𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
mene ne
hukuncin mace ta zo wajen saurayinta ba tare da tasa hijab ba?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Asali dai
shari'a ta umarci Maza da Mata su rintse idanunsu ga barin yiwa junansu kallo
irin na sha'awa kamar yadda Allah(ﷻ) ya fada:
قل للمؤمنين يغضوا
من أبصارهم ويحفظوا فروجهم ذالك أزكي لهم………إلخ
MA'ANA:
(Ya
Muhammad(ﷺ) ka gayawa Muminai (Maza) su rintse idanunsu kuma su kiyaye
farjinsu, hakan shi ne yafi tsarkaka a garesu………
To amma
shari'a ta yi izini ga mai neman aure ya kalli matar da ya ke so ya aura, to
sai dai kuma Malamai sun yi saɓani dangane da cewa ina ne iyakar gwargwadon
inda ya kamata maneminta ya kalla a jikinta? Wasu daga cikin Malamai sai suka
tsananta da yawa sukace bai halatta a ga komai a jikintaba, wasu Malaman kuma
sai suka sassauta da yawa, sukace ya halatta a ga komai a jikinta amma banda
tsiraicinta kaɗai, daga cikin hujjarsu akwai wannan Hadisi na Manzon Allah(ﷺ)
da ya ke cewa:
إذاخطب أحدكم
المرأة فإن استطاع أن ينظر إلي ما يدعوه إلي نكاحها فليفعل،
Ma'ana:
Idan dayanku
yana neman mace da aure, to idan ya samu ikon ya kalli abinda zai ja hankalinsa
ya aureta to ya aikata (ya kalla):
Sannan kuma
akwai Malaman da suka tsaya a tsakiya, wato ba su tsananta da yawa ba kuma ba
su sassauta da yawa ba, wanda ko shakka babu mafi yawa daga cikin Malamai sun
tafi ne a kan wannan ra'ayi na tsaka-tsakiya, daga cikin hujjarsu akwai wannan
aya da Allah(ﷻ) ya ke cewa:
ولا يبدين زينتهن
إلا ما ظهر منها.
Ma'ana:
Ka da Mata
su bayyana adonsu sai dai abinda ya ke bayyanan ne daga ciki. (Fuska da tafin
Hannu):
Danhaka
Malaman da ke Mazhabobin Malikiyya, Shafi'iyya, da kuma Hanafiyya. sukace
iyakar fuska da tafukan hannu kaɗai ya halatta manemin aure ya gani, su kuma
Mazhabin Hanabila sukace ya halatta a kalli dukkan gurinda a bisa ga al'ada
yakan bayyan a ganshi a jikinta, wato kamar wuyanta, hannayenta, kafafuwanta,
da kuma gashin kanta. Musamman ma yayinda mace ta ke cikin gida tana yin wasu
'yan aikace-aikace irin na cikin gida.
To amma
maganar da tafi inganci kuma tafi dalilai masu Ƙarfi kamar yadda mafi yawan
Malamai suka rinjayar ita ce, ya halatta mai neman aure ya kalli fuskarta da
tafukan hannayenta da wuyanta, da duga-duganta, da kuma gashin kanta in buƙatar
hakan ta kama, sai dai wasu Malaman sukace idan ya kalla sau ɗaya shikenan ya
wadatar daga nan bai halatta ba ya sake kallo. amma wasu Malamam sukace ya
halatta ya mai-maita kallonta idan buƙatar hakan ta kama, ko da kuwa ba tare da
tasan yana kallonta ɗin ba, sai dai bai halatta ya yi mata kallo irin na
sha'awa ba wanda zai sa shi yaji daɗi a ransa. Sannan wannan hukuncin yana
tabbatuwa ne a kan Mutumin da ya zo neman aure tsakaninsa da Allah da gaske
yakeyi ba wai da wasa ko yaudara ya ke yi ba, sannan yana da tabbas ko kuma
zato mai rinjaye na cewa idan ya nema za a karɓeshi a yarda da da shi.
Sannan da
sharaɗin ya kasance babu wani wanda yake nemanta a baya da har suka riga amince
da shi a kan ya nemeta, saboda Manzon Aʟʟāн(ﷺ) ya hana wani ya nemi aure a kan
neman wani:
шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'αʟαмυ
Mυѕтαρнα Uѕмαи
08032531505
Ga Masu Buƙatar
Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/DIcJIƘrWyLP0oBOMSnDi5P
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.