𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum, Malam da fatan duk kuna nan lafiya, don Allah tambayata ita ce: mene ne hukuncin zagin zakara, kuma shin kukan da zakara ke yi yana da wata fa'ida ce a addinance? Don Allah a taimaka a amsa mani wannan tambayar?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus
Salám, 'yar uwa gaba ɗaya
ma zagin dabbobi ko la'antarsu bai halasta ba, saboda Imrana ɗan Husaini Allah ya ƙara
masa yarda ya ba da labari cewa: wata rana Manzon Allah ﷺ yana cikin halin tafiya, sai ya ji wata mata
da take kan raƙuma ta tsine wa raƙumar, da Manzon Allah ﷺ ya ji haka sai ya ce:
"ku ɗauke kayan
da ke kan raƙumar
nan, ku ƙyale
ta, saboda an riga an tsine mata". Kamar yadda Muslim ya ruwaito a hadisi
mai lamba ta (2595).
Sai wannan ya
nuna bai halasta mutum ya zagi wata dabba ko ya tsine mata ba, ko kuma mutum ya
zagi abin hawansa ko ya tsine masa ba.
Game da kuka
ko carar da zakara ke yi, ya tabbata daga Abu Hurairata Allah ya ƙara
masa yarda cewa: Lallai Annabi ﷺ
ya ce: "Idan kuka ji carar zakara to ku roƙi Allah daga falalarsa, saboda lallai ya
ga Mala'ika ne, idan kuka ji kukan jaki kuwa to ku nemi tsari daga Allah,
saboda lallai Shaiɗan
ya gani". Albukhariy (3303), Muslim (2729).
Wannan hadisin
sai ya nuna cewa idan zakara ya zo yana cara ba zagin sa ya kamata a yi ba,
addu'a aka sunnanta a yi, saboda Mala'iku suna kusa da su ɗaga addu'ar bawa zuwa ga
Allah Maɗaukakin
Sarki.
Sai dai wasu
malaman sun ce: Ma'anar hadisin nan ba yana nufin zakara ba ya yin cara har sai
idan ya ga Mala'ika ba ne, haka ba yana nufin jaki ba ya yin kuka har sai idan
ya ga Shaiɗan ba ne,
sau da yawa sukan yi kukan saboda wani abu da ya bijiro masu, ba don saboda da
ganin Mala'ika ko Shaiɗan
ba, duk da kukan nasu yakan zamo saboda ganinsu ɗin,
to amma dai ko ma dai mene ne, an so a yi addu'a a lokacin da aka ji carar
zakara, sannan a nemi tsari idan aka ji kukan jaki...
Duba Mir'átul
Mafátih Sharhu Mishkátil Masábih (8/167).
Allah Ta'ála
ne mafi sanin dai-dai.
Jamilu
Ibrahim, Zaria.
Ga Masu Buƙatar
Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Fc3hX6HoDt65aKhhKOiDpX
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.