Ticker

6/recent/ticker-posts

Fitattun Dabi’un Maguzawa

Abdullahi, I. S. S. (2008) “Fitattun Ɗabi’un Maguzawa” Maiduguri Journal of Linguistics and Literary Studies (MAJOLLS) Vol. X Department of Languages and Linguistics, University of Maiduguri, Page 77–82 ISSN: 1595-6873

Fitattun Ɗabi’un Maguzawa

Daga,

Ibrahim Abdullahi Sarkin Sudan Ph. D
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
e-mail: ibrasskg@gmail.com
GSM: 0803 6153 050

1.0 GABATARWA

Kowace al’umma ta duniya akwai irin kallon da wasu mutane na daban suke yi mata. Wannan kallo yakan bayyana ra’ayi a kan abin da aka fahimta ko aka hango a rayuwar al’uma. Ana samun irin wannan sharhi ne a sakamakon wasu mu’amala da ta wanzu da waɗannan mutanen da ake sharhi a kansu. Idan mu’amalar mai kyau ce to ana sa ran irin wannan sharhi ya yi kyau da armashi. Ida kuwa hulɗar da aka samu mara kyau ce kamar ta yaƘi ko gaba, to a kullum za a rinƘa jin munanan sharhi a kan wannan al’uma. Haka ma ba a sa ran a ji wani abin arziki dangane da halaye ko ɗabi’un al’umar idan tun farko akwai dangantakar wasan barkwanci a tsakaninsu da juna kamar wandda take tsakanin Fulani da Barebari ko Katsinawa da Nufawa ko Zagezagi da Kanawa da dai saurnsu. To tambayar da za ta tusgo a nan ita ce, wane irin kallo za a yi wa al’ummun da ake ganin ba abin da ya raba su illa yanayin tunani da imani ko bambancin abin bauta?

MaƘasudin wannan maƘala shi ne, nazarin fitattun ɗabi’un Maguzawa da ninyar a yi musu adalci duk da saɓanin addini da ke tsakaninsu da ’yan’uwansu Hausawa. A ƘoƘarin cimma wananan manufa, za a so sanin ko su wa ake kira Maguzawa, kuma me ya bambanta su da mutanen da ake kira Hausawa? Sanin wannan zai taimaka wa tsokacin da za a yi a kan fitattun halaye ko ɗabi’unsu.

2.0 MAGUZAWA

Masana da yawa sun yi rubuce-rubuce a kan mutanen da ake kira Maguzawa. Misali, Krusius (1915), Greenberg (1946), Adamu (1980) Last (1980) Ibrahim (1982 da 1985) Akadu (2001) Magaji (2002) Abdullahi (2008) da dai sauransu da dama. Daga cikin waɗannan nazarce-nazarce wasu sun mayar da hankali ne a kan addinin Maguzawa, wasu a kan sana’oinsu, wasu a kan tarihinsu, wasu kuma a kan al’adunsu. Babu ɗaya daga cikin waɗannan da ma waɗanda ba a ambata ba da suka yi saɓani dangane da ainihin mutanen da ake yi wa laƘabi da Maguzawa. Duk sun tafi a kan cewa, Maguzawa Hausawa ne waɗanda ba musulmi ba, kuma addini da tunaninsu na gargajiya su ke yi musu jagoranci wajen gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Ta fuskar tarihi kuwa, wannan suna da ake yi musu a ganin masanan, ya samo asali ne bayan da wasu daga cikin Hausawan suka karɓi addinin musulunci a matsayin addininsu. Wannan ya sa suka yi ƘoƘarin bambanta kansu da waɗanda ba su kaɓi addinin ba ta hanyar kiransu da suna Maguzawa. Bayan wannan kuma, musulmin sun bambanta kansu da Maguzawa ta hanyar ɗaukar kansu su ne Hausawan. A taƘaice, Hausawa su ne musulmin da Hausa ita ce harshensu. Su kuma Maguzawa su ne Hausawan da ba musulmi ba kuma addininsu shi ne addinin gargajiya wanda suka gada daga iyaye da kakanni. To ko dai yaya lamarin ya kasance, Maguzawa Hausawa ne. Ba su da wani harshe illa Hausa, kuma Ƙasar Hausa ita ce Ƙasarsu.

3.0 ƊABI’UN MAGUZAWA

Sakamakon bincike-binciken da masana suka yi da irin kallon da mutane suke yi musu, da mu’amalar da ake yi da Maguzawa sun tabbatar da cewa, Maguzawa mutane ne da ke da kyawawan halaye da ɗabi’u masu ban sha’awa da Ƙayatarwa in ban da ɗan abin da ba a rasa ba da ya saɓa wa rayuwar mutane musamman ‘yan’uwansu Musulmi. A wannan fasalin za a kalli yadda halaye ko ɗabi’un Maguzawa suke a idon manazarta.

3.1 Tsare Gaskiya

Hausawa suna yi wa gaskiya kirari da “dokin Ƙarfe” Maguzawa mutane ne da aka sani da faɗar gaskiya. Duk wanda ya yi hulɗa da Maguzawa ta kasuwanci ko a wata mu’amala zai tabbatar da haka. Abu ne mai wuya dattijon Bamaguje ya buɗe baki ya yi Ƙarya don kawai ya kare mutuncinsa ko don ya sami wani abin duniya. Wannan ba abin mamaki ba ne domin tun a tarbiyyarsu ta tsafi akan ladabtar da su daga illar yin Ƙarya. Misali, Maguzawa suna da tsafin gida. Kusan kowane gida akan ajiye wani jan dutse, ko tama ko dutsen ƘanƘara a Ƙofar gida ko a wani wuri na musamman a cikin gidan, a matsayin tsafin gidan. Wannan tsafin da shi akan dogara wurin gudanar da al’amurra a gidan. Idan ana gardama a kan wani abu ko aka zargi wani da aikata wani abu ya musanta, akan zo wajen tsafin gida a rantse.[1] Duk Bamagujen da ya yi imani da tsafin gidansu, ya kuskura ya rantse da shi a kan Ƙarya to babu shakka ranar zai baƘunci lahira.

A wani misalin kuma, a al’adar Maguzawa, kafin a kai amarya ɗakinta (gidan miji), akan kai ta wurin tsafin da suke bauta wa ta rantse a kan ba ta taɓa sanin ɗa namiji ba. Idan ta rantse kan Ƙarya to takan tozarta kai tsaye ko ma ta rasa rayuwarta gwargwadon irin tanadin da tsafin ya yi.[2] Ire-iren waɗannan tsafe-tsafe su suka yi wa Maguzawa jagoranci tun fil azal dangane da hana su yin Ƙarya. Bamagujen asali, yakan gwammace a kashe shi da ya yi Ƙarya a kan abin da bai faru ba.

3.2 Taimakon Juna

Maguzawa mutane ne masu ɗabi’ar taimakon junansu. Babu mai raba Bamaguje da ɗan’uwansa. Irin zaman da Maguzawa ke yi na gandu shi ya tabbatar da haka. Idan Bamaguje yana da ɗan da ya isa aure, shi zai yi masa komai na hidimar auren, kuma ya ci gaba da ciyar da shi. Shi kuma ɗan don nuna godiyarsa, yakan ci gaba da aiki a gonar uban (gandu) har da matarsa. Kuma duk amfanin gonar da aka samu na uban ne. Idan bukin Bamaguje ya tashi na aure ko haihuwa ko mutuwa, komai nisan inda dangi suke za su zo muddin dai suka sami labari. Kuma zuwan da za su yi ba hannu sake ba. Hatta da karen gidan Bamaguje sai ya san ana buki a gidansu. ‘Yan’uwa sukan kawo gudummawa fiye da yadda ake tsammani. Rashin abin yin buki bai sa Bamaguje ya ɗaga bukin gidansa, domin ya san dangi za su taimaka.

3.3 Ɗiyauci na Ƙyamar Ɗan Hali

Sata ga Bamaguje mummunar ɗabi’a ce. A al’adar Maguzawa, abin kunya ne a kama mutum ya yi sata. Laifin sata a tunanin Maguzawa yakan shafi ’ya’ya da jikoki da ma zuri’a gaba ɗaya ta hanyar hana masu samun aure ko Ƙyamar auren mata daga wannan zuri’ar. Maguzawa Sata takan sa Bamaguuje barin gari har abada. Don kare al’umar Maguzawa daga wannan mummunar ɗabi’a an yi tanadi na musamman ta hanyar tsafin da suke bauta wa. Misali, ga masu bauta wa tsafin Uwar gona,[3] ba yadda za a yi su yi sata su kwana lafiya. Kuma kayansu, musamman amfanin gona bai satuwa ga kowane mahaluki. In kuwa har mutum ya kuskura ya yi satar, to cikinsa zai kumbura ya mutu. Wanda ya yi satar da wanda ya sayi kayan satar da wanda ya ci kayan satar duk za su baƘunci lahira a wannan ranar. Haka kuma dole ne a ja gawar wanda Uwar gona ta kashe (a sakamakon satar da ya yi) da igiya, ana barbaɗa toka har wurin da za a bizne shi. Ba a yi masa shagali ko wani bukin mutuwa. In ba haka ba to duk ‘yan’uwansa maza za su rinƘa mutuwa ɗaya bayan ɗaya cikin ‘yan kwanaki.[4] Gudun irin wannan abin kunya shi kan sa sai dai Bamaguje ya ga an kamo ɓarawo amma ba a zarge shi da yin sata ba. Hatsin Bamaguje yakan shekara cikin gona ba tare da tsoron wani ya kwashe ba.

3.4 Kare Ɗiyaucin Zuriya

Yin lalata (tarawa tsakanin mace da namiji ba tare da aure ba) yana daga cikin munanan ɗabi’u da Bamaguje ya nisanta. Don haka suke alfahari da tsarkakakkiyar zuri’a. Kamar yadda bayani ya gabata, dole ne kafin a kai mace ɗakin mijinta sai an tabbatar da ta kai budurcinta. In ba haka ba ya zama abin kunya gare ta, da iyayenta da ma danginta. Irin al’adun da ake gudanarwa na tsafi don tabbatar da ɗiyaucin mace sun bambanta daga wuri zuwa wuri, duk da yake akwai Maguzawan da ba su gudanar da wannan al’adar. Ta ɓangaren namiji shi ma tun a wurin tsarance,[5] da zarar ya yi ƘoƘarin lalata yarinyar da yake nema aure asirinsa zai tonu, ya tozarta a al’uma, ya ma rasa mata. Dole ya bar gari. A wurin Maguzawan Kainafara[6] ma har bayan an haihu sai sun yi tsafin tabbatar da ɗan nasu ne ko ɗan zina ne. Don haka maza da mata a al’umar Maguzawa da wannan takunkumi ake haihuwarsu, su kuma girma da shi, su kiyaye shi don kare mutuncinsu da mutuncin zuri’arsu.

3.5 Ladabi Da Biyayya

Maguzawa mutane ne masu ladabi da biyayya ga na gaba. Suna yi wa ’ya’yansu tarbiya a gargajiyance ta yadda yaran su ma za su tashi suna girmama mutane, ba lalle sai iyayensu kaɗai ba. Bamaguje ba ya walaƘanta iyayensa. WataƘila ɗaukar nauyi da biya musu bukatun rayuwa har bayan sun yi aure shi ya sa ’ya’yan suke tausayawa, suna yi wa iyayen duk abin da ya kamata su yi waɗanda al’ada ta tanada a matsayinsu na iyaye. A lokacin da uba ya tsufa, ya fara rauni wurin noma, ’ya’ya manya su ke da alhakin ɗauke masa ci da sha. A al’adar Maguzawa, komai tsufan mutum, in ya yi magana ta zauna. Ba mai musawa ko sauya masa magana. Wani abin sha’awa ga rayuwar Maguzawa dangane da tarbiyya ita ce, sukan matsa nesa da ’ya’yansu idan manya za su yi hirarsu wadda ba su son ’ya’yansu su koya. Haka su ma mata suke yi a cikin gida.

3.6 RiƘon Amana Da AlƘawali

Bamagujen mutum yana da riƘon amana. Duk abin da za ka ba shi don ya ci amanar wani, gara ya rasa abin da yake nema na rayuwa. Haka ma lamarin alkawari yake gare shi. Misali, idan aka ajiye magana da Bamaguje cewa, a haɗu rana kaza ko lokaci kaza, to sai dai ka tarar da shi yana jira. Suna da riƘon amana musammam dangane da wani abu da aka ba su su kula da shi kamar gona ko amfanin gona ko ’ya’yan dangin da suka mutu ko dukiya da dai sauransu.

3.7 Wayo da Daɗin Baki

Masu mu’amala da Maguzawa sun shaide su da wayo wurin gudanar da al’amurra. Sukan ce abu ne mai wuya ka yaudari Bamaguje ko ka zalunce shi. Idan kuwa ka ci nasarar yin haka to ka tabbata in ya gane wata rana sai ya rama, ko da ga ‘ya’yanka ne in ba ka da rai. Wannan ya sa na tuna da labarin “Dan hakin da ka raina” na cikin littafin Magana Jari Ce juzu’i uku. A cikin labarin, Anunu mahaucin birni ya yi wa Bamaguje wayo ya karɓe masa saniya a kan ’yan kuɗi kaɗan. Da Bamaguje ya zo rama cutar da aka yi masa sai da Anunu ya yi da-na-sani a kan cutar Bamaguje da ya yi. Ta fuskar iya magana kuma, ta bakin Bamaguje ake jin gangariyar Hausa. WataƘila wannan na faruwa ne saboda zamansu cikin daji da rashin son gurɓata zuri’a ta hanyar auren waɗanda ba Maguzawa ba. An haife su a cikin Hausar, da ita suka tashi, da ita suke magana.

3.8 Son Mutane

Maguzawa mutane ne da ba su da Ƙyamar mutane. Ba su da ɗabi’ar rashin son mu’amala ko sakin jiki da mutane. Ba su da Ƙyamar cin abinci a kwano ɗaya da wanda ba Bamaguje ba sai dai su a Ƙyamace su.[7] Ta fuskar auratayya ma, idan ’yarsu ta nace a kan Musulmi take so, sai su bar ta ta aure shi. Haka ma ba su Ƙyamar ibadar da Hausawa Musulmi suke yi, kamar salla da azumi. A sakamakon kyakkyawar mu’amalarsu da mutane, wasunsu har sukan aiwatar da ladubba na addinin Musulunci kamar faɗar Allah Sarki, Insha Allah, Masha Allah, Bisimilla, Alhamdu Lillahi, ka ce dai Musulmi ne. Sukan tanadar wa Musulmin da ke hulɗa da su tabarma da buta don yin alwalla da salla idan sun ziyarce su. Suna gamawa za su naɗe su ajiye a wuri na musamman sai in wani ya zo. Idan suka yi baƘo, galibi sukan ba shi tabarma su koma Ƙasa su zauna. Maguzawa mutane ne masu son raha. Kusan duk wanda yake kusa da su sukan mayar da shi kamar abokin wasa. Suna sha’awar yin ba’a da wasa da dariya da mutane.

3.9 Yawan Kyauta da HaƘuri

Maguzawa mutane ne masu kyauta. Abin su ba ya tsone musu ido. Abin kunya ne su yi baƘo su rasa abin da za su ba shi na tsaraba. Haka kuma, a wurin mu’amalarsu, mutane ne masu haƘuri. Ba Ƙaramin saɓani ke sa Bamaguje zare dantse ba, duk da yake ba ya son a rena shi. Haka sukan yi banza da mutanen da suke tsarguwar su musamman abokan wasa a kan ɗabi’unsu da suka saɓa wa Musulunci. Ba cikin sauƘi akan ga ɓacin ran Bamaguje ko a ga yana buga-in-buga ba.

3.10   Son Sharholiya

Bamaguje mutum ne mai sha’awar shan giya. Tana daga cikin abin da ya fi ba muhimmanci dangin shaƘatawa. Haka kuma suna da sha’awar tara mata da yawa. Ɗaukakar Bamaguje, da matsayinsa, da darajarsa a al’umma sun dogara ne ga yawan iyalan da ya tara. Haka ma suna sha’awar yin bukukuwa. Suna kashe dukiyarsu wurin gudanar da buki. Suna ba wasannin dara da gaɗa a dandali muhimmanci. Haka kuma, mutane ne masu sha’awar doki. Duk Bamagujen da ya Ƙasaita dole ne ya nemi doki ko dawaki ya ajiye. Akan gane girma ko matsayin mutum ta la’akari da yawan dawakin da ya zo da su wurin bukin hawan sadaka (Bukin Mutuwa na Shekara). A irin wannan buki ba abin da Bamaguje yake taƘama da shi, daga doki sai tsafi.

3.11  Taka-Tsantsan Da BaƘon Abu

Maguzawa musamman a wannan zamani sukan guji karɓar baƘo ko baƘon abu sai fa in ya biyo ta hannun shugabanninsu ko kuma wanda ya san su ya tabbatar musu da cewa, abin nan ba zai cuta musu ba. Maguzawa mutane ne masu taka-tsantsan da wani baƘo wanda ba su sani ba, ba su san manufarsa ba.

3.12  Yarda da Gabaci

Ƙwarewa kan tsafi da yawan shekaru da yawan dukiya ko yawan zuri’a su ake la’akari da su wurin ba da shugabanci a al’umar Maguzawa. Ƙwarewa a tsafi ya danganci bayar da magungunan cuta ko biyan bukatun rayuwa da buwaya da kuma sihirce-sihircen da suka shafi noma da yin fice a kan sa. Yawan shekaru kuma abu ne da suke girmamawa saboda ladabi da biyayyarsu. Sun yarda da cewa, “babban yatsa ko ba ta cin tuwo ta iya ɓare malmala. Yawan zuriya kuma abu ne da suke ganin yake jawo musu martaba a idon jama’a har a yanke shawara kai tsaye ta buƘatar shugaba a gida ya jagoranci unguwa ko Ƙauye. Suna ba shugabanni girma da aiwatar da bukatunsu kai tsaye. In suka gitta kara ba mai tsallakewa. Irin waɗannan shugabanni su ke yi musu jagoranci a rayuwarsu ta yau da kullum. Maguzawa sun fi sha’awar su saurari dattijo mai shekaru irin nasu, ba yaro ba. A kowane lokaci sukan rena sauraron yara, saboda ganin cewa sun fi su shekaru, ba abin da za su gaya musu na hikima ko burgewa. Sun fi son su saurari magana mai ma’ana daga dattijo. Wannan shi ya sa ko da wurin buki aka je, kowane rukunin jama’a sukan zauna ne ta la’akari da shekarunsu. Maguzawa ba su zama tare da ’ya’yansu suna hira ko shan giya.

3.13  Kiyaye Al’adu

Maguzawa mutane ne masu sha’awar riƘe da kiyaye al’adunsu. Ba su so mutane su yi musu shisshigi a kan al’adun nasu. Haka kuma ba su kan yi karambani a kan lamarin wasu Ƙabilu. Duk abin da suka sani dangane da al’adar mutanen da sukan ziyarce su, suna kiyayewa. Haka su ma suna la’akari da abin da suka tarar na al’adun mutane idan suna baƘunci.

4.0 NAƊEWA

Wannan maƘala ta yi ƘoƘarin yin adalci ne wajen kallon Bamaguje kamar yadda aka fahimci yake a zahiri kuma ba tare da amfani da wani mizani na tarihi ko wata dangantaka wurin auna shi a idon mutane ba. Mu’amala a cikin wannan al’uma ta Maguzawa na shekaru fiye da biyar don nazartar wasu al’adu nasu shi ya haifar da wannan nazari. Duk da yake ba a nazarci kallon da abokan hamayyar su suke yi musu ba don kwatantawa a tabbatar da sahihancin wannan nazari, a fili yake cewa, Maguzawa mutane ne da ke da kyawawan ɗabi’u na zahiri kamar yadda rubuce- rubucen magabata suka nuna, kuma wannan nazari ya tabbatar. Wannan nazari tamkar matashiya ce ga manazarta da su ƘoƘarta kallon kowace al’uma ta duniya bisa tafarkin da suka ginu a kai.

5.0 MANAZARTA

Adamu, M. T. (1997) Asalin Hausawa da Harshensu. Ɗan Sarkin Kura Publishers, Kano.

Adamu, M. (1976), “The Spread of Hausa Culture in West Africa 1700 – 1900” Savanna No 5 Vol. 1, A Journal of the Environmental and Social Sciences. Published at Ahmadu Bello University, Zaria.

Adamu, M. (1977) “The Economics of Culture Among The Hausa during the Present Millenium A. D.” Culture Seminar Ahmadu Bello University, Zaria.

Akodu, A. (2001), Arts and Crafts of the Maguzawa and some Educational Implications. Gaskiya Corporation Limited. Zaria – Nigeria.

Alhassan, H. da Sauransu (1982), Zaman Hausawa

Aliyu, A. Y. (1973) “Asalin Hausawa” a cikin littafin Bukin Makon Hausa Jami’ar Bayero Kano,

Bunza, A. M. (1995) “Magungunan Hausa a Rubuce: (Nanzari Ayyukan Malaman Tsibbu),” Kundin digiri na uku, Jami’ar Bayero, Kano.

Bunza, A. M. (2006) Gadon Feɗe Al’ada Tiwal Nig. Ltd: Lagos.

Bunza, A.M. (1990), “HayaƘi Fid Da Na Kogo: (Nazarin Siddabaru Da Sihirin Hausawa)”, Kundin Digiri na Biyu, Jami’ar Bayero, Kano.

Charanchi, R. (1999), Katsina Dakin Kara: Tarihin Katsina Da Garuruwanta, Northern Nigerian Publishing Company Limited, Zariya.

 Fletcher, D. C. (1929) “The Kai-na-Fara.” Extract from Re-assessment Report on ’Yanɗaka District, Katsina Emirate, Zaria Province. M. P. No K. 8833 National Archives and Monuments, Kaduna.

Furniss, G. (1999), Poetry, Prose and Popular Culture in Hausa, Edinburgh University Press, London.

Greenberg, J. (1946) The Influence of Islam on a Sudanese Religion: Monographs of the American Ethnological Society. J. J. Augustin Publisher, New York.

Ibrahim, M. S. (1982), “Dangantakar Al’adu da Addini: Tasirin Musulunci Kan Rayuwar Hausawa”, Kundin Digiri na Biyu (M.A. Hausa), Jami’ar Bayero, Kano.

Kado, A. A. (1987), “Kainafara Arnan Birchi”, Kundin Digiri na farko (B.A. Hausa), Jami’ar Sakkwato.

Krusius, P. (1915), “Maguzawa” Archiu, Anthropologies, NF Vol. XIV.

Lawal, A. T. (1986), “Al’adun Hausawa Jiya da Yau”, Kundin Digirin farko Jami’ar Sakkwato.

Madauci I. da wasu (1968) Hausa Customs Northern Nigerian Publishing Company, Zaria.

Magaji, A. (2002) “Wasu Al’adun Hausawa: Yanaye- yanayensu a Ƙasar Katsina.” Kundin digiri na uku, Ja’mi’ar Bayero, Kano.

Malumfashi, A. A. (1987) “Hausa Language Speech Usage Norms: A Case Study of Maguzawa Society in Malumfashi Area”, Bayero University, Kano.

Marriage. Manchester University Press, United Kingdom.

Malumfashi, A. I. (1988) ‘Wauta A Rayuwar Bafullace: Gaskiya Ko Shaci Faɗi?’ MaƘalar da aka gabatar a taron Ƙara wa juna sani, a Cibiyar Nazarin Harsunan Nijerya, Jami’ar Bayero, Kano.

Morel, E.D. (1968), Nigeria Its Peoples and Problems, Frank Cass and Company Limited London.

Ottenberg, P. and Simon (Ed.) (1960), Cultures and Ethics of Africa, H. Wolff Book Mfg.Co., Inc. U.S.A.

Safana, Y.B. (2001), “Maguzawan Lezumawa (Babban Kada) Gundumar Safana”, Kundin Digiri na farko, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Sufi, A. H. (2001) “Hanyar Kiran Maguzawa Zuwa Ga Addinin Musulunci.” MaƘalar da aka gabatar a taron Kwamitin Yaɗa Addinin Musulunci na Jihar Kano.   

Tremearne, A. J. N. (1913) Hausa Superstitions And Customs. John Bale, Sons and Danielsson, LTD Oxford.

Yahaya, I. Y. da wasu (editoci, 1982), Studies in Hausa Language, Literature and Culture: Procedings of the Second International Conference, Centre for the Study of Nigerian Languages, Bayero University, Kano.

Yusuf, A. B. (1986), “Wasannin Maguzawan Ƙasar Katsina”, Kundin Digirin farko, Jami’ar Sakkwato.



[1] Muhammadu Sani Ibrahim, “Dangantakar Al’ada Da Addini: Tasirin Musulunci Kan Rayuwar

 Hausawa.” Kundin digiri na biyu, Jami’ar Bayero Kano, 1982, shafi na 33.

[2] Dubi lamba ta 1, shafi na 171.

[3] Uwar gona aljana ce da Maguwa ke bauta wa. Dubi lamba ta 1, shafi na 32 don Ƙarin bayani

[4] Hirarmu da da wani Bamaguje mai suna Tukunya Jikan ƘwanƘi (ɗan shekara 82) a Ƙauyen ƘwanƘi cikin

 Ƙaramar hukumar Bakori Jihar Katsina, a ranar 22-02-06.

[5] Tsarance wata al’ada ce ta Maguzawa inda saurayi zai tafi gidan budurwar da yake so ya aura, su kwana

 tare kan shimfiɗa ɗaya ba tare da wani abu ya faru ba.

[6] Maguzawan Kainafara wasu Maguzawa ne da ke zaune a Birchi a da cikin Ƙasar Kurfi ta jihan Katsina ta

 yanzu.

[7] Na tabbatar da haka a lokacin da nake zagaya Ƙauyukan Maguzawa don tattara bayanai a kan wasu al’adu

 nasu. Ga misali, na sha hura a Ƙwarya ɗaya da Babban Kada (shugaban Maguzawan Lezumawa), a Ƙasar

 Safana cikin Jihar Katsina, a lokacin da na ziyarce shi a ranar lahadi 26-02- 06.

Post a Comment

1 Comments

ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.