Ticker

6/recent/ticker-posts

Bullar Wasu Fasahar Baka Na Hausa A Karni Na Ashrin Da Daya: Takaitaccen Nazari A Kan Sababbin Kirari Da Karin Magana

Maƙalar da Aka Gabatar a Taron Ƙara Wa Juna Sani Na Ƙasa da Ƙasa Na Uku Wanda Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya da Kimiyyar Harshe Ta Shirya a Ranakun 18-22 Mayu, 2017. Kuma an Buga ta a cikin Mujallar KADAURA Jounal of Hausa Multiti Disciplinary Studies Vol.1, No. 4, 2018 Special Edition.

Kirari

Ɓullar Wasu Fasahar Baka Na Hausa A Ƙarni Na Ashrin Da Ɗaya: Taƙaitaccen Nazari A Kan Sababbin Kirari Da Karin Magana

Rabi Mohammed
Jami’ar Jihar Kaduna, Nijeriya.
Email: rabimohammeddatti@gmail.com
G.S.M: 08060771666/08080381801

Tsakure

Nau’oin fasahar baka na Hausa su ne a matsayin adabin baka na azancin magana, kamar karin magana, da tumasanci da kirari, da arashi, da baƙar magana, da barkwanci, da salon magana/ƙarangiya, da gatse, da kacici-kacici, da shaguɓe, da ba’a da gugar-zana, da sara, da dungu, da waskiya, da santin magana, da zambo, da zaurance, da habaici, da sauranau. A Wannan maƙala za a yi ƙoƙarin nazarin wasu kirari da karin magana ne na Hausa da suka bayyana a wannan ƙarni na ashirin da ɗaya. Da ma kamar yadda aka sani kirari da karin magana jiyo su kurum ake yi daga bakin mutane, sannu a hankali su fantsama cikin rubuce-rubuce ta fuskoki daban- daban. Waɗanda za a yi nazari a nan, sun samu ne ta kafar sadarwa ta zamani (whatsApp) a bisa wasu dalilai waɗanda ke da muhimmanci a tabbatar da nazarinsu a rubuce ta yadda komai tsawon zamani za a samu abun dogaro idan wasu nazarce-nazarce sun taso. An gano lallai yana da kyau a dinga taskace kirari wuri ɗaya a rubuce, saboda yara manyan gobe, ko kuma don gudun kada wata rana a wayi gari a neme shi a rasa shi sam.  Ana fata wannan nazarin har wa yau, zai taimaka wajen daɗa fito da fasalin kirari da karin magana da yadda ake gina su da saƙon da suke dunƙulewa. Za kuma a yi ƙoƙarin rarrabe waɗannan sababbin kirari da karin magana da aka kawo da waɗanda suka wanzu tun asali.

 

1.0    Gabatarwa

     Manufar wannan takarda ita ce, ta taskace kuma ta yi nazarin wasu sababbin kirari da karin magana a Hausa. Domin cim ma wannan ƙuduri, za a fito da bayanai gida-gida. Za a bibiyi ayyukan da suka gabata a fito da ma’ana da asali da dalili da kuma fasalce-fasalce na kirari a Hausa. Bayan an yi haka, sai a kawo kirarin da aka samo sannan a yi nazari da sharhi a kai. Idan an juyo ga karin magana, nan ma za a yi bayanai ne ta yadda aka yi game da kirari.  

2.0 Kirari a Hausa

     Ma’anar Kirari

Masana da dama sun bayyana ma’anar kirari daban-daban, ga kaɗan daga cikinsu:

     Alhassan da Zarruƙ (1976), sun bayyana kirari a matsayin nau’i na fasahar shirya taƙaitaccen kwatance, wanda ya ƙunshi bayanin abubuwa ko halaye ko al’aumura. Sun ƙara da cewa kirari yana cikin rukunnan nan na zantuttukan Hausa masu hikima da zurfin ma’ana da nasiha. Kuma kirari koyaushe akwai mai shi, wato akan lanƙaya kirari ga mutum ko wani abu da ba mutum ba, mai rai ko mara rai, kamar aljani ko ƙasa da sauransu.

     Gusau, (1979/80), shi kuma ya ce: “Kirari shi ne faɗin wasu kalmomi ga wani waɗanda za su yi masa daɗi da cicciɓa shi a idon jama’a.”

     Ƙamusun Hausa (2006:246) ya bayyana ma’anar kirari da cewa, “Zaɓaɓɓun kalmomin da ake furtawa a tsare don zuga ko kambamawa”.

     Bunza kuwa, (2009: 140), ya ce: “Za a fi fayyace ma’anar kirari idan aka nazarci waƙoƙin `yantauri ko manoma ko maƙera ko mafarauta ko ɓarayi da sauransu.”

     A taƙaice kirari nau’i ne na fasahar shirya taƙaitaccen kwatance wanda ya ƙunshi bayanin abubuwa ko halaye ko al’amura. A iya cewa kirari shi ne kuɗa da kurari cikin hikima, ishara da isar baka, rurawa da razanarwa da ruba (cika baki). (Alhassan da Zarruƙ 1982).  

 Asalin Kirari

     Haka kuma masana ba su yi ƙasa a gwiwa ba, sun kawo asalin kirari. Ga abin da wasu suka ce:

     Kafin Hausa, (1985), ya bayyana cewa “Asalin kalmar kirari daga kira ne, watau a nemo mutum ya zo ya fito fili ya nuna kansa ko kuma wani ya fito ya nuna shi.” Har wa yau ya danganta asalin kirari da Kalmar ‘ƙira’ wadda ke nufin aikin sarrafa ƙarfe a wuta. Idan ƙarfe ya yi ja a wuta maƙeri yana fito da shi ya yi ta makar sa da guduma har sai ya biyu. Sannan ya sa zarto ya koɗa shi yadda zai zama wani abu daban da siffarsa ta asali. To a cewar Kafin Hausa, kamar yadda maƙeri ke wannan aiki, haka ɗan ma’abba kan wasa mutum ya sa kaifinsa ya tashi yadda ba tsoro a gare shi. Ya kuma ƙara bayani da cewa wasu manazarta sun danganta kalmar kirari da iƙirari. Watau mutum ya furta abu da kansa, wanda shi Kafin Hausa, (1985) ya ce, bai yarda da ra’ayinsu ba domin wani ma yana yi wa wani kirari. Sai dai yana ganin al’adar nan ce ta manazarta da masana adabi da harshen Hausa ta a kullum Hausa ba ta da abin kanta sai dai ta yafo na Larabci.   

     Shi ma Bunza, (2009: 140), ya nuna cewa asalin kalmar kirari ‘kira’ take nufi, inda akan sa kalangu ko ganga ko murya a kira wani da ƙarfi don ya fito a ɗebe tababan abin da ake faɗa a kansa. Idan da kiɗa aka yi kiran, to take ke nan. Yayin da kuma aka sa baki aka fara kiɗa, shi ne an yi kirari. A can gaba ya ƙara cewa: “Asalin kirari yaƙi, da faɗa, da nuna bajinta.” Ya kuma tabbatar da cewa idan aka lura da waƙoƙin Narambaɗa mafi yawan gindin waƙoƙin sigar kirari gare su.

     Shi kuwa Malumfashi, (2014:20), game da asalin kirari ya tofa albarkacin bakinsa inda ya ce: “Kirari yana ɗaya daga cikin rukunnan adabin bakan Bahaushe da ya gada tun kaka da kakanni, don haka ba wata al’umma da za ta yi iƙirƙrin cewa ita ta koya wa Bahaushe hikimar aiwatar da kirari.”

Dalilan Yin Kirari

Ana yin kirari saboda waɗannan dalilai:

Don razanar da abokan gaba.

●Don koɗa wani a yi masa washi ko talla ko zuga.

●Don a yi nuni, a yi wa mutane hannunka-mai-sanda.

●Don a inganta azancin magana. Kirari ba ya inganta sai bisa tafarkinsa na al’adu da sana’o’i. ana yin sa don a nuna hikimar zantukan Hausa.

●Don a nuna cewa da ma can shi zance ne ginanne da ake ɗabowa daga rumbun adabi kana a zo a ƙawata adabin da shi.

Matsayin Kirari

     Kirari na ɗaya daga cikin manyan rukunan adabin baka na Hausa. Ana gina kirari ne cikin fasaha da tsari don a kambama mutum ko wani abu da ba mutum ba. Bunza, (2009: 140), ya bayyana cewa: “Kirari a nazarin adabi abu ne wanda ya fi zambo da habaici faɗi da rassa da jiigogi da kayan ciki.” Har wa yau Bunza ya nuna shi kirari ma’auninsa yana da zubi irin na waƙa amma ya fi waƙa shiga jiki. Abin da ya bambanta kirari da waƙa, zaɓen kalmomi masu nauyi da shiga jiki da mamaye zuciya.

     Ta wata fuskar, Alhassan da Zarruƙ, (1982), sun tantance suka nuna lallai kirari wani babban ginshiƙi ne a rukunin adabin baka wanda ke bayyana al’adar al’umma. Haka kuma suka nuna kirari na ciyar da al’umma gaba ta fuskar ilmantarwa da faɗakarwa gami da nishaɗantarwa. Daga cikin furucin da Zarruƙ, (1982), ya yi a gabatarwa, ya ce: “A fagen nishaɗi kam babu wanda bai san matsayin kirari ba. domin kirari shi ne gishirin kiɗa da waƙa da sauran al’amuran da suka shafi bukukuwa. Shi ne kuma sinadarin take da zambo. Bayan haka, kirari nau’i ne na fasahar harshen Hausa.   

 Lokacin Yin Kirari

     Kirari ba kodayaushe ne ake yin sa ba, sai da dalili. A al’ummar Hausawa, ana yin kirari bisa dalilai na bukin aure, da bukin suna, da shagulgulan sallah, da naɗin sarauta, da ayyukan al’umma, da wasanni irin su dambe da kokowa, da wasu sana’o’i irin su ƙira da saƙa da rini da saye da sayarwa. Haka kuma kirari na wanzuwa a ayyuka irin na rubutaccen adabi. Mode, (2013:279-280).

 Fasalin Kirari

     Manzarta daban-daban sun fasalta kirari zuwa gida biyu, wasu uku, wasu huɗu waɗanda Mode (2013: 279), ya yi bitar su, sannan ya tabbatar da ra’ayinsa cewa, kirari za a iya kallonsa ko raba shi gida biyu ne: Kirarin mutane da kirarin waɗanda ba mutane ba.

     Bisa fahimta dai in an ce ‘kirarin mutane’, to ya shafi mutum ɗin ne kai tsaye. Ko dai shi mutum ɗin ya yi wa kansa kirari, ko wani mutum daban ya yi wa wani mutum ko mutane kirari. Kirarin da ya shafi mutane an fasalta shi zuwa na maza da na mata. Na matan an sake fasalta shi zuwa na uwargida da na amarya da na `yanmata. Sannan akwai kirarin yara maza da mata da dai sauransu.

     Idan kuwa an ce ‘kirarin waɗanda ba mutane ba, to akwai masu rai da marasa rai. Masu rai kamar aljannu ko dabbobi ko ƙwari; marasa rai kamar wurare ko ma duniyar kacokan, da duwatsu da koguna da sammai da hadari da ruwa da zafi da sanyi da sauransu ba iyaka.

     Kowane irin kirari dai, shi mutum ɗin ne ke tsara shi. Kuma yana la’akari da abubuwa da dama ne na daga siffa ko halayya ta mutum ko wani abu, sai ya fito da shi ƙarara ta fuskar kambama shi ko ɗaga dajarsa bisa wani abu daban. Alhassan, (1982), ya faɗi cewa: “Idan aka sami wata halitta mai tsananin jaruntaka ko gwaninta ko mai yawan rikiɗa, wacce ba ta iya tsayuwa a kan halinta da aka sani, akan shirya mata kirari na musamman, saboda ya nuna siffofinta da halayenta a fili, a karɓi na karɓa, a guji na gudu.”

     Shi kuma Zarruƙ, (1982) ya ce; “Duk abin da ya burge Bahaushe, ko wanda ya ba shi tsoro, ko ya iya gagarar sa, ko ya ba shi mamaki, to lallai za ka ji ya yi masa kirari. Saboda haka dabbobin daji, kamar su zaki da giwa da damisa da kura da sauransu, duk suna da kirari. Wani kirarin yana gwada ƙarfin dabbar ne, ko faɗanta, ko wasu halayenta na tsoratarwa.” Ya ci gaba da bayyana cewa: “A muhimman abubuwa na ƙasar Hausa, kusan babu wanda ba shi da kirari. Garuruwa da sauran nau’o’i da mutane maza da mata, yara da manya, duk suna da irin nasu kirari. Ana yi wa namiji kirarin mazakuta. Mace ana yi mata kirari game da halayenta na mata. Haka nan tsoho da yaro, duka akwai abin da ake faɗa game da su a cikin kirari. Da aure da haihuwa da mutuwa, duka babu wanda bai sami kirari ba. kowane ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa, in ka ji tarin kirare-kiraren da aka yi masa, zai ba ka mamaki.”

3.0 Wasu Samfurin Kirari a Ƙarni na Ashirin da Ɗaya

  Kirarin Mata

     An samu wannan kirari ne ta kafar sada zumunta ta zamani (WhatsApp) a watan Okotoba, 2016. Amma a rubuce ya zo kamar haka:

Mata masu duniya, ku ba da tuwo ku ba da other rum!

Mata masu mulkin di oda rum, komai iko da taƙamar mutum a oda rum sai ya bi!

Mata hidimarku na da kyau, balle a oda rum!

Mata iyayen kowa komai mulkinsa!

Mata in babu ku inkomplit!

Mata a jinjina maku, rashinku asarar namiji, rashinku hargitsewar namiji, rashinku a oda rum garari ne!

4.0 Nazari da Sharhi

     Zarruƙ, (1982), ya nuna a fagen nazari dai kirari wani rukuni ne na fasahar harshen Hausa da al’adun mutanenta. Ita kuma wannan fasaha ta harshe, ta baka ce ko rubutacciya ce, ita ake kira adabi. Watau idan an ce adabin Hausa, an kira dukkan fasahar harshen Hausa ke nan. Adabin Hausa kuwa, da ma fanni ne guda wanda ake tsayawa a yi nazarin sa a makaranta. Saboda haka idan an yi nazarin kirari, kamar an ɗauki wani rukuni ne a cikin adabin Hausa.” Don haka a nan za a yi nazari da sharhi game da wannan sabon samfurin kirarin da aka kawo ta fuskar bayyana dalilin samuwarsa da fasahar da aka dunƙule a ciki gami da saƙon da kirarin ya samar.

     Wannan kirari ya samu ne a dalilin kalaman da shugaban ƙasar Nijeriya, Muhammadu Buhari ya yi. Ya mayar da raddi ne game da maganganun da matarsa (A’isaha Buhari) ta yi a kafar yaɗa labarai na BBC Landan. Shi dai shugaba Buhari ya ce (cikin harshen Ingilishi): “I don’t know which party my wife belongs to, but she belongs to my kitching, and my liɓing room, and the other room.” Wannan al’amari ya faru ne a watan Okotoba shekarar dubu biyu da goma sha shida (2016 Miladiyya), wanda ya zo daidai da watan Muharram shekarar 1438, bayan hijirar Annabi Muhammad (SAW) daga Makka zuwa Madina. Ita dai A’isha Buhari ta yi ƙorafi ne game da salon mulkin maigidanta, shugaba Buhari. Shi kuma aka bi diddigin jin ta bakinsa, shi ne ya furta kalaman da aka gani da Ingilishi. Waɗannan kalamai waɗanda a cikin harshen Hausa ke nufin, “Ban san jam’iyyar da matata take ba, amma na san dai ita ke kula da madafata da ɗakin hutawata da kuma ɗayan ɗakin.” Wannan ne ya jawo hankalin `yan Nijeriya suka yi ta cecekuce kowa yana faɗin ra’ayinsa. Kwatsam sai ga ɓullar wannan kirari ta kafar sada zumunta (Whats App), wanda shi ma ya ja hankulan mata da dama ta inda suka riƙa nuna gamsuwarsu da wannan sabon kirari.

     Wannan kirari dai an tsara shi ne da ka, amma ya riski mutane ne a rubuce ta kafar sadarwa ta zamani. Idan aka kalli yadda aka yi watanda da harshe a wannan kirari, farko za a fahimci an yi abin da ake kira ‘Ingausa’, wato gwama harshen Hausa da Turanci wajen isar da saƙo. Wannan shi aka sanya a rukunin Hausar `yanboko. Sai dai bisa fahimtar wannnan nazari, kalaman Turancin da suka shigo cikin kirarin su ne suke ƙara tabbatar da dalilin tsara wannan kirari lallai sanadin furucin shugaba Buhari ne wanda ya yi maganar oda room wanda ya fito mana da Buharin a fili a gane ko shi wane ne. Wato ya yi kinaya (saye) a maganarsa kasancewarsa daga al’ummar Hausa waɗanda aka san sun gaji kunya. Faɗin wannan magana ta ja hankalin ai’umma ciki da wajen ƙasar Nijeriya. Bisa fahimta ‘The other room’ na nufin ‘ɗakin kwanciyar bacci’ wanda a Hausance ake cewa ‘turaka’. Buhari ya tabbatar matarsa kaɗai take da `yancin shiga ta kwana tare da shi bisa yadda aka sani a al’adar zaman aure na mata da miji. Haka kuma ta fuskar addini, maganar tasa dutse wanda ya tabbatar da cewa shi musulmi ne kuma zuciyarsa na nan a ɗarfane da abin da addinin ya tabbatar.

     Misali, an tambayi Annabi Muhammad (SAW) cewa:

“Wace mace ce ta fi?” sai ya ce: “Wadda take sanya mijinta farin ciki idan ya dube ta, take yi masa biyayya idan ya umurce ta, kuma ba ta ƙin yi masa biyayya saboda son zuciyarta ko dukiyarta ta inda ba ya so.” (Nasa’i).

 

A wani hadisi kuma Annabi (SAW) sai ya ce:

“Idan mutum ya kira matarsa zuwa ga shimfiɗarsa kuma ta ƙi zuwa, ya kuma yi fushi game da hakan a wnnan dare, to mala’iku za su yi ta tsine mata har zuwa safiya.” (Bukhari/Muslim)

    

     Addinin musulunci ya tabbatar da matsayin ma’aurata. Namiji shi ne ke jagorantar gidansa gaba ɗaya. Wajibi ne kuma mata ta yi wa mijinta cikakkiyar biyayya wadda ba ta saɓa wa Allah ba. Yin wannan shi zai ba matar aure damar shiga Aljanna bayan ta koma ga mahaliccinta. Annabi Muhammad (SAW) ya ce:

“Idan mace ta mutu alhali mijinta yana farin ciki da ita, to za ta shiga aljanna.” (Tirmidhi).

     Wannan kaɗan ke nan daga cikin ɗimbin Hadisai ingantattu daga hasken Alƙur’ani game da matsayi da muhimmancin miji a wajen matarsa. Don haka maganar Buhari ta auna koyarwar addinin musulunci kasancewarsa musulmi da kuma al’adarsa ta Hausa.

     Ta wata fuskar kuma, idan muka dubi ainihin ƙunshiyar kirarin da aka gina ta dalilin kalaman shugaba Buhari, za mu iya cewa wannan ba sabon kirari ne na mata ba. An daɗe ana yi wa mata kirari wanda ke nuna isa da muhimmancin mace kamar yadda Allah ya halicce ta. Idan babu ita to rayuwar namiji garari ɗin ne; kuma namiji inkompilit yake, wato bai zama cikakke ba a cikin al’umma. Faɗin haka ya yi daidai tunda ko shugabanci mutum zai nema ba ya samun goyon bayan al’umma matuƙar ba shi da matar aure.  Wato su mata Allah ya ba su darajar da babu mai ƙarfin ƙwace masu a duk duniya in ba mahaliccin nasu ba. Shi ya sa a kirarin aka ji an ce:

Mata masu mulkin di oda rum, komai iko da taƙamar mutum a oda rum sai ya bi!

Mata hidimarku na da kyau, balle a oda rum!

Mata iyayen kowa komai mulkinsa!

Wato wannan kirari a fakaice an isar wa shugaba Buhari saƙo. Mata suna ganin ya nuna wa duniya shi ne jagorar matarsa, har ma wasu suna ganin ya tauye mata `yanci a siyasance. Don haka suke tuna masa komai isarsa a matsayin namiji idan ya zo oda rum (turaka), to sai ya lallaɓa matarsa. To ba ga Buhari kaɗai ba, ko ma wane ne namiji a rukunan al’umma sai ya bi mace ya lallaɓa ta don ya samu biyan bukata. Wannan daraja da Allah ya ba mata suna alfahari da shi tun zamani mai tsawo. Tuntuni da ma akwai kirarin mata da ke cewa:

●Sannunku mata masu kayan daɗi,

                                                   Mata masu abun bayarwa,

                                                   Dare naku safiya ta mazajenku,

   Ku kai mutum lahira ku dawo da shi,

                          Mata ku sha wuya ku yi kuka, ku ji daɗi ku yi kuka,

        Mata masu kukan da ba hawaye ko tsino,

                                                 Sannunku mata iyayen kowa,

             In ba ku ba gida, in kun yi yawa gida ya ɓaci

            Mata cikinku damina, gefenku ciyawa mata,

                                A auro ku don ana son ku, a sake ku don takaicinku mata,

                                                Dariyarku ta fi sata ciwo mata,

                    Ku kira namiji yayanku, ku yaye masa aljihu mata,

                        Mazanku su yi mulki a waje, su zo gida ku mulke su,

                    Malami ya ba da karatu ya zo gida ku ba shi darasi,

                                              Mata masu lilon shillawa,

                                              Mata masu fitillun tagulla a gaba,

                                              Masu yawo da kujerun zamansu,

                       Maza su ɗau nauyin wasu, su zo gida ku ɗau nauyinsu,

        A ba ku ku raina, a hana ku ku yi Allah ya isa,

           A bar ku, ku sangarce, a yi maku faɗa ku yi yaji,

                                             A kore ku a je bikonku,

                                             Ciyawa ba ta ka da ku sai yaryaɗi mata,

                                            Butulu maganin kangarar namiji,

                                         A ci da ku; a sha da ku; a yi maku sutura; amma gobe ku ce me aka

                                             taɓa yi maku?

                                           Ku auri mutum idan kuna son sa, gobe ku ce da shi ƙaddara ce ta sa

                                             zama da shi,

                                             Ku zalunci mutum kuma ku kai ƙararsa,

                                             Ku yi laifi a ba ku haƙuri mata,

                                             Mata masu mayar da sarki Bafade,

                                            Mata dangin iblis, ko iblis na tsoron ku,

                                            Mata a ci yau a ci gobe sai ku mata,

 Ku sha sha’aninku mata dole a zauna da ku,

                                           Dole a nemo a ba ku,

                                           Dole a lallaɓa ku mata,

                                          In kuwa an ƙi, dare ya yi jiki yai tsami!

 

`Ga kuma wani kirarin da ya jima a tsakanin al’ummar Hausawa:

                                            

                                              Yanmata adon gari,

                                              In ba ku ba gari,

                                              In kun yi yawa gari ya ɓaci.

                                             A ba ku, ku raina a hana ku, a ji kunya.

A so ku, ku wahalar, a ƙi ku, a tagayyara.

                    A amince maku ku yi yaudara, a yaudare ku, ku rama.

                                            `Yanmata ƙarfen ƙafa mai wuyar cirewa,

                                        A kula ku, ku yi wulaƙanci, a bar ku ku wuce a kwana ana da- na-

                                             sani!

                                    Mata gumbar dutse; murucin kan dutse ba ku fito ba sai da kuka

                                             shirya.

    

     Idan an lura waɗannan kirare-kirare sun daɗe da ginuwa a tsaknin al’ummar Hausawa. Don haka idan an kwatanta da wanda aka kawo a matsayin sabo, za a tabbatar ba sabo fil yake ba saboda fasalinsu ɗaya; ƙunshiya ko saƙonsu ɗaya ne duka kamar yadda aka faɗa. Kirarin da aka gina a dalilin kalaman Buhari ya tabbatar mana da kalmomin da ya furta na Ingilishi wato ‘oda rum’ (other room). In ban da wannan, za a iya cewa kirarin tamakar bita ne na kirarin mata da ya daɗe ana yin sa. Ba kuma zai kankaru ba domin an jingina kirarin ne bisa yanayin halitta da kuma ɗabi’u irin na mata ɗin.

Kirarin Uwargida

     Wannan nazari har wa yau ya yi kiciɓis da wani kirarin da ya shafi mata ta kafar sada zumunta (WhatsApp), a ranar 02 ga watan 02, shekarar 2017.  Kirarin ya zo ne cikin murya ba a rubuce ba, sai aka shifce kamar yadda aka ji daga bakin wata mace kamar haka: 

Ke amarya mara galihu

Ke amarya mara `yanci

            Ke amarya `yar cin arziki

            Ke amarya mai kwaɗayi

            Ke amarya me ƙananan `ya`ya

            Ki ba uwargida fili ga ni nan fitowa

            Uwargida sarautar mata

Uwargida zuciyar miji

Uwargida sirrin miji

Uwargida rayuwar miji

Uwargida ɗawainiyar miji

Sai ni nan uwargida wadda na raba mijinki daga Ahmad ya koma baban Abba

Sai ni nan uwargida wadda na raba shi da tuzuru ya koma magidanci

Sai ni nan uwargida wadda na koya mai farin ciki fiye da zaman dakali

Sai ni nan uwargida wadda na hana shi jin sanyin waje ya koyi jin ɗumin cikin gida

Sai ni nan uwargida wadda ni ce farko kafin ke, kuma `ya`yana ne farko kafin naki, kuma tirenin ɗina za ki zo ki tadda.

 

Ke amarya karere! Kar fa ki manta Nana A’isha matar Annabi Muhammad (SAW) ta ce ba ta taɓa kishi da wata mace ba, face Khadija uwargidan Manzon Allah (SAW), kuma bai daina maganarta, bai daina tunaninta, bai daina labarinta, Nana A’isha tana baƙin cikin wannan abu, tana kishi da matar da ba ta taɓa gani ba, domin isa na uwargida.

 

Ke amarya! Matsa ki ba masu gida su samu wucewa,

Amarya! Matsa ki ba ni wuri, in a gida ne sai an ba ni fyf bedrum saboda ɗakina da `ya`yana, na jama’ana, gefen `ya`ya maza, `ya`yanki ko ƙanana suna gefen masu aiki amarya! Allah Sarki amarya! Ki yi haƙuri, wanda ya riga ka barci, dole ya riga ka tashi.

 

Amarya sabuwar zuwa, amarya baƙuwa! Zauna ki ga tirenin ɗin da na wa mijinki, haka za ki hau ki ci gaba da tafiya a kai, domin kuwa ke macijiya ce ba ki da raminki sai dai in wani ya haƙa ki shiga. Ke macijiya ce ba ki san sanda muka taho a kan gada ba muna tafiyarmu, sai da muka zo bakin birij mun zo mun tsallake, kafin a gan ki. Ba ki san ta wace Katanga muka taho ba, me kika sani game da mijina? Me kika sani game da jin daɗinsa? Me kika sani game da rayuwarsa? Komai ne kika zo kika samu, tirenin ɗina kika bi a kai. Ya za kiyi? Ya za ki yi sabuwa? Ya za ki yi karere?

 

Sai ni nan uwargida sarautar mata! Mulkin gida, farin cikin mijina, abin shawararsa, daga uwarsa sai ni. Ni ne abokiyar shawararsa, ni ne farin cikinsa,

 

Ke karere mai ƙananan yara! Ki yi biyayya manyan `ya`ya su sa naki a makaranta, ki yi biyayya manyan `ya`ya su taimaki naki, ki yi biyayya manyan `ya`ya su duba ki

 

Haba amarya! Haba amarya karere! Haba `yar Basakkwaciya! Haba `yar Basakkwaciya! Ki kwantar da kanki! Ki kwantar da kanki a inda aka fi ƙarfinki ki ba uwargidanki fili ta sanar da ke waye mijinki domin ki samu wurin tsugunnawa!

 

5.0 Nazari Da Sharhi

     Kamar yadda aka faɗa, an yaɗa wannan kirari ne cikin muryar mace ta kafar sadarwar zumunta (WhatsApp). Ba a ambaci sunan wadda ta yi ba, sai dai ɗan bayani a rubuce tare da wani hoto da ke nuna mace da namiji bisa kan gado suna sumbantar juna. Kuma hoton ya nuna suna cikin kwalliya irin ta amarci da angonci. Wannan hoto shi aka alaƙanta da wannan kirari cewa wai wata amarya ce ta tura wa uwargidanta hoton da nufin takalar hankalinta. Ita kuma da ta gani, sai aka ce ta yi wannan raddin kalamai na kirari ta tura wa amaryar da mijinta ya auro. Sannan kuma bayan haka ta faru, sai aka sake yaɗa wata magana ta muryar wata mace, ba a rubuce ba mai cewa:

Ke kuma uwargida, me kike taƙama da shi ne da za ki wani karanto, kina haɗa kanki da Nana Khadija ma, kya ma hwara? Za ki ce wani Nana Khadija kaza-kaza? Ibadan da take yi kina yi ne, in ban da bin bokaye da abun nan da rawan kai ba abun da kike yi. Sannan kina wani cewa Nana A’isha! Ai Nana A’isha ita ce mafi soyuwa ga Annabi, ballantana har ki ce wani Nana A’isha kaza-kaza, kaza-kaza. Da kike zancen `ya`ya da wani mene ne? to wa ya san gawan fari, in Allah ya tashi ɗaukewa sai ya ɗauke duka `ya`yan naki, ko kuma ya shiryar da `ya`yan na amarya ya bar naki uwargida, ballantana ki ce wani abu. Uwargida! Uwargida! Uwargida in ban da ma hauka ba abun da kika riƙa faɗi. gaba ɗaya tsantsan haukanki ne da jahilci kika faɗi kawai, (tsaki).  

 

     Wannan martini da aka ce amarya ta yi, in an lura ba kirari ba ne. Ana zaton ba amaryar gaske ba ce ta yi tunda karin harshen ba tsantsan karin Sakkwatanci ba ne wanda aka sa rai a ji saboda a kirarin da uwargida ta yi, ta ce “`yar Basakkwata”. Sai dai lallai raddi ne ga wannan kirari da uwargida ta yi.

     Duk da cewa wannan kirari kwanan nan aka haife shi, bai kai ma ga iya zama ba, ballantana rarrafe da tafiya, to ba za a iya tabbatar da haƙiƙanin dalilin yin shi ba. Bisa bincike da mai wannan maƙala ta faɗaɗa ta kafar sada zumunta, an gano cewa mata da yawa sun ji wannan kirari. Wasu sun tafi a kan cewa akwai matsala babba ta yaɗa ƙarya a kafar sada zumunta ta zamani (soshiyal midiya). Abun da za a turo a bidiyo daban, abun da za a haɗa daban, ko rubutaccen bayani ko hoto. Wannan matsalar kuma na faruwa ne kila, saboda wasu ba su rufe auto midiyansu, sai kawai su shiga cikin ma’ajiya hotunansu, su zaɓo hoton da ya dace da batun, su haɗa su watsa don tsabar son su zama na farko wajen yaɗa zance. Ana gane hakan ne ta inda jama’a sun san wannan hoto da muhallinshi kila tun shekara biyu ko fiye, kwatsam kuma sai ga shi an liƙa shi da wata magana an ce ai yau ko jiya ma abun ya faru.

     Ko ma dai mene ne, da ma kirari da karin magana, idan sun ɓulla da wuya ne a yi saurin cafke gaskiyar wanda ya fara furtawa. Wannan kirari a iya cewa ko haka nan ma, saboda kishi irin na mata, ba sai amarya ta takali uwargida ba. Za ma a iya samun macen da ita kaɗai ce wajen mijinta, kuma ta zauna ta shirya wannan kirari, ta kuma watsa da nufin cusa wani saƙo a zukatan mutane.

     A bisa faifan nazari, kirarin da uwargida ta yi wa kanta na nuni da cewa lallai mace ta farko a gidan miji ita ce kan gida. Babu tantama lokacin da suka yi auren saurayi da budurwa kowa bai san kamun ludayin zaman aure ba. A hankali ana kwana ana tashi ake shaƙuwa da juna ta fuskoki iri-iri. Za a haifi `ya`ya waɗanda tabbas babu kankara, dole ne ka ji ana wa uba laƙabi da baban wane; ko kuma uwa a ce mata maman wane. Babu yadda za a yi a ce daga baya idan namiji ya ƙaro aure a ce amarya ɗaya take da uwargida a wurin miji ta wannan fuska. Dole ne ta saurari uwargida ta koyi wani abu. A bisa al’adar Bahaushe ma, ai babu yadda za a yi ne amarya ta kira sunan uwargida saboda wannan daraja tata. A dole ne amarya ta ce da uwargida ‘yaya’. To amma a wannan ƙarni da muke ciki, wannan tarbiyya ta Bahaushe ta mutu murus musamman a birane. Idan aka lura ai kalaman da amarya ta aika a matsayin raddi ga kirarin uwargida babu hikima sam kuma babu tarbiyya a ciki. Kirarin uwargida kuwa ya nuna hikima da ilimi da tarbiyya duka. 

     Dangane da hikima dubi waɗannan kalamai daga cikin kirarin:

Uwargida sarautar mata

Uwargida zuciyar miji

Uwargida sirrin miji

Uwargida rayuwar miji

Uwargida ɗawainiyar miji

Sai ni nan uwargida sarautar mata! Mulkin gida, farin cikin mijina, abin shawararsa, daga uwarsa sai ni. Ni ne abokiyar shawararsa, ni ne farin cikinsa,

 

Akwai hikima da ta kira kanta masarauciya, zuciya, sirri, rayuwa ko ɗawainiya duka ga mijinta. Sarautar mata na nuna matsayin matar farko a wajen miji cikin kishiyoyi. Zuciyar miji na nuna cewa ita ce ta fara shiga ransa a matsayin matarsa, kuma ita ta fara sanin duk wani sirrinsa kafin wata ta shigo gidan. Ita ce ma rayuwarsa gaba ɗaya na nufin komai mijin zai aiwatar sai da shawararta. Ta riga ta shiga jini da tsokar mijinta, ta saba da dangisa waɗanda ko su ba su iya cewa wani abu na game da ɗan nasu, ba tare da sun shawarce ta ba. Ɗawainiyar miji kuwa na nufin wahalhalu duk uwargida ta fi juriya a kai. Misali kila ta aure shi tun ba shi da komai har Allah ya azurta shi, a cikin haka sai kwatsam ya ƙaro aure. To babu yadda za a tantance gaskiyar uwargida a kirarinta, sai lokacin da Allah ya jarabci mijin da rashin kuɗi ko wata rashin lafiya mai tsanani ta kama shi, face an ga uwargida ta jure ɗawainiya da mijin nata. A wannan ƙarni da muke ciki mata da yawa ba su da juriya ta fuskoki da dama ga ɗawainiya da miji. Kila da ma abun hannunsa ya sa ta aure shi, don haka za ka ga ta fara noƙe-noƙe da cewa ita ba za ta iya wahala ba.

     Haka kuma, wata hikimar a kirarin sai inda ta ce:

 

Allah Sarki amarya! Ki yi haƙuri, wanda ya riga ka barci, dole ya riga ka tashi

 

Ma’ana ita uwargida da ta riga auren mijin nasu, dole ne ta fi ta sanin komai na gidan mijin nasu. Kuma dole ne sau da dama a ba ta matsayinta na babba.

     Idan muka ɗauki batun ilimi, a cikin kirarin an ji inda uwargida ta tunatar da amarya mai rawar kai da cewa:

Ke amarya karere! Kar fa ki manta Nana A’isha matar Annabi Muhammad (SAW) ta ce ba ta taɓa kishi da wata mace ba, face Khadija uwargidan Manzon Allah (SAW), kuma bai daina maganarta, bai daina tunaninta, bai daina labarinta, Nana A’isha tana baƙin cikin wannan abu, tana kishi da matar da ba ta taɓa gani ba, domin isa na uwargida

 

Wannan yana nuna mana uwargida mai yin kirari ba jahila ba ce tunda ta ɗauko misali daga rayuwar gidan manzon Allah (SAW), don ta tabbatar wa amarya maganarta dutse ne.

     Batun tarbiyya kuwa a cikin kirarin, za mu iya duba waɗannan kalamai:

Sai ni nan uwargida wadda na raba mijinki daga Ahmad ya koma baban Abba

Sai ni nan uwargida wadda na raba shi da tuzuru ya koma magidanci

Sai ni nan uwargida wadda na koya mai farin ciki fiye da zaman dakali

Sai ni nan uwargida wadda na hana shi jin sanyin waje ya koyi jin ɗumin cikin gida

Sai ni nan uwargida wadda ni ce farko kafin ke, kuma `ya`yana ne farko kafin naki, kuma tirenin ɗina za ki zo ki tadda.

 

Lokacin da mace ta auri mjin fari ba su da ɗa, a tarbiyyar ɗan Bahaushe mace ba ta kiran sunan miji, sai dai ta ce malam ko maigida da sauransu. A wannan ƙarni kuma an samu sauyi inda za a ji mace tana kiran mijinta da baban wane, kamar yadda ya fito a kirarin cewa ta raba mijinta da Ahmed ya koma baban Abba. Ke nan kafin su samu ɗa, tana kiran mijin nata da sunansa, wanda a da Bahaushiya wane ita. Sannan akwai kunya musamman ɗan fari, a da uba ko uwa wane su! Sai dai a alƙanta ɗa da ƙanin uba ko wan uba. Amma a wannan kirarin an gwada irin sauyin da wannan ƙarni ya zo da shi. Sai dai duk da haka ba za a ce tarbiyya ta rushe ba. Watakila saboda ci gaban samun ilimin addini ga mata ya sa suka fi cewa baban wane kamar yadda akan ji Larabawa na cewa abu wane. Akwai alamun tarbiyya ke nan tunda ta daina kiran mijinta da sunansa, sai dai ta ce baban Abba. Sannan tarbiyya ce ƙarara a inda kirarin ya nuna uwargida ta iya bi da mijinta ta yadda kullum idan ya dawo daga aiki, to yana liƙe da ita a cikin gida, babu zaman dakali wajen hira. Da ma idan ka ga mjin aure yana yawan zaman waje, to gaskiya bai samu tarbiyyar ƙwarai daga matarsa ba. Uwargida ta ƙara da cewa tirenin ɗinta dole amarya za ta tarar. Wannan haka yake domin akan samu rikici a tsakanin kishiyoyi inda sau da dama amarya takan yi ƙorafin wasu abubuwa da ta tarar ana gudanarwa a gidan mijin idan ya saɓa wa ra’ayinta. Sai ka ga ana ta rikici tana nuna uwargida ta cutar da gidan tunda ba ta bi da mijin ya saba ba. A yayin da aka samu uwargida ta gari, za ta tarbiyyantar da miji yadda ake so. Amarya idan ta shigo za ta samu sauƙi wanda shi ne ya fito a kirarin. Kalaman uwargida a kirarin akwai lumana tunda ta ce:

Ke karere mai ƙananan yara! Ki yi biyayya manyan `ya`ya su sa naki a makaranta, ki yi biyayya manyan `ya`ya su taimaki naki, ki yi biyayya manyan `ya`ya su duba ki

 

Haba amarya! Haba amarya karere! Haba `yar Basakkwaciya! Haba `yar Basakkwaciya! Ki kwantar da kanki! Ki kwantar da kanki a inda aka fi ƙarfinki ki ba uwargidanki fili ta sanar da ke waye mijinki domin ki samu wurin tsugunnawa!

 

     Ta yi kira ga amarya da ta kwatar da hankalinta domin ta ci arzikin gidan. Wannan haka yake tunda sau da dama manyan `ya`ya su ne suke ɗauke wa uba ɗawainiyar iyali ko yana raye ko a mace. Idan a raye ne, kila rauni na shekaru ya zo, ga shi yana da ƙananan yara `ya`yan amrya. Idan amarya ta sa tsiya a gidan miji kuwa, ta ƙi mutunta uwargida, ya za a yi `ya`yan uwargida su kyautata wa na amarya? Ai zuciya an halicce ta ne da son mai kyautata mata. Shi ya sa uwargida ta jaddada wa amarya a matsayin nasiha, in ta ji ruwanta. Don haka wannan ya nuna uwargida tana da tarbiyya daidai gwargwado a kalamanta. Kalmar da za a iya cewa ta bayyana ɓacin zuciyar uwargida ita ce, ‘karere’, wadda take nufin `yar karo. Za kuma a iya fahimtar cewa kirarin ya nuna mana akwai buɗewar ido saboda kila tasirin al’adun Turawa. Wato in an kwatanta kirarin da wanda ya daɗe cikin al’ummar Hausawa, za mu fahimci akwai zaƙewar mata a yau. Domin nazarin Kafin Hausa, (1985) ya nuna cewa ba safai mata kan yi kirari ba a ƙasar Hausa, watau su fito fili su yi ihu suna kirari. Amma sukan yi wa wani abu kirari, shi ma ba sosai ba. A wasu kalaman kuma aka nuna cewa mutum yakan yi wa matarsa kirari idan ta yi masa wani abu wanda ya ba shi sha’awa. A yau kuwa sai ga shi mace na aikawa da muryarta ta kafar sada zumunta ta zamani tana yi wa kanta kirari. Saɓanin da, kunya ba ta barin mata su fito da kansu haka, har su fayyace abin da ke zuciyarsu. Har wa yau, za mu iya fahimtar kirarin da aka gina na uwargida a da ya fi ɗaukar zurfin ma’ana. Dubi dai inda aka ce: 

 

Uwargida sarautar mata

                                                           Uwargida uwar katarere                                          

                                                          Kwari tankarin gida

                                                         Fara gutsura mai farar akaifa,

                                                        Kin ga ta kowa taki ta yi wuyar gani.

                                                         

Wannan kirarin ya dunƙule duk abubuwan da uwargidan ƙarni na ashirin da ɗaya ta bayyana. Babu dai wanda zai bugi ƙirji ya ce ga wanda ya gina wannan kirari domin ya sha bamban da na wannan ƙarni da muke ciki. Kirari ne wanda ya daɗe kuma babu kalmar da ta fito a ciki wadda za ta iya fayyace mana jinsin wanda ya gina kirarin. Saɓanin wanda aka kawo ɗan yau, akwai kalmomin da suka tabbatar da cewa mace ce ta gina kirarin. Kamar inda aka ce; “Sai ni nan uwargida.” Sannan ya tabbata mace ce saboda ta sigar murya aka gina kuma aka sadar wa jama’a ta kafar sada zumunta ta zamani (whatsApp). Idan an lura sabon kirarin ya ginu amma bai zo a bisa sigarsa ta asali ba wanda za a iya cewa sabon salo aka samu ke nan.

 

6.0 Karin Maganar Hausa

      Ma’anar Karin Magana

     Karin magana nazari ne na halin rayuwa a dunƙule cikin maganganu gajeru irin na hikima. Masana da dama sun tofa albarkacin bakinsu game da ma’anar karin magana. Misali:

 Yunusa, (1977) ya kira ko ambaci karin magana a matsayin Dunƙulalliyar Magana ne. A cikin gabatarwar littafin nasa sai ya bayyana abin da ake nufi da Hausa a Dunƙule da cewa: “Hausa a dunƙule zance ne dogo a dunƙule wuri ɗaya, wato taƙaitacce.”

    Ɗangambo, (1984) kuma y ace: “Karin magana dabara ce ta dunƙule magana mai yawa a cikin zance ko `yan kalmomi kaɗan cikin hikima.”   

     Furniss, (1997) ya dubi ma’anoni daban-daban na masana da manazarta game da karin magana wanda shi kuma a nasa kalmomin ya tabbatar da cewa, karin magana na nufin dunƙulƙlliyar magana ce wadda take ƙunshe da ɓoyayyiyar ma’ana wadda kuma mai sauraronta sai ya nemi ciko ko ƙarin bayani a kanta.

     Karin magana na nufin magana ta musamman wadda sai an yi tsokaci ake ganewa. Ƙamusun Hausa (2006: 235).

Asali Karin Magana

     Malumfashi da Nahuce (2014:31), a bisa fahimtarsu da bayanan wasu manazarta, sai suka ce ce: “Karin magana ta samo asali ne tun lokacin da Ɗan Adam ya ƙirƙira fasahar mayar da zance mai tsawo ya zuwa gajere. Babu wani takamamman lokaci da aka keɓe cewa nan aka fara, sai dai babbar hikimar da ke tattare da wannan shi ne karin magana ta ratsa kowane fanni na rayuwar Bahaushe.

Matsayin Karin Magana

     An ɗauki karin magana a matsayin wani gishiri mai ba da ɗanɗano a cikin zance na yau da kullum ga duk wanda ya iya harshen Hausa. Sannan mawaƙa da sha’irai suna yawan amfani da wannan hikima a cikin waƙoƙinsu. Wannan na nuna lallai karin magana ya kai ƙololuwa domin irin matsayinsa ta fuskar adabi. Ga shi dai asalin karin magana adabin baka ne, to amma za a gan shi yana karakaina a dukkan wani nau’i na rubutaccen adabi ko na baka. Waɗannan sun shafi waƙa da zube da kuma wasan kwaikwayo. Kai ba a nan zancen ya tsaya ba, idan an duba mutum yakan siffanta kansa da wani karin magana har ya rikiɗe ya koma kirarinsa, maimakon kowa da kowa. Misali:

Ko ba a gwada ba, linzami ya fi ƙarfin bakin kaza: Karin magana ke nan.

Yaro duban ni da kyau! Ko ba a gwada ba, ka san cewa linzami ya fi bakin kaza: Kirarin ke nan.

Lokacin Yin Karin Magana

     Karin magana kamar yadda aka faɗi, gishiri ne a cikin zance, ya tabbata koyaushe ake yin shi. Amma ba kowa yake da fasahar baka ba. Sai dai duk lokacin da mutane biyu ko fiye suka haɗu kuma magana ta shiga tsakaninsu, da wuya ne ba a ji wani ya yi karin magana ba. Kafin Hausa, (1985), shi ma ya ratso kalamai cikin nazarinsa game da kirari, ya ce: “Kirari ya yi kama da karin magana ta fuskar cewa, duk lokacin da bukata ta taso a cikin taɗi ana iya sa su don mutum ya nuna gwanintarsa kan harshen.” Wannan ya tabbata cewa kowane lokaci ya kama ana wanzar da karin magana. 

Fasalin Karin Magana

     Yunusa, (1977), bai fasalta karin magana yadda wasu masana suka yi daga bayansa ba, ya dai ce suna da yawan gasken gaske. A cikin littafin dai ya kawo karin magana fiye da ɗari shida ya bayyana ma’anonin wasu daga ciki. Ya dai jero su ne bisa tsari na Abjadin boko, wato tun daga kan waɗanda suka fara da harafin ‘A’ a jere har zuwa harafin ‘S’.

     Masana irin su Malumfashi da Nahuce (2014) kuwa, sun fasalta karin maganar Hausa bisa dalili ko yanayi ko bigire na yadda aka gina ta. Sun dai nuna rabe-raben karin magana suna da yawa, amma kaɗan daga waɗanda nazarinsu ya kalato kuma suka kawo misalansu su ne:

Fasali                                                   Misali

Karin magana mai ƙwar ɗaya:                       Matambayi ba ya ɓata

Karin magana mai ƙwar biyu:                      Kowa ya ci zomo, ya ci gudu

Karin magana mai labari:                            Gaba ta kai ni, gobarar Titi a Jos

Karin magana mai ‘In Ji’:                          Zama wuri ɗaya tsautsayi ne, in ji Kifi

Karin mgana mai ‘Sai’:                             Sai bango ya tsage ƙadangare ke samun wurin fita.

Karin magana mai ‘An ce’:                       Ba dole ba, an ce wa ɓarawo ruga.     

Karin magana mai ‘Daga’:                       Daga ƙin gaskiya, sai ɓata.

Karin maga mai ‘Ko’:                              Ko kurum, Magana ce.

Karin magana mai ‘Dole’:                       Dole uwar na ƙi.

Karin magana mai ‘Har’:                         Cin danƙo har da su kaza.

Karin magana mai ‘Ta’:                           Ta malam ba ta wuce amin.

Karin maga mai ‘Tun’:                             Tun ranar gini, ranar zane.

Karin maga mai ‘Ana’:                             Ana so, ana kai kasuwa.

Karin maga mai ‘Wanda’:                        Wanda ya gani, shi ka faɗa.

Karin maga mai ‘Da-na-sani’:                   Da-na-sani ƙeya ce, a baya take.            

Karin maga mai ‘A’:                                 A dafa a daka, sai kalwa.

Karin maga mai ‘Da’:                              Da kai da kaya duk mallakar wuya ne.

Karin maga mai ‘Ba’:                               Ba a canza wa tuwo suna.

Karin maga mai ‘Tasirin Gargajiya’:        Sanin wurin bugu, shi ne ƙira.

Karin maga mai ‘Tasirin Musulunci’:        Azumi ba salla, holoƙo.

Karin maga mai ‘Tasirin Zuwan Turawa’:  Jirgin sama ba ruwanka da kwalta.

     Idan an duba littafin nasu za a ga sun kawo misalai na karin magana da yawa a ƙarƙashin kowane fasali. A nan kuwa an zaɓo ɗai-ɗai ne don a gwada misali. Bayan hakan, sai suka rattabo ratayen karin magana sama da dubu shida bisa tsari na Abjadin boko. Wato tun daga harafin ‘A’ zuwa harafin ‘Z’ don amsa sunan littafin nasu.

7.0 Wasu Samfurin Karin Magana a Ƙarni Na Ashirin da Ɗaya

     Su ma waɗannan karin magana an tsince su ne suna yawo a kafar sadarwa ta zumunta (WhatsApp) a watan Maris ta shekarar 2017. Su ne kamar haka:

i) Boka ya ci kuɗinmu, `yan Shi’a sun ji saukar Buhari a Nijeriya.

ii) Haƙuri dole, wai ɗan Shi’a ya ga Buhari a Bila

iii) Ka ji ɗan albarka, matar talaka ta ji muryar sarkin Kano.

8.0 Nazari da Sharhi

     Da yake an ce wani abu game da nazari a sama, yanzu kai tsaye sai a ce kamar yadda aka gani, waɗannan karin maganganu guda uku suna cikin fasalin karin magana mai labari waɗanda sun samu ne ta dalilin salon mulki a Nijeriya. Karin magana ta farko da ta biyu ta ambaci sunan Buhari. To ba wani ba ne face shugaban ƙasar Nijeriya Muhammadu Buhari. Abin da ya wakana shi ne, shugaban ƙasa ya yi tafiya zuwa ƙasar Landan (Birtaniya), domin hutawa da kuma duba lafiyarsa. Wannan ya sanya `yan Nijeriya da dama cikin zulumi, wasu kuma cikin farin ciki. Masu farin cikin tafiyarsa su ne suka yi ta fatar Allah ya sa sai gawarsa ce za ta dawo. Cikin ire-iren waɗannan mutane, akwai `yan Shi’a waɗanda suke ganin baƙin shugaba Buhari saboda ƙarƙashin mulkinsa ne aka kashe masu mabiya Shi’a da yawa a Zariya. Kuma an kame masu shugaba (Ibrahim El-Zakzaky) wanda har zuwa lokacin tattara wannan bincike yana tsare. An yaɗa jita-jitar suna tsaface-tsaface don dai Buhari ya mutu, kada ya dawo. Ikon Allah kuma da ya sha ƙarfin kowa da komai, sai ya ƙaddara dawowar Buhari sumul bayan ya kwashe fiye da wata guda a Birtaniya. Wannan lamari shi ya sa masu zulumi a lokacin tafiyar Buhari suka maye gurbin `yan Shi’a wato farin ciki. Wannan farin ciki ya sa an ƙago waɗannan karin magana mai cewa:

Boka ya ci kuɗinmu, `yan Shi’a sun ji saukar Buhari a Nijeriya.”

Haƙuri dole, wai ɗan Shi’a ya ga Buhari a Bila”

Wato ga Buhari ya dawo, sai dai wanda ya so mutuwarshi ya ɗauki haƙuri, tunda ya shiga fadar gwamnati da nufin ci gaba da aiki. Kuɗinsu da suka ba bokaye kuma sun sha ruwa. Mutane sun gina waɗannan karin magana da nufin miƙa saƙonsu ne ga maƙiya shugabancin Buhari. Suna tabbatar masu cewa Allah ya fi ƙarfinsu tunda ya hukunta dawowar Buhari ba tare da ya mutu kamar yadda suka so ba. Shi ya sa karin maganar ta ce haƙuri dole, da kuma boka ya ci kuɗinmu.

     Karin magana mai cewa: Ka ji ɗan albarka, matar talaka ta ji muryar sarkin Kano.” Ta samu ne saboda salon mulkin sarkin Kano na yanzu, wato Sunusi Lamiɗo Sunusi II. Mulkin nasa ya kalli matsalolin zamantakewar aure ne tsakanin musumi a jihar Kano. Don haka ya kafa kwamiti na malaman addinin musulunci don su kawo masa rahoto game da sharuɗɗan musulunci  ga yin aure ko ƙara aure. Sannan mulkinsa ya jaddada a matsayin doka wadda kowa zai bi don a sama wa mata sauƙi na wahalhalun da suke samun kansu a ciki sakamakon gallazawar mazajen aurensu. To da yake talakawa sun fi shan wahala, sarkin ya fi karkata a gare su. Wannan yunƙuri na sarkin Kano ta faranta wa jama’a da dama rai muasamman mata. Shi ya sa kwatsam sai ga wannan karin magana. Ita dai matar talaka babu abin da ya fi mata face ta sa wa sarki albarka, in ji masu hikimar magana.

Masana sun tabbatar da cewa karin magana tana ƙunshe da muhimmin saƙo. Misali Yunusa, (1977) ya ce: Ita irin wannan magana sau da yawa takan faɗakar da mutane ko kuma ta yi masu habaici. A wani lokacin kuwa takan yi kama da kirari.” Da haka kuwa za mu tabbatar da cewa karin maganganun da wannan maƙala ta kawo ta yi nazari a kansu, an yi hannunka mai sanda ne ga al’umma don su fahimci kurakurensu.

9.0 Kammalawa

     A Wannan maƙala an yi ƙoƙarin kawo wasu kirari ne da wasu karin magana da aka tsinto ta kafar sada zumunta kamar dai yadda bayani ya gabata. Haƙiƙa an fahimci lallai harshen Hausa da adabinsa da ma al’adunsa, na tafiya tare da kowane irin zamani. Game da kirare-kiraren da aka kawo, an tabbatar akwai asalinsu da daɗewa. Sai dai an fahimci akwai tasirin irin zamanin da ake ciki a kirare-kiraren. An gano kuma an tabbatar da cewa a tattare da kirari da karin magana har yanzu akwai ɗimbin hikima da zurfin ma’ana mai ɗauke da saƙo na musamman. An kuma ƙara fahimtar cewa kirari koyaushe akwai mai shi, wato kullum akan lanƙaya kirari ga mutum ko wani abu da ba mutum ba; yayin da karin magana ta kasance gishiri ne a cikin zance. Sai dai dukkansu ana aiwatar da su a duk lokacin da bukata ta taso a cikin zance don mutum ya nuna gwanintarsa ta fuskar sarrafa harshen Hausa da isar da saƙo cikin hikima.

 

MANAZARTA

Tuntuɓi mai takarda.

Post a Comment

0 Comments