A cikin shekarar 1909 Gwamna Luggard ya umurci Hans Vischer wanda ake yi wa laƙabi da Ɗan Hausa, da ya sake buɗa wata makaranta a Kano. Domin a horar da malamai ‘yan ƙasa musulmi da za su yi aikin koyarwa (Graham, 1966:79). Da tafiya ta miƙa sai aka dinga buɗe makarantu a Lardunan jihohin Arewa.
Bin Diddigin Silalen
Tubalin Ginin Littafin Ruwan Bagaja
Dr.
Adamu Rabi’u Bakura
08064893336
1.0 Gabatarwa
Ƙudirin wannan maƙala shi ne, ta
binciko asalin zaren tunanin da Abubakar Imam ya yi amfani da shi a yayin da
yake fafutukar tattara tubullan tayar da ginin littafin Ruwan Bagaja. Gasar ƙagaggun labaran Hausa
da aka aiwatar a shekarar 1933 da ta zama sanadin ficensa a fagen rubutattun ƙagaggun labaran
Hausa, har duniya ta san shi.
Sai dai gurin wannan maƙala ba zai cika ba
sai ta waiwaya baya. An shiga fagen tarihi, domin asami damar sanin abin da ya
shuɗe, ta kowace fuska
yana da amfani ga rayuwar ɗan adam, musamman manazarta. Dalili kuwa, masana tarihi
sun ce, duk wanda bai san abin da ya wanzu kafin a haife shi ba, zai taƙaita ga sanin abin da
ya ji ko ya gani, ba tare da gane sanadin aukuwar hakan ba. Wannan ne ya sa maƙalar ta bi diddigin
tarihin kafuwar makarantu boko, da hanyoyin da aka bi wajen ɗabbaƙa rubutattun ƙagaggun labaran Hausa
cikin sigar rubutun Romawa (boko). Haka an kawo dalilan da suka haifar da
wanzuwar hukumomin inganta adabi a ƙasar Hausa da ƙas ashen ƙetare. An kuma nuna
irin rawar da suka taka wajen tabbatar da muradinsu na aza harsashin ginin
rubutattun ƙagaggun Labaran Hausa. Ko ba komi ai an ce “ Waiwaye adon
tafiya”. Domin yin haka, zai bai wa mai karatu haske game da inda aka fito da
inda za a dosa.
2.0 Makarantun Boko Na Farko A Ƙasar Hausa.
Bayan Turawan Mulkin Mallaka sun
kafa mulki a ƙasar Hausa.Daga nan suka shiga tunanin buɗe makarantu domin
koya wa ‘ya’yan Hausawa karatun boko. An kafa makarantun ne don su sami waɗanda za su taimaka
musu wajen gudanar da ayyukkan mulki da suka shimfiɗa. A sakamakon haka
ne, suka buɗe makarantar farko a
Sakkwato cikin shekarar 1905 a ƙarƙashin shugabancin
Mista Burden da mataimakinsa Malam Ibrahim wanda daga baya aka tura shi Ingila
domin ya ƙaro Ilimi (Graham, 1966:59) da ( Taiwo, 1986:45). Da
farko Razdan na Sakkwato bai sami haɗin kan sarakunan yankin ba game da sabon
tsarin ilimin, don gudun kada ‘ya’yansu su zama kiristoci (Ibrahim, 1979:32).
Da suka fahinci lamarin ba haka yake
ba. Sai suka yi na’am da shirin bayar da ilimin. Wannan ne ya sa Sarkin Gwandu
ya tura yara biyu, haka sarkin Tambuwal ya aika da yara biyu. Ƙoƙarin samun jerin
sunayen ɗaliban farko na
makarantar ya faskara. A daidai shekarar 1907 makarantar tana da ɗalibai 36, waɗanda aka tura daga
gidajen Sarakunan Sakkwato da Gwandu da Argungu, kamar yadda ( Taiwo, 1986:45)
da ( Malumfashi, 2009:36) suka bayyana. Wannan ya kawar da ra’ayin da ke cewa,
makarantar farko an assasa ta ne a kano ba Sakkwato ba. Abin kula a nan shi ne,
Razdan da ya buɗa makarantar ai
wakilin gwamnati ne, ya yi haka a madadin gwamnatin. Hasali ma ba wani jami’i
da ke sama da shi da ya taka masa birki kamar yadda aka yi wa ‘yan mishan a
yayin da suke ƙoƙarin buɗa makarantunsu a yankunan musulmi. An kuma ci gaba da
koyo da koyarwa, har an kawo wani akawu da ke aiki a sashen mulki da ya saba da
aikin koyarwa, a matsayin ƙaramin malami domin ya taimaki Malam
Ibrahim wajen koyar da ɗalibai darussa na
tsawon awa huɗu a sati (mako). Ba
wata rubutacciyar shaida da ta nuna an rufe makarantar. Makarantar ce aka ci
gaba da faɗaɗawa tun daga
makarantar lardi ta zama ta midil, ta koma kwalejin gwamnati har zuwa lokacin
da ta kasance Kwalejin Nagarta a yau 2013. Don haka ne aka ɗauki cewa, ɗaliban makarantar
boko na farko sun fito ne daga Sakkwato ba Kano ba. Akwai kuma tabbacin cewa,
Sarkin Musulmi ya ɗauki ɗawainiyar bayar da kuɗaɗen gudanar da
makarantar. An kuma sami bayanan da suka nuna ɗalibai uku na makarantar sun kamala
karatunsu, sun kuma kama aiki a Ofishin Razda a kan matsayin mataimakan akawu a
shekarar 1907 (Taiwo, 1986:45).
A cikin shekarar 1909 Gwamna Luggard
ya umurci Hans Vischer wanda ake yi wa laƙabi da Ɗan Hausa, da ya sake
buɗa wata makaranta a
Kano. Domin a horar da malamai ‘yan ƙasa musulmi da za su
yi aikin koyarwa (Graham, 1966:79). Da tafiya ta miƙa sai aka dinga buɗe makarantu a
Lardunan jihohin Arewa.
3.0 Matakan Samar da
Rubutattun Ƙagaggun Labaran Hausa a Sigar Rubutun
Boko
Bayan kafuwar makarantu boko da yaɗuwar ilimin zamani a
Nijeriya ta Arewa. Abu na farko da aka fuskanta shi ne, matsalar ƙarancin litattafan
karantawa a makarantun. Yayin da Hans ya tafi hutu Ingila a shekarar 1911, ya
gudanar da tarurruka da masu ruwa da tsaki ga sha’anin mulkin ƙasar, domin ganin an
samar da littattafan karatu don shiga sabuwar shekarar karatu cikin watan
Oktoba (Graham,1966:83). Ya kuma fuskanci matsalar rashin takamaiman abjadin da
zai mayyaze saututtukan harshen Hausa a sigar rubutun boko (Graham,1966).
‘Yan Mishan sun haɗu a Lakwaja, suka
gabatar da buƙatar samar da tsayayyen abjadin da zai ƙunshi wasu
saututtuka, na harsunan Hausa da Nufanci da Yarbanci da harsunan da ke Lardin
Binuwai. A harshen Hausa, sun amince da a yi amfani da haruffa 29, idan aka
cire harafin “q” da “x” a wajen rubuce-rubucen adabin mishan (C.M.S., 1911/NN).
A Nijeriya ta Arewa, Hans Vischer ne
mutun na farko da ya fara shata ƙa’idodin rubutun
Hausar boko. A tsarin abjadinsa ya amince da ayi amfani da haruffa 28, ya cire
haruffan “c” da “q” da “v” da “x”. Ya yi tsokaci a kan baƙaƙe da wasulla da auren
wasali kamar “ai” da “au” da wakilin suna, da zagi, da yadda ake samar da jam’i
da lokuttan aikatau. Ya aminta da a rubuta kalmomin Larabci da suka danganci
shari’a da addini kamar yadda ake furta su a harshen Hausa. Sunayen Larabci
kuwa za a rubuta su kamar yadda suke. Kalmomin Ingilishi kuwa sai a fassara su
da Hausa (Vischer, 1912:3) da (Graham,1966:86) da (Zaruk, 1988:116-7).
George Parcy Bargery ya yi wa
abjadin Hausa wasu gyare-gyare da suka haɗa da:
Watsi da tagwan
harafin “ch” ya ɗauki “c”. Ya amince da harafin “sh” da “ts”. A
wajen ɗauri kuwa, ya yi
amfani da “ssh” da “tts”, ba “shsh” da “tsts” ba.
Ya yi amfani da waƙafi a gaban
hamzatattun baƙaƙe a madadin ɗigagga da ake sawa a ƙarƙashinsu, misali: ‘b,
‘d, k’.
Abjadin Bargery ya fi kusanta da
lafuzzan Hausa fiye da na sauran da suka gabace shi. Ƙa’idojinsa na raba
kalma sun fi na sauran , kamar yadda Zarruk (1980: 117-8) ya nuna.
4. 0 Samar Da
Hukumomin Inganta Adabin Hausa
Bayan wannan, sahihiyar hanyar da
aka fara bi domin ganin an samar da ingantaccen harsashin gina ƙagaggun labaran Hausa. Haka kuma an yi azamar samar da wasu
hukumomi a cikin gida, da ƙasar Turai da aka aza wa alhakin
kyautata adabin Hausa da kuma haɓaka shi. Hukumomin da aka ratayawa alhakin
tafiyar da wannan aikin su ne:
(i) Hukumar Ƙasa Da Ƙasa Ta Nazarin
Harsuna Da Al’adun Afirka ( International Insitute Of African Languages And
Cultures) mai cibiya a London.
(ii) Hukumar Fassara
(Translation Bereau). Da farko a Ofishin Makarantar Ɗan Hausa, Kano. A
shekarar 1930 ta sami ofishinta na dindindin a Ƙofar Tukur-Tukur da
ke Zariya.
(iii) Hukumar Talifi
(Literature Bereau) mai cibiya a Zariya.
(iv) Hukumar Yaƙi Da Jahilci
(Northern Regional Literacy Agency (NORLA) mai cibiya a Zariya.
Waɗannan hukumomi sun yi rawar gani ta
haujin biyan muradun da suka sa aka kafa su, a cikin fasalin da ya dace.
5. 0 Tarihin Samuwar
Gasar Rubutattun Ƙagaggun Labaran Hausa
Bayan da Turawan Mishan da haɗin gwiwar gwamnatocin
mulkin mallaka sun samar da Hukumar Nazarin Harsuna Da Al’adun Afirka. Hukumar
ta aza harsashin ginin adabin Afirka cikin sigar rubutun boko, musamman
rubutaccen ƙagaggen labaran Hausa, a shekarar 1929. A farkon shekarar
ne hukumar tare da hukumomin da ke kulawa da lamurran ilimin ƙasashen Afirka suka
shirya gasar rubutun ƙagaggun labaran Hausa, da wasu harsunan nahiyar (zube).
An gudanar da gasar ne a London, inda akasarin waɗanda suka fafata malaman makarantar
boko ne. A gasar an gabatar da
littattafai 37. Littattafai goma daga ciki na harshen Hausa ne, littattafai sha
biyar sun fito daga harshen Suto. Littattafai tara daga harshen Ganda. Littafi
biyu kuwa daga harshen Madingo suke. Littafi ɗaya a cikin harshen Mende aka rubuta
shi.
Ba wani littafi da ya zo na ɗaya. An sami littafai
biyu da suka sami kyautar fam goma kowannansu. A harshen Suto ‘yantakara huɗu suka sami kyautar
fam biyar. Haka kuma, wasu uku suka sami kyautar fam uku. A harshen Hausa kuwa,
‘yantakara biyar ne suka sami kyautar fam uku kowannansu. Daga cikin
littattafan da suka sami kyauta a harshen Hausa sun haɗa da:
Hausa Stories na H.G.B.
Nuhu,
Hausa Stories na Malam
Dodo,
Zaman Dara na Malam
Ahamet Metteden,
Littafin Karatu Na
Hausa na Malam
Bello Kagara,
Takobin Gaskiya na Malan
Nagwamatse Ɗan M. Alƙali Sakkwato (Westerman,1933:102-3).
Abin kula a nan shi ne, hukumar ba
ta wallafa waɗannan littattafai ba.
Ta dai buƙaci hukumomin ilimi da ƙungiyoyin Mishan da
lamarin ya shafa, su taimaka su buga. Sai dai har zuwa yau, babu wani
rubutatcen bayanin da aka ci karo da shi mai nuna an buga littattafan.
5. 1 Littattafan Ƙagaggun Labaran Hausa
Da Aka Fara Wallafawa
Tun lokacin da aka fara ƙoƙarin samar da
littattafan ƙagaggun labaran Hausa. Ba a sami littafi ko ƙwara ɗaya da aka wallafa
ba, domin koyarwa tare da nishaɗantarwa ga al’umma. Domin har zuwa farkon shekarar 1933,
ba wani wallafaffen rubutaccen littafin ƙagaggen labaran
Hausa. Hana rantsuwa littafin Fatima wanda Dokta Walter R. Miller ya wallafa,
wanda Church Missionary Society Bookshop suka buga a Legas cikin shekarar 1933.
Sai dai littafin bai yi fice ba, sakamakon jigon da ya ƙunsa na yaɗa addinin mishan.
A cikin shekarar ne, gwamnati ta
hango buƙatar wallafa littattafan ƙagaggun labarai cikin
harshen Hausa, don amfanin masu koyon Hausar boko. Wannan buƙata ta sa R.M. East
yin rangadin sassan Arewacin Nijeriya. An gana da ‘yan boko game da manufar da
aka sanya a gaba ta shiga gasar rubuta ƙagaggun labaran
Hausa. Kuma an yi alƙawalin za a bayar da kyauta ga wanda ya nuna hazaƙa a kuma buga
littafinsa duniya ta san shi (Ibrahim, 1979:34). Wannan gasa ita ta samar da
littattafan ƙagaggun labaran Hausa da suka yi fice, waɗanda suka haɗa da:
Ruwan Bagaja na Malam Abubakar Kagara,
Ganɗoki na Malam
Bello Kagara,
Shaihu Umar na Malam
Abubakar Tafawa Ɓalewa,
Idon Matanbayi na Malam
Muhammadu Gwarzo,
Jiki Magayi na R.M.East
da Tafida, da kuma
Iliya Ɗanmaiƙarfi na Malam
Ahmadu Ingawa, kamar yadda (Ibrahim, 1979:34) ya nuna. Ayyuka da dama kamar,
East, R.M. (1941), da Baldin, S. (1977), da Yahaya, I.Y. (1988), da Malumfashi,
I..(2009) ,da Adamu, A.A.(2009) bas u sanya shi ciki sahun littattafan gasar
farko ba. An dai nuna an wallafa shi a shekarar 1951, bayan shekara 17 da yin
gasar.
Duk da kasancewar waɗannan ne aka zaɓa a matsayin waɗanda suka sami
nasara. An tsara wasu da aka yi ƙudurin wallafawa. Sai
dai hakan bai samu ba. Littattafan kuwa su ne:
Boka Buwayi na Malam
Nagwamatse,
Yarima Abba na Malam
Jumare.
Wannan ita ce gasa ta biyu, a cikin
tarihin rubutaccen ƙagaggun labaran Hausa. Kuma ita ce ta zaƙulo mutane masu
hikima da suka bayar da gagarumar gudummawa, wajen haɓaka karatun boko da
rubutaccen adabin Hausa.
Littafin Ruwan Bagaja, ya samu
nasarar zama na farko a gasar. Littafin
yana ƙunshe da babi takwas ban da gabatarwa. Littafin ne ya
fito da Abubakar Imam fili har duniya ta
san shi. Saboda irin yadda littafin ya samu karɓuwa a hannun Turawa. Ko kuma a
ce, alƙalan gasar, da suka
yanke hukunci cewa, littafin ne ya zama zakara a kan wasu dalilai da za a iya
gani nan gaba.
6. 0 Tubalan Ginin
Littafin Ruwan Bagaja
Abubakar Imam ya ƙaga littafin ne ta
hanyar, tsakuro nan, da can, ya haɗa labaran da ke cikin littafin. Littafi yana ƙunshe da tubalai a ƙalla guda biyar, da
mawallafin ya yi amfani da su wajen gina
littafin nasa. Tubalan kuwa su ne:
6. 1 Tatsuniyar Ruwan
Bagaja :
Idan aka ɗauki taken littafin
ana iya cewa an samo shi ne daga tatsuniya mai suna “ Tatsuniyar Ruwan Bagaja”.
Ita dai wannan tatsuniya ta ƙunshi labarin ‘yar bora, wadda aka yi
wa ƙagen
ta yi fitsari a ƙirgi. Don haka, aka tura ta kogin Ruwan Ruwan Bagaja
wajen wanke ƙirgin. Tafiyarta kogin ya zama sanadin ta sami alheri mai
yawa tare da martaba. Ta samu dukiya mai ɗinbin yawa. Ga yadda aka nuna a tatsuniyar:
“Da ta fasa sai tag a mutane sun ci ado sun hau dawakai ana busa algaita ana yi
mata kirari. A ɗora ta kan doki aka
raka ta gida. Duk ƙamshin turare da bushe-bushe suka cika gari” (Yahaya,
1971:42 bk4). A ɗaya ɓangaren kuma, sarkin
garinsu ya aure ta. Wannan ya faru ne sakamakon dangana da rashin kwaɗayi da tare da
ladabin da ta nuna ( Yahaya, 1971:33, Bk4).
A littafin Ruwan Bagaja, an nuna
Alhaji ya tafi neman Ruwan Bagaja, a sakamakon cin mutuncin da sarki ya yi wa
mijin mahaifiyarsa a bainar jama’a (Imam, 1994:5-6). Tafiyar ta zamar masa
alheri. Ya samo zobe daga Sarkin Aljannu, wanda ke da wani bawa mai yin hidima
ga zoben tare da biyan buƙatun wanda ya mallaki zoben. Ga yadda aka nuna “Da za mu
rabu, ya kawo wani zobe ya ba ni na zinariya, ya ce shi ma yana da bawa kamar
na takobin nan. In na ji na matsu, na goge shi sai bawan ya fito, don ban iya
riƙon
takobin nan” ( Imam,1994:40). A ɗaya haujin kuma, ɗan sarkin garin ya
warke daga cutar da ke addabarsa (Imam,1994:42-4).
6. 2 Tatsuniyar Gizo
da Hankaki
Idan aka duba littafin Ruwan Bagaja,
za a tarar akwai alaƙa a tsakaninsa da tatsuniyar. Domin a labarin, an nuna
Alhaji Imam ya tsunduma a cikin ruwa. Da
ya nutse ya sadu da garin ‘yanruwa. Ga yadda aka nuna lamarin “..Yau ga yaran
banza, sun dai mai da mutane makafi. Ai na san mun kawo. “sai na diro daga
jirgi wai in faɗa ƙasa. Da faɗawata sai na nutse,
na yi ƙasa! Abin ikon Allah sai na isa wani gida a ƙasan tabkin, na tarad
da waɗansu irin mutane masu
manyan kawuna. Ashe ‘yan ruwa ne, suka yi maraba da ni” (Imam,1994:16). Wannan
ya auku ne sakamakon rashin godiyarsa ga yaransa guda biyu. Haka a tatsuniyar
gizo da hankaki, an nuna gizo ya tsunduma cikin ruwa bayan hankaki sun gudu sun
bar shi a kan itaciyar dabinon. A wani ƙaulin, ɓaure da ke tsakiyar
ruwa. Ga yadda tatsuniyar ta nuna “…Sai ya faɗa cikin ruwa tsundum. Ya nutse can ƙasa. Sai kuwa ‘yan
ruwa suka gan shi suka ce, “La, ga shi ya zo, ga shi ya zo” (Yahaya, 1974:7
bk1). Wannan duk sakamakon rashin godiyarsa a kan karamcin da hankaki suka yi
masa tun da farko ta hanyar ba shi dabino. Irin waɗannan kamance da
kusance ya sa ake zaton daga tatsuniyar aka gina labarin. Dalili kuwa,
tatsuniyar ta riga littafin samuwa.
6. 3 Tatsuniyar Gizo
da Fatalwa
A cikin kayan cikin littafin an nuna
Alhaji Imam ya karɓi san Zandoro ɗan Zantori a bisa
sharaɗin, bayan kwana
bakwai zai dawo a biya shi ta hanyar taɓa kansa. In ya kasa zai tafi da shi ya yanka
ya ba gunkinsa jini ya sha. Ga yadda lamarin yake “..Wa zai amshi sana, in an
yi kwana bakwai in zo ya taɓo kaina?” (Imam, 1994:16) Labarin bai da wani bambanci da
abin da ke cikin tatsuniyar gizo da fatalwa, wadda aka nuna gizo ya karɓi saniyar Fatalwa
bisa sharaɗin bayan shekara ɗaya za ta dawo ya taɓa kanta. In ya kasa
za ta je da shi ta yanka ta sha jininsa. A tatsuniyar an nuna cewa “ Fatalwa
tana yawo da santa cewa “ Wa zai karɓi sana, in shekara ta dawo in zo ya taɓa kaina? (Rattray, 1913) Bambancin da ke takaninsu shi
ne na suna. A littafin an ce Zandoro, a tatsuniyar kuma aka ce Fatalwa a wani ƙaulin aka ce Mutuwa.
Hanyoyin da aka yi amfani da su wajen kuɓuta duk kusan ɗaya ne. Domin kuwa, lokacin da Zandoro
ya je a taɓa kansa ya sami
Alhaji Imam na cikin ɗaki. Ya tsaya na
tsawon lokaci yana jiran shi ya fito, har ya kai ga yi masa magana. Shi kuma
Alhaji ya ce wai ya tsaya lallaɓe bangon ɗakinsa da ya tsage. Lokacin da Zandoro ya sunkuya ya leƙa cikin ɗakin ya ganar wa
idonsa yadda ake ɗinke bango, sai Imam
ya yi farat ya shafa kan zandoro ya ce na taɓa, mutane suka shaida ya taɓa. An nuna shi kamar
haka a littafin, “…To fito, alƙawali ya cika!” Sai na ce masa, Dakata
kaɗan, in gama lallabce
bangon ɗakin nan da ya tsage
da damina”. Ya ce, “Kai yaya ake ɗinkn bango? Na ce ba wuya a garinmu, leƙo ka gain.” Sai ya
cuso kai don ya gain. Sai na yi farar na taɓa kansa, na ce, “ Ah na taɓa!” (Imam,
1994:16-17).
A tatsuniyar Gizo da Fatalwa ta irin
wannan hanyar ce aka kuɓuta. Shi ma Gizon ɗaki ya shiga, Fatalwa
ta yi ta jiransa har ta ƙagara ta yi masa magana. Sai ya ce, wai ruwan da ya zube
ne yake tsinta. Jin haka sai ta sunkuya ta ga yadda ake tsintar ruwa. Da ga nan
sai ya yi farat ya taɓa kanta. Shi ma
mutane suka shaida ya taɓa. Ga yadda aka nuna
a tatsuniyar “ To fito alƙawali ya cika!” Gizo ya ce mata, “ jira ni kaɗan ruwa suka zube,
ina tsincewa ne” Sai ta ce, “ Kai yaya ake tsintar ruwa? Bari in leƙo in ga yadda ake
tsintar ruwa”. Sai ta saka kanta ɗakin, sai ya yi farat ya taɓa. Ya ce, Eh! Na taɓa! Duk waɗannan tatsuniyoyin sanannu ne a farfajiyar ƙasar Hausa. Sai ɗan bambancin da akan
samu a cikin su. Saboda wannan kusanta ne, ake kyautata zaton cewa, da waɗannan tatsuniyoyi ne
ya yi amfani wajen gina wasu sassan littafin Ruwan Bagaja.
6. 4 Ma’ul Haya (The
Water of Life)
Birniwa (1981-2) da Malumfashi
(2009) sun nuna cewa, an gina littafin
Ruwan Bagaja a kan wani littafin Larabci da ake kira “MA’UL HAYA” wanda
Turawa suka fassara da “ WATER OF CURE”. Masu wannan ra’ayi sun nuna cewa,
Larabawa sun riga Turawa samun wayewar kai. Wannan ya sa, suka koyi harshen
Larabci. Hakan ne ya ba su damar fassara wasu abubuwan Larabci ciki harshen
Ingilishi. Ko ma tatsuniyar Ruwan Bagaja ana kyautata zaton daga Larabci aka
samo ta. A lokacin da malaman zaure suka karanta irin waɗannan littattafai na
Larabci. Su kuma suna gaya gaya wa mutane a yayin da ake gudanar da darussa.
Wai daga nan ne ake jin tatsuniyar ta bayyana (Tsiga,1986).
Ana kyautata zaton akwai wasu
tubalai da aka ciro daga wani littafi mai suna The Brothers Grimm Fairy
Tales musamman a labarin “The Water of Life”. Misali a littafin Ruwan
Bagaja, an nuna cewa, Yarima ɗan sarki ba ya da lafiya, sai an kwantar an tayar. Liman,
uban Imam ya bayar da shawarar a nemi Ruwan Bagaja a ba Yarima ya sha, zai
warke. Shawarar ta baƙanta wa sarki rai har ya muzanta Liman a bainar jama’a.
Wannan lamarin ne sanadin fitar Imam zuwa neman Ruwan Bagaja (Imam, 1994:5-6).
A labarin The Water of Life kuwa an nuna sarkin ne ba lafiya, ‘ya’yansa
suka damu matuƙa, har wani tsoho ya bayar da shawarar a nemo Ruwan
Bagaja. Ga yadda aka nuna. “Wata rana, sai sarki ya tashi da rashin lafiya, sai
a kwanta, sai a tayar. Ciwo ya tsananta, har an fitar da zuciya ga rayuwarsa.
Rashin lafiyar sarkin, ta sanya ‘ya’yan nasa cikin yanayi na damuwa. Wata rana
suna yawo a cikin lambun sarki, sai suka haɗu da wani tsoho. Tsohon ya tambaye su abin da
ke damun mahaifinsu, sai suka bayyana masa. Tsohon nan y ace, “Na san maganin
da zai warkar da shi, da za a sami Ruwan Bagaja ya sha kaɗan, da ya warke. Sai
dai samun rowan ne ke da wahala”(Grimms, 1906:306). In aka dubi wannan a iya
cewa, Imam ya sauya suna ne kawai domin babu wani bambanci a tsakani.
A littafin Ruwan Bagaja, an nuna
Imam ya fita neman Ruwan Bagaja. “Ya isa wani dutse mai kogo, inda ya sami wani
tsoho a ciki yana ibada, wato wan Liman da aka muzanta. Tsohon ne ya buga ƙasa ya bayyana masa
inda Ruwan Bagaja yake, wato hannun aljannu (Imam, 1994:4). Yayin da aka
nuna ɗan autan sarki ne ya haɗu da wadan tsoho a
cikin dokar daji, wanda ya bayyana masa inda zai samo ‘The Water of Life’
da yadda zai same su. An nuna lamarin kamar haka “Ɗan autan sarki ya
fita nema Ruwan Bagaja. Ya haɗu da wada a kwaren tsauni da cikin daji. Ya bayyana masa
cewa, mahaifina bay a da lafiya, sai a kwanta, sai a tayar. Ina neman inda zan
sami Ruwan Rayuwa. Dan Allah ka taimake ni , ka faɗa mini, idan ka san
inda suke” (Grimms, 1906:309).
Haka kuma, kamar yadda Imam ya gamu
da abubuwa masu ban al’ajabi wajen shiga rijiyar Sinaini. Ya ga saniya tana
tatsar Bafillatana, da doki bisa mutum, da kare na zagi, da sauran su. Haka aka
zayyana ɗan autan sarki ya haɗu da zakuna baki buɗe. Ba su iya yi masa
komi. Da wasu masu sarauta da ba sa iya cewa ƙala, da wani takobin
tsafi da sauran su. Ga abin da ka bayyana, “Zan bayyana maka inda za ka samo
ruwan. Rowan da kake nema suna cikin wata sammatatciyar rijiya ce. In Allah Ya
so za ka isa wajenta salum alum. Zan ba ka sihirtatcen ƙarfe da yankan burodi
biyu. In ka isa ka daki ƙyauren ƙofar da wannan ƙarfen sau uku, zai buɗe. Za ka tarar da
miyagun zakoka buɗe da baki. Ka jefa
musu burodin za su bari ka wuce” (Gramm, 1906:309). Duk waɗannan abubuwa ne da
ake zaton Abubakar Imam ya tarkato, ya haɗa, ya tayar da labaransa bayan ya sauya musu
kama.
6. 5 Alfun Laila Wa Laili
Duk wanda ya taɓa karanta Dare Dubu
Da Ɗaya
zai haƙiƙance an yi amfani da salon tsarinsa wajen gina labarin
littafin Ruwan Bgaja. Misali, Imam ya soma gini littafinsa ta hanyar bayar da
labarin wani mutun wai shi “Koje Sarkin Labari”. A ɗaya littafin ma da
irin wannan salo aka soma. Inda Shaharuzadi ta yi ta ba sarki Sharuzaman
labarai iri-iri. Aikin sarkin shi ne, kashe budurwa a daren da ya kawar da
budurcinta. Duk da haka saboda hikimarta. Bayan ya sadu da ita. Ta ce za ta gaya
wa ‘yar uwarta labarai wanda shi ma sarkin ya kwaɗaita da ya ji labaran (Edgar,
1970:1-11).
A Ruwan Bagaja, Imam ya nuna cewa,
cikin tafiye-tafiyen Alhaji, ya isa wani gari da ake kira Tambutu. Da ya shiga
garin, ya wuce fadar sarki, inda sarki
ya saukar da shi. Daga baya ya shaƙu da wani tajiri,
wanda ya yi wa ƙaryar cewa, shi falke ne, shanunsa na baya, alhali shanun
wasu ne. Wannan ƙaryar ta sa tajirin ya amince da Imam har ya rinƙa ba shi bashi, a kan
waɗancan shanun da ya yi
ƙaryar
mallaka (Imam, 1994:7). Wannan ya yi daidai da yadda Ma’aruf Baduku ya shirya
wa sarki a cikin “Hikayar Ma’aruf Baduku da Matarsa Fatima” da ke cikin Alfu
Laila (Mac, 1893:329) Malumfashi (2009) ya nuna. Shi Ma’aruf da ya sauka a
garin, sai ya yi wa sarkin ƙaryar baro dukiya a baya. Har ya kai
ga cin bashi wurin sarki a kan alƙawalin in dukiyarsa
ta iso, sarki ya ɗebi duk abin da yake
buƙata.
Har Ma’aruf ya kai ga auren Gimbiya, ‘yar sarki a kan sadakin da ke ciki waccan
dukiyar da ya yi ƙaryar mallaka.
Kamar yadda aka zayyana cewa, Alhaji
Imam ya je Ruwan Bagaja a rijiyar Sinaini. Yayin da aka nuna Jaudaru ya je ɗauko kayan tsafi a
cikin taskar tsafi. Haka ma, tamkar yadda aka nuna Imam ya ɓata wajen ƙirga ɗaki na biyar daga
dama, ya shiga na shida. Sai ya ruɗe ya ƙirga na huɗu daga hagu, ya shiga
na biyar. A Ruwan Bagaja Imam ya ce: “Da kutsa kai sai ya ji an ce, “ya yi
kuskure ku buge shi! Aka same ni tatas aka jeho ni wajen gari duk da takobin
nawa har na karye a ƙafa….(Imam, 1994:39)”. Wannan ya yi kama da yadda aka
nuna Jaudaru ya yi kuskuren shiga ƙofofin taskar. Shi ma
Jaudaru da ya isa ɗakin da mahaifiyarsa
take. Ya kasa yi wa mata zindir tamkar yadda aka shata. Har ya haddasa ma kansa
matsala. Nan take matar nan, ta fasa kururuwa da ƙarfin gaske, ta ce:
“A aaah. Ooooh!! Ya yi kuskure ku buge shi! Haba ai sai aka rufe shi da bugu da
mari da mangari kamar ruwan sama. Aka yi masa ligi-ligi, ba ya ko motsi, sannan
aka jeho shi waje…..(Mac,1839:110) da Malumfashi (2009).
6. 6 Muƙamat al- Hariri
Idan aka yi wa littafin nazari na
basira za a tarar cewa, marubucin ya yi amfani da salon da ke cikin littafin.
Shi ma marubucin ya tabbatar da haka, a wata hira da aka yi da shi, a inda yake
cewa: “Littafin Ruwan Bagaja wata dabara ce na samo daga wani littafi na Larabci
mai suna Muƙamat al – Hariri. A labarin ya nuna
mutum biyu ne, ɗaya yana ƙoƙarin ya wayance ɗaya a irin hanyar
wayo da dabara na Larabawa. To ni kuma sai na ɗauki mutum biyu ta irin wannan salon,
amma kuma na yi amfani da irin hanyar wayancewa ta Hausawa da dabarunsu a
rayuwar Hausa (Kano, 1995:88)”.
Malam Zurƙe da ya yi amfani da
shi a cikin labarin , ba shi ya ƙago sunan ba. Domin
akwai shi a wani lokaci da ya shuɗe a Katsina. Dokta Abubakar Imam ma ya
tabbatar da wanzuwarsa a inda yake cewa: “ Amma shi Malam Zurƙe wani mutum ne mai
ban dariya a kasuwar Katsina. Tun muna yara mukan so mu je kallon sa. Abin da
yake yi shi ne, sai ya saka tsummoki yana bin kasuwa yana kiɗa yana rawa. Tun
asali ba a san shi da Malam ba, ni ne na sa mishi Malam Zurƙe don labarin ya yi
armashi (Kano, 1995:90).
7. 0 Kammalawa
A iya namu bincike
mun fahimci cewa, littafin yana ƙunshe da wasu abubuwa
da aka fassara daga littattafan Larabci da na Turanci. Haka kuma, an yi amfani
salon juyar ayyukan wasu. Shi ma
Abubakar ya tabbatar da haka a inda ya ce: “Abin da kawai ya dame ni shi ne, in
karanta wata dabara ta wasu marbuta in fahimci inda suka dosa, sai in ajiye in
ci gaba da ƙirƙiro tawa dabarar ta hanyar hasken da na samu daga nasu
dabarun” (Kano, 1995:88). Haka ya fito fili yana bayyana cewa: “… na kwaikwayi
salon wasu labarai wani littafi na Larabci mai suna Maƙamat al –Hariri. A
cikin labaran akwai sunayen wasu mutane su biyu, Abu Zaidi da Harisu, Su ne na
mayar Alhaji Imam da Malam Zurƙe (Kano,1995:90).
Wannan maƙala ta bayar da haske
game da kafuwar makarantun boko a ƙasar Hausa. Da
hanyoyin da aka bi wajen shimfiɗa harsashen ginin ƙagaggun Labaran
Hausa. Ta kuma yi tsokaci a kan hukumomin inganta adabi, da tarihin samuwar
gasar ƙagaggun labaran Hausa. An kuma bayyana jerin littattafan
farko da aka fara bugawa. An yi haka ne, domin a ɗora tarihi a kan nagartatcen ma’auni.
Musamman ganin cewa, wasu masana, Allah bai nufe su da samun damar aza hannayensu a kan wasu rahotanni da Turawa
suka taskace ba, da suka danganci rubutattun ƙagaggun Labaran
Hausa.
Kamar yadda ya gabata
ne, an fahimci cewa, an gina littafin Ruwan Bagaja, a kan abubuwa da dama. Daga
cikin su akwai adabin baka na Hausa. Musamman tatsuniyar Ruwan Bagaja, da
tatsuniyar Gizo da Hankaki, da tatsuniyar Gizo da Fatalwa, ko Mutuwa. Ma
rubucin ya yi amfani da wasu littattafan
Larabci. Misali Littafin Ma’ul Haya, da
Alfun Laila Wa Laili, da Muƙamatul al-Hariri. An kuma yi amfani
da barkwanci da waɗanda hankali bay a ɗauka. Bai tsaya kawai
nan ba, har ya haɗa da wasu abubuwa day
a gain a rayuwa ta zahiri, kamar Zurƙi.
Wannan wata manuniya
ce, a kan yadda ilimin addinin musulunci ya yi tasiri ga rayuwar marubucin.
Fatata ita ce, maƙalar ta zama sharer fage game da wasu sassan da ban taɓo ba, domin zurfafa
bincike.
MANAZARTA
Tuntuɓi mai takarda
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.