𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum mallam na
kasance mai aiki a unionbank na wata shida a shekara sai na huta na wata shida
, ba a biya na salaryi dan ina hutu. to kwanakin baya na saurari wani scholar
yana bada fatawa cewa babu kyau musulmi ya yi aiki a banki wai ko da aikin
security ne. haramu ne saboda akwai haramci a ayukan da banki keyi kaman bayar
da bashi kuma abiya da kuɗin ruwa help me out saboda yanxu lokaci ya kai wanda
zan koma bakin aiki amma ina tsoron ciyar da iyali na da haramu
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus salam Warahmatallahi
Wabarkatahu
Indai irin bankunan da suke
amfani da kuɗin ruwa ne, to bai halatta ka yi aiki a cikinsu ba. Ta kowacce
fuska.
Hujjah anan ita ce Hadisin Jabir
bn Abdillah Al-Ansary (ra).
"Manzon Allah ﷺ ya tsine wa
mai cin Kuɗin ruwa, da mai bayarwa, da mai rubutawa, da mai shaidawa. Yace
Dukkansu daidai da daidai suke a cikin laifin (zunubin).
(Sahihu Muslim, Hadisi na 1598).
A cikin Sharhin da ya yi ma
wannan hadisin, IMAMU SHARAFUDDEEN AN-NAWAWY (rah) ya ce: "Wannan hujjah
ce Ƙarara wacce take nuna haramcin yin aikin rubutu ko shaidawa a cikin duk
wata hulda tsakanin mutum biyu masu cinikin kuɗin ruwa. Kuma ya nuna haramcin
taimakawa wani a cikin Aikata saɓon Allah".
Babu makawa duk mutumin da yake
aiki a irin waɗannan bankunan dole ne zai taka rawa a cikin harkar kuɗin ruwa.
Ko mai gadi ne, ko mai shara ne,
ko Clerk ne. Sannan kuma dole ne abiyashi albashi da kuɗin ruwa.
Don haka gara ka nemi wani aikin
mai tsafta.
"Duk wanda yaji tsoron
Allah, to Allah zai sanya masa Mafita. Kuma zai azurtashi ta inda ba ya zato.
Duk wanda ya dogara da Allah, to shi Allah ɗin zai isar masa"
(Suratul-Talaƙ ayah ta 2 - 3).
WALLAHU A'ALAMU.
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan
Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.