Ticker

6/recent/ticker-posts

Rubutaccen Wasan Kwaikwayon Hausa a Ƙarni Na Ashirin Da Ɗaya: Tsokaci Kan Ma’aunin Nakasa A Littafin Daƙiƙa Talatin Na Ado Ahmad Gidan Dabino

Tsakure: Kimanin kashi goma sha biyar cikin ɗari na al’ummar duniya suna rayuwa da wani nau’i na nakasa. A Nijeriya kaɗai, sama da mutane miliyan goma sha tara (19) suke ɗauke da nau’o’in nakasa mabambanta, (Amamgbo, 2009). An lura cewa a wasu lokutan, ana ware nakasassu daga samun hakkokinsu da damammakinsu. Wannan wariya da ake nuna wa nakasassu ta samu ne ta hanyoyi da dama waɗanda suka haɗa da rashin ba su wani muhimmanci; rashin fifita al’amuran da suka shafi nakasassu daga fannin gwamnati a dukkan matakai da kuma rashin samar da wadatattun tsare-tsare da dokokin da za su bunƙasa tare da kare haƙƙoƙin nakasassun. Yawanci nakasa takan haɗu da wani nau’i na gazawa amma ba kowane nakasasshe ne yake zama kasasshe ba. Wannan tunani shi ne ya fito ƙarara a cikin littafin Daƙika Talatin, ɗaya daga cikin rubutattun wasannin kwaikwayon Hausa da aka samu a ƙarni na 21. Wannan maƙala ta ta’allaƙa ne kan fito da yadda marubucin littafin Daƙika Talatin wato Ado Ahmad Gidan Dabino ya kalli batun nan da ke nuni da babu nakasasshe sai kasasshe. An yi tsokaci kan rayuwar Ado Ahmad Gidan Dabino da kuma ɗaurayar littafin nasa na Daƙiƙa Talatin. Daga bisani an daddale bayanin yadda ake kallon nakasa ta fuskoki mabambanta, sai aka fayyace ma’aunin marubucin kan nakasa cikin waɗannan fuskoki huɗu da aka zayyano kamar yadda suka fito a littafin Daƙiƙa Talatin.



Rubutaccen Wasan Kwaikwayon Hausa a Ƙarni Na Ashirin Da Ɗaya: Tsokaci Kan Ma’aunin Nakasa A Littafin Daƙiƙa Talatin Na Ado Ahmad Gidan Dabino

Na

Abdullahi Mujaheed

Sashen Harsunan Nijeriya Da Kimiyar Harshe, Jami’ar Jihar Kaduna

 I-mel: mujaheedabdullahi@gmail.com

    Waya: +2348069299109, +2348156747550

Da

Abubakar Hayatuddeen

Ɗalibi a Sashen Harsunan Nijeriya Da Kimiyar Harshe, Jami’ar Jihar Kaduna

    Waya: +2348038220526

 

1.0    Gabatarwa

Rubutaccen wasan kwaikwayo na Hausa in an kwatanta shi da aiwataccen wasannin kwaikwayo (irin su fina-finai da wasannin kwaikwayo na talabijin da na rediyo), za a tarar cewa rubutaccen wasan kwaikwayon bai sami wani isasshen tagomashi ba kamar sauran nau’o’in wasannin kwaikwayo a ƙasar Hausa, ta fuskar samuwa da yawaita. Wannan ba ya rasa nasaba da yadda samuwar rubutaccen adabi ya ginu cikin tarihin al’ummar Hausawa, daidai da al’ummomin da Bahaushe ya koyi karatu da rubutu daga gare su (Larabawa da Turawa). Har ila yau, ko da aka sami zaunuwar tadar rubuta wasan kwaikwayo cikin littafi bayan zuwan Turawa, marubutan Hausa ba su mayar da hankali ga rubutaccen wasan kwaikwayo ba kamar ƙagaggun labarai da rubutattun waƙoƙi. Shi ya sa batutuwan da suka fito cikin jigogin rubutattun wasannin kwaikwayon ba su taka kara sun karya ba; galibi sun fi karkata ga batun rayuwar aure da barkawanci da nishaɗantarwa da ɗan abin da ba a rasa ba na zamantakewa.

Har ila yau, daga lokacin da aka fara samun rubutaccen wasan kwaikwayo, wato 1902, har zuwa 1988, an sami wasanni 27 ne kawai. Daga bisani kuma, sai akan sami wasu marubuta suna fitowa da wasu jifa-jifa. Misali Barau Bambale ya rubuta wasan Kukan Kurciya. Sai kuma wannan marubuci Ado Ahmad Gidan Dabino, wanda ya rubuta wasannin Malam Zalimu  da Ina Mafita? da kuma wannan da aka nazarta, Daƙiƙa Talatin, (Hassan, 2017). Sai kuma aka yi nasara wannan wasan ya zo da wani hoto (nakasa ba kasawa ba) wajen isar da saƙonsa, wanda ba a saba da ganin irin sa ba cikin rubutattun wasannin kwaikwayon Hausa. Kwanan nan kuma an sami ɓullar wani sabon littafin wasan kwaikwayo mai suna Tarkon Mut’a na Bashir Yahuza Malumfashi.

Da yake akwai hujjar da ta nuna cewa bambancin da ake nuna wa nakasassu ba shi ne haƙiƙanin sakamakon da ya janyo gazawarsu ba, illa ɗabi’ar nuna bambanci da wariya da mutane suka ƙirƙiro kuma suka tasirantu da ita. Shi ya sa a wannan maƙala aka bi diddigin wasan Daƙiƙa Talatin na Ado Ahmad Gidan Dabino, aka fayyace cewa su ma nakasassu a matsayinsu na ‘yan Adam suna da haƙƙin su bayar da gudummawarsu tare da amfanuwa da ayyukan cigaban al’umma.

2.0     Ado Gidan Dabino Cikin Tarihi

An haifi Ado Ahmad Gidan Dabino, MON, a shekarar 1964 a garin Ɗanbagina da ke Ƙaramar Hukumar Dawakin Kudu.[1] Ya girma a Unguwar Zangon Barebari a cikin birnin Kano. Bai sami yin karatun boko da ƙuruciya ba, sai dai ya yi karatun allo da na Islamiyya daga shekarar 1968 zuwa 1974.  Daga bisani ya yi karatun yaƙi da jahilci a shekarar 1984 zuwa 1986, sannan ya shiga sakandare ta dare a makarantar G.S.S Wurare Kano a shekarar 1987 zuwa 1990. Ya sami shaidar diflomar ƙwarewa kan yaɗa labarai a Jami’ar Bayero daga shekarar 2004 zuwa 2005, (Gidan Dabino, 2015: 112).

Shahararren marubucin littattafan Hausa ne, sannan mai shiryawa da bayar da umarni a shirin fina-finan Hausa, kuma ɗan jarida. Ya rubuta littattafai na ƙagaggun labarai da dama waɗanda suka haɗa da In Da So Da Ƙauna1-2  da Masoyan Zamani 1-2  da Hattara Dai Masoya 1-2  da Wani Hani Ga Allah 1-2  da Duniya Sai Sannu da Kaico!. A ɓangaren wasan kwaikwayo kuma ya rubuta Malam Zalimu da Daƙiƙa Talatin da Ina Mafita? Haka kuma ya yi wasu rubuce-rubucen a fannonin tarihi da zamantakewa waɗanda suka haɗa da Mata Da Shaye-Shayen Kayan Maye: Ina Mafita? da Sarkin Ban Kano, Alhaji Dr. Mukhtar Adnan. Wasu daga cikin littattafan nasa an fassara su zuwa harshen Ingilishi, (Gidan Dabino, 2015:112-113).

Bugu da ƙari, tare da shi aka kafa wasu ƙungiyoyi kamar Ƙungiyar Marubuta ta Nijeriya Reshen Jihar Kano, (ANA) da Ƙungiyar Masu Shirya Fina-finai ta Jihar Kano da kuma Ƙungiyar Marubuta ta Raina Kama. A taƙaice, idan aka ce Ado Ahmad Gidan Dabino komai da ruwanka ne cikin harkar rubuce-rubucen ƙagaggun labarai da wasan kwaikwayo da fina-finan Hausa, to, ba a sharara ta ba. Wannan ya sa a ranar 29 ga watan Satumba na shekarar 2014 Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta karrama shi da lambar yabo ta ƙasa mai taken, Member of the Order of the Niger (MON) bisa hidimta wa jama’a da yake yi cikin ayyukansa, (Gidan Dabino, 2015: 114).

3.0    Ɗaurayar Littafin Daƙiƙa Talatin

Daƙiƙa Talatin  ɗaya ne daga cikin littattafan wasan kwaikwayo da Ado Ahmad Gidan Dabino ya rubuta a shekarar 2015. Littafin mai shafi 111 ya fito a daidai lokacin da ya dace, domin ko ba komai, ya kashe wa ɗalibai da manazarta ƙishin da suke fama da shi na rashin isassun littattafai kan wasan kwaikwayo na Hausa.  

Wasan Daƙiƙa Talatin ya ginu ne a kan babban jigon da ya mamaye jigogin adabin zamani na wannan ƙarni, wato soyayya da kuma tsarin zamantakewa ta sha’anin zaman iyali. Soyayya ce ta ginu tsakanin wani saurayi, Yassar, da kuma wata budurwa, gurguwa, mai suna Zannira. Daga ƙarshe dai an yi aure, amma ango ya mutu kafin amarya ta tare, balle ma a mori zaman auren, (Hassan, 2017).

A ranar biki, bayan an ɗaura aure, amarya ta ziyarci ango, yana tare da abokansa, suka ɗan keɓe a ɗaki da amarya na wasu mintuna, amarya da ƙawarta suka koma gida. Daga nan ango ya fita zuwa shago domin ya yi wasu ‘yan saye-saye, bayan ya sallami baƙonsa da ya zo daga Legas. A nan ya gamu da ajalinsa, inda mota ta buge shi, ya mutu.

Ashe a wannan ganawar da suka yi da amarya ta ‘yan mintuna, alaƙa irin ta miji da mata ta shiga a tsakaninsu. Daga bisani Zannira ta je asibiti tare da Aminu, abokin marigayi Yassar, mijinta, likita ya tabbatar tana da juna biyu. Abin ya zama abin mamaki matuƙa har ya haifar da zargi da cece-kuce tsakanin iyayen Zannira da iyayen Yassar da kuma sauran jama’ar gari a kan ko dai Aminu (abokin Yassar ɗin) ne ya yi mata cikin? Da yake suna aiki tare kuma kusan kodayaushe suna tare. Wannan muhallin shi ne ƙololuwar rikicin da wasan yake ɗauke da shi:

 

Inna Mai Koko:  Ba zai yiwu ba, ina! Ta yaya za a ce daga ɗaura aure ko awa biyu ba a yi ba

 yaro ya mutu amma a ce wai yarinya ta samu ciki da shi? A ina ta samu, a                    maganar da suka yi da shi ko a numfashi ko yana lahirar ya yi mata cikin? Ina! Haram giya a gidan liman! Kuma ba da mu ba gaɗa a maƙabarta (shafi na 71).

 

Wannan badaƙala ta sa har sai da aka tafi kotu domin a yi shari’ar shin wa ke da wannan juna biyu na Zannira? Iyayenta sun ce na Yassar ne domin ta shaida musu haka. Iyayen Yassar kuma suka ce ba su yarda ba domin a iya saninsu babu wata haɗuwa ta aure da aka yi tsakanin Yassar da Zannira har ya mutu.

A ƙarshen shari’ar, sai da alƙali ya buƙaci likita ya zo ya yi wa jama’a bayanin sakamakon gwajinsa, da kuma abin da ya gano cewa Zannira tana da ciki. Ya kuma yi dogon bayani a kan yadda ciki yake shiga, har zuwa haihuwa, duk jama’a suna sauraronsa. Bayan ya gama bayani kowa ya gamsu, kuma har iyayen Yassar, bisa jagorancin Inna Mai Koko, suka gamsu cewa lallai ciki na Yassar ne:

Inna Mai Koko:  (Idanunta suna ƙwalla) Ranka ya daɗe, na gamsu da bayanan da wannan        

yaro likta ya yi. Ashe Yassar bai rasu ba tun da ga shi ya bar wani abu a        cikin matarsa. Allah ya ji ƙan Yassar ya gafarta masa, ya sa ya huta, ya albarkaci cikin da ya bari (shafi na 103).

 

Fitattun taurarin wannan wasa na Daƙiƙa Talatin su ne Yassar da Zannira da Aminu da Amina da Samira da Inna Mai Koko da Dr. Amir (likita) da Alƙali da Ka-Fi-Rediyo (maroƙi). Sauran taurarin sun haɗa da Habu da Iro da Alhaji Abdullahi da Alawiyya da Mairo da Malam Isa da Sadiya da Ladi da Alhaji Bashar da Tashare da sauransu.

Dangane da jigo, idan aka yi la’akari da yadda likita ya warware abin da ya kusa ya gagari alƙali warwarewa, za a iya ɗaukar amfanin ilimin kimiyya a matsayin wani jigo na wannan wasa.  Domin kuwa wannan wasa ya yi ƙoƙarin nuna wa Hausawa cewa ilimin zamani, musamman wanda ya shafi likitanci, zai iya warware wasu matsaloli masu sarƙaƙiya na rayuwa, baya ga kula da lafiya da bayar da magani, (Hassan, 2017).

Wani jigon da za a iya gani cikin wannan wasa shi ne soyayya, musamman idan aka yi la’akari da karin maganar Hausawa da suke cewa ‘shan koko, ɗaukar rai’. Wasu samari suna neman mata kyawawa masu kyan diri da sauran wasu siffofi na mata da suke jan hankalin namiji, sai ga shi Yassar duk waɗancan abubuwa ba su  rufe masa ido ba. Gurguwa ya ji yake so, yake kuma ƙauna (Hassan, 2017).

Amma a wannan maƙala, batun nan da Hausawa kan ce ‘babu nakasasshe sai kasasshe’, shi ne aka ɗauka a matsayin jigon da ya ratsa wasan na Daƙiƙa Talatin. An yi la’akari da rayuwar Zannira a matsayin gurguwa amma duk da haka ba ta kasa ba wajen ba da gudummawarta ga rayuwar al’umma, ta hanyar kafa da jogarantar ƙungiya don taimaka wa mata da koya masu sana’o’in dogaro da kai. Haka kuma nakasarta ba ta zamo mata ƙalubale ba wajen jajircewa ta ƙwato ‘yancinta a kotu game da zargin da ake mata na cikin Yassar da take ɗauke da shi. A haka ta yi rayuwarta har ta sami ɗaukaka da karramawar da wasu lafiyayyun ma ba su samu ba. Saboda ba ta kasance kasasshiya ba, duk da tana da nakasa.

4.0      Yadda Ake Kallon Nakasa

Nazarin nakasa fage ne da ke ƙoƙarin bayyana batutuwan da suke ɗamfare da zamantakewa da al’adu da siyasa waɗanda suka jiɓanci yadda ake kallon nakasa da nakasassu. A bisa yadda mutane suka fahimci nakasa, akwai hanyoyi guda huɗu da aka gano kuma ake amfani da su don fuskantar al’amarin nakasa:

4.1 Hanyar Neman Magani

An ɗauki mutumin da yake da nakasa a matsayin mai wata cuta wanda ke buƙatar ya warke domin samun dacewa da sauran jama’a cikin al’umma. Wannan nakasasshe ana ganin sa a matsayin mara lafiyar da yake buƙatar magani, kuma ana ware shi a matsayin wanda yake buƙatar taimakon magani. A wannan tsari, duk da ana neman magance ko haɓaka lafiyar al’umma, ana ware nakasassu daga cikin al’umma, ana ɗaukar su a matsayin marasa lafiyar da suke buƙatar magani. Sa’annan ƙwararru za su shawarta irin kulawar da nakasassu ke buƙata, su nakasassun ba su da ta cewa(IDDC, 2002).

 

4.2 Hanyar Ba Da Sadaka/Taimako

An ɗauki mutumin da yake da nakasa a matsayin mara galihu, cima-zaune wanda ya cancanci a ji tausayinsa, kuma yake buƙatar a ba shi sadaka. A wannan tsari, ana ɗaukar nakasassu a matsayin marasa daraja, masu dogaro da wasu, waɗanda suke buƙatar a tausaya masu ko a taimake su. Hakan ya sa ba a samar wa da nakasassu ayyukan yi, ana ɗaukar su a matsayin waɗanda ba za su iya ba da wata gudummawa ga al’umma ba ko su taimaki kawunansu(IDDC, 2002).

4.3 Hanyar Zamantakewa

An mayar da hankali ne kan al’umma, ba a ɗauki nakasasshe a matsayin matsala ba. Sai dai an fi mayar da hankali ne kan kawar da bambance-bambance da haɗin kai. A wannan tsari, an fi mayar da hankali ne a kan ganowa tare da kawar da ɗabi’u munana da matsalolin muhalli da hukumomi waɗanda suke zama tarnaƙi ga haɗuwar kai, don a samar da dama ga nakasassu da ma waɗanda ba nakasassu ba, wajen samun muhimman abubuwan more rayuwa kamar ilimi da aikin yi da sauransu. Haka kuma a shigar da nakasassu cikin al’umma ba tare da wariya ba (IDDC, 2002).

4.4 Hanyar ‘Yanci

An ɗauki cewa nakasasshe cikakken ɗan ƙasa ne wanda yake da ‘yanci. Masu wannan ra’ayi suna ƙarfafa nakasassu ne su shiga a fafata da su wajen samar da cigaba, sannan su riƙe wasu muƙamai a wasu ma’aikatu, tare da samar da tafarkin da za a bi a sami cim ma nasarar samun waɗannan haƙƙoƙi. A wannan tsarin, ana bin dabarun samar da dokokin da suka dace don kawar da shamakin da al’umma suka samar a tsakanin nakasassu da sauran al’umma. Sa’annan a ƙarfafi nakasassu su sami damar bayar da gudummawa wajen cigaban al’umma, gwamnati ta ɗauki alhakin samar da haƙƙoƙin nakasassun (IDDC, 2002)..

Abin lura a nan shi ne, hanyoyi guda biyu na bayar da sadaka da hanyar tallafin magani sun mayar da hankali ne ga nakasasshe a matsayin wata matsala da ake buƙatar a ga wasu ƙwararru sun shawo kanta. A ɗaya ɓangaren kuma, hanyar zamantakewa da hanyar ‘yanci sun mayar da hankali ne ga al’umma da hukumominta da tsare-tsarenta a matsayin ɓangarorin da suka gaza waɗanda suke buƙatar gyara don samar da daidaito ga nakasassu a wurin cigaban al’umma.

5.0    Ma’aunin Ado Gidan Dabino Kan Nakasa Cikin Littafin Daƙiƙa Talatin[2]

Kamar yadda aka bayyana a baya, cikin hanyoyi ko fuskokin da al’umma ke kallon nakasa, hanyar zamantakewa da hanyar ‘yanci sun fi dacewa da batun da Bahaushe kan ce ‘babu nakasasshe sai kasasshe’. Domin kuwa hanyoyin sun mayar da hankali ne ga ƙarfafa nakasassu su shiga a fafata da su wajen samar da cigaba, sannan su riƙe wasu muƙamai a wasu ma’aikatu, tare da samar da tafarkin da za a bi domin su mori haƙƙoƙinsu na rayuwar yau da kullum kamar kowane ɗan’Adam, ba tare da nuna wani bambanci ba.  Wannan ita ce fuskar da Ado Ahmad Gidan Dabino ya fayyace nakasa a littafin Daƙiƙa Talatin. Zannira ita ce fitacciyar tauraruwar da aka gina wasan a kan ta. Kuma marubucin ya nuna ta a matsayin ‘nakasasshiya’, wato gurguwa mai tafiya a kan keken guragu, amma duk da haka ba ta ɗauki wannan ƙalubale na gurgunta ta ƙwallafa wa ranta ba, ballantana ya dame ta har nakasar ta zame mata kasawa. Maimakon haka, ta shiga an dama da ita a fannonin rayuwa na zamantakewa da soyayya da neman ilimi da sana’a da sauransu.

5.1 Soyayya

A yawancin lokuta nakasassu na fuskantar wariya a mu’amala ta soyayya, inda sai sun yi da gaske wajen kawar da kai ga irin ƙalubalen da suke fuskanta.  Amma ita Zannira ƙarfin zuciyarta ya lulluɓe nakasar da take da shi a idon Yassar, ya ji duk duniya ba wadda yake so sai ita. Shi ya sa ko da abokinsa Habu ya ƙalubalance shi a kan me ya gani ga gurguwa (nakasasshiya) ya maƙale mata duk da akwai masu ƙaunarsa da yawa? Ce masa ya yi:

Yassar:  Duk na san da su, amma babu wadda ta kwanta min a rai   kamarta, kuma ita nake            

              so ba gudu babu ja da baya. Kuma ka san masu iya magana suna cewa, ‘abin son rai

 ne ƙawa da makauniya.’ Idan har mai ƙafa zai tsani gurguwa, mene ne laifinta? Ai ba                 ita ta ɗora wa kanta ba, haka Allah ya so ya gan ta, kai ma ba ka wuce haka ta same ka ba, don haka in wasu suka ƙi ka za ka ji daɗi? Duk mutum mutum ne, yana da darajarsa wadda Allah ya ajiye a tare da shi. (Shafi na 2)

 

A nan, marubucin ta bakin Yassar ya nuna cewa nakasasshiya kamar kowace mace tana da ‘yancin a yi kowace irin mu’amala da ita har da soyayya, ba tare da la’akari da nakasar ba, domin haka Allah ya so ya gan ta, ba kuma don ba ya son ta ba. Sa’annan Allah zai iya jarabtar kowa da nakasar idan ya ga dama. Har ila yau, wannan tunani na marubucin ya sake fitowa ƙarara inda Alawiyya ƙawar Samira budurwar Yassar ta biyu ta yi furucin izgilanci ga Zannira lokacin da suke hira a ofis ɗin Yassar tare da Aminu abokinsa, Yassar ɗin ya yi caraf ya taka mata birki:

Yassar: (A fusace ya nuna ta da yatsa).  Ke Alawiyya, ba na son cin mutunci da wulaƙanci,

kin ji ko? Ku masu ƙafafun da me kuka fi gurguwar? Kuma kada ku manta abin son rai ne mai mata uku ya auri jaka. (Shafi na 21)

 

5.2 Sana’a

Saɓanin yadda galibi ake kallon nakasassu a matsayin waɗanda ba su da wata sana’a da za su iya yi da ta wuce bara, Ado Gidan Dabino ya nuna cikin wasan Daƙiƙa Talatin cewa nakasassu za su iya sana’o’i da dama domin samun abin masarufi da dogaro da kawunansu. Abin da kawai suke buƙata shi ne a ƙarfafa masu gwiwa cikin al’amuransu, shi ya sa Yassar ya kasance mai ƙarfafa gwiwa ga Zannira wajen neman ilimi musamman abin da ya shafi koyon sana’a kamar yadda ya shaida wa Samira a tattaunawarsu kan Zannira:

Yassar: Sunanta Zannira; Makarantar Koyon Sana’a ta gama bana, kuma bayan aurenmu za

            ta cigaba da karatu, da yardar Allah. (Shafi na 5)

 

Marubucin ya nuna ƙarara cewa ko da nakasa mutum ba zai kasa koyon sana’a ba, musamman idan an ƙarfafa masa gwiwa. Shi ya sa Zannira ta yi makarantar koyon sana’a kuma ta rayu a matsayin mai ƙarfafa gwiwa ga mata domin su nemi hanyoyin sana’o’in dogaro da kawunansu. Ta cim ma gagarumar nasara sakamakon ƙwarin gwiwa da goyon bayan da Yassar da Aminu da Amina suka riƙa ba ta.

5.3 Daraja ta Musamman

A wasan Daƙiƙa Talatin, Ado Ahmad Gidan Dabino ya tabbatar da cewa nakasassu suna da wata daraja ta musamman, domin haka bai dace a wulaƙanta su ba. Wannan ya fito ta bakin Sadiya lokacin da suke tattaunawa da Yassar a kan buge Zannira da ƙawarta Samira ta yi da motarta da gangan saboda tsabar kishi:

Sadiya: (Cikin nuna damuwa) Kash! Ban ji daɗi ba da ba ka san inda take ba da har gida ma

sai in je in duba ta, ai mutum daraja gare shi, musamman ma wanda yake da wata lalura a tare da shi. Ba komai ni zan yi wa Samira magana kan wannan rashin kirkin da ta yi, kuma zan nuna mata ba ta yi daidai ba. (Shafi na 16)

 

A nan Samira cikin tausayawa ta nuna cewa ɗan’Adam daraja gare shi, ko da kuwa yana ɗauke da wani nau’i na nakasa a jikinsa. Domin haka, ya fi dacewa a kowace mu’amala a ba nakasasshe darajarsa kamar kowane ɗan’Adam.

5.4 Gudummawa ga Al’umma

Wani abin burgewa marubucin ya jaddada cewa nakasassu ma za su iya bayar da gudummawa ga rayuwar al’umma, ba tare da nakasar da suke ɗauke da ita ta zame masu cikas ko ƙalubale ba. Har ila yau, ƙarfafawa da goyon baya kawai suke buƙata, kamar yadda a wasan Daƙiƙa Talatin Zannira ta kafa kuma ta shugabanci ƙungiyar Babu Nakasasshe Sai Kasasshe domin yaƙar zaman banza da mutuwar zuciya da kuma wayar da kan mata da matasa domin samar da hanyoyin dogaro da kai. An ga haka ƙarara a lokacin da ƙungiyar Zannirar ta kira taro domin ƙaddamar da ƙungiyar da kuma gabatar da jawabai a kan ‘Muhimmancin Sana’o’i ga Mata Ma’aurata da Sababbin Hanyoyin Dogaro da Kai’:

Yassar: Ga waɗanda suka san Zannira, sun san gurguwa ce, amma wannan bai hana ta neman

ilimi da kuma dogaro da kanta ba, wanda wasu daga nan ne suke shiga bara da maula da sace-sace saboda mutuwar zuciya. Saboda haka ne ma ya sa ta kafa wannan ƙungiya ta yaƙi da zaman kashe wando ga maza da mata da kuma wayar da kan jama’a bisa dogaro da kai. Yanzu zan gabatar da Zannira don ta gabatar da takardarta mai taken Muhimmancin Sana’o’i ga Mata Ma’aurata da Sababbin Hanyoyin Dogaro da Kai. Bayan ta gama duk masu tambaya suna iya yi mata tambaya game da abin da ta gabatar. Malama Zannira Bissimilla. (Shafi na 32)

 

Wannan gabatarwa da Yassar ya yi wa Zannira ta dunƙule dukkan bayanan da suke jaddada fahimtar marubucin wasan Daƙiƙa Talatin cewa lallai nakasassu ma suna iya bayar da gudummawa ga rayuwar al’umma ta fuskoki mabambanta kamar yadda kowane mutum mara nakasa zai iya, musamman in an ƙarfafa masu gwiwa.

Har ila yau, a hirar Aminu da budurwarsa Amina sun sake jaddada irin gudummawar da Zannira ke ba al’umma:

Amina: Ni na rasa wane abu ne gurguwa take da shi da ya sa mu masu ƙafa kuke banzantar

da mu kuna liƙe wa gurguwa? Ko dai akwai wani sirrin ne da ba mu sani ba?

 

Aminu: Sirrin kawai na tsayawa tsayin daka wajen taimaka wa jama’a da gurguwa take yi,

            shi ya sa take da farin jini. (Shafi na 88)

 

Wannan ya nuna cewa irin gudummawar da Zannira take ba al’umma ya sa ta yi zarra cikin tsara, har ma wasu suke kishi da ita. Kenan, nakasarta ba ta zama tarnaƙi gare ta ba, wajen taimakon kanta har ma da taimakon al’umma.

5.5 Babu Nakasasshe Sai Kasasshe

 

Kamar yadda Bahaushe kan ce ‘nakasa ba kasawa ba ce’, Ado Ahmad Gidan Dabino ya nuna a wasan Daƙiƙa Talatin cewa nakasasshe zai iya soyuwa a zukatan jama’a fiye ma da wanda ba shi da nakasar, har ya tabbatar wa da duniya cewa babu nakasasshe sai kasasshe. Ga abin da Kwamishinar Mata ta ce cikin jawabinta wajen taron karrama Zannira kan ayyukan da ƙungiyarta ke yi:

Kwamishinar Mata: (Bayan ta gama yin gaishe-gaishen manyan baƙi sannan ta tsunduma

cikin jawabinta). Babban abin farinciki ne a ce yau a jiharmu an sami mace wadda take gurguwa amma tana koyar da mutane sana’o’i da kuma dogaro da kai. Wannan ya daɗa tabbatar mana da sunan ƙungiyar tasu Babu Nakasasshe Sai Kasasshe. Muna fata a sami irin Zannira da yawa a cikin jihar nan tamu, babu shakka za a ga abubuwan al’ajabi nan da ‘yan shekaru. (Shafi na 107)

 

Mahalarta Taro: (Suka kama tafi) Raf! Raf!! Raf!!!

 

Kwamishinar Mata: Ya kamata matasanmu maza da mata su yi koyi da wannan ‘yar talika

Zannira, wajen yin tsayiwar daka da jajircewa da sa kishin zuci a al’amuransu na rayuwa. Dukkanmu yanzu mun yarda cewa, Babu Nakasasshe Sai Kasasshe. Allah ya cire mana nakasar zuciya da kasawarta.(Shafi na 107)

                       

A nan, Ado Gidan Dabino ta bakin Kwamishinar Mata ta jaddada cewa nakasa a zuciya take, duk wata nakasa in ba a zuciya aka nakasa ba, to tabbas ba za ta zamo naƙasu ko cikas ga rayuwar mai ɗauke da nakasar ba, ba za ta hana a shiga a fafata a bayar da gudummawa a kowane ɓangare na zamantakewa ba. Domin kuwa, babu nakasasshe sai kasasshe kamar yadda taken ƙungiyar Zannira ya nuna.

6.0    Kammalawa

Ƙasar Nijeriya ta sa hannu a Taron Haɗa Kan Ƙasashen Duniya kan haƙƙoƙin nakasassu (CRRD). Wannan taro ya samar da tsarin da za a bi a haɓaka tare da samar da kariya ga haƙƙoƙin nakasassu tare da zayyano wajibcin da ke kan ƙasashe irin su Nijeriya wajen tabbatar da nakasassu suna da cikakkiyar dama wajen yanke shawara da bayar da gudummuwa a dukkanin ɓangarori na rayuwa, waɗanda suka haɗa da samar da dokoki da tsare-tsare. Amma duk da wannan sa hannu da Nijeriya ta yi, akwai babban giɓi a Nijeriya ta fuskar cigaban nakasassu da kare haƙƙoƙinsu. Shi ya sa har yanzu a Nijeriya, yawancin jama’a da ƙungiyoyi suna bayar da sadaka ko tallafin magani ne a matsayin aikin da suka sa gaba game da ‘inganta’ rayuwar nakasassu.

Ɓullar littafin Daƙiƙa Talatin a wannan ƙarni na 21, ya zama tamkar susa a gurbin ƙaiƙayi. Domin ko ba komai ya zo da wani saƙo da ba a saba da ganin irinsa a rubutattun wasannin kwaikwayo na Hausa ba, sa’annan ya share wani sabon fage na nazarin nakasa a adabin Hausa. Saboda haka wannan takarda ta nazarci ma’aunin nakasa a littafin Daƙiƙa Talatin; Bayan shimfiɗa game da rubutaccen wasan kwaikwayo, an kawo tarihin marubucin wasan wato Ado Ahmad Gidan Dabino, daga bisani aka rattabo hanyoyin da ake kallon nakasa a mu’amalance da kuma yadda marubucin ya sarrafa nakasa a cikin wasan, ta amfani da ma’aunin da ke fayyace cewa ‘babu nakasasshe sai kasasshe’.

 

 

7.0    Manazarta

Abubakar, Y.A (1972); The Political and Administratiɓe Implications of the Rehabilitation of

        Beggers. Ibadan: University, Press.

 

Amamgbo, O.C, (2009); Nigeria Planning for Golden Jubilee? Consider the Physically  Challenged, http://www.iddconsortium.com

 

Bunguɗu, H. U. (2015); “Nazarin Waƙoƙin Bara Na Ƙarni Na Ashirin Da Ɗaya A Zamfara.” Kundin Digiri Na Uku. Sakkwato: Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

 

Coleridge, P. (2001); Disability, Liberation and Deɓelopment. Chapter 1: Why This Book?. Oɗford: An Oɗfam Publication.

 

Gidan Dabino, A. A. (2015); Daƙiƙa Talatin. Kano: Gidan Dabino Publishers.

 

Hassan, S. (2007); “Sharhin Wasan Kwaikwayon Daƙiƙa Talatin Na Ado Ahmad Gidan     

       Dabino MON.” Cikin Jaridar Leadership Hausa ta ranar,  9/11/2107.

 

IDDC, (2002); “Making Inclusion a Reality in Deɓelopment Organisations”. International Disability and Deɓelopment Consortium.

 

Malumfashi, A. (2014); “Adabin Hausa Jiya Da Yau: Me Ke Faruwa Da Rubutun Waƙa Da Zube Da Kuma Wasan Kwaikwayo?” Jawabin Da Aka Gabatar A Bikin Makarantar Malam Bambadiya (Facebook Group) Ranar 06/09/2014. Kaduna: Jami’ar Jihar Kaduna.

 

Muhammad, Ɗ.(1983); “Ɓisual Imagery in Blind Poetry: Comments on Aliyu Namangi’s Imfiraji and Audu Makaho’s Tabuka.” African Language Seminar Paper presented in the Department of Nigerian and African Languages, Ahmadu Bello University, Zaria.

 

Mujaheed, A. (2017); “Adabin Bara: Nazarin Waƙoƙin Salisu Sa’in Makafin Zazzau.”Kundin Digiri Na Biyu. Zariya: Sashen Harsuna da Al’adun Afirka, Jami’ar Ahmadu Bello.

 

Sarkin Gulbi, A.(2007); “Nazari A Kan Al’adar Bara A Ƙasar Sakkwato.” Kundin Digiri na Biyu. Sakkwato: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

 

Shehu, B. (2016); “Sababbin Wasannin Kwaikwayon Hausa Nazari A Kan Littafin Malam Zalimu.” Kundin Digiri Na Ɗaya. Kaduna: Sashen Harsuna Da Kimiyar Harshe, Jami’ar Jihar Kaduna.

 

https://hausa.leadership.ng/2017/11/09/sharhi-sharhin-wasan-kwaikwayon-da%c6%99i%c6%99a-30-na-ado-ahmad-gidan-dabino-mon/

http://www.iddconsortium.com

https://www.disabled-world.com/definitions/disability-models.php

http://www.nigeriaɓillagesƙuare.com/indeɗ2.php?option=content&dopdf=1&id=11938, Saturday, 04 April 2018.

 



[1] Hira da Ado Ahmad Gidan Dabino MON, a Dandalin Taurari Cikin Shirin Gari Ya Waye na Gidan Talabijin na Arewa 24

 

[2] A hirar da na  yi da Gidan Dabino ranar 18/02/2019 ya bayyana min cewa labarin Daƙiƙa Talatin ba labari ne da ya taɓa faruwa ba, ya ƙirƙira ne don nusar da mutane cewa kowane mutum yana da tasa darajar a wajen al’umma. Burinsa shi ne mutane su ɗauka nakasa ba kasawa ba ce, ƙaddara ce daga Allah take samun mutum. Kuma wani nakasasshen ma ya fi wani mai lafiyar amfani a cikin al’umma.

Post a Comment

0 Comments