tafiyar da manufofinsu a cikin lumana.

A tsarin mulkin Turawa, bayan daular Usmaniyya an karkasa wannan ƙasa zuwa mulkin ɓangare- ɓangare da lardi- lardi wanda yake a ƙarƙashin gwamna Lord Lugard ne yake shugabancin gwamnonin ɓangare. Shi ne babban wakilin Ingila wanda yake sanar da Ingila yadda al’amurran mulki ke wakana a wannan ƙasar. Gwamnan ɓangare shi yake da alhakin tsara kasafin kuɗin shekara-shekara. A cikin kowane ɓangare a kan sami larduna da yawa. Bayan gwamnan ɓangare ya tsara kasafin kuɗin shekara-shekara yakan kai wa gwamna tarayya domin neman amincewarsa.

Zuwan Turawa ƙasar Hausa ya hana sarakuna gudanar da wasu hukunce- hukunce, misali kamar hukuncin kisa ko yanke hannu, amma bai hana su gudanar da wasu ba, kamar jangali da karɓar haraji da daidaita tsakanin mutane ko al’umma baki ɗaya. Zuwan Turawa mulki ya kawo wa sarakunan ƙasar Hausa wani sabon tsarin mulki. Koma bayan na da da ake amfani da hukuncin Allah da Manzo sallahu alaihi wasalam (Wato Shari’ar Musulunci). A lokacin kuma Turawa suka fara hana yin cinikin bayi da kuma bautar da mutane.

3.4 Asalin Bauta A Ƙasar Hausa

Bauta a ƙasar Hausa ta samo asali ne tun lokacin da ake yaƙe-yaƙe, tare da kai hari daga wannan gari zuwa wancan. Idan wannan gari ya samu galaba a kan wani sai a kama mutanen garin domin a mayar da su bayi. Sannan a kwashe dukiyarsu domin a kai wa sarkin gari.

Sarakunan ƙasar Hausa kan yi amfani da bayi maza da aka kamo musu a matsayin bayin gidan sarauta da kan yi aikace-aikace da dama a gidan sarki da fada. A wasu lokutan kuwa, sukan yi amfani da musamman bayi maza wajen musaya a lokacin da suke buƙatar sayen waɗansu abubuwa. Misali an yi wani lokaci da sarkin Kano ya taɓa aikawa da bayi Bida domin a kawo masa kayan doki. (Maradun 1992)

A wasu masarautun ƙasar Hausa, bayi na da matsayi na musamman wanda kowa yake da irin aikin da yake gudanarwa a fada ko gidan sarki. Wani lokacin ma a kan ba su muƙamai a mafi yawan masarautun ƙasar Hausa, domin amincewa da su da irin ƙoƙari da suke nuna wa idan an saka su wani aikin. Mafi yawan muƙamin da ake ba wa bayi za ka tarar wanda ya shafi tsaron ƙasa ne ko kuma kula da lafiyar sarki ko kuma iyalansa.

Akasarin bayi mata kuma a kan kai su ga sarakuna a wancan lokaci, wasu su aura; wasu kuma a tura su gidan ‘ya’yansa mata domin su dinga yi musu hidima, ko cikin gidan sarki domin yi wa iyalan sarki hidima ta yau da kullum.

3.5 Hanyoyin Mallakar Bawa

Hanyoyin mallakar bayi suna da yawa. Akwai waɗansu Shari’a ta amince da su. da kuma waɗanda gargajiyar Bahaushe ta amince da su. Waɗanda gargajiyar Bahaushe ta amince da su, ga su kamar haka:

1              Yaƙi- Ana iya mallakar bawa ta hanyar yin yaƙi. Duk wanda ya ci galabar ɗan uwansa, yakan kama duk mutanen garin dukkansu ya mayar da su bayinsa.

2              Kyauta- Wannan ita ma hanya ce da za a iya mallakar bayi da ita, wanda wani sarki na iya aika wa ɗan uwansa sarki kyautar bawa ko bayi, ko wani mai hannu da shuni ya kai gaisuwa ga sarki don girmamawa. Misali yadda Gwaggo uwar gida ta bayar da Gurzula kyauta a lokacin auren Marafa Ɗan Baba, domin aikace-aikacen yau da kullum.

3              Cira- Wannan hanya ce da ake iya samun bawa, ta yadda za a samu wani tsakar rana ya je wani gari ya ɗauko wani a kan doki da ƙarfi, ana bugansa har ya kai labari da haka.

4              Hari- Wannnan ma hanya ce ta mallakar bawa yadda idan wani gari sun kai hari a wani gari, suka kori mutunen garin duk wanda ya saura sai su ɗauki shi a matsayin bawa.

5              Saya- Wannan hanya ce da ake iya mallakar bawa ta hanyar saya. Idan mutum yana da kuɗi zai iya zuwa kasuwa da kuɗinsa ya saya, to in ya samu, to ya zama mallakarsa har abada. Misali a garin Sakkwato yadda Gwaggo Uwar gida ta sayo Gurzula Silai biyu a tsohowar kasuwan Sakkwato.

6              Biyan Bashi- Biyan bashi shi ma wata hanya ce ta mallakar bawa, wanda ake biyan bashi in ba shi da abin da zai biya ko ya biya da bawa ko shi kansa ya zama bawan.

7              Gado- Gado hanya ce ta mallakar bawa, wacce mahaifi ke mutuwa ya bar wa iyalansa. Wannan ma kamar yadda iyalai za su iya mallakar dukiyarsa haka suke iya mallakar duk bayin da yake da su.

            Waɗanda Shari’a ta amince da su kuma ga bayanin kamar haka: A zamanin Annabawa da suka gabata an samu wasu ƙabilu sukan bautar da mutanensu, a matsayin horo na laifi da girmansa ya kai miƙati; kamar sata da sauran ire-iren su. Misali irin wannan, kamar yadda ya zo a cikin suratul Yusufa. An bayyana cewa a lokacin da Annabi Yusufa yake ƙoƙarin riƙe ɗanuwansa. Sai ya sa aka saka zobensa a cikin awonsa. Bayan tafiyarsu aka kira su aka tuhume su, suka ce, su ba ɓarayi ba ne. Sai Annabi Yusufa ya yi musu tambayar cewa wanda duk aka sami zoben a cikin kayansa mene ne hukuncinsa? Suka ce shi ne hukuncinsa a bautar da shi. Ga ayar nan kamar yadda ta zo a cikin Alkur’ani mai girma:

Sai suka ce “Sakamakon wanda aka samu a kayansa shi ne sakamakon, kamar haka muke saka wa azzalumai” (Suratul Yusufa 75)

A zamanin Jahiliyya kuwa a kan yaƙi mutane a bautar da su don fin ƙarfi, ko kuma wanda bashi ya yi masa yawa a kansa, ba zai iya biya ba; shi sai a bautar da shi. To, amma da Musulunci ya zo sai duk ya hana wannan ya kuma takaita hanyoyin mallakar bawa kamar haka:

1-    Yaƙi

Yaƙi don ɗaukaka kalmar Allah Maɗaukaki yana ɗaya daga cikin hanyoyin mallakar bawa a Musulunci, kamar yadda ya zo a suratul Nisa’i:

 Ubangiji ya haramta muku katangaggun (wato masu mazaje,) sai abin da hannunku ya mallaka (na kuyangi, waɗanda aka ribato su a yaƙi). suratul nisa’i 24)

Yaƙi na ƙwatar kai, shi ma ana samun bawa ta sanadinsa. Misali a ce kafirai su auka wa musulmi, to ko don ƙwatar kansu da rayukansu dole ne su ma su yaƙe su kamar yadda Allah, maɗaukakin yake cewa:

“Idan suka yaƙe ku, ku yaƙe su. Wannan shi ne sakamakon kafirai” (Surah 2:191).

2-    Sayayya ko Biyan Bashi

Sayen bawa ita ma wata hanya ce ta mallakar bawa da Shari’a ta amince da ita. Haka ma za a iya mallakar bawa ta hanyar biyan bashi. Domin haka, za a iya ƙiyasi na kuɗi a kan bawa, kuma bawa zai iya zama a matsayin kuɗi. Shi ya sa za a iya biyan bashi da shi. Ashe ke nan wanda ya yarda aka biya shi bashi da bawa, wannan biyan bashin ya zame masa sanadiyar mallakar wannan bawa.

3-    Kyauta

Kyauta ita ma hanya ce ta mallakar bawa ko da kuwa shi mai ba da kyautar ba Musulmi ba ne. Misali Sarkin Masar Muƙauƙisu ya yi wa Manzon Allah Sallahu alaihi wa sallam kyautar Mariyatul Kifɗiyya

4-    Gado

A cikin hanyoyin mallakar bawa akwai gado. Idan mutum ya mutu ya bar bayi, to yadda za a raba dukiyarsa, haka za a raba bayinsa. (Amma ban da bayin waɗanda Ubangijinsu ya kulle (saɗaka) har sun haifu da shi). Shi ma bawa a matsayin dukiya yake, kuma a iya gadonsa shi da abin da ya mallaka.

5-    Haihuwa

Idan mutum yana da baiwa, to duk abin da ta Haifa na Ubangijinta ne, ko da kuwa aure ta yi da wanda yake ba bawa ba, kuma suka haifu. Wannan abin da suka Haifa bawa ne, domin ita bauta uwa take bi.

3.6 Hanyoyin Da Ake ‘Yan ta Bawa

Hanyoyin da ake ‘yan ta Bayi a ƙasar Hausa. Akwai hanyoyi da dama da Hausawa ke bi domin ‘yan ta Bawa. Ga hanyoyin Kamar haka:

1-    Fansa

Fansa na nufin ubangidan Bawa ya ɗora masa wani sharaɗi ya ce idan ka yi ka za ka fanshi kanka. Ya danganta da irin yarjejeniyar da suka yi. Matuƙar Bawan ya cika waɗannan sharuɗa na yarjejeniya to ya ‘yantu.

2-    Bawa ‘yantacce

Wannan kuma, ubangidan da kansa ya ga dama ya ce na ‘yanta ka, to wannan Bawa ya ‘yantu har tsawon rayuwarsa.

3-    Baiwa uwar ‘ya ‘ya

Uwar ‘ya’ya, wato idan ubangidanta ya haihu da ita, kuma Allah ya ɗauki ransa. Wannan Baiwa ta ‘yantu. Wato ta zama mai ‘yanci

4-    Bakance

Bakance shi ne ubangidan Bawa ya yi bakance da Bawa ya ce, idan ka za ya kasance zan ‘yanta ka. To! Wannan abin yana kasance wa Bawan ya ‘yantu.

Haka kuma, akwai hanyar da Musulunci ya sake kawo na ‘yanta da Bawa, waɗanda suka haɗa da:

i-             kaffarar kisa

ii-            Kaffarar rantsuwa

iii-          Kaffarar Zihari

iv-          Kaffarar Karya Azumi

Duk waɗannan hanyoyi Musulunci ya kawo su domin Bawa ya samu yanci. Shi Musulunci yana ƙara ƙarfafawa da a ‘yanta Bawa.

3.7 Cinikin Bayi A Ƙasar Hausa

Ƙasar Hausa da ma Nijeriya baki ɗaya, da wasu ƙasashen Afirka ta yamma sun zamanto a cikin wani yanayi na wannan ya kai wa wannan hari, wancan ya kai wa wancan hari. Har idan ɗaya ya sami galaba a kan ɗan uwansa ya kama mutanen garin tare da kwashe musu dukiya baki ɗaya. Mutanen idan Turawa daga Amirika da West Indian da Ingila suka zo, sai su dinga sayan bayin, amma cinikin ya kasace na musaya ne. Ba kuɗi za a bayar ba, Turawan kan zo wa da Sarakuna da Madubi ko Bindiga ko wasu makamai ko wani abu makamancin wannan. Su kuma su bayar da bayin kwatankwacin darajar abin da Turawan suka kawo musu.

Su kuma bayin da Turawan suka saya za a kai su Legas a tara su a Barakon (wato wani abu mai kama da kwantina), a jera su a layi; a sa musu turu a wuya wanda a cikin wannan kwantina nan za a ajiye su. Tsabar wahala nan wasunsu za su mutu, wasu kuma su kamu da cuttuka. Daga nan Legas za a ɗebe su sai ƙasar Turai. Idan an kai su can, za a kai su gonakai su dinga noman rake da abubuwan da ba sa nuna da wuri, kamar Mangoro da Kwakwa da sauransu. Bayan aikin gona kuma a kan kai su gidaje domin yin wasu aikace-aikace na cikin gida.

3.8 Gurbin Bayi a Masarautun Ƙasar Hausa

Sarauta a ƙasar Hausa tsohon al’amari ne wanda ya ɗauki shekaru da yawa ana aiwatar da shi a yankin, wanda sha’anin sarauta baya gudana yadda ya kamata har sai an yi maganar bayi a kai. Domin bayi suna taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da harƙoƙin mulkin a masarautun ƙasar Hausa.

Bayi a ƙasar Hausa suna da na su rawar da suke takawa a masarautun ƙasar baki ɗaya. Kamar yadda Maradun (1992:52). Ya ce “An so ma samun sarautun bayi a masarautun ƙasar Hausa tun a kusan ƙarshen ƙarni na goma sha takwas”. A lokacin ne aka fara naɗa bayin gidan sarki da kuma fadawa. Don haka, wannan aikin zai duba wasu masarutun da suke ƙasar Hausa kamar haka: Gobir da Katsina da kuma Kano, domin mu ga irin rawar da sarautun bayi ke takawa a masarautun ƙasar Hausa.

3.8.1 Gurbin Bayi Masarutar Gobir:

A masarautar Gobir, bayi na da gurbi na musamman ta yadda kowa yana da aikin da yake gudanarwa a fadar sarki. Wannan Sarauta ce da aka so ma ta tun lokacin da ake yaƙe- yaƙe da kai hare-hare a tsakanin wannan gari da wancan.

An kuma samu ci gaba da samun sarautun bayi a ƙasar Hausa har zuwan lokacin da aka samu canje-canjen zamani. Maradun (1992:52)

            A masarautar Gobir akwai bayin gidan Sarki da na fada da suka haɗa da, kamar yadda Bangon Gobir ya tabbatar:[2]

i-     Sarautar Galadiman gari

Galadiman gari shi ne uban gijiya (Bayi) wato shi ne shugaban bayi duk wani abu da za a yi a fada sai an sanar da shi. Kuma shi ne, wakilin bayi a fada. Ita wannan sarautar har yanzu aikinta yana nan, duk da sauye- sauyen zamani da aka samu.

ii-    Sarautar Baraya

Baraya shi ne mai kula da dukkan lamuran da suka shafi abin da yake tsakanin mutanen gari da sarki. Shi yake shige da fice tsakani. Ita ma wannan sarautar har yanzu aikinta yana nan, duk da sauye- sauyen zamani da aka samu ba ta canja ba.

iii-  Sarautar Bango

Bango shi ne mai kula da duk matsalolin da suka shafi cikin gidan sarki da bargar dawakin sarki. Ita wannan sarautar ta Bango har yanzu aikinta yana nan, duk da sauye- sauyen zamani da aka samu.

iv-  Sarautar Ajiya

Ajiya aikinsa ɗaya da Baraya akwai abubuwan da ake ba shi da ya yake kulawa da su, kamar ranar Sallah ko yaƙi ya kan ɗauko tambura ya miƙa wa sarki da hannunsa. Ita wannan sarautar Ajiya har yanzu aikinta yana nan, duk da sauyin zamani da aka samu.

v-    Sarautar Garkuwa

Garkuwa aikinsa a masarautar Gobir shi ne mai kula da dukkan garkuwar da take fada, kuma ko da yaƙi za a fita shi yake raba wa mutane garkuwa ya kan ce, idan an dawo ka kawo mun, in ka mutu magajinka ya dawo mun da ita. Wannan sarauta ta garkuwa aikinta ya ragu saboda yanzu ba a yaƙi, amma har yanzu yana da aikin da yake yi a fada. Duk da yake yanzu aikin da garkuwa yake yi mafi yawanci ya koma wajen Bango.

vi-   Sarautar Ma-ja- Sirdi

Kula da sirdin da sarki yake hawa shi ne babban aikin maja sirdi. Wanda idan an ɗaura sirdin ya kan zo ya saka hannu ya jijjiga ya ji ya ɗauru ko bai ɗauru ba. Idan ya ɗauru shi ke nan, in bai ɗauru ba ya kan ce a sake ɗaure shi. Sirdi kuwa ko da yaƙi za a je ko hawan Sallah dole ne maja- sirdi sai ya duba sirdin kafin hawan sarki. Shi ma a halin yanzu aikin ya koma wajen Bango, shi yake yin aikin da maja- sirdi yake yi yanzu. Amma in an zo hawan Sallah ya kan yi hawa shi asali wanda aka bawa sarautar maja-sirdi.

vii- Sarautar Barga

Barga aikinsa a fadar sarkin Gobir shi ne, bargar dawakin sarki shi yake kula da ita da ɗaukar ɗawaniyarta na kowane irin aikin ne. ita ma wannan sarauta akwai ta amma babu aikin.

viii-           Sarautar Shamaki

Shamaki shi jakada ne tsakani Barga da Sarkin Dawaki da magajin gida da sarkin zagi da uban turke shi yake kai kawo tsakani.

ix-  Sarautar Shantali

Lokacin da sarki zai fita wajen yaƙi ko wata lalura Shantali ne zai riƙe shantulan Sarki da sarki yana son ɗahara ko a wajen yaƙi idan shantali sai ya bawa sarki. A da a Gobir guda sha biyu suke da shi, amma yanzu bai wuce guda uku ba suka saura ba.

 

 

x-      Sarautar Shimfiɗa

Shimfiɗa shi mai kula da shimfiɗar sarki duk inda sarki ya je in zai zauna shimfiɗa ne yake yi masa shimfiɗa, amma yanzu saboda sauye- sauyen zamani yanzu aikin shimfiɗa ya kau saboda yanzu kujera ake sakawa.

xi-    Sarautar Majidaɗi

Majidaɗi ɗan mowa ne, wanda ke jin daɗi sarki wanda duk abin da ya nema gun sarki zai yi masa. Wanda haka ya sa duk wani abu in ana buƙata a gun sarki majidaɗi ake samu. Shi kuma ya kai buƙatar ga sarki.

xii-   Sarautar Magajin Madawa

Magajin Madawa yana cikin zarumai. Aikinsa a masarautar Gobir shi ne, idan sarkin bai samu damar zuwa wajen yaƙi ba sai ya wakilta shi, ya zama jagoran yaƙi, kuma ana tsammata masa nasara.

xiii- Sarautar Ƙuwaru

Sarkin kuwaru aikinsa shi ne, kula wa da kuwarun sarki duk lokacin da sarki zai yi amfani da su ya kan ɗauko ya ba shi su. Kuma shi ne yake yi wa sarki washi. Wato, kirari abin da ake nufi da Kuwaru shi ne, wasu takalma ne da ake sawa wanda suke zuwa har guiwa. Wanda ko harbi aka yi baya huda su.

xiv-  Sarautar Cina Barka

Cina barka yana tare da zarumai amma aikinsa shi ne yake ɗaukar sarki ya ɗora bisa doki.

xv-   Sarautar Sarkin Kanwa

Sarkin kanwa karkara gare shi, idan wani yana buƙatar gona wajen sa zai je ya ba shi, duka gonakai da dazuzzuka suna hannunsa ne. Duk wanda yake buƙata sai da izini sarkin kanwa, haka kuwa ko da sarki ne zai bayar da gona sai ya haɗa mutum da sarkin kanwa ya ba shi.

xvi-  Sarautar Sarkin Bazai

Sarkin Bazai aikinsa a fadar Gobir shi ne, yana cikin manyan dakarun yaƙi.

xvii-            Sarautar Sarkin Ƙofa

Sarki kofa ƙarƙashin sarkin bazai yake, amma babban aikinsa shi ne kula da ƙofofin gari, wajen buɗewa da rufewa. Kuma shi yake raba mutane masu kula da ƙofofin kullum.

xviii-           Sarakunan Zarumai

a)    - Sarautar Ƙyaure

Kyaure shi ma yana cikin dakarun sarki. Kuma duk kyauren da aka yi su, shi zai sa a kawo su.

b)    Sarautar Baran Makka

Shi ma Baran makka shi ne shugaban dakurun sarki wanda in ka ga an taɓa sarki sai dai bayan ransu.

c)    Sarautar Ara

Ara shi ma yana cikin dakarun sarki.

d)    Sarautar Tarno

Sarkin tarno aikinsa a fada shi ne mai kula da masaƙa da masaƙu da suke ƙasar, wanda idan sun saƙa idan sarki yana buƙata sai a kai masa. Yanzu wannan sarauta aikinta babu domin yanzu babu masaƙa.

e)    Sarautar Makoda

Shi kuma wannan babban aikinsa shi ne mai kula da masu sussuka da masissiku zai dinga za ga wa suna biyan kuɗi a matsayin haraji, har yanzu wannan sarauta ana amfani da ita.

f)     Sarautar Makama

Duk da yake wannan sarauta babu ita a ƙasar Gobir aronta a ka yi, amma tana cikin sarautun bayi. Babban aikin mai riƙe da wannan sarauta shi ne duk wanda ya yi laifi shi ake turawa domin kamo mai laifin.

g)    Sarautar Kibiya

               Babban aikinsa shi ne a lokacin yaƙi yana gaban sarki, kuma kwarensa akwai a ƙalla kibiya ɗari, kafin a kai ga sarki sai dai ba shi da rai. Haka kuma bayan an dawo zai zo ya tare ƙofar gidan ya hana sarki shiga har sai an zo an ce masa ya ara wa sarki gidan saboda shi yake gadin gidan. Nan za a ce za a sallame ka, shi kuma nan za a bashi kyautar arƙila ko kundumi wato zani ne irin na matan sarki.

h)    Sarautar Tsara

Tsara da kibiya aikinsu guda ne.

xix-  Sarautar Garangamau

               Shi ma yana cikin zarumai masu tsayawa gaban sarki, haka kuma shi ne mai bai wa sarki nishaɗi. Yana kuma faɗar gamtsi a gaban sarki kowanne iri ne.

xx-     Sarautar Masu

               Shi ne mai kula da masu, haka kuma shi ne yake sa ake ƙira su. Wanda idan za a je wajen yaƙi ko wani hawa shi yake raba wa mutane masu, amma in an dawo kowa zai dawo da su.

xxi-  Sarautar Lifida

               Shi ne shugaban masu lifida, wasu abubuwa ne kamar garkuwa wanda in za a fita yaƙi mayaƙa kan saka su a jiki, wanda duk harbin da aka yi bai samunsu.

xxii-            Sarautar Tamindau

               Babban aikinsa shi ne ba wa sarki magani na kafin jiki da sauran asirai na kariya.

xxiii-           Sarautar Uban Turke

               Uban Turki aikinsa shi ne, duk wani turke da yake nan shi yake da hakkin kula wa da shi, ko da kuwa a wajen yaƙi ne ko wata hidima ta dabam. Sayensa da kafa shi. Haka kuma shi yake da hakkin kula da ƙasar da ake saka wa dawaki ya tabbatar an zuba ta.

xxiv-           Sarautar Sarkin Zagi

               Sarkin zagi shi ne gaba ga sarki a kowane lokaci, haka kuma lokacin da sarki ya saka kafarsa ɗaya kan fangami shi ke tallafa masa ya ɗora shi kan doki. Haka kuma in dare ya yi sarkin zagi ke zuwa ya yi masa matsa. A ƙarƙashinsa akwai:

a)    Sarautar Sarkin Karma

               Sarkin karma shi ke kula da duka ‘yan tauri da ke ƙasar Gobir kuma yana ƙarƙashin sarkin zagi ne.

b)      Sarautar Sarkin Daji

               Sarkin Daji aikinsa shi ne, duk wani wanda yake harbin bindiga shi ne shugabansa. Shi ma yana ƙarƙashin sarkin zagi

xxv-Sarautar Tazal

               Babban aikin mai riƙe da wannan sarauta shi ne, dafa wa sarki magani da aka kawo ma sa.

xxvi-           Sarautar Sarkin Arna

               Aikinsu guda da Tamindau.

xxvii-         Sarautar Inna

               Shi ma aikinsu guda da tamindau da sarkin arna

xxviii-        Sarautar Saye

               Shi ma babban aikinsa shi ma kawo wa sarki magani buwaya da sauransu, amma aikinsu ɗaya da sarkin arna da tamindau da Inna.

3.8.2 Gurbin Bayi a Masarutar Katsina:

A ƙasar Katsina ma tamkar sauran masarautun ƙasar Hausa ne, wato akwai gurbin bayi a masarautar. Ana tunanin tun zamanin Sarki korau a 1445- 95. Aka fara naɗa masu riƙe da muƙaman bayi. Ga kaɗan daga cikin muƙaman bayi da suke Masarautar Katsina: Maradum (1992:25-27)

i-       Magayaƙi

Yana daga cikin manyan bayin sarki da ke kula da al’amurran da suke da dangataka da yaƙi.

ii-     Sarkin Bai

Shi yake taimaka wa magayaƙi.

iii-   Sarkin Yara

Yana ɗaya daga cikin mataimakan magayaƙi.

iv-   Ajiya

Ajiya wannan shi yake ajiye kayayyaki tare da kuɗi.

v-    Baraya

               Shi yake kula da wajen kwanciyar Sarki (Baraya). Aikinsa ne ya tabbatar da harabar baraya tana tsabtace a kowane lokaci. Haka kuma shi yake kula da kayan da suke cikin baraya tare da dabbobi.

vi- Sintali

                 Wanda ke riƙe da wannan muƙamin ana masa kirari da “Shantali na Bayin sarki”. Babu lokacin da za a ga sarki ba a ga Shantali ba. Abin da kawai yake raba Shantali da Sarki shi ne bacci. Haka kuma Shantali shi yake da alhakin ajiye butar sarki.

vii-           Turaki

                 Yana ɗaya daga cikin fadawan sarki da a kan sa su ayyuka na musamman.

viii-         Kashaka

                  Yana daga cikin yaran sarki da yakan sanya su ayyuka a lokacin da yake buƙata.

ix- Ɗankafi

                 Aikinsa kula da wajen bizne mutane.

x-   Ubandawaki

                 Shi yake kula da dawaki.

xi-Sarkin Karma

                 Shi ne shugaban ‘yan tauri

xii-          Sarkin Baka

                 Yana kula da masu harbin baka.

xiii-        Sarkin Bindiga

                 Yana kula da maharba Bindiga.

 

xiv-        Sarkin Zagi

                 Shi ne shugaban Dogarai

xv-           Ganuwa

                 Shi yake kula da ƙofofin Shiga birni, tare da tabbatar da tsaro.

                 Wannan shi ya tabbatar mana da cewa a masarautar Katsina matuƙar aka fitar da bayi a sha’anin mulki lallai, babu wani abun da ya saura na daga mulkin. muƙaman bayi suna taka muhmiyyar rawa wajen bunƙasa da kyautatuwar mulki da tsaro a duk masarautun da suke ƙasar Hausa.

3.8.3 Gurbin Bayi a Masarautar Kano:

A ci gaba da bayanin yadda gurbin bayi suke a masarautun ƙasar Hausa, da yadda suke gudana a sassa daban-daban na ƙasar, kamar yadda wata Malama Zara’u Ibrahim Waya (2000) masaniyar tarihi da al’adun masarautun Kano ta yi bayanin Muƙaman sarautun bayi kan taimakawa sarkin Kano wajen al’amurran mulki. Malamar ta yi bayani game da yadda tsarin sarautun bayin suke a shekarun baya da kuma yanzu. Sarautun bayin Sarkin ma hawa-hawa ne. galibi an fi ba manya daga cikinsu sarautu na musamman wanda yake kuma mataimaka za su riƙa taimaka masa wajen gudanar da ayyukansa. Manya bayi sarkin Kano su ne:

1-      Shamaki

2-      Ɗanrimi

3-      Sallama

Waɗannan bayi su ne manyan bayin sarki kuma kowanne daga cikin su yana da hakimansa a ƙarƙashinsa. Khalil (2006:32)

1-    Shamaki ne babba a cikin bayin Sarki, wanda saboda haka ne ake masa kirari da “Shamaki Korau kan bayi”. Babban aikinsa shi ne kula da tsakanin hakimai da Sarki. Shi ake fara gani kafin sarki ya fito daga cikin gida, kuma shi ke yi wa mutane iso ga sarki. Kowanne hakimi in zai gaida sarki sai da saninsa. Haka kuma da Shamaki ake kama kafa idan ana neman wata sarauta a gun sarki. Haka kuma duk wata Magana da ta shafi hakiman ƙauyuka to Shamaki ne ki shigar da maganar gun sarki.

Idan sarki ya zauna a fada, Shamaki ne yake fara yin gaisuwa, sannan sauran jama’a su yi. In za a tsawatarwa mutum a fada shi ke yi. Kuma shi ke zama gaban motar sarki yana riƙe da sandar sarki, in kuma a kan doki sarki yake, shamaki yana dab da shi.

Akwai wasu ayyuka da dama waɗanda suke a ƙarƙashin mulkin Shamaki, amma ba shi ne yake aikata su ba, kamar aikin da ya shafi gini da ƙira da dukanci da sauransu, hakiman da suke ƙarƙashinsa ne ke yi. Hakiman kuwa sun haɗa da:

1-      Ciroman Shamaki

2-      Sarkin Lifida

3-      Madakin Shamaki

4-      Maƙaman Shamaki

5-      Sarkin Malafa

6-      Turakin Shamaki

7-      Sarkin Hawa

8-      Sarkin Dukawa

9-      Sarkin Maƙera Farfaru da babbaƙu

10-  Uban Dawaki

11-  Sarkin Ruwa

12-  Maja Sirdi

13-  Sarkin ƙofa

14-  Sarkin Busa.

Waɗannan hakimai da aka zayyana su a sama ƙananan hakiman Shamaki ne, kuma duk gidansa suke zaune. Shi ne mai kula da su, ya kuma ba su umarnin gudanar da duk wani aiki da ya ta so. Haka kuma akwai manyan hakimansa waɗanda suma suna da mataimaka a ƙarƙashinsu, kamar haka:

Magajin Aska

Magajin aska muƙami ne da yake a masarautar Kano, wanda aikinsa shi ne, yi wa sarki aski da yi masa ƙaho idan buƙatar haka ta ta so, da yi wa ‘ya ‘yan sarki kaciya da yi musu ɓalli-ɓali. Duk waɗannan Magajin aska ne kawai ke yin su.

A ƙarƙashin Magajin aska yana da mataimaka don aikinsu shi ne, su tabbatar sun biya buƙatar duk wani bafade da yake cikin fadar, amma wanda ya shafi sana’arsu. A cikinsu akwai:

1-      Galadiman Aska

2-      Madakin Aska

3-      Ciroman Aska

4-      Makaman Aska

5-      Turakin Aska

Babban Zagi

Babban zagi shi ma yana ƙarƙshin Shamaki ne, kuma shi ne shugaban zagagen sarki. Babban aikinsa shi ne idan za a yi hawa ya jera zagagen nan goma sha biyu a gaban sarki. Shida daga gefen Shamaki, biyar a hannun Ɗanrimi, guda gefen sallama. Haka kuma idan sarki zai hau ko sauƙa daga kan doki babban zagi shi ne zai dafa masa.

Babban zagi shi ma yana da muƙarrabai a ƙarƙashinsa, kamar haka:

1-      Galadiman zagi- yakan rataya koriyar alkyabba kuma ya riƙe wuƙa da taƙobi. In sarki ya buƙaci amfani da su, Galadima ya kawo.

2-      Makaman Zagi- Makaman Zagi shi ne na uku a gaban sarki, shi yake riƙe da sandar girma.

3-      Turakin Zagi- Turakin Zagi shi ne ya ke riƙewa makaman zagi aikinsa idan wata lalura ta faru.

4-    Wazirin Zagi.- Yana rataya bargo, sannan ya riƙe buta a hannunsa. Kuma haƙƙinsa ne kula da yadda aka gyara doki da sarki zai hau. Kuma idan sarki ya sauƙa shi zai je ya ɗaure dokin.

Masu

Masu, shi ne ƙarshen zagagen da ke gaban sarki, shi ne yake riƙe da tagwayen masu a hannunsa, yakan rataya bargo ya riƙe takalman sarki waɗanda idan ya sauƙa daga kan doki zai sanya.

Madakin Zagi

Madakin zagi kan rataya bargo ya riƙe buta a cike da ruwa a ciki, hikimar yin haka shi ne, idan sarki ya nemi biyan buƙata cikin halin tafiya ba sai an nemo ba.

Sarkin Gini

          Yana cikin manyan hakiman Shamaki, babban aikinsa shi ne kula da gine-gine da suke a gidan sarki. Yana da muƙarrabai kamar haka:

1-      Madakin gini

2-      Makaman gini

3-      Galadiman gini

4-      Ciroman gini

5-      Turakin gini

Sarkin Kyankandi

          Sarkin Kyankyandi shi ma yana ƙarƙashin Shamaki ne, babban aikinsa shi ne ɗaukar kyankyandin kaya idan sarki zai yi hawa ko tafiya a kan ko da sarki zai buƙata ko ya yi kyauta da su. Shi ma yana da muƙarrabai a ƙarƙashinsa, kamar haka:

1-      Galadiman Kyankyandi

2-      Turakin kyankyandi

3-      Ciroman kyankyandi

4-      Madakin kyankyandi.

Sarkin Tamburra

Sarkin tambura, shi ma yana ƙarƙashin Shamaki; babban aikinsa shi ne kaɗa tambura idan an naɗa Sarki ko ana hawan Sallah. Ga muƙarrabansa kamar haka:

1-      Makaman tambura

2-      Ciroman tambura

3-      Turakin tambura

4-      Galadiman tambura

2-    Sarautar Ɗanrimi

Sarautar Ɗanrimi, sarauta ce daga cikin sarautun bayin sarki. Daga Shamaki sai Ɗanrimi a kan darajar muƙami. Aikin Ɗanrimi ya fi yawa a fada, bayan haka kuma shi ne yake kula da gidajen sarki da suke waje, kamar gidan Fanisau da Ɗorayi da na Nasarawa. Haka kuma gonakin sarki duk suna hannun Ɗanrimi ne duk aikin da za a yi shi ke da hakkin kula da su.

A cikin gida kuma aikin Ɗanrimi shi ne, kula da inda sarki ke zama a ƙofa ta arewa a lokacin zaman fadanci. Haka kuma, a zamanin Turawa shi ne manzon sarki tsakaninsa da Rasdan. Haka kuma yanzu da babu Turawa aikinsa yakan je wajen gwamna ya sanar cewa sarki yana zuwa. Kuma ranar Sallah in shamaki baya nan shi ke shigowa da hakimai domin gaisuwa. A lokacin hawan Sallah kuma yana kusa da shi ta ɓangaren hagun. Muƙarrabansa sun haɗa da:

1-      Madakin Ɗanrimi

2-      Barden Ɗanrimi

3-      Ɗansarai

4-      Sarkin tukurwa

 

 

 

 

Sarkin Dogarai

          Sarkin dogarai shi ne kamar wakilin doka, kuma yana da dogarai da yawa a ƙarƙashinsa. Aikinsa duk wanda ya gagara ko ɓarawo ko wani mai laifi to shi ake turawa ya zo da shi. Haka kuma a lokacin yaƙi shi da Madaki ne ke kan gaba. Babban aikin sarkin dogarai da yaransa shi ne tsaron lafiyar sarki da iyalansa. Ga muƙarrabansa kamar haka:

1-      Makaman Dogarai

2-      Madakin Dogarai

3-      Sarkin yaƙin Dogarai

4-      Turakin Dogarai

3-    Sarautar Sallama

Sarautar Sallama tana daga cikin manyan bayin sarki, wanda daga Ɗanrimi sai sallama, a kan yi masa kirari da “ sallama alkhairin Bayi”, domin shi ba a yi masa gefe a gidan sarki, ko’ina ya iya shiga komai dare idan ya zo da magana za a buɗe masa ƙofa ya ga sarki. Sallama ake gayawa idan ana buƙatar buga bindiga shi kuma ya sanar da sarkin bindiga. Haka kuma idan sarki yana zaune a majalisa idan wata Magana ta ta so ta cikin gida sallama ake yi wa ita ya gabatar da ita.

Har ila yau Sallama shi ke raba abinci in sarki ya yi tafiya, kuma duk wata kyauta ta sarki shi ke raba wa. Idan sarki ya yi niyyar yin kyauta a wani talaka ko malami sallama ake ba wa ya bayar da ita. Kuma sallama shi ke shigar da ƙara a gaban sarki. Yana da hakimai kamar haka:

1-      Mabuɗi

2-      Barden sallama

3-      Kilishi- Kilishi shi ke kula da shifiɗar sarki, duk idan sarki zai zauna kilishi ne zai masa shimfiɗa.

4-      Magajin Ɗankama-

5-      Maitari- shi ne shugaban ‘yan bindiga, shi yake ba da alburusai da kuma umarnin buga bindiga idan ana buƙata.

Ta la’akari da waɗannan, su ne za su tabbatar mana da cewa lalle bayi suna da gurbi a masarautar Kano da ma sauran masarautun ƙasar Hausa baki ɗaya.

3.9 Haramta Cinikin Bayi

Haramta cinikin Bayi a duniya baki ɗaya, abu ne da aka fara shi shekaru da dama. Wanda Musulunci ya tarar ana harkar bauta a duniya. Addinin Musulunci ya ba da gudumawa wajen kashe cinikin bayi a duniya baki ɗaya. Wanda kullum Musulunci kwaɗaitar wa yake a kan a ’yanta bayi kamar yadda Allah (S.W.A) Yake cewa a cikin suratul Mujadala aya ta uku

Waɗanda suka zihari a matayensu sannan suka dawo kan abin da suka faɗa a baya za su ’yanta baiwa muminakafin su shafi matansu. Wannan kuma ana yi muku wa’azi ne da shi. Allah mai ba da labari a kan abin da kuke aikatawa.

Wannan ayar tana nuna cewa duk mijin da ya kwatanta matarsa da mahaifiyarsa to zai ’yanta bawa, da wannan ya tabbatar da cewa musulunci shi kullum ƙarfin guiwa yake bayar wa a kan a ’yantar da bayi ba wai a bautar da su ba.

 

Haka kuma, Allah Ya sake cewa a cikin suratul Ma’ida aya ta 89 Allah ba ya kama ku saboda yasassa a cikin rantsuwoyinku, kuma amma Yana kama ku da abin da kuka ƙudurta rantsuwoyi (a kansa). To kaffararsa ita ce ciyar da miskini goma daga matsakaicin abin da kuke ciyar da iyalanku, ko kuwa tufatar da su, kokuwa ’yantawar baiwa munina. Sa’an nan wanda bai samu ba, sai azumi kwana uku. Wannan ne kaffarar rantsuwoyinku idan kun rantse. Kuma ku kiyaye rantsuwoyinku kamar wannan ne Allah Yake bayyana muku ayoyinSa, tsammaninku kuna godewa.

Haka kuma, Allah yana cewa duk wanda ya rantse to zai ciyar da abinci ga miskinai guda goma, abincin ma irin wanda yake amfani da shi, ko kuma ya tufatar da su. Idan haka ba ta sa mu ba to sai ya ’yanta bawa. Wannan ma ya nuna cewa musulunci kullum hani yake a kan bauta.

Haka a cikin suratul Nisa’i aya ta 19 Allah cewa ya yi bai kasance ba ga mumini ya kashe mumini, sai dai a kuskure duk wanda ya kashe mumini a kuskure zai ’yanta baiwa mumina, sannnan zai ba da diyya a iyalansa, sai dai iyanlan sun yafe. Idan kuma mutum ya kasance yana daga cikin maƙiyanku kuma mumini ne ba musulmi ba sai ya yi Kalmar shahada idan haka ta faru za a ’yanta baiwa mumina. Idan wanda aka kashe ɗan tsakanin akwai alƙawari za a ba da diyyar ga iyalansa sannan za a ’yanta baiwa mumina, idan kuwa mutum bai samu damar baiwa ba zai yi azumi wata biyu a jere don neman gafarar Ubangiji. Allah Ubangiji ya kasance akwai shi da hukunce- hukunce da yawa.

Haka kuma, wannan ayar ma haka ta nuna cewa duk wanda ya kashe mumini da gangan to zai ’yan bawa, sannan bayan ya ’yan bawa zai bawa iyalan mutumin diyar ran da ya kashe, sai dai idan iyalan mutumin sun yafe masa to wannan babu laifi.

 

Haka kuma akwai Hadisai daga Manzon Allah sallalahu alaihi wassalam da suke ƙara tabbatar da cewa musulunci ya ba da gudumawa wajen hana bauta a duniya baki ɗaya. Kamar yadda ya ce a cikin Sahihul Bukari

An karɓo daga Muhammadu Ɗan Musana Al’nazi daga Yahya Ɗan Sa’id daga Abdullahi Ɗan Sa’id ana ce masa Ibn Abi Hundu an karɓo daga Isma’il bin Abu Hakim daga Sa’idu bin Murjana daga Aba Huraira shi kuma daga Manzon Allah Sallahu alaihi wassalam ya ce duk wanda ya ’yanta mumina Allah zai ‘yanta dukan gaɓa daga gare ta zuwa shi daga wutar Jahannama

 

Haka kuma, daga Abu Huraira cewa Manzo Allah Sallahu alaihi wassalam yana cewa duk musulmin da ya ’yanta musulmi Allah zai kuɓutar da gaɓoɓinsa daga wutar Jahannama.

Duk waɗannan suna nuna muhimmancin ’yanta bayi, da irin yadda musulunci ya ba da gudumowa wajen haramta cinikin bayi a duniya, har Allah Ya yi alƙawarin aljanna ga wanda ya ’yanta. Saboda shi addinin musulunci so yake a ’yantar da Bawa. Shi musulunci bai taɓa cewa a yi bauta ba sai dai a ’yanta. Wannan ita ce hanya ta farko da ta fara taimakawa wajen kashe bauta ko cinikin bayi a duniya baki ɗaya.

Daga baya kuma, a shekarar (1787) an samu wasu Malaman kirista suka haɗa kwamiti wanda Reverend Thomas Clarkson da Wilberforce wanda su ne suka jagoranci tafiyar suka fara yin wa’azi suna cewa duk mutum dai-dai yake da ɗanuwansa ɗan Adam. Wannan zalunci ne a dinga bautar da mutane. Kwance-ta-shi har ya samu ma goya baya suka dinga yaƙar take haƙƙin bil adama da wayar da kan mutane daga wannan mugunyar hanya a duniya baki ɗaya. (Crowder 1981:33)

An samu waɗansu mutanen Afirka da suke zaune a Ingila su biyu waɗanda suka yi rubutu mai take Thought and Sentiment on slavery in 1787. Da Olaudah Equiano wanda aka fi sani da Gustavus Vassa sun yi rubutun ne aka irin yadda ake gudanar da kasuwar bayi a Afirka. Bayan shekara 21 a ka samu wasu gungun mutune su ma masu yaƙi da sayar da bayi.

 Haka kuma akwai lokacin da ‘yan majalisar Ingila suka gabatar da ƙudirin haramta cinikin bayi a shekarar 1807 wanda suka kafa kwamiti mai ƙarfi. Wanda suka kafa wata kotu a Sierra Leone a ƙarƙashin vice Admiral duk wanda aka kama dajirgi ya ɗauko bayi za a yi masa hukunci a nan.

Sai kuma wani dalilin Haramta cinikin bayi a duniya da ma ƙasar Hausa baki ɗaya. Ita ce Industrial Revolution wato, ci gaban zamani da aka samu ta fuskar ƙere-ƙere a ƙarni na sha takwas. Wannan hanya ta taimaka ainun wajen kawo ƙarshen cinikin bayi gaba ɗaya. Domin sun gano cewa a wancan lokaci aikin da inji guda zai yi a rana ɗaya tafi ta bayi dubu da za su yi kwana biyu zuwa biyar suna yi. Da suka fahimci haka sai suka ga cewa bayin ba su da wani sauran amfani a gun su. Sai kuma aka shiga hidimar mayar da bayi daga wajen da suka fito. A wannan lokacin aka kai su Laberiya da kuma Saliyo.

Waɗannan hanyoyi su ne suka taimaka wajen daina saye da sayarwa da ake yi wa Bayi a ƙasar Hausa dama duniya baki ɗaya.

3.10 Naɗewa

A cikin wannan babin da ya gabata an tattauna muhimman batutuwa da suka shafi bauta a ƙasar Hausa. Wanda mun duba zuwan Musulunci ƙasar Hausa da kuma zuwan Turawa Nijeriya. Sannan kuma aikin ya duba me ake nufi da bauta da kuma asalin bautar a ƙasar Hausa, da kuma hanyoyin mallakar bawa da kuma ‘yanta shi. Daga bisani aka duba gurbin bayi a masarautun ƙasar Hausa domin duba irin rawar da suke taka wa. Da cinikin bayi yadda ya gudana da yadda aka Haramta cinikin bayi.



[1] Wannan an samu shi ne daga shafin yanar gizo ranar 14/07/2016 www.wiktionary.org

 

[2] Hira Abubakar Bangon Sarkin Gobir, a gidansa da misalin karfe 12:02pm 14/01/2017

Post a Comment

0 Comments