Wannan muƙala ta ƙunshi wani ɓangare daga cikin ɓangarorin adabi wato waƙa kuma rubutacciya. Ganin yadda waƙa take da matuƙar amfani ga jama’a kuma ta kasance wata hanya ta isar da saƙo a cikin sauƙi ga...
+2347031280554
1.0 TSAKURE
Wannan muƙala ta ƙunshi wani ɓangare daga cikin ɓangarorin adabi wato waƙa kuma rubutacciya. Ganin
yadda waƙa take
da matuƙar
amfani ga jama’a kuma ta kasance wata
hanya ta isar da saƙo a
cikin sauƙi ga al’umma.
Marubuta na wancan lokaci sun yi amfani da waƙa wajen isar da saƙwannin su ga jama’a. Bayan
wannan ma shahararrun malaman nan da suka jaddada addinin musulunci wato su
Mujaddadi Shehu Usmanu ɗanfodiyo da ƙanensa Abdullahin Gwandu da ɗansa Muhammadu Bello da ‘yarsa
Nana Asma’u da dai sauran almajiransa sun yi amfani da waƙa wajen isar da saƙonsu ga al’umma.
Wannan ya sa masana da manazarta suka yi aiki a kan wannan ɓangare. Don haka mu
ma zamu ɗan duba wani ɓangare da ya shafi nazarin waƙar don samun ƙarin haske ga wani abu da
ya shige wa jama’a duhu.
1.0.1 GABATARWA
Fagen adabi fage ne mai tarin yawa wanda masana da
manazarta da yawa suka gudanar da aiki a kansa, kuma har a yau suna a kai wajen
gudanar da bincike na duk wani abu da ya shafi adabi. Wannan muƙala ba wai ta
ƙunshi dukkan ɗaukacin adabi ba. Amma za ta bayar da ƙarfi a kan rubutacciyar
waƙa. Ba rubutacciyar waƙa za a nazarta gaba ɗayanta ba. Za a dai ɗan yi
tsokaci ne dangane da abin da ya shafi Jigo da Gajerce Jigo da Warwarar Jigo,
duk a cikin rubutacciyar waƙar nan ta Mu’azu Haɗejia ta Yabon Ubangiji.
2.0.2 Jigo
ɗangambo (2007:12) Abin da ake nufi da jigo shi ne saƙo,
manufa ko abin da waƙa ta ƙunsa, wato abin da take magana a kai.
Jigo a fagen adabi yana nufin manufar marubuci, wadda
dukkan bayanai suka dogara da ita. Saboda haka ana iya cewa Jigo shi ne irin
saƙon da marubuci ke son sadarwa ga jama’a kuma duk wani salo da tsari ko wata
dabara da marubuci zai yi amfani da su, zai yi hakan ne da nufin isar da
saƙonsa ga jama’a. Sarɓi, (2007:71).
Da wannan muke gani Jigo a matsayin igiya maɗaura kayan
kowane rubutu da aka yi a fagen adabi ta kowane ɓangare wato Zube da Waƙa da
Wasan Kwaikwayo in ba da shi ba to kayan za su kwance. A nan jigo na nufin
burin zuciyar mawaƙi ko marubuci wanda yake son jama’a su fahimta.
Kaftin Suru Ummaru ɗa, Allah ya jiƙansa da rahama yana faɗa
a waƙarsa mai suna Jigo. Ya ce:
Kay yi waƙa ba jigo,
Ya yi riga ba taggo,
Yai awaki ba faggo,
Ga amarya ba ango,
Ban ga amfani nai ba.
Wannan ya nuna ke nan in aka yi waƙa ba a san jigonta ba to
tana da rauni. To abin lura a nan shi ne, ba waƙa kaɗai ba koma wane irin
rubutu ne in dai babu jigon da ya sa aka yi shi to aikin banza ne bai da wani
amfani.
A waƙar Mu’azu Haɗeja ta Yabon Ubangiji, da muka nazarta
mun gano cewa Jigon wannan waƙar dai shi ne TAUHIDI.
Galibi idan mai rubutu bai fito a fili ya faɗi jigon
waƙarsa ba to mai nazari yakan yi la’akari da wasu muhimman kalmomin fannu da
waƙa ta ƙunsa don ya gane inda aka dosa. Wannan ya ba mu damar zaƙulo babban
jigon wannan waƙar ta amfani da wannan hanyar. Ga kuma hujjar daga waƙar:
Baiti na (2) “komi ka gan shi duniya farko gari,
Ko ka gaya mini Rabbu waf fare shi?”
Ko shakka babu idan mutum ya kalli baitocin waƙar zai ga cewa duk TAUHIDI take
magana a kai, kamar dai yadda za a gani a gaba cikin warwarar jigo da zai biyo
baya.
2.0.3 Gajerce Jigo.
ɗangambo
(2007:15) ya ce, “A nan wurin za a bi waƙa a taƙaice baiti bayan baiti ana
taƙaita abin da mawaƙi yake faɗa. Za a yi haka ba tare da yin sharhi, bayyana
ra’ayi ko wani dogon bayani ba. Misali ana iya cewa a baiti na 1-3 ya ƙunshi
yabon farawa, baiti na 4-7 ya ƙunshi gabatar da Jigo.
Idan aka yi la’akari da abin da magabata suka faɗa dangane
da Gajerce Jigo za a ga cewa, wannan wurin yana buƙatar a fito da hoton bayanin
waƙar a taƙaice ana iya ɗaukar ɗiya ko baitoci na waƙar rukuni-rukuni a fito da
muhimman abubuwan da take magana a kai.
Anan
wurin za a bi waƙa a taƙaice baiti bayan baiti ana taƙaita abin da marubucin
waƙar ya rubuta/faɗa. Za a yi haka ba tare da yin sharhi ko bayyana ra’ayi ko
wani dogon bayani ba. Ga dai yadda abin yake a wannan waƙar ta Yabon Ubangiji.
1. Mabuɗin waƙar:
Ya fara da ambaton sunan Allah Ubangiji a baiti na 1
2. daga baita na
3-7, 19-21, 61-65, da na 70 suna bayani ne a kan kaɗaitar Ubangiji.
3. Baiti na 18 da
68-69 suna nuna buwayar Ubangiji.
4. Baiti na 22-32,
54-60, da 71-73 suna bayanin ƙarfin ikon Allah Ubangiji.
5. baiti na 33-38
suna bayanin wadatuwar Ubangiji.
Yadda mawaƙin/marubucin waƙar yake nunawa cewa Allah Shi ne
da arziki kuma idan mutum yana alfahari ya ba ka arziki to sila ce Allah Ya ga
dama.
6. Baiti na 39- 40
suna bayanin siffofin Ubangiji, kamar yadda marubucin ya kawocewa Allah mai
haƙuri ne kuma mai ji ne Yana kuma gani.
7. Baiti na 41-45
suna bayani ne a kan Mala’ikkun Allah haka dai marubucin waƙar ya ci gaba da
kawo mala’ikkun Allah, kuma ya bayyana cewa duk abin da mutum ya aikata suna
rubutawa.
8. Baiti na 46 da
na 47- 49 suna bayanin tashin alƙiyama. Bayan ya kawo Mala’iku, sai ya kawo
zancen Lahira da yadda ake karɓar sakamako.
9. Baiti na 48-
50, suna bayani a kan Tawassuli.
10. Baiti na 51- 52, suna
tsarkake zati Ubangiji.
11. Baiti na 53 yana bayani a
kan kyautar Ubangiji.
12. Baiti na 54 - 60, suna
bayanin ikon Ubangiji.
13. Baiti na 66 - 67, suna
bayanin adalcin Ubangiji.
14. Baiti na 74 - 75, suna
gargaɗi ga masu girman kai, saboda girman kai abu ne maras kyau.
15. Baiti na 76 - 78, suna
yabon Manzon Allah (SAW).
16. Baiti na 79, marubucin ya
faɗi sunansa.
17. Baiti na 80. ya yi ƙoƙarin
rufe waƙarsa tare da kawo yawan baitocin waƙar. A nan ne kuma ya dakata.
2.0.4 Warwarar Jigo
Anan za a yi sharhi ne kan Jigo gaba ɗayansa. Za a duba shi dangane da jawaban jigo, da kuma abin da waƙar ta faɗa a taƙaice. To amma muhimmin abin shi ne za a duba lungu-lungu na waƙar dangane da jigo tare da ƙarin bayani daga dukkannin abin da za a iya danganta waƙar da shi. Misali ana iya kawo ƙarin bayani don kafa hujja da misalai daga Alƙur’ani, Hadisi, littattafai, muƙalu, da ra’ayoyi iri daban-daban da dai sauran bayanai da za su taimaka wajen gane abin da waƙar ta ƙunsa da inda aka dosa. ɗangambo, (2007:16)
A ɗan tunaninmu a nan mai nazari yake da babban aiki kuma ja! Domin ana son ya tsattsafe bayanan da waƙar ta ƙunsa ya fito da su daki-daki. Sannan kuma yana da kyau a kalli waƙar ɗaka da waje wato dangantakar waƙar da Alƙur’ani Mai Tsarki ko Hadissai ko wani tarihi na musamman ko ambaton ayyukan ci gaba, ko wata magana mai matuƙar muhimmanci, da dai duk abin da mai sharhi zai iya gano asalinsa ta fuskar waƙa. Ashe ke nan ana son a yi nazarin ƙwaƙwab ga waƙar. Wannan fili ne na faɗin fahimtar mai nazari dangane da abin da ya gano game da waƙar da yake sharhi a kai.
A nan za a yi sharhi na gaba ɗaya tare da fitowa da saƙwannin wannan waƙa daki-daki domin ganin yadda abin yake wakana. Yanzu bari mu mayar da homa ruwa don ganin iya abin da za mu kamo na wannan sharhin da ya ƙunshi Jigo da Gajerce shi da Warware shi. Ga yadda abin yake.
Mawallafin wannan waƙar ya fara buɗe waƙarsa da cewa:
Baiti na (1) “Na fara talifi da sunan Ubangiji,
Subhanahu Mannanu babu kamar Shi.”
Wannan tana ɗai daga cikin hanyoyin da mafi yawan marubuta waƙoƙi suke amfani da ita.
Bayan mawaƙin ya fara da sunan Allah a baiti na farko, sai ya fara gabatar da gundarin jigon waƙar a baiti na biyu, wato TAUHIDI, inda yake cewa:
Baiti na (2) “Komi ka gan shi a duniya farko garai,
Ko ka gaya mini Rabbu waffare Shi?”
Wannan yana nuna Shi Allah babu wanda ya halicce Shi, kuma komi ka gani a duniya Allah ne ya halicce shi. Wato Allah Shi ne na Farko kuma Shi ne na ƙarshe, kamar yadda ya bayyana a cikin sunayenSa 99 “Al’Auwalu, Al’Akhiru”.
A baiti na 3 ne mawallafin ya fara warwarar wannan jigo inda ya ce:
(3) “Duk wanda ya yi farko ƙarshe garai,
Sai Rai guda ne babu mai kaushe Shi.”
Daga baiti na 4-15, ya ci gaba da warwarar wannan jigo yana nuna kadaituwar Allah (SWT) yana cewa , “Shi ba Shi da ɗa, ko uba ko uwa ko mata ko wani mataimaki , ko abokin shawara ko abokin aiki ko mai yi Masa wata hidima. Kamar yadda ya tabbata a cikin Alƙur’ani mai tsarki a cikin Suratul Ikhlas (SWT) kamar yadda yake cewa a wasu baituka kamar haka:
Baiti na (9). “Rayin da bai gajiya bare Shi yi gyangyaɗi,
Hali na gajiyawa yana ga wanin Shi.”
Baiti na (11). “Rayin da babu uwa gareShi bare uba,
Shi ba shi da ɗa balle a san jikanShi.”
Baiti na (15). “Albaulu, ga’iɗu ko jima’i ba shi yi,
Shi hadisi ne ajizi mai yin shi.”
Daga baiti na 17- 23 mawallafin ya yi bayanin buwayar mulkin Allah (SWT) inda yake bayanin cewa baya saye baya sayarwa, kuma ganinSa ya buwayi dukkan ‘yan’Adam. Haka kuma yana bayanin cewa Allah (SWT) ba ya da mataimaki a cikin mulkinSa, wato ba ya da waziri ko Hakimi ko Alƙali ko wani mai taimako kamar yadda ya tabbata a cikin wasu Hadisai na manzon Allah (SAW) cewa Shi Allah (SWT) Wahadahu ne La sharikalahu, wato Shi kaɗai yake ba ya da abokin tarayya. A wani wurin kuma Yakan ce Subhanahu Wa Ta’ala (SWT) wato tsarki ya tabbata a gare Shi kuma mulkinsa ya ɗaukaka. Haka kuma ya bayyana cewa mulkin Allah (SWT) Shi ya mallaki dukkan mulkin waninSa, kamar yadda yake a baiti na (19)
Baiti na (19). ‘Sarkin da ba Shi Waziri ba Shi da Hakimi,
Shi ba Shi da Alƙali balle a san MuhutinShi.”
A baiti na 24-31, ya yi bayanin irin kyauta da kuma adalci na Allah (SWT) yana nuna cewa Shi Allah (SWT) Shi ne mai ba da kyauta ga wanda ya so, kuma Ya hana wanda ya so, a lokacin da Ya so a duniya da lahira., kamar yadda yake a cikin “Bismillahir Rahmanir Rahim” wato “Da sunan Allah Mai Rahama (kyauta) Mai jinƙai.” Kuma da kyautarSa ne mai kyauta ke yin kyauta. Kamar yadda yake a baiti na 24.
Baiti na (24). ɓa ya ganin ƙyashin abin da ka mallaka,
Ko me ka samu Shi ya ba ka don son Shi.”
A baiti na 32, da 54-60, ya yi bayanin ikon Ubangiji Allah (SWT) cewa Shi ke aikata yadda ya so a lokacin da ya so, babu mai cewa don me? Kamar yadda ayar Al’ƙur’ani Mai tsarki ta nuna, “Fa’alun Liman Yurid” wato Shi Allah Shi yake aikata abin da ya ga dama. Haka kuma a cikin wata Ayar ta Al’ƙur’ani Mai tsarki yana cewa, “ Inna Laha Ala kulli shai’in Ƙadir” wato Shi Allah yana da iko a kan komai. Mu dubi waɗannan baitukan don gani yadda Marubucin ya ce.
Baiti na (32) “Shi ne ke aikata yadda ya so Wahidun,
Don babu mahalukin da za shi kwaɓe Shi.”
Baiti na (58) “Duka duniya idan sun ka so ka da arziki,
Idan ya sa ma faƙru babu mai ba ka shi.”
Daga baiti na 33-37 ya ci gaba da bayanin kyautar Allah (SWT) inda ya ce kamar hasken Rana da Wata ne, ya wadaci duniya baki ɗaya.
Daga baiti na 39-40, ya yi bayanin wasu daga cikin sunaye da siffofin Ubangiji inda yake cewa:
Baiti na (39). “Shi ne Sami’un, Basirun Mai ji Mai gani,
Komai Ya ɗarsa a zuciya Ya san shi.”
Baiti na 41-45, Mawallafin ya yi bayanin Mala’iku da Allah ya sa ga kowane ɗan’Adam domin su rubuta dukkan ayyukansa masu kyau da marasa kyau. Waɗannan mala’iku ba su ci ba su sha, ba su barci, aikin su kawai suke yi kuma ba su saɓon Mahaliccinsu. Duba wannan baitin.
Baiti na (41) “Hairan da sharran wanda duk ka aikata,
Da mala’iku da suke rubutu don shi.”
A baiti na 46-49, ya yi bayanin tashin Alƙiyama da yadda hisabi zai kasance, wato wanda ya yi aikin ƙwarai zai karɓi littafinsa da hannun dama, wanda ya yi mumunan aiki kuma zai karɓi nasa littafin da hannun hagu. Ga dai yadda abin yake a cikin baitukan.
Baiti na (46) “Kowa abin da ya aikata ran lahira,
Ran nan ake jimilla a ba shi abin shi.”
Baiti na (47) “Wani za a ba shi kitabihi bi yaminihi,
Wannan rabon aljanna ne a gare shi.”
Baiti na (49) “Wani ko ta ƙirji za a hudo zaharihi,
Hannun hagun sannan a ba shi abin shi.”
A baiti na 52-53, ya yi bayanin yadda Allah (SWT) yake haƙuri da bayinSa, da kuma himmatuwa a wajen roƙonsu. Misali.
Baiti na (52). “ Sarkin da ba Shi fushi balle Shi yi ɓaɓɓaki,
Haƙuri gare Shi Ubangijin Al’arshi.”
Baiti na (53).“ Mai bai wa kowa ba a cewa Ya hana,
Kowa ya ce bai ba shi ya saɓe shi.”
A baiti na 61-67, marubucin ya ci gaba da bayanin kaɗaituwar Allah (SWT) da kuma wadatuwar Shi da zatinSa, cewa ba ya buƙatar komi wurin kowa kuma Shi kaɗai yake ba Shi da abokin tarayya, har ya ba da misali daga Suratul Ikhlas (Ƙulhuwal Lahu) ga dai abin da ya ce:
Baiti na (61) “Can suratul Iklasi ga ayarSa nan,
Shi wahidul-Ƙaharu ba na biyun Shi.”
A cikin baiti na 68-73, marubucin waƙar ya ci gaba da bayanin buwayar Ubangiji a kan mulkinSa, cewa Shi ne yake da iko a kan komai, kuma ba shi da wani tamka a cikin mulkinSa, sannan babu wani abu da yake da kama da Shi.
Daga baiti na 74-75, yana yin gargaɗi ga mutane masu girman kai cewa duk wanda ke taƙama da girman kai to lallai zai hadu da taɓewa. Ya ƙara da tunatar da masu saurare/karanta waƙar cewa kowane mutum ya dogara ga Allah ba ga waninSa ba. Kuma a daina yin girman kai.
A baiti na 79-80, Mawallafin waƙar yana ƙoƙarin rufe
waƙarsa da ambaton sunansa, tare da bayyana wa jama’a adadi/yawa baitocin
waƙar.
Baiti na (79). “Ni ne Mu’azu Haɗejia ni na yi wallafar,
Haza a ƙallu minal ƙalili yabon Shi.”
Baiti na (80). “ Baiti tamanin ne a nan muka dakata,
Ƙirga shi sosai don ka san jimlar shi.”
3.0 KAMMALAWA
A cikin kalen nazarce-nazarcen da aka yi dangane da abin da
ya shafi adabi. An gano cewa a kowane rubutu na wannan ɓangare, jigo shi ne
ƙashin bayansa. A ɗan nazarin da aka yi a wannan waƙar wadda Mu’azu Haɗejia ya
rubuta mai suna “Yabon Ubamgiji” an gano cewa Babban Jigon waƙar shi ne
TAUHIDI. Muƙalar ta ƙara da Gajerce Jigon don sauwaƙawa ga mai nazari. Ba nan
abin ya tsaya ba, sai da har aka Warware Jigon domin mai nazari ya ƙara
fahimtar waƙar ciki da waje. An kuma kafa hujjoji da baitukan waƙar dangane da
abin da marubucin ya faɗa a waƙar, da fatar wannan zai amfanar da al’umma
baki-ɗaya.
MANAZARTA
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.