Ticker

6/recent/ticker-posts

Lalurar Kida A Bakin Makada

LALURAR KI'DA A BAKIN MAKA'DA
(Hasashen ďaliban Al’ada ga Makomar WaƘoƘin Baka)

DAGA

ALIYU MUHAMMADU BUNZA
SASHEN NAZARIN HARSUNAN NIJERIYA,
JAMI’AR USMANU ďANFODIYO SAKKWATO
mabunza@yahoo.com 0803 431 6508

TSAKURE

An yi bincike abin a zo a gani a kan makaɗa da mawaƙan ƙasar
Hausa. Ni a nawa sani babu wani fanni na Hausa da ya samu
tagomashin bincike kamar na waƙa. A iya sanina an gabatar da fiye da
kundayen digirin PhD 16 na fannonin waƙa daban-daban da kundayen
MA fiye da 50 amma babu wanda ya himmatu ga ƙwaƙwalo tunanin
makaɗa a kan kiɗa da waƙa. Ganin haka, wannan ɗan bincike ya taɓo
mawaƙan baka 11 domin ya ji ta bakinsu. An ciro ɗiyan waƙa 17 daga
bakunan makaɗan da suka furta matsayin kiɗa a wajensu. An raba
wannan nazari zuwa sassa 13 domin a bayyana ma’anonin matanonin
ɗiyan waƙar da aka kafa hujja da su. A wajen makaɗan Hausa
musamman ‘yan shige/haye kiɗa wata ƙaddara ce da ta riske su. A
ɓangare ɗaya kuwa, waɗanda suka gada burinsu su aje su tuba. An
gano abubuwa bakwai da ke sa makaɗi ya aje kiɗa ya tuba. Ga alama,
nan gaba kaɗan, Hausa za ta yi hasarar fitattun makaɗan gargajiya ta
fuskar tsufa, tuba da mutuwa. Da za a taskace ayyukkan fitattun
makaɗa tun dare bai yi ba, da an huta da ɗirkaniya mota cikin randa.

GABATARWA


Babu wata al’ummar duniya ta za ta yi bugun gaba da cewa, da saukakken
addininta ta samu kanta. Bayan da aka zauni ƙasa, aka miƙe ƙafafu, aka more wa
ƙuruciya, da yaranta, da tsufa, da zamani, saukakkin addinai suka riski ɗan Adam.
Gabanin su, mutane sake suke ba ƙaidi, bakin gudunka bakin ladarka.Bayyanar
addinai ya zo da rarrabe al’adu miyagu, da na gari, da yardaddu, da harantattu.
Bahaushe na daga cikin al’ummar da wannan guguwar ba ta tsallake ba. Gabanin
hasken saukakkin addinai a ƙasar Hausa, addinan gargajiya ke jagorantar
zamantakewa. Cikin addinan da al’adun, kiɗa da rawa da waƙa wasu sinadaran
rayar da al’umma ne. Ai don haka Bahaushe ke ce wa makaɗa: “Makaɗa ran gari”.
Da ba don kiɗa ba da gari ya watse, a bar kangayen gidaje. Duk da yake ko bayan
da musulunci ya miƙe ƙafafunsa ƙasar Hausa ba a daina kiɗa ba, amma ana
kallonsa wata lalura ta daban.

KI'DA A MA’AUNIN BAHAUSHE JIYA


Manufata da jiya shi ne, jiya mai nisa tun gabanin Bahaushe ya sunsuni
addinin littafe. Gobe a ma’aunin manazarta al’ada tana ɗaukar ma’anar ranar
haɗuwar bawa da mahillicinsa. Idan kuwa suka ce, “Yau”, to zamani ne mai tsawo
daga yanzu da muke magana har zuwa ranar da za a kwanta kushewa. Don haka, a
jiyar Bahaushe kiɗa babbar sana’a ce da ta keɓanta ga gidaje na musamman da
suke taskace tarihin al’umma. A jiya, makaɗa a ƙasar Hausa mutane ne zaɓaɓɓu,
fitattu, ƙwararru kuma amintattun al’umma da koyaushe ake kishin kare su da
martabarsu. Makaɗi ba ƙyalle ba ne a ko’ina yake zaune a garin Bahaushe. In ba su
ba gari, in kuma sun yi yawa gari ya haɓaka. Garin da ba makaɗi matacce ne,

kurman gari ne mutanensa ba su da wata alfarma ta dole da maƙwabtansu za su sa
masu hannu. Bukukuwan matakan rayuwar Bahaushe uku, aure, haihuwa da
mutuwa kiɗa ne gishirin haɗa su.
A tsarin rayuwar jiya ta Bahaushe tsaron ƙasa da kiɗa yake tafiya, don haka
ake da kiɗin yaƙi da kiɗin tauri. Siyasar ƙasa, kiɗa ke fitar da amonta da
martabarta, don haka ake da makaɗan fada. Tattalin arzikin ƙasa kiɗa ke inganta
shi, don haka ake da makaɗan noma, farauta, ƙira, fawa, su, da sauransu. Walwala
da sakewa kiɗi ke kyautata su, kiɗin gambara da gumbe da zari sun isa misali.
Addinin kansa da kiɗa ake aiwatar da shi bisa ga amon goge da garaya da ƙwarya.
Sadarwa ta cikin gida da unguwa da gari, da gari da gari, kiɗa ke taka rawar gani ta
fuskar tambari da ƙaho da kuge da gwarje da makamantansu. A ƙasar Hausa ta
jiya, babu wata rawa da za a taka ba da makaɗa ba. Don haka nake ganin kiɗa wata
lalura ce babba da Bahaushe ya samu kansa cikinta wadda ta yi masa tarnaƙi a
rayuwarsa.

KI'DA A SIKELIN YAU NA BAHAUSHE


Yau ta Bahaushe ta ƙunshi abubuwa masu yawa. A taƙaice, tana ɗaukar,
bayan saduwar Bahaushe da wasu al’ummomi da can da bai san su ba. Bayan
saduwar Bahaushe da saukakkin addinai. Bayan fitar Bahaushe ƙangin mulkin
mallaka. Bayan da addinin musulunci ya zauni ƙasar Hausa ba zama na tsangwama
ba. Na so in ba da ƙarfi ga bayanina na ƙarshe, wato addinin musulunci da
Bahaushen yau.
Shaƙuwar da Bahaushe ya yi wa addinin musulunci ba ‘yar kaɗan ba ce. Irin
kamun kai na nisantar ƙarya da sharholiya da masha’a da kare mutunci da martabar
kai da ta zuriya da ta waɗanda ke ƙarƙashinsa, kiɗa bai tazarar shiga a wurin. Da
yawa daga cikin kaɗe-kaɗen Bahaushe musulunci ya saka su ciki tarkacen

hululuwa na tsallake dokokin iyakokin addini. Da sannu, makaɗan da suka rage da
wannan ɗan hayaƙin, da suka rungumi musulunci suka aske kiɗa suka tuba suka
kama hanyar karatu kai tsaye. Waɗanda ba su tuba ba shari’a ta hana su miƙe
ƙafafunsu irin na jahiliyyar farko. Duk da yake shari’a ta kau da kai ga wasu kaɗekaɗe,
irinsu kaɗa dundufa don bukin aure ko kiɗin yaƙi. Haka kuma, wasu
musulmi suka shigo da kiɗa a wuraren aiwatar da ibadojinsu kamar kiɗin mandiri
da ire-iren su. Wannan duk bai sa makaɗa suka yi watsi da fassarar farko ba,
domin sun san da kiɗa wani abin kai gida ne da Annabawa Allah zai fara umurta
da shi. Da wannan hujja ce wasu makaɗa suka fara tunanin tuba daga kiɗa/kiɗi.

ƙUNSHIYAR KI'DA


Kiɗa sauti ne mai jan hanakali da yin gangami a zo a sheƙe aya. Ya fi
burgewa idan an haɗa shi da rawa da ihe-ihe. Ya fi ƙawata fage idan an haɗa mata
da maza. Yana da jan hankali idan ana tafiyar da shi a waƙa. Idan ya kankama da
makaɗa da ‘yan rawa sukan fita hayyacin kansu, musamman idan kiɗin bori ne da
noma da farauta da tauri da ƙira da su da sarauta. Kirare-kiraren da ke cikinsa da
masu yin kiɗa da wanda ake yi wa kiɗa da na sanƙira cike suke da turnuƙun
maguzanci na sauran danshen addinan jiya na gargajiya da ke nesa-da-nesa da
aƙidojin musulunci. Gaskiyar Bala Ganɗo da ke cewa:
Jagora: Kiɗan duma farauta
:Goge ka kiɗan bori
:Dum mai salati
:Garkan Malam yaka komawa
Gindi: Ba a gane manya
:Sai ci ya samu

Ta tabbata cewa, kiɗa ka tayar da tuban arne domin ƙunshiyarsa cike yake
da zuga da washi da salon ingiza mai kantu ruwa mai haddasa santsi da ɓarin baki
daidai yadda ɗan’anace ke gaya wa Shago:

Jagora: Wandara in kana biyat ta kiɗina
:Wallai ina halaka ka
:Sai na kai ka inda ba ka hitowa
Yara: Sai mu rage kiɗi mu sassauta mai
:Don kar ya haukace baki ɗai

Waɗannan rubabi-rubabin zantuka da ke kai mai furta su, da wanda ake yi
wa su, da mai sauraren su ga da-na-sani su ne haɗarin kiɗa ga aƙidar addinin
Bahaushe na yau “musulunci”.
A hasashen Bahaushe, kowa na iya ya yi waƙa kamar yadda kowa na iya ya
zama mawaƙi. Waƙar ba ta fi damuwar Bahaushe ba kamar kiɗa. Wannan shi ne
dalilin da ya sa idan mawaƙi/makaɗi ya tuba, akan ce: “Ya tuba da kiɗa”. Ida ana
son a fayyace sana’arsa akan ce: “Ai makaɗi ne” domin kiɗin ya fi fice da wuya a
ce, “Ai mawaƙi ne”. Mawaƙi na iya ya kasance malami masani, amma makaɗi da
wuya a same shi haka domin kiɗa bai dace ga malami ba.

LALURAR KI'DA


Hausa gabanin karɓar addinin musulunci idan wani na aikata wani aikin da
shi kansa ya san ba ya son aikata shi, sukan kira irin wannan da sunan “kaya”.
Wani lokaci su ce, ya zama ‘alaƙaƙai’. Da musulunci ya zo, kalmar “lalura” ta
maye gurbinsu. Idan Bahaushen yau ya yi amfani da kalmar ‘lalura’ yana nufin abu
kamar dole-dole, ga shi ba a son aikatawa kuma ba a daina aikatawa ba. Idan mai
aikata abin ya kai ga faɗar abin a bayyane cewa, ya damu da abin, ko yana son ya
daina abin ko bai gaji abin ba ga uwa bale uba, da rana tsaka ƙadara ta riske shi,

abin ya zama “lalura”. Wannan nazarin na ganin haka sha’anin waƙa yake ga mafi
yawan mawaƙan Hausa.
A ɗan binciken da na yi, da hirar da na yi da wasu mawaƙan Hausa, da hirar
da na ji ana yi da su, ko aka gaya mini an yi da su, sukan nuna ƙyamarsu ga waƙa.
Da yawa daga cikin mawaƙanmu na Hausa idan aka bi diddigin tarihin rayuwarsu
za a ga:
i. Ba su gaji waƙa ba ga uwa da uba ta-tsaka ce ta rutsa da su.
ii. Ba sa sha’awar a ce ‘ya’yansu su gaje su.
iii. Wasunsu tun ana so, suna so, sai su tuba.
iɓ. Wasu na nuna sha’awarsu ga tuba tun ba su yi ba.
ɓ. Wasu kan nuna damuwarsu na mutuwa suna kiɗa.
ɓi. Wasu kan nuna nadama kan kasancewarsu makaɗa.
ɓii. Wasu kan yi fatar sauya fasaha daga kiɗa zuwa makaranta.

Ire-iren waɗannan abubuwa da ake tsinta a baukanan mawaƙan baka ya
kyautu a ce an keɓe musu wani wuri da za a nazarce su. Yana kyau manazarci ya
san ba kowace magana ake yin banza da ita ba. Hangen waɗannan abubuwa na ga
ya kyautu a kalle su da idon nazari bisa ga yadda su makaɗan ke kallon su.
Makaɗan da ke da ire-iren waɗannan kalamai sun ɗauki kiɗa wata lalura da ya
kyautu a ce sun aje, sun dangane, sun tuba, sun nemi wata hanyar gamawa lafiya
da duniya. Wannan hasashen ya sa na yi wa binciken taken: ‘Lalurar Kiɗa a Bakin
Makaɗa.’ Ga yadda abubuwan suke:


GADON KI'DA


A al’adance, Bahaushe na bugun gaba da gado sosai. Wanda ya gaji abu
daga mahaifinsa ko kakansa, ya fi wanda bai gada ba, ko da kuwa wanda bai gada
ba ya fi suna da sanin abin. Wannan ne dalilin Hausawa na yi wa ɗan gado suna
‘ɗan asali’ wanda bai gada ba kuwa ‘ɗan haye’ ko ‘ɗan shige’. Ashe gaskiyar wani
yaron Garba ɗanwasa Gummi (mai kiɗin tauri) da ya tsima wani ɗan gado sai ya
yi kirari da cewa:

“Kai Garba! Kai Garba!
Mu ka tauri,
Mu tauri ka so,
Mu mun ka gadi tauri,
Mu tauri yaz zama ma dole.”

'Dan tauri ke nan ke bugun gaba da gadon tauri da ya yi. Dubi Ja’e ɗan
Dikko Canda (ɓarawon tumaki), da mahaifinsa Canda ya rasu, Gambo ya kai
yawon waƙa gidansu yana gaya wa Ja’e:

Jagora: Ja’e na san Canda ba shi nana,
:Ga matata tana da ciki,
:Yac ce “Baba tahi yawon duniyakka”
:In kana kusa sa aka yankewa da rago
:In ba ka nan kusa, sa aka yankewa da rago
:Sunan da haramun za a yin shi
:Gambo ban kashe ko sisin kwabo ba.”

Ga ɗan ɓarawo na bugun gaba da ya gaji sata, to bale ɗan malami ko ɗan
Sarakai. Saɓanin haka, dubi yadda makaɗi ke nunawa a bayyane cewa, shi bai gaji
kiɗa ba duk da kasancewarsa a halin da yake bayanin waƙa yake yi, ana
saurarensa, ana yi masa kyauta, da kari, amma yana cewa:

Jagora: “Ni ban gadi in yi kiɗi ba,
:Zaman gadon gidanmu karatu
:Da yin salla da yin alwalla.
:Ihm!”
(J. B. Zauro: Waƙar Sa’adatu)
Da kiɗa bai zama wa J. B. Zauro lalura ba, da ba zai furta wannan ɗan waƙa
ba. Wannan ɗan waƙa ba tuntuɓen baki ba ne, domin ya ambaci abin da ya gada
daga iyayensa. Ga alama, yana burin ya koma ga turken iyayensa ya daina yin
sharholiya, ɗirkaniya mota cikin randa.
Wanda bai gaji kiɗa ba, ko ya shiga sana’ar kiɗa komai zurfin da ya yi a ciki
rashin asali ke rage masa kuzari. Wani makaɗin ‘yan-dandi mai suna ɗantaro a
waƙarsa ta sharar fage yana cewa:

Jagora: “Kiɗi gado ne
:Amma ɗantaro
:Bai gada ba.”

Wai me ya sa suke son su kuɓutar da iyayensu cewa ba su gaji kiɗa daga
gare su ba? Dalili kuwa shi ne, kiɗa wata sana’a ce da ba ta bajinta ba, kuma tana
da ƙura-ƙura a fuskar addini da rage mutunci da ƙima ta cika kamala irin ta
‘yantaccen mutum ga mai yin ta. Idan mutum ya sami kansa ciki da rana tsaka don
haka zai so mutane su san ba daga iyaye abin ya samo asali ba. Yana dai son a
gane abin ƙaddara ce ta riske shi, ba tarbiyar iyaye ce ba.


ƙADDARAR KI'DA


A al’ada, Hausawa na gani idan yaro na karatun allo aka ba shi naƙalin
samun karatu, idan karatun bai samu ba sai basirar ta koma ta azancin magana da
waƙa. Wata ƙila, shi ya sa ake samun ‘ya’yan manyan malamai cikin wannan
lalura a kasa gane da ina suka tsince ta. Marigayi Garba Maitandu Shinkafi na daga
cikin ‘ya’yan malaman da wannan ta-tsaka ta risga da su, ga yadda bayanin yake:
Jagora: Ban gadi kiɗi ba
:Ni kiɗi azanci na
:Yas sa ni yi nai
:Kaina zan wasa
:Garba ɗan Jibo
:Dogo ɗan baba Makau
Yara: Nufin Allah shi yas sa
:Abubakar waƙa
:Yas samu taushi
Gindi: Yana roƙon manyan mutane
:Mun bi ciki dajin Kwale
:Garba mun ishe kura na ta wasa

Garba gidan malamai ya tashi a Shinkafi, a faɗarsa azanci ne ya sa shi waƙa.
A faɗar wasu, fahamin karatun da aka yi ya yi yawa dole a sama wa magana wani
wuri da za ta fita in ba ga allo ba ga takarda ko ga turun waƙa. Don haka ƙaddara
ce ta riske shi ba da gado ba.


MAKAɗA A BAKIN MAKA'DA


Hausawa sun ce, mutum ba ya nuni gidansu da hannun hagu. Kowane
ma’aboci sana’a yana so ya ce, “Ni ne wane.” Idan har abokin sana’a na nuna
damuwarsa da kasancewarsa cikin sana’ar da yake yi, abin ya zan wata lalura ta
daban. A bincikena na samu wasu makaɗan da ke bugun gaba da fannin kiɗansu,
amma kuma a wata fuska su nuna kiɗan an ƙaddarto ne a kansu ba da son rai ba.
Alhaji Gambo Fagada, duk da cika bakin da yake yi na zama limamin mawaƙan
ƙaddara da hasara yana yawaita faɗar:

Jagora: Haliku Allah san da yay yi ni,
:Ban aza in zan mai kiɗi ba,
:Yau ga ni, ina yawo da ganga.

Makaɗa in ba ɗan gado ba ne, ba ya son a ce wa mahaifinsa makaɗa. Ga shi
makaɗi, yana kuri a ce masa makaɗi amma ba ya son a ce ɗan makaɗa. Da
malamin kiɗa Narambaɗa na jereƙe cikin bakandamiya faɗa yake:

Jagora: Kyawon ɗan mallami
Yara: Ya zan ka zuwa makaranta
Jagora: Shi ɗan runji
Yara: Shi ɗauki yuƙa daidai an nan
Jagora: Shi dillali
Yara: Da an saye shi bari ad daidai
Jagora: Shi kau makaɗi
Yara: Ya gyara turu
:Daidai an nan
Jagora: Ni kam kun gane ni
Yara: Na gyare turuna
:Sai zuba waƙa nikai
:Kama da ta Alfa Zazi
Gindi: Gwarzon Shamaki na malam toron giwa
:Baban Dodo ba a tamma da batun banza.

Narambaɗa fitaccen makaɗin Sarauta ne, bai gaji kiɗa ga mahaifinsa ba.
Mahaifiyarsa ta gaji kiɗa ga mahaifinta Sarkin Kiɗan Badarawa. Don haka ne bai
ce: “ɗan makaɗi kau.”Domin shi ba ɗan makaɗi ba ne, fasaha ce ta huje shi ya ci
gaba da zuba waƙa irin ta Shehu Alfa Zazi, madahan Annabi (SAW). A nan ma, da
alamun kiɗa lalura ne gare shi.

https://www.amsoshi.com/2017/09/27/kaska-wakar-farfesa-aliyu-muhammad-bunza/


SAKAMAKON MAKADI


A shari’ar musulunci kiɗi bai samu gata ba sosai yadda mawaƙa ke son ya
samu, wanda shi ne dalilinsu na yi ɗari-ɗari da shi. Nassi ya zargi kiɗin hululuwa
da jahiliyya ya kuma hukunta shi. Ga saƙon wani shararren Shehi na addinin
musulunci Ibn ƙayyim (Allah Ya yi masa rahama):

Nassi: “Wa tikraaru nushi minnaa lahum,
Li ya’azira fiihim ilaa rabbinaa.
Falammas tahaanuu bi tambihinaa,
Raja’ana ilal laahi fii amrinaa.
Fa’ishnaa alaa sunnatil Musɗafaa,
Wa maatuu alaa tintinaa-tintinaa.”
Fassara: Yawaitar nasiharmu kullum gare su,
Kwaɗaitar rabon Jalla don wajibina.
Wulaƙanta zance yawan kau da huska,
Mu koma ga Allahu komai mu daina.
Mu rayar da Sunna mu bar bin hululu,
Tafashen kiɗa tintinaa-tintinaa.
(Fassarar: A. M. Bunza, marubuci)

Bayanin Shehin malami Ibn ƙayyim na nuna ƙyamar kiɗa ga shari’a da
buƙatar a nisance shi. Bayanin ya yi canjaras da fahintar Bahaushe na ganin munin
sana’ar kiɗa a addini. Wani fitaccen mai wa’azi a Jamhuriyyar Nijar a wajajen
shekarar (1975 – 80) Malam Muhammadu mai Zabura ya fassara amon babban
kalangu da kurkutu (ƙwazagge) kamar haka:
Kalangu sautinsa: Muna ganin Annabi dai!
Kurkutu sautinsa: Ko kusa! Ko kusa! Ko kusa!

A ganin Hausawa, kiɗi ko ya zan na lalura lokaci gare shi, don haka ba sai
makaɗi ya mayar da abin sana’a ba. Rashin aikin yi da lalaci ke sa bin makaɗa ana
shan kiɗa. Duk wanda wani abu mai amfaninsa ya shagaltar da shi, shi da makaɗa
sai dai karin dole don kar a yi masa zambo. Wani makaɗin samari ya tabbatar da
wannan a waƙarsa ta ƙattan gari da ke cewa:

Jagora: Kai mai kiɗi kiɗa in jiya
:Ba ka da aiki ni ba ni da
:Mu taru mu lalace mu duka
:Kain! Kakanni ka tingan tigan!

Malam Mu’azu ƙanen Hali Argungu ya tsoratar a waƙensa da cewa:

“Bale kan makaɗin kalangu
Wasar ‘yan mata
Ba shi ganin Sidi lahira sai ya tuba.”
Waɗannan abubuwa ne makaɗan da suka musulunta ke hange su razana.
Hali Rayya mai gurmi ya yi wannan tunanin wurin da yake cewa:
Jagora: Ga ni ina kiɗi cikin mata
:Matan aure suna kallona
:Ka san mai kiɗi in naz zo
:Ni, ba ta da lalama sai kamtsa.
(Waƙar Wanakiri Dodon Kwanya).

Da wuya a yi kiɗi ba a hautsina maza da mata ba, don haka duk wani
makaɗin da ke tunanin makomarsa ya san ya saɓi Allah. Wannan ke sa, wasu na
bayan fage ke sa bakinsu cikin sha’anin kiɗa su furta miyagun kalamai har ya
shiga ga kunnen makaɗa su razana. Yaro Hore mai kiɗin noma na cewa:

Jagora: An ce Yaro ya nakkashe
:An ce zunubin waƙa garan
:To! In zunubin waƙa garan
Yara: Ga wani can zunubin mata garai
Sanƙira: Zunubinai ya hi naka Yaro!
Gindi: Aiki yai mai daɗi ƙwarai
:Gungaman noma ɗan Bala
Babu wai, mawaƙa na sane da irin kallon hadarin kaji da al’umma ke yi
musu don haka suke son su ga sun bar lalurar kiɗa da ransu.


DANGANE KI'DA DA TUBA


Hausawa na cewa, abin da duk ke gidan sarki yana cikin kasuwa. Yadda duk
mutane ke kallo makaɗa haka makaɗa ke kallon kiɗa. Domin kuɓuta daga tarkon
lalura, za a ji makaɗan na begen barin kiɗa a zantukansu. Gambo Fagada na cewa:

Jagora: In nit tuna da ɓarayi
:Waɗanda nam mutu
:In ji awa in bar kiɗin ga.

Makaɗa ɗan’anace na jan wannan batu a bakandamiyarsa ta Shago yana
faɗar:

Jagora: Wata rana ka iske
:Ba mu kiɗin ga
:Au walau mun mace
:Walau tsohewa

Wasu lokuta sukan fito ƙarara su nuna buƙatarsu ga tuba tun mutuwa ba ta
riske su da ganga ba. Dubi faɗar Gambo:

Jagora: San da nay yi nuhin
:Hajji mijin Kulu
:Na yi nuhin in tuba dac can

Da yake abubuwan da suka wakana, suka wakana bai tuba ba can, sai ya
dawo gida Allah Ya nufe shi da tuba. Lallai Narambaɗa ya furta niyyarsa ta tuba
ɓato-ɓato a waƙar Sardaunan Isa, da yake cewa:

Jagora: Fatata ka yi Sarki Isa
:In yi ma waƙa
:Kowa shi jiya
Yara: Yannan in yada kiɗi
:In tuba
Gindi: Na riƙa ka da girma
:Abdu ƙanen mai daga
:Kan da mu san kowa
:Kai mun ka sani Sardauna


TUNA BAYA


Hausawa na cewa, in ana cin ɓorai a daina tonon cikinsa. Don haka gyartai
ya ce, a bar tuna baya da ya ci sarauta. Adon tahiya waiwaye. Makaɗa sukan yi
waiwaye ga asalinsu na iyayensu idan ba gadon kiɗa suka yi ba. Idan makaɗi ya
tuna baya, ya hangi wurin da aka sa gaba, sai ya karaya, ya yi fatar zama wani abu
ba makaɗi ba. Marigayi Garba Maitandu na cewa:

Jagora: Kiɗin ga nas soma
:Rabbana ka sa duka
:In mai she shi waƙe
:Ina begen Mamman na Dije
Yara: Zucciyata ta koma inda Mustafa
:Turu sai in aje shi
Gindi: Mun bi cikin dajin Kwale
:Garba mun ishe kura na ta wasa.

Tuna bayan da Maitandu ke yi a nan shi ne, ya san gidan karatu aka haife
shi, ga al’adar gidan karatu kuwa yabon Annabi Muhammadu (SAW) shi ne
madararsu. Da Allah Ya dubi Maitandu da idon rahama ya ƙaddare shi da tuba,
kuma ya tuba yana kan gadon gidansu malanta. Allah Ya yafe masa. Irin wannan
tuna baya Alhaji Gambo Fagada ya yi shi da ya ga ana dubansa da gefen ido na
zamansa makaɗi ya ce:

Jagora: Ko gidan giya nike
:ɗan Liman za a ce mini
:Jikan Liman za a ce min
:Don Liman yah haifi Gambo
:Ka ga bai ci amanar mai kiɗi ba
:Don ko ya aika ni Borno
:Shekarata goma sha huɗu
:Sha huɗu ko nar ratci sittin
:Yau ga ni ina yawo da ganga

Tunawa da Gambo ya yi na cewa, ya ratsi hizo sittin na Alƙur’ani, ga shi
ɗan Liman, jikan Liman, kuma rungume da ganga, abin takaici ne. yadda aka
kwakkwahe ɗiyan waƙar daga ƙarshe, akwai alamun nadama ga kasancewa
makaɗi wanda ke nuna ana kyarkyarar tuba. Haka kuma, aka yi, Allah Ya ƙaddare
shi da tuba, 2008.

ME KE HADDASA TUBAR MAKA'DI?


Ga ‘yan abubuwan da muka tsinta daga ɗiyan waƙoƙinsu za mu iya mu yi
hasashen tubar makaɗi a fagen waƙa. Kaɗan daga cikin fitattun makaɗan da suka
tuba akwai:
i. Makaɗa Abubukar Akwara Sabon Birni (1876 – 1962) ya tuba da
kiɗa 1945 bayan ya dawo da aikin Hajji. An ce, ya tarar da an tuɓe
sarkin da yake yi wa kiɗa Sarkin Gobir Shawai. Ya koma waƙoƙin
madahu.
ii. Makaɗa Muhammadu Inyaga Argungu ya tuba da kiɗa a shekarar
1975 bayan ya dawo daga aikin Hajji. Shi ne makaɗin Sarkin Kabi
Muhammadu Mera 1959 – 1996.
iii. Makaɗa Jibril ɗan Dodo Mai Tabshi ya rabu da kiɗin taushi ya koma
makaranta ya zama babban malami.
iɓ. Alhaji Muhammadu na Jankiɗi ya tuba da kiɗin taushi ya koma
makaranta ya zama babban malami a garin Gusau.
ɓ. Makaɗa Manu ɗakin Gari (Ala Suddan) ya tuba da kiɗa ya kama
salati yanzu ya tsufa ƙwarai.
ɓi. Hajiya ‘Yarkana Sakkwato, ta tuba kuma ta ce wani mafarki ta yi ba
ta gaya wa kowa, don haka ta dai tuba (2009).
ɓii. Garba ɗanwasa Gummi Makaɗin Tauri, ya tuba da waƙa, shekarar da
aka kafa shari’ar musulunci Zamfara, ya rasu shekarar.
ɓiii. Alhaji Muhammadu Gambo Fagada mai waƙar ɓarayi ya tuba da kiɗi
shekarar 2008.
iɗ. Makaɗa Garba Maitandu Shinkafi ya tuba da waƙa, ya koma
makaranta. Ya zama babban malami a birnin Kano gabanin ya rasu.
Ya rasu Gusau, an binne shi a Shinkafi.
ɗ. Amadu Doka ya tuba shekarar 2011 a hirar da aka yi da shi Asabar,
11-11-2011 a ɓ.O.A. (Muryar Amurka) ya ce, saboda wa’azin da ake
yi ya ji ya tuba, yanzu yana nan yana Sarauta a Jahar Kaduna.

Idan muka nazarci waɗannan makaɗa goma (10) da dalilin tubarsu da
abubuwan da suka biyo baya ga tubarsu, za mu iya hasashen dalilin da ke sa
makaɗa tuba ga lalurar waƙa kamar haka:

i. Aikin Hajji: Al’adar musulman ƙasar Hausa ce, da duk suka ci nasarar
zuwa Hajji lafiya akan tuba ga kowane aikin da addini ya zarga kamar
dambe da kokuwa da kiɗa da sauran wasanni.
ii. Shauƙin komawa makaranta a yi karatu na daga ciki. Da ma makaɗa
haziƙai ne, sun ɓata basirarsu a fagen sharholiya. Da sun tuba sai su
kama karatu har su kai ga zama shaihunan malamai.
iii. Tsufa na daga cikin mafarin tuba. Za a kai ga shekarun da basira ke
rufewa, murya ta kasa, gaɓoɓi su nemi a rage musu kaya. Daga nan
sai a tuba, irin yadda ta auku ga Alhaji Musa ɗanƙwairo, Maradun.
iɓ. Rasuwar jagoran ƙungiya na sa yaransa su dangane kiɗa su tuba,
musamman idan suna da kyakkyawar hulɗa kuma suna da masaniyar
ya taɓa taya musu tuba gabanin ya mutu. Wannan ce ta faru ga yaran
Ibrahim Narambaɗa, hatta da Maisa’a da ya raya ƙungiyar da baya ya
tuba.
ɓ. Mutuwar uban gidan mawaƙi wani mafarin tubar uban kiɗansa ne. an
ce, da Sarkin Kabin Argungu Sama ya rasu, Jada ɗantanoma ya tuba
da kiɗa, ya koma Kamba ya rasu.
ɓi. Yi wa uban gidansa marabus daga gadon da yake bisa, na sa uban
kiɗansa ya tuba da kiɗa. Makaɗa Abubakar Akwara, bayan ya dawo
Hajji ya tarar da an tuɓe Sarkinsa Sarkin Gobir Shawai, sai ya tuba.
ɓii. Wayewar kai irin ta addini na sa makaɗa tuba, musamman waɗanda
babu gehen da tawilin wani nassi zai kare tuntuɓen harshensu. Ina
ganin a yau, babu sauran makiɗa Sata da Caca da Kwartanci da Giya
da Bashirwa da Shawai, ɗan abin da ya ɗan rage shi ne kiɗin tauri da
bori. Tubar Alhaji Muhammadu Gambo Fagada na iya shigowa a
wannan rukunin.
Bisa wannan bincike za mu ce, lalurar waƙa babba ce a kan mawaƙan Hausa
musulmai musamman idan aka kalli dalilan shigansu kiɗa da dalilan da ya sa suka
tuba.

SAKAMAKON BINCIKE


Babu al’ummar da ba ta yi jahilliyar irin nata zamani ba gabanin kanta ya
waye ta shiga sahun wayewar ƙarninta. Larabawa sun yi irin wannan zamani, ya
wuce, sun taskace adabinsu har yanzu ba a ƙoshi da shi ba. Turawa sun yi irin tasu
ta wuce, adabin da suka taskace su ne suke kai ƙasashen da suka rena a matsayin
karatun boko. Sinawa da suka taskace nasu, ya zama wata ɗaukaka gare su a yau,
musamman a fannin kiwon lafiya da kasuwanci. Babu shakka guguwar jaddada
addinin Musulunci, da tsarkake zukata, da ƙasa, da al’adun mutane, da wuya ta bar
itaciyar kiɗa da wani sansami mai amfani a jikinta. Tsofaffin makaɗa sun rasu,
ƙungiyoyinsu sun mutu, yaransu da suka rage sun tsufa, masu masƙi ga jiki sun
tuba, sauran da suka rage yau ‘yan kame-kame ne kawai. Sabon salo na kaɗekaɗen
zamani da ya shigo mu, bushaƙin iska ne, haka zai mutu kamar mutuwar
adabin kasuwar Kano. Babban aikin da ke gaban duk wani manazarci da masani a
fannin Hausa shi ne, ƙoƙarin taskace waƙoƙin bakanmu, ta fuskar rubuta su, da
tace su a fayafan radiyo, da nazarinsu, a kundace su, a wallafa su a bar wa na baya
kayan nazari kamar yadda sauran al’ummomin duniya suka yi. In ba a yi haka ba,
akwai alamar salwantar karuruwan harshenmu da kalmominmu na fannu, da
mawaƙan suka adana. Lokaci ya yi kusan ƙurewa, amma ba a makara ba, don rana
ba ta faɗi ba. To! Himma ba ta ga raggo.


NA'DEWA

Ka da tubar makaɗi ta ba ka mamaki komai shahararsa a waƙa, ka binciki
dalilin shigansa cikin kiɗa da dalilin tubarsa. A koyaushe makaɗan da suka gaji
kiɗa, idan suka sami damar sauke faralin Hajji ba su son su ƙara wasu manyan
kaya, don haka sai tuba. Wasu kuwa shaƙuwarsu da addini da son karatu ke
gaggautar da tubarsu. A wajen wasu, mutuwar uban gida ko saukarsa daga karagar
da yake bisa, na sa su sauke tare da shi. Abin da na ɗan gano a wannan bincike shi
ne, kiɗa bai sake cin wata kasuwa mai ma’ana ba tun bayan bayyanar hasken
addinin Musulunci a ƙasar Hausa. Haka kuma, babu mai wata sana’ar da bai son a
gaje shi ko ya mutu a kanta kamar makaɗa. Matuƙar Bahaushe bai gaji kiɗa ba, ba
ya son a jingina mahaifansa da kiɗa, shi da kansa ke tsarkake su kamar yadda
muka ga misalai daki-daki a bakin makaɗa.

MANAZARTA


Auta, A. L. 1988. “Gudummuwar Waƙoƙin Makaɗan Baka Dangane da Adana
Tarihi”, kundin digirin MA, Kano: Jami’ar Bayero.
Bunza, A. M. 2009. Narambaɗa. Wallafar IBRASH, Lagos.
Bunza, A. M. 2011. “Rashin sani ya fi Dare Duhu” muƙala. Sashen Nazarin
Harsunan Nijeriya. Katsina: Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua.
ɗakingari, H. M. 2010. “Gudummuwar Mata a Adabin Baka: (Tsokci a kan
Waƙoƙin Baka na Mata a Jihohin Sakkwato da Kabi da
Zamfara)”, kundin digirin PhD, Sakkwato: Jami’ar Usmanu
ɗanfodiyo.
Gusau, S. M. 2009. “Waiwaye a kan tarihin rayuwar Muhammadu Gambo na Kulu
Makaɗin ɓarayi”, muƙala, Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya,
Sakkwato: Jami’ar Usmanu ɗanfodiyo.
Gusau, S. M. 2005. Makaɗa da Mawaƙan Hausa. Kano: Benchmark Publishers
Limited.
Gusau, S. M. 2008. Waƙoƙin Baka a ƙasar Hausa: Yanaye-yanayensu da
Sigoginsu. Kano: Benchmark Publishers Limited.
Ibrahim, M. S. 1982. “Dangantakar Al’ada da Addini: Tasirin Musulunci a kan
Rayuwar Hausawa ta Gargajiya”, kundin digirin MA, Kano:
Jami’ar Bayero.
Tukur, T. 1984. “Mawaƙa da Matsayinsu a Al’umma”, cikin Studies in Hausa
Language Literature and Culture, The First International Hausa
Conference. July, 1978. Kano: Jami’ar Bayero.
Umaru, G. 1986. “Mamman Yaro Hore da Waƙoƙinsa”, kundin digirin BA,
Sakkwato: Jami’ar Usmanu ɗanfodiyo.
Zurmi, M. A. 1986. “Rayuwar Alhaji Kassu Zurmi da Waƙoƙinsa”, kundin digirin
BA, Sakkwato: Jami’ar Usmanu ɗanfodiyo.


www.amsoshi.com

Post a Comment

2 Comments

ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.