𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
Alaikum. lna kwana malam barka da warhaka Malam don Allah haske nake son a kara
min akan Azkar da abubuwan da ake faɗa yayin Azkar, na gode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus
salam, to ita dai kalmar Azkar kalmace ta Larabci, kuma jam'i ne na kalmar
Zikir, wadda ke da ma'anar ambato, ko tunawa dasauransu. Amma a Musulunci idan
aka ce Azkar (أذكار) ana nufin zikirori da suka ƙunshi karatun Alƙu'ani da
addu'o'i da salatin Annabi ﷺ da istigfári da kuma abin da ya jiɓanci hakan.
Mafificin
zikiri shi ne karatun Alƙu'ani mai girma, duk wani zikiri da mutum zai yi yana
bayan karatun Alƙur'ani mai girma ne. Kuma Allah Maɗaukakin Sarki ya yi umurni
da yin zikiri a wurare da dama a cikin Alƙur'ani mai girma daga ciki sun haɗa
da inda Allah yake cewa:
1- "Ya
ku waɗanda suka yi imani ku ambaci Allah ambato mai yawa".
Suratul
Ahzáb: 41.
2- "Ku
ambace ni zan ambace ku, kuma ku gode mini kada ku kafirce min".
Suratul Baƙara:
152.
3- "Ku
roƙi gafarar Ubangijinku, sannan ku tuba zuwa gare shi".
Suratu Huud:
3.
4- "Ku
roƙi gafarar Allah, lallai Allah mai gafara ne mai rahama".
Suratul Baƙara:
199.
Ku roƙi
gafara a nan ana nufin ku yi istigfári. Daga cikin zikirori akwai zikirin
Safiya da Yammaci, da zikirin kwanciya barci da na tashi daga barci, da na
shiga banɗaki da na fita, da zikirin shiga gida da na fita, da zikirin hawa
ababen hawa, sannan akwai zikirorin da ake yi bayan an idar da sallar Farillah,
don samun zikirorin da ake yi bayan an idar da sallar farillah sai a duba
Amsoshin Tambayoyinku na 144, sai kuma a duba amsar tambaya ta 123 don samun
zikirin da ake yi idan mutum ya shiga matsananciyar damuwa ko baƙin ciki.
A tambaya ta
003 kuma za a sami addu'ar da Manzon Allah ﷺ kan yi wa mamaci. Sai kuma a duba
tambaya ta 010 don samun addu'ar Istikhara, tambaya ta 023 za a sami addu'ar
neman tsari da ake yi wa ƙananan yara, idan aka dubi tamabaya ta 047 kuma za a
sami addu'o'in warware sihiri, idan aka duba tamabaya ta 054 za a sami addu'ar
da ake karantawa idan wani ɓangare na jikin mutum yana ciwo.
Duka waɗannan
a taƙaice ne, ki tintuɓi ingantattun malaman Sunnah don samun zikirori
ingantattu na Manzon Allah ﷺ. Kuma ki nemi littafin GARKUWAR MUSULMI, wato
(HISNUL MUSLIM), shi ma za ki fa'idantu ba ɗan kaɗan ba, saboda nan ba zai yiwu
a iya kawo maki zikirorin nan yadda suka dace ba, sai dai kawai a yi taɓa ka
lashe a nan.
Allah S.W.T
ne mafi sani.
Jamilu
Ibrahim Sarki, Zaria.
Ga Masu Buƙatar
Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.