Ticker

6/recent/ticker-posts

Nazari Kan Jawabin Kama Aiki Na Zababbun Gwamnonin Jihar Zamfara Daga Shekara Ta 2007 Zuwa 2019 (6)

Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu Jami’ar Tarayya Gusau.

Nazari Kan Jawabin Kama Aiki Na Zaɓaɓɓun Gwamnonin Jihar Zamfara Daga Shekara Ta 2007 Zuwa 2019 (6)

NA

NASIRU HASSAN

 

Jawabi

BABI NA BIYAR

KAMMALAWA

5.0 GABATARWA

Da sunan Allah mai rahama mai jinƙai. Dukkan godiya ta tabbata ga Allah mai kowa mai komai, Ubangijin  dukan halittu, wanda ya kasance tun kafin kasancewa ta kasance.

 

Salati da ɗaukaka su ƙara tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu (SAW), da alayensa da sahabbansa da masu binsu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

 

A wannan babi na ƙarshe, za a gabatar da wasu ‘yan shawarwari ga ‘yan uwa ɗalibai da jawabin taƙaitawa da na kammalawa da ta’arifin wasu kalmomi da rataye da kuma manazarta wato ayyukan da aka duba domin ƙarin bayani.

 

5.1 TAƘAITAWA

A wannan mataki, an taƙaita dukkan abubuwan da suka faru a cikin nazarin kasancewar kowane farko na da ƙarshe, saboda haka, wannan ɓangare na bayani kan abubuwan da aka yi ne a taƙaice.

 

Wannan aiki an kasa shi gida biyar, sannan akwai manazarta da rataye. A babi na farko ya ƙunshi gabatarwa, dalilin gudanar da bincike, muhallin bincike, manufar bincike, hanyoyin gudanar da bincike, muhimmancin bincike, farfajiyar bincike, matsalolin bincike da kammalawa. A babi na biyu ya ƙunshi bitar ayyukan da suka gabata wanda ya haɗa da gabatarwa da waiwaye kan ayyukan da suke da alaƙa da wannan, kamar bugaggun littafai, kundayen bincike, kundain digiri na biyu da kuma maƙalu da kammalawa. A babi na uku ya ƙunshi gabatarwa, taƙaitaccen tarihin jihar Zamfara, yawan jama’a, albarkatun ƙasa, sana’o’i yanayinta, ma’anar harshe, ma’anar siyasa, yaɗa labarum siyasa, kafuwar jam’iyyun siyasa, lafazin siyasa da manufarta a siyasance da kuma kammalawa. A babi na huɗu, ya ƙunshi gabatarwa, maanar salo, salo da siyasa, salo da lafuzzan siaysa, salo da sarrafa harshe, sai nazarin jawabin kama aiki na zaɓaɓɓun gwamnonin jihar Zafmara a shekarar 2007 da 2011 da kuma 2019. Sai kammalawa. A babi na biyar kuma ya ƙunshi gabatarwa, taƙaitawa, shawarwari, jawabin kammalawa, ta’arifin wasu kalmomi, rataye da manazarta.

 

5.2 SHAWARWARI

Ana iya ba da shawara cewa, siyasa abu ce mai amfani, amma idan ta karkata ga ba da gudummuwa ga al’umma, ba neman matsayi da gina kai ba. Maƙasudin yin siyasa shi ne samun ra’ayoyi daban-daban masu nufin gina al’umma da ƙasa. Abu na farko shi ne samun kafofin gudanar da zaɓuka da mutane na gari su shugabanci al’umma. Yana da kyau a cigaba da ilmantar da al’umma, ilimi ingantacce, wanda zai canja tunanensu daga son kai zuwa son ƙasa. Shi wannan ilimi ya ƙunshi na addini da na zamani. Ba a samun cigaba da ƙarya da zamba da son kai da cuta da sata da ƙarɓar rashawa. Duk waɗannan na danƙwafe ƙasa da sana’o’inta da tattalin arzikinta, ta koma ƙasa maras amfani.

 

Sannan akwai buƙatar son harshen da mutum ya tashi da shi, domin shi ne kawai zai fahimtar da shi sosai game da rayuwa da kuma muhimmancinta ta hanyar al’adunsa. Wannan na cikin illolin da siyasa ta haifar mana, rashin samun harshe na ƙasa sai da aka aro na turawa, wanda masu amfani da shi basu da yawa. Duk da cewa ana amfani da harsunan iyaye wajen jawaban siyasa, iyakarsu nan, idan aka tafi majalisa da kotu da harkokin gwmanati duk da turanci ake yi, wanda ‘yan boko kawai ke fahimta. Saboda haka, akwai alamar son kai na cewa su kaɗai ke iya wa, wato su za su yi ko yaushe.

 

5.3 JAWABIN KAMMALAWA

Dukan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin halittu, tsira da aminci su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu da Alayensa da sahabbansa da masu binsu da kyautatawa har zuwa rana sakamako.

 

Masu iya magana kan ce “Komai ya yi farko to zai yi ƙarshe, tafiya ta yi tafiya, tun ana tunanen irin batun da za a bayar har zuwa yadda za a tattara bayanan su zamo abin da suka zama ga shi Allah ya yarda an zo ga fagen yin jawabin kammalawa.

A taƙaice dai an kutsa ga masana daban-daban kuma an yi ƙoƙarin fito da bayanai dangane da wannan bincike waɗanda ake ganin masu alfanu ne ga al’umma da ɗaliban ilimi kamar yadda masana suka yi bayani kan a bin da ya shafi tarihin Zamfara da ma’anar siyasa da shugabanci da ma wasu abubuwa da dama da aka yi bayani a baya. Wannan aikin an ba shi taken “NAZARI KAN JAWABIN KAMA AIKI NA ZAƁAƁƁUN GWAMNAN JIHAR ZAMFARA DAGA SHEKARAR 2007 – 2019”.

 

A nan wannan bincike ya kawo ƙarshe da aka gudanar, muna roƙon Allah (SWT) ya sa shi mai amfani a garemu da kuma ɗaukacin al’umma gaba ɗaya, ya kuma sa ya zama sanadin ɗaukakar harshen Hausa a faɗin duniya.

 

Sakamakon da wannan aiki ko bincike ya gano shi ne:

·         Ta hanyar wannan nazari an gano irin yadda zaɓaɓɓun Gwamnoni ke gudanar da jawabansu da irin alƙawuran da suke yi zuwa ga al’ummarus, da kuma yadda suke ƙoƙarin cika alƙawuran

·         Haka ma an gano ta hanyar wannan bincike irin muhimmancin da ke tattare wajen nazartar irin waɗannan jawabai, domin ta hanyar nazari ne ake fito da ɗimbin abubuwa da suka shafi harshe da salo da kuma sarrafa harshe.

·         Haka kuma ta hanyar wannan nazari an gano irin kalaman da ‘yan siyasa kan yi amfani da su musamman gwamnoni, wajen jawo hankalin jama’arsu don su yarda da abin da suke faɗa.

 

5.4 TA’ARIFIN WASU KALMOMI  

1.      Alaye                          =          Iyalan gidan Annabi (SAW)

2.      Bagire                         =          Wuri

3.      Bincike                       =          Nazari

4.      Farfajiya                     =          Muhalli, Haraba

5.      Gudana                      =          Cigaba

6.      Tuntuɓa                     =          Bibiya

7.      Sigogi                         =          Ire-ire

8.      Mu’amala                  =          Hulɗa

9.      Maƙasudi                   =          Manufa

10.  Rangwame                =          Jinƙai, tausayi, nasiha, sauƙi

11.  Ɓullowa                     =          Fitowa

12.  Ƙirƙira                        =          Samarwa

13.  Ɗumi                          =          Zafi

14.  Bishiyoyi                   =          Itatuwa

15.  Kuza                           =          Zinari

16.  Ƙiraga                         =          Fatu

17.  Manufa                      =          Dalili

18.  Ɓirɓishi                      =          Alama

19.  Maƙalu                       =          Takardu

20.  Ɗorawa                      =          Azawa, Farawa

21.  Internet                      =          Yanar gizo

22.  Sharhi                         =          Bayani

23.  Kwatantawa =          Sifantawa

24.  Martani                      =          Mai da jawabi

25.  Martaba                     =          Ƙima, daraja

26.  Rataye                        =          Waiwaye

27.  Fanni                          =          Sashe

28.  Shige                          =          Kama

29.  Tattaunawa               =          Harhaɗawa

30.  Natsuwa                    =          Amincewa, yarda, gamsuwa

31.  Ɗorawa                      =          Azawa, farawa

32.  Sharhi             =          Bayani

33.  Kwatantawa =          Sifantawa

34.  Martani                      =          Maida jawabi

35.  Tattarawa                  =          Harhaɗawa

36.  Natsuwa                    =          Amincewa, yarda, gamsuwa

 


 

4.5 RATAYE

Samfari na ɗaya (2007)

“Da sunan Allah mai rahama mai jinƙai, tsira da aminci su tabbata ga Manzonsa Annabi Muhammadu (SAW).

 

Ina fara wannan jawabi da godiya ga Allah maɗaukakin sarki da ya nuna man wannan rana mai cike da tarihi, wato lokacin karɓar ragamar mulkin Jihar nan, inda aka samu tarihin da ba a taɓa samu ba a siyasar ƙasar nan, inda aka samu gwamna mai barin gado ya miƙa wa mataimakinsa ragamar mulki.

 

Ina ƙara miƙa godiya ga al’ummar jihar Zamfara da kuka bamu goyon baya ganin mun samu nasara ta hanyar jefa mana ƙuri’unku a jam’iyyarmu ta ANPP, inda aka zaɓi dukan ‘yan takararmu a kowane mataki.

 

Ya ku masu girma mahalarta wannan taro goyon bayan da kuka ba gwamnatin da ta gabata. Ina fatar ku cigaba da bani shi domin kawo ayyukan raya ƙasa da na haɓaka tattalin arzikin wannan jiha. Zamu cigaba da shirye-shiryen tsohuwar gwamnati ta “Alhaji Ahmad Sani Yariman Bakura” tare da fito da wasu sababbi kamar inganta noma duba da irin gudummuwar da yake bayarwa wajen haɓaka tattalin arziki.

 

Za mu ba da kulawa ta musamman a ɓangaren ilimi da gine-gine da ɓangaren kiwon lafiya da samar da ruwan sha masu tsafta da taimaka wa samari maza da mata.

 

Daga ƙarshe ina tabbatar wa da iyayenmu sarakuna cewa wannan gwamnati za ta tafi da ku tare da karɓar shawarwarinku. Ina ƙara godewa Allah maɗaukakin sarki da kuma dattijan wannan jam’iyya tamu mai albarka da al’ummar jihar Zamfara baki ɗaya.

 

SAMFURI NA BIYU (2011)

Ina matuƙar godiya ga Allah maɗaukakin Sarki da kuma godiya ga Shuwagabannin Jam’iyya, musamman jagora Alh. Ahmad Sani Yariman Bakura, ina ƙara godewa al’ummar Jihar Zamfara da kuka fito ƙwanku da ƙwarƙwatarku kuka zaɓe ni a wannan matsayi da nake kai a yau. Wannan babu ko shakka nasara ce tamu baki ɗaya. Bayan haka, ina kira ga waɗanda suka sha ƙasa a wannan tafiya (‘Yan adawa) da su zo mu haɗa hannu waje ɗaya domin cigaban wannan jiha tamu baki ɗaya ta kowane fanni. Dukaninmu Zamfarawa ne, babu abin da ya fi mana Jiharmu. Don haka, dole mu haɗa kanmu domin ba za mu bari ‘ya’yanmu da jikokinmu su lalace kan siyasa ba”

 

“Za mu mai da hankali ganin an dawo da ɗaliban da suka bar makarantunsu a sanadiyar rashin biya masu kuɗaɗen makaranta tare da basu ilimi kyautata faɗin jihar nan. Haka ma za mu jawo masana’antu da masu hannu da shuni da su saka jari a wannan jiha domin cigaban tattalin arziki a wannan jiha, Wannan gwamnati ba za ta ɗauki sakaci da almubazziranci da dukiyar jama’a ba.

 

Gwamnatin da ta gabata ta bar ɗimbin bashin biliyoyin kuɗi kama daga na bankuna zuwa na ‘yan kwangila wanda ya kawo sanadin taɓarɓarewar tattalin arzikin jiha.

 

Daga ƙarshe, ina kira ga al’umma da ku bamu goyon baya domin fito da wannan jiha halin da take ciki”.

 

SAMFURI NA UKU (2019)

Ina godiya ga Allah Subhanahu wata ala da ya nuna mana wannan rana da na zama gwamnan Zamfara.

 

Yau rana ce mai cike da tarihi gare ni da jam’iyyata ta PDP wanda ba a taɓa samu ba a tsawon shekara ashirin (20) ana gudanar da mulkin wannan jiha.

 

Jama’ar Zamfara zaɓe ya ƙare don haka, mu aje duk wani bambancin siyasa mu haɗu mu ciyar da jiharmu gaba. Alhamdulillahi! Yau ni ne Gwamnan Zamfara don haka zan yi aiki da kowa domin gudanar da mulki a wannan jiha insha Allah!

Ina sane da ƙalubalen da jihar nan take fuskanta, jama’ar Zamfara na buƙatar gwamnati da za ta kula da matsalar tsaro da ke addabarsu. Zamu yi duk mai yiwuwa domin kawo ƙarshen matsalar tsaro a faɗin jihar nan.

 

An san jihar Zamfara da noma, abin damuwa ne idan aka yi la’akari da sunan da ta yi a ƙasa da duniya baki ɗaya. Don haka, zamu farfaɗo da noma ta hanyar tallafawa manoma da inganta noman zamani na (ZACAREP) ta hanyar tallafawa manoma don inganta noma. Haka ma zamu bunƙasa ilimi wajen ganin duk yaranmu sun shiga makaranta. Haka ma zamu tallafawa harkokin lafiya. Zamu fito da hanyoyi don samar da gine-gine musamman a babban birnin jiha Gusau. Mun lura da cewa an barmu baya, gwamnati za ta gina hanyoyi don ganin an yi amfani da albarkatun ƙasa da Allah ya hore mana don kakkaɓe talauci da samar da walwala a faɗin jihar nan, tare da kula da yan gudun hijira da suka bar muhallansu sanadiyar rashin tsaro a yankunansu.

 

Daga ƙarshe, ina addu’a ga Allah subhananu Wata’ala da ya bamu damina mai albarka da yabanya mai yawa amin”.

 


 

MANAZARTA

Tuntuɓi masu gudanarwa.

Post a Comment

0 Comments