Citation: Baba Mohammed Shehu & Dahiru Yalwa Mohammed (2017). Surkullen ‘Tsari’ A Rayuwar Bahaushe: Nazarin Sukullen Kariya A Yankin Guddiri. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 5. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
SURKULLEN
‘TSARI’ A RAYUWAR BAHAUSHE: NAZARIN SUKULLEN KARIYA A YANKIN GUDDIRI
Na
Baba
Mohammed Shehu
Da
Ɗahiru
Yalwa Mohammed
TSAKURE
Masana sun kalli Hausa ta fuska biyu wato Hausar
Gabas da ta Yamma. Yankin Guddiri yana cikin rukunin Hausar Gabas. Shi kuma
surkulle wasu tarin kalmomi ne da akan furta masu wuyar haddacewa, a inda akan
yi hargitsa ballen kalmomi da ke da surkin harsuna daban – daban domin neman
kariya ko magani ko wata biyan buƙata.Wannan takarda ta yi ƙoƙarin fito da ire-iren surkulle
na neman kariya da Hausawan yankin Guddiri suke amfani da su. Takardar ta fito
da ire-iren surkulle na neman tsari da suka haɗa da na mutuwa da na takaba da
na zaman makoki da sauransu.
1.0. GABATARWA
Masana da manazarta na yi wa al’ada kallo ta fuska uku wato fuskar furuci
ko ambato da baka (faɗar baki) ko aiwatarwa da gaɓoɓi da kuma fuskar ƙudurtawa a zuciya (Bunza 2006). Wannan takarda za ta yi ƙoƙarin fito da ire-iren surkulle waɗanda suka shafi
mutuwa da takaba da tattalin lahira da zaman makoki da kuma al’amarin da ya
shafi sha’anin fatalwa a yankin Guddiri na ƙasar Hausa.
1.1 MA’ANAR SURKULLE
Bunza (2006) ya yi fashin baƙin surkulle inda ya nuna cewa, asalin
kalmar ta Hausa ce wadda take da tushe guda biyu ‘sur’ da ‘kulle’. Tushen ‘sur
ya yi daidai da tushen surru, wanda a ganin wasu, surkulle kan ɗauki
ma’anar surutu. Kuma gaɓoɓin
‘kulle’, wanda suka yi daidai da ƙulli
na maganin gargajiya da ake yi don warkar da ciwo.
Haka kuma Adamu (1994) ya
bayyana surkulle da cewa: ‘Surkulle wasu jerin maganganu ne a sassarƙe da ake ƙirƙirar su cikin Hausa da Larabci. Akan
cukuɗa a
furta da nufin bayyyana wasu abubuwan mamaki don cim ma biyan buƙata.
Shehu (2013:22) ya bayyana
maganar kalmar surkulle da cewa:
‘Surkulle kitsa wasu kalmomi
ne
ko maganganu (da fatar baki) da ake
surka kalmomin Larabci da Hausa
cikin kalami na yanki-faɗi domin
aiwatar da wata biyan buƙata’
Shi kuma Almajir (2009) ya kalli surkulle ta fuskar yanaye-yanayensa tare
da nuna muhimmancinsa ga rayuwar Hausawa. Daga ciki, ya bayyana nau’o’in
surkulle tare da fito da masu yinsa.
Binciken Shehu(2002: 14) ya bayyana cewa, asalin surkulle ya samu ne a
sakamakon cuɗanyar Hausawa da Fulani a ƙasar Hausa. Wato a wannan ra’ayi, ana
ganin kamar surkulle ya samo asali ne daga Fulani.
A dangane da bayanan da suka
gabata, surkulle shi ne ire-iren lafuza da akan furta da fatar baki waɗanda
sau tari ba su da wata ma’ana; akan surka harsuna daban-daban domin neman biyan
wata bukata.
An gudanar da wannan bincike
ne a wurare daban-daban na yankin Guddiri ta ƙasar
Hausa da suka haɗa da : Garin Azare da
Madara cikin Ƙaramar Hukumar
Katagum. Sannan an ziyarci garuruwan Beli da Ganuwa da ke Ƙaramar Hukumar Shira. Har ila yau, an
ziyarci garuruwan Dambam a ƙaramar
Hukumar Dambam da Zadawa a ƙaramar
hukumar Misau da kuma Ariri a ƙaramar
hukumar Zaki dukkansu a cikin Jihar Bauci.
Yayin gudanar da binciken,
an yi amfani da hanyar hira ta baki da baki a tsakanin mutane. A tattare da haka, an zanta da adadin mutane da yawansu
ya kai goma sha biyar (15) maza goma (10) mata biyar (5) domin samun sahihan
bayanai. Duk da cewa maza ne suka fi yawa, amma an fi samun cikakkun bayanai
wurin mata. Wannan na nuna cewa, a yankin Guddiri mata sun fi yin surkulle a
wannan fuska ta rayuwa.
1.2 MATSAYIN SURKULLE A YAU
Surkulle daɗaɗɗiyar al’ada ce wadda
a da al’ummar Hausawa suke rungume da ita. Haka kuma Hausawa a mafi yawan
lokaci suna tafiyar da al’amuran rayuwarsu ne ta hanyar amfani da surkulle.
Idan aka dubi yadda Bahaushe yake tunkarar abin da ya shafi kariya da neman
biyan bukatun rayuwa, sai a tarar da surkulle yake tinƙaho. Wato da surkulle ake warware matsaloli da suka shafi
taɓin hankali ko daidaitawa tsakanin aljanu da marar lafiya
ko maita ko kuma matsaloli da suka shafi sana’o’i irin su : Bokanci ko
Wanzanci ko Tsibbu da sauransu Hausawa na tafiyar da su ne ta hanyar surkulle
(Bunza 2006 :261).
Al’adar surkulle a yau abu ne da ke (kan gaba wajen) samun koma - baya
a tsakanin al’ummar Hausawa. Wannan kuwa ya faru ne sakamakon haɗuwar Hausawa da baƙin al’ummomi. Saboda kasancewar Hausawa al’umma ce da take
da matuƙar son jama’a, ya janyo takan
rungumi duk wata al’ummar da ta yi alaƙa da ita tattare da
al’adunta, yadda hakan ya janyo ita kuma take ƙoƙarin rasa wasu daga cikin muhimman
al’adunta. a sanadiyyar irin haka, ya
sa a yau mafi yawan matasa a tsakanin al’ummar Hausawa ba su san wannan al’ada
ta surkulle ba.
Wani dalili kuma da ya sa surkulle ke ci gaba da samun koma-baya musamman ɓangaren maza shi ne
tasirin addini da kuma zuwan ilmin karatu da rubutu na boko. Waɗannan
al’amura sun taimaka wajen daƙushewar
al’adar surkulle.
1.3 TARIHIN ƘASAR
GUDDIRI
Masan sun kawo ra’ayoyi
dangane da tarihin ƙasar
Guddiri. Hamma, (1981:9-10) a ƙoƙarin bayyana asalin kalmar Guddiri, ya
yi nuni da cewa kalmar asalinta daga harshen Fulfulde aka samo ta, wato ‘Leddi
ngudduri’ manufa ‘yar ƙaramar
ƙasa ko ƙasa
da aka yanke. A nan, ke nan daga wannan manufar ne aka samo sunan yankin
‘Guddiri’. Haka kuma Hamma (1981), ya ƙara
bayyana da cewa lokacin da malam Ibrahim Zaki ya je karɓar
tuta wurin Shehu Usman Ɗanfodiyo,
domin a nuna masa iyakar masarautarsa sai Shehu ya ce masa duk da cewa dukkan
yankunan nasa ne ( na Shehu) ya yanke masa iyaka, wato sai Shehun ya ce masa,’Ƙasarka ita ce ‘yar Gundur’ ko ‘Yahu
Leddi ma ngunduri’ manufa, na ba ka ‘yar ƙaramar
masarauta ko yankakkiyar ƙasa.
Lokacin da mal Ibrahim Zaki ya ga an nuna iyaka ta masarautarsa sai kuma ya
bukaci Shehu ya yi masa addo’a saboda ƙasarsa
ta samu yawan al’ummar musukmi. Wannan shi ya haifar da samuwar ƙasar Guddiri.
Ƙasar
Guddiri ɗaya
ce daga cikin yankunan ƙasar
Hausa wadda take da daɗaɗɗen
tarihi. Masana da dama sun bayyana ra’ayoyinsu dangane da kalmar Guddiri. Azare
(2017: 26) da ya ambato Bello (1992) ya bayyana cewa ƙasar Guddiri ƙasa ce ta Hausa wadda take arewa maso
gabashin Nijeriya da ake samun ta a tsakanin jihohin Bauchi ,Yobe da kuma
Jigawa. A bisa ga wannan ra’ayi na Bello (1992), an bayyana cewa ƙasar Guddiri ta yi iyaka da ƙasar Bauchi .
Haka kuma masana sun bayyana
cibiyar ƙasar Guddiri ita ce Katagum. Sauran
garuruwan wannan ƙasar
sun haɗa
da: Azare da Misau da Shira da Gamawa da Yayu da Jama’are da Saɗe da
Dambam da Lanzai, dukkansu suna arewacin jihar Bauchi ta yanzu suke. Sannan
akwai garuruwan Kiyawa da Birnin Kudu da Gwaram , a jihar Jigawa, Azare
(2017:7-8).
Ƙasar Guddiri, ƙasa ce mai rairayi, musamman ma ta arewacin yankin.
Sannan, tana da koguna waɗanda suka ratsa ta ƙuryar arewamaso gabas ;
waɗanda suka haɗu da tafkin Chadi ( Lake Chad). Ibinola,(2009 : 3) .
Bisa ga bayanai da suka gabata, za mu iya bayyana cewa ƙasar Guddiri ƙasa ce mai daɗaɗɗen
wadda masana suka gudanar da bincike ta fuskoki daban-daban.
2.0. SURKULLEN TSARI A RAYUWAR
SAURAN JAMA’A
Yanzu bari mu duba ire-iren surkulle da ba su dangaci magani ba. Wato waɗanda suka shafi
al’umma baki ɗaya, ba lallai sai bokaye ko ‘yan bori ko matsibbata ba.
Surkulle ne da kowa na iya yin su.
A ƙarƙashin wannan
rukuni, za a yi nazarin surkulle, da suka shafi mutuwa da takaba da tattalin
lahira da zaman makoki da kuma na fatalwa da kuma neman tsari daga ire-iren
mutanen da ake ganin za su iya cutarwa.
Surkulle ya yi tasiri kan waɗannan al’amura da aka ambata a yankin Guddiri. Waɗannan surkulle suna
nan da dama kuma kala- kala a yankin Guddiri sai dai ya danganta daga wuri zuwa
wuri.
2.1. SURKULLE NA JIN LABARIN WANI YA
MUTU
Subuhaaka wa innii mayyitu
In lookacii yaa arzama
Sarikatun wa sarikaatu mautu
Atiidu da Raƙiibu matambayaa
Ku yii masa tambaya da sauƙii
Baa da raazanarwaa ba.
Wannan surkulle ana yin sa
ne a yayin da aka bayyana wa mutun cewa wani ya mutu wato in aka faɗa wa
mutum ya zo jana’izar wani ya mutu, sai wanda aka gayyata ya yi wannan
surkulle.
Fa'’idar da ke tattare da
wannan surkulle ita ce, furta surkullen da aka ambata a sama yana hana mutum ɗimaucewa
idan ya ji bayanin mutuwar.
Wani abin lura a wannan
surkulle shi ne za a ga yana da tasirin harshen Larabci a cikinsa. A tattare da
haka akwai subuhaaka da ‘wa’ da ‘innii’ da kuma ‘mayyitu’. An saƙala gaɓoɓi
biyu a ƙarƙashin
kalmar ‘subuhakaa’ don a kauce wa faɗin
‘subuhaanaka’ ne ‘wa’ na nufin ‘da’, ‘innii’ ‘ni’ ake nufi, sannan ‘mayyitu’
kuma an shafe baƙin ƙarshe na asalin kalmar mayyitun ta
larabci amma dai duka mai mutuwa ko mamaci ake nufi. Haka a jimlar ‘in lookacii
yaa arzama’ ana nufin idan lokacin mutuwa ya zo. Kalmar ‘sarikaatu’ tana nufin ɗanɗana
zafin mutuwa. A dunƙule,
amfanin surkullen shi ne yana nuna yi wa wanda aka ji labarin ya mutu addu’ a
ne da cewa matambayan kabari su yi masa (ga shi mamaci) tambaya da sauƙi.
2.2.
SURKULLE NA SHIGA GIDAN DA AKA YI MUTUWA
Ku shaa, ku shaa
ku shaa ruwanku,
wata raanaa naamu
zaa a shaa.
Cikin wannan surkulle, a
jimlar farko ta ‘ku shaa, ku shaa’ a ganin masu binciken, jimlar tana nufin
mamacin da ma sauran waɗanda suka mutu a wannan
gida, su kasance cikin halin jin daɗi,
‘ruwaa’ da aka ambata ana nufin ruwan alkausara ko kuma zaman jin daɗi a
kabari.
Haka kuma kamar yadda
majiyarmu ta bayyana, ambaton ‘wata rana namu za a sha’ yana nufin shi ma wanda
aka gayyata, wata rana shi ne zai mutu, mutane su yi gayyar tasa mutuwar.
2.3.
SURKULLE NA WANKAN GAWA
Bismillaahi allaahumma
suturhu, wa rufauhuu
fii ƙabarin ƙabaraata
har abadaa, bari mu
wankee shi, kafin a wankee
mu,
ba mu san ranar kauraa ba,
ba mu san wanda zai wankee
mu ba.
A dai bisa yadda muka zanta
da mutanen da muka yi hira da su, amfanin surkullen shi ne ana ƙoƙari
ne a tsabtace gawar ne daga irin zunubin da ta ɗauka,
a zamanta na duniya.
Harshen Larabci ya yi tasiri
matuƙa a cikin wannan surkulle, musamman idan
an yi la’akari da kalmomin ‘Bismillahi’ da ‘allahumma’ da ‘fii’ da kuma
‘kabari’. Waɗannan kalmomi an aro su ne daga harshen
Larabci kai tsaye wanda bisa ma’ana suna nufin farawa da sunan Allah, da ‘ya
Allah’ da ‘cikin’ da kuma ‘kabari.’ Sannan kalmomin: ‘suturhu da rufauhu’
kalmomi ne da aka baddala su ta hanyar yi musu ɗafin
ƙeya na ‘hu’ a ƙarshensu. Kalmar ‘suturhu’ tana nufin a
yi wa mamaci sutura, wato a sanya shi cikin likkafani. Ita kuma kalmar rufauhu
a nan tana nufin a rufa masa (mamaci) asiri manufa idan an sanya masa likaffani
a rufe tsiraicinsa ko kuma neman ya samu tsira a lahira da kuma a kwanciyar da
zai yi a kabarinsa. Haka kuma a jimlar ‘ba mu san raanar ƙauraa ba’ an yi amfani da kalmar ƙaura wadda take nufin sake wurin zama,
wato daga duniya zuwa lahira. Abin lura a nan dai shi ne wannan surkulle addu’a
ce ake yi wa mamaci ya samu tsira da zaman jin daɗi a
kabari bayan ya mutu. Abin da za a iya fahinta a wannan surkulle shi ne samuwar
tasirin harshen Larabci. Kalmomin ‘Bismillaahi da Allahumma da kuma Suturhu’
duka kalmomi ne na larabci aka surka da harshen Hausa.
2.4. SURKULLE NA FITAR DA GAWA DAGA
GIDA
Wani nau’i na surkulle da ake samu a yankin Guddiri shi ne na fita da gawa
daga gida bayan an gama shirya ta. Surkullen da ake yi kuma shi ne :
Kai Duwa, kai Duwaa-Duwa,
Baa ni wuriina in wuce,
wuceewaa,
Yaushe ka san ni, yau ne ka san ni
Ka san sunaana? Naas an ka
nan
San ‘yaa’ yanka. Inaa su
duwai,
Inaa su Musaa da Isa ya
jabbakaari,
Yaa Rasuullahi shaafa kainaa
Shafaa’atii, yii masa ceetoo
muu
Maa mu samuu’.
A wannan surkulle na fitar
da gawa daga gida zuwa yi mata jana’iza (Sallah) zuwa a kai ta kabari, akwai
wata hikima ko dabara mai kama da hira tsakanin mutum biyu. A matakin farko na
surkullen ana magana ta hanyar ambaton suna ‘kai Duwa kai Duwa’. Duwa ana nufin
wai suna ne na mala’ika. Ba ni wuriinaa in wuce’ wai da zarar an faɗi
haka sai kuma mai yin surkulle ya sake cewa, wuceewaa, yaushe ka san ni, yau ne
ka san ni ka san sunana?,’ sai kuma a sake cewa naa san ka naa san ‘ya’yanka,
inaa su Duwai ina su Musa da Isa. Wato ana nuna an san Duwa da ‘ya’yansa da ma
sauran manyan mutane annabawa. Daga ƙarshe
sai a ƙarasa da ambaton ‘yaa Rasuulillahi
shaafa kainaa shafaa’afii, yii masa ceetoo, muu maa mu samuu.
A wannan surkulle za a iya
lura da cewa yana da tasirin Larabci a cikinsa; a inda aka yi amfani da
kalmomin ‘yaa da ‘rasuulallahi’ da kuma shafaa’afii dukkansu na larabci ne.
rasuulallahi na nufin manzon Allah. ‘shafaa’a fii n’ na nufin ceto a cikin – wato
ana neman manzon Allah ya yi ceto, wanda shi ma mai addu’ar zai samu shiga
ciki.
2.5. SURKULLE NA DUBA GAWA DON GUDUN
KADA TA YI FATALWA
A yankin Guddiri da ma sauran yankuna na ƙasar Hausa, sun yi imani da cewa, idan mutum ya mutu zai
iya yin fatalwa. Wato bayan an binne shi zai riƙa fitowa daga kabarinsa yana dawowa duniya wurin mutanen
da suka san shi. Kuma Bahaushe yana tsoron irin wannan dawowar wato fatalwa. Don
haka idan mutum ya mutu sai a riƙa
yin wannan addu’ar.
A uuzu, A uuzu bil kamata.
Rubuuwata hai’aata bika,
Wa’alayya harmun harama.
Wannan nau’i na surkulle
yana da amfani ta fuskar samun kariya daga gamuwa da fatalwa kowace iri, ba sai
lallai ta ɗan’uwan mamaci ba. A wannan surkulle za a ga akwai tasirin Larabci sosai a
cikinsa. Kalmomin Larabcin a cikinsa sun haɗa da: ‘A’ uuzu da
‘bil’ da ‘bika’ da ‘wa’ da kuma ‘alayya’. A’uuzu na nufin da, kalmar ‘alayya’
na nufin a gare ni. Sauran kalmomin : ‘rubuuwata’ da ‘haiaata’ da kuma
‘harmun’ ba su da wata cikakkiyar manufa da za a iya bayyana su da ita. An dai
yi wani abu ne mai kama da hargitsi-ballen surka larabci da Hausa a cikinsu.
2.6
SURKULLE DON KADA MIJI KO MATA TA YI FATALWA
Tarnakin tarmaaka, dabalnalin
Dabaibayin bakin sa, taf ka ba ruwaa,
Ka yi kwance, kwanciyar
barcin har abada
Ba da taasoowaa ba.
Wannan surkulle da ya gabata
yana da amfani ga miji ne ko macen da mijinta ya rasu ya bar ta. Amfanin wannan
surkullen shi ne a yayin da miji ko mata ta yi wannan surkulle, mijin ko matar
ba za ta dinga ganin fatalwar mijin nata ba.
Haka kuma wani abin lura shi
ne wannan surkulle ma yana da tasirin addini a cikinsa. Za a ga inda aka fara
da yin ‘ bismillahi’ sannan akwai kalmomin ‘bi’ da ‘a’alaa’ wato ma’anar wannan
shi ne farawa da sunnan maɗaukaki sarki Allah.
2.7. SURKULLE NA ZAMAN MAKOKI
Zaman makoki shi ne zaman karɓan gaisuwa da dangin mamaci ke yi na tsawon kwana uku. A
bisa al’adar Bahaushe duk wanda ya mutu akan yi zama na wuni uku. Haka kuma
abin yake a yankin Guddiri ma. Ana fara zaman daga ranar da aka yi jana’izar
mamaci.
surkulle da ake yi shi ne:
Jingim maa jingim
Fankam kara fankam
Allah shi kaɗai yake
A gare shi ba wani
Sai shi.
Wannan surkulle ne da ake yi
a daidai lokacin da aka fara zaman makoki (wato karɓar
gaisuwa). A bisa ga bincikenmu, wannan surkulle ba shi da wata takamammiyar
fa’ida da ake yi dominta.
Har wa yau, za a ga an
maimaita ambaton kalmomin, ‘jingim’ da kuma ‘fankam’. Kalmar ‘jingim’ tana
nufin yawa, wato taron yawan mutanen da ke zama a wurin karɓar
gaisuwar mutuwa (ta’aziya) ne kalmar ‘fankam’ ita ma ta ƙunshi makusanciyar manufar da kalmar
‘jingim’ wato tana nufin taruwar yawan jama’a ne masu zaman gaisuwa a wurin
zaman makoki.
3.0
IRE-IREN SURKULLE DA SUKA DANGANCI SHA’ANIN TAKABA
A ƙarƙashin
wannan akwai ire-iren surkulle daban-daban kamar haka:
3.1
SURKULLEN SHIGA TAKABA
Takaba wani ko wasu
ayyunannun kwanaki ne da matar da mijinta ya rasu ya bari ke ƙillace kanta ta hanyar zama a gida har
tsawon wata huɗu da kwana goma. Akwai surkulle da mata
ke yi na shiga ka fara takaba kamar haka:-
Bismillahi warkafun,
Bi a’al zugum
Taalikai zugum-zugum
Gidaa da shaiduu, a nan zaa
mu faara takabaa.
Wannan surkulle, yana da
amfani saboda yana yin nuni ne game da shiga takaba da mata ke yi. Haka kuma
amfanin wannan surkulle shi ne neman kariya daga sharrin iskoki a lokacin da
suke yin takaba. A wata fuskar kuma mazauna wannan yanki (na Guddiri) sun bayyana
mana cewa, mai shiga takabar tana yin wannan surkulle ne saboda ta yi saurin
samun mijin aure, bayan ta gama idda.
Wannan surkulle shi ma akwai aron kalmomin Larabci a cikinsa. Wato
ana ayyana shiga takaba ne ta hanyar wannan surkulle. Jimlar ‘bi a’alaa zugum
taalikai zugum-zugum’ na nuna halin juyayin mutuwa ko mutumin da ya mutu ne,
ambaton ‘a naan za mu faara takaba’ yana nuna shiga takaba ne kai tsaye.
3.2.
SURKULLEN WANKAN MAI TAKABA MAKO-MAKO
Wannan binciken ya fahimci
cewa, idan mace ta shiga takaba a yankin Guddiri sau ɗaya
kawai za ta yi wanka a mako, wato ranar Juma’a. Don haka, yayin da aka zo yi
mata wankan ana yin wannan surkulle:
Allaahumma innii waraa ta
janii
Bi ismika tirkaamaa tirkaa.
Da farko,amfanin wannan
surkulle dai shi ne mai takaba za ta samu kariyar isaka. Haka kuma kamar yadda
muka zanta da wani a garin Azare (da ke yankin Guddiri) , an bayyana mana cewa,
a yayin da mace take yin takaba, akwai wani hamami da ke jikinta wanda ke jawo
hankalin iska. Ana ganin karanta wannan surkulle, zai kawar mata da wannan
hamami.
Haka kuma wannan surkulle ya
ƙunshi kalmomin Larabci a cikinsa. Sai
dai kuma kalmar, ‘wara’a’ ta yi kama da ta filatanci mai ma’anar zuwa.
‘Allahumma’ na nufin ya Allah ‘Bi’ na nufin da, ‘ismika’ kuma shi ne ‘sunanka’.
Wato da sunan Allah. Kalmar ‘tirkaa’ ta yi kama da kalma mai ma’ anar
dukiyar gado da aka bari kafin a yi rabon gadon, amma a nan tana nufin hoɓɓasan
yin kwanaki bakwai na wancan, ma’ana dukan kwanakin ake nufi cewa an yi musu
niya guda.
Yayin da aka fara wankan
kuma sai a ce :
Ilaahii zunubi algaya
Akalahuu wal lawaaya
A cikin wannan surkulle za a
iya ganin tasirin harshen Larabci. Misali kalmar ‘ilaahi’ na nufin Ubangijina,
‘zunubi’ na nufin laifuka da aka aikata na haramci ‘akalahuu’ aka cinye, ‘wal’
da, ‘ lawaaya’ kalmomi ne marasa ma’ana cikin wannan surkulle. A nan, a wannan
surkulle ana neman gafara ne da kuɓuta
daga aikata kuskure yayin wancan.
3.3.
SURKULLEN GAMA WANKA
Yayin da aka gama wanka kuma
sai a ce:
Alluhudun hudun
Tafi dum
Wannan surkulle ne da ake yi
bayan an gama wancan takaba. Surkullen ba shi da wata ma’ana. Sai dai kamar
yadda muka zanta da wani malami ya bayyana cewa ana yin surkullen be don kariya
daga sharrin iskoki ka da su yi wa mutum wata illa. Sai dai kalmar ‘dum’ ana nufin kada mai wanka ta ji bugu
‘dum’ na dundu a bayanta. Wato kada aljani ya buge ta kafin fita
daga ban-dakin.
3.4.
SURKULLEN RUFE KOFA DA DARE
Ana yin surkullen kamar
haka:-
Sama lu’un aala lu’un
A’uuzubillahi lu’un
Urtun addaashimii
Mace addaashimaa
A cikin wannan surkulle ma kamar sauran, za a iya ganin da tasirin Larabci
a cikinsa. Misali Kalmar ‘aala’ daga’ala’ take wadda take nufin kan ko ‘bisa’
haka kuma kalmar ‘a’uuzubillaahi’ a nan tana nuna neman tsarin Allah. Sauran
kalmomin kuwa za a ga babu wata ma’ana keɓaɓɓiya za
a dangantata da su.
Har ila yau, wani abin lura kuma shi ne akwai maimaicin kalmar lu’un sau
biyu. A cikin wannan ma akwai nashewar ƙwayar sauti ta
wasalin ‘ii’ta kalmar ‘addashimii’ ta Koma ‘aa’ a kalmar ‘addaashimaa’. Kalmar
da ta kare da ‘ii’ tana nuna jinsin namiji, wadda ta ƙare da dogon wasali ‘aa’ tana nuna jinsin mace wato an yi
amfani da hanyar ƙirar kalma ta kumburi na kalma a
wannan surkulle.
3.5. SURKULLEN SHIGA ƊAKI GA MAI TAKABA
Daga cikin abubuwan da ya shafi takaba a yankin Guddiri sun haɗa da karatun shiga ɗaki na farko
lokacin da takaba ta kama mace, yadda take ambaton wannan surkullen.
Saahuuna maa ‘uuna
Kaucee daga nan
Zan wuce
Abin sha’awa dangane da wannan surkulle shi ne yadda ya kasance Hausa
tsantsa babu surkin Larabci a cikinsa ko kaɗan kalmomin
surkullen yawancinsu ba su da wata tabbatacciyar ma’ana idan ban da kaɗan daga cikinsu. Misali
a kalmar ‘kaucee’ ana nufin sanar da iskokin wannan gida da za a shiga da su ba
da wuri ana so a shiga gidan. Ana ambaton hakan ne domin kada a yi wa iskokin
da ke gidan laifi bisa tsarinsu na zaman gidan.
A kalmomi biyu na farko a
surkullen suna da tsarin gaɓobi iri ɗaya
ne na buɗaɗɗun
gaɓoɓi
masu dogayen wasula a gaɓoɓi
biyu na farkon kowace kalma (daga cikinsu). Kalmomin ‘saahuuna’ da ‘maa’uununa’
kalmomi ne na yabo da girmama iskokin da ke gidan da aka yi mutuwar
3.6.
SURKULLE DA MAI TAKABA TAKE YI KAFIN TA KWANTA A GADO DA DARE
Wannan surkulle ana yin sa
na kamar haka:
Allaahu yaa Allah, yaa
ubangijin
Saamuuna da gaskiyaa laa
isimuka,
Da suunansa yaa ta zanni agafirrunaa
Allah kwantar ha’an arina in
kaa kai
Numfaashiinaa, ka kai ni
muuminaa,
Ka taashee ni saa ilaa.
Wannan surkulle na da tasirin harshen Larabci shi ma. Wato
an yi amfani da aron kalmomin Larabci da dama a cikin wannan surkulle da ya
gabata. Kalmomi ne da yawancinsu suke nuni da mahalicci da kuma tuba a wajen
mahalicci Allah. Manufar kalmomin wannan surkulle suna da alaƙa da abin da surkulle ke nuni da shi
sosai da sosai. Za a ga kalmar ‘yaa’ da Allahi’ da ‘Ubangiji’ da ‘samuuna’ suna
nuna yabon Ubangiji Allah ne. Wani abin kula ko lura kuma shi ne wato sammai
(jam’in kalmar sama). Sannan kalmar ‘agafirrunaa’ na nufin gafara ko yafewar
Ubangiji ne. sai dai an yi nannagen baƙin
‘r’ domin a kauce wa kalmar agfirnaa ta asalin harshen larabci.
Wannan surkulle har wa yau
nuna al’adar nan ta Musulmi mumini da in ya zo kwanciya da dare, irin yadda
yake addu’a da komawa tare da sallamawa zuwa ga Allah. A nan ken an addu’ar
surkullen ta kunshi al’ada da addini ne.
3.7.
SURKULLE NA SHIGA BANDAKI
Wannan surkulle ana yin sa
kamar haka:
Wa auli Rabbuka hattaa
Yaa tattakimu, yaa kai
Baawaa, raanar sakankan
Ceewar; it ace kaala, yaa
Fadaa annabi Muusa yaa
Fadda laabudda baa makwaa.
A wannan surkullen ma kamar
a sauran ne, za a ga an yi aron kalmomin larabci da yawa a cikinsa.Wannan nau’i
na surkulle ana yin sa ne domin neman tsari daga gamuwa da aljani a bandaki.
Kamar yadda ya gabata a wasu
surkullen da aka ambata a baya, wannan surkulle yana da tasirin Larabci. An yi
aron kalmomi Larabci da dama a wannan surkulle. A jimlar ‘wa auli Rabbuka’ ana
nufin alkiyama cewa babu tababa ranar za ta zo.
Mafi yawan waɗanda
aka zanta da su a wannan kasha mata ne. Don haka yawan-yawan surkulle da aka
tattara suka kasance na sha’anin mata. Wannan ya faru ne saboda wannan ɓangare
ya fi mayar da hankali ne kan sha’anin mutuwa musamman kuma an fi mayar da
hankali kan ɓangaren takaba.
3.8.
SURKULLE NA NEMAN TSARI DAGA MUTUMIN DA AKE SHAKKA KAN WANI LAMARI
Wannan karatu na surkulle
kuma ana yin sa kamar haka:
Kutkulan dukulaini karaa
Wa kaalahuu, laulaini karaa
Wa huwabuu bushu’aini karaa
Wa buruuta kasbaini kara
Ayyuu kaana buruuji kasbaini
karaa
Innallaaha kaana aliiman
hakiimaa
Suururu kundi sharri, wahya
subuhaana aaya tamat
A wannan surkulle da ya
gabata, za a ga bisa manufa da fa’ida, yana da alaƙa da dalilin da ya sa ake yin sa. Wato
akwai kalmomin da ke nuni da hakan da suka haɗa
da: ‘dukulaini’ karaa, wa huwabuu, kasbaini da kuma sharri’. Kasancewar
surkullen ya ƙunshi aron kalmomi da
dama daga harshen larabci kusan a dukansa, za a ga waɗannan
kalmomi, kalmar dukulaini na nufin shiga. A kalmar an sarƙafa‘duku’da ‘laini’ sai suka bada
ma’anar shiga tsakanin abu biyu. Kara kuma kalma ce ta Hausa wanda ake nufin
karan ya shiga tsakanin mai surkulle da wanda ake neman tsari daga gare shi.
Kalmomin wada huwabu suna sanar da shi mutum da ba ayarda da shi ba. Sannan
kasbaini na nuna tsakanin, an yi wa wannan ɗafin
goshi ne na ƙasa domin a kauce
ambaton ‘baini’ kai tsaye. Kalmar sharri kuma ma’anata a fili yake ana nufin
sharrin mutumin da ba a yarda da shi ba.
A wannan surkulle za mu ga
ya yi surkin ko ya ƙunshi
kalomomin Hausa da na Larabci waɗanda
ke yi nuni da neman kauce wa sharrin mutumin da ake shakka a kansa ka da ya
cutar.
Wannan binciken ya yi ƙoƙarin
fito da ire-iren surkullen da suka shafi mutuwa a yankin Guddiri na ƙasar Hausa. A inda aka gano cewa,mazauna
wannan yanki na ƙasar
Guddiri, suna amfani da surkulle a lokuta daban-daban a ta fuskar abubuwan da
suka shafi mutuwa.A tattare da haka, takardar ta gano cewa masu amfani da
surkullen, sukan yi ƙoƙarin danganta mafi yawan surkullen da
harshen Larabci.A hannu guda kuma sukan jingina da hakan, su nemi kariya ta
tsarin guje wa shiga wata larura. Wanda a ra’ayin wannan takarda suna son a
sama wa surkullen gurbi ta fuskar addini.
MANAZARTA
Abubakar R. U. (2006). Camfi
da Surkullen masu Bayar da Magunguna a Ƙasar
Hausa. Kundin digiri na ɗaya, Shashen Harsunan
Nigeria, Jami’ar Bayero Kano
Adamu, M. T. (1985). Tarihin
Samuwar Ilmin Tsibbu ga Al-ummar Hausawa. Illmi Cikin Mujallar Nazarin Harshen
adabi da Al’adu na Hausa kundi na Uku wanda cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Bayero Kano ta tsara.
Adamu, M. T. (1998). Asalin
Magungunan Hausawa da ire-irensu, Kano Ɗan
Sarkin Kura publishers ltd.
Adamu, M. T (1990). Siddabaru A Ƙasar Hausa. Kundin
Digiri na Biyu Sashen Harsunan Nijeriya Jami’ar Bayero, Kano.
Abdulƙadir, U. F ( 2009). Tarihin Kafuwar Masarautar Katagum (1807 –
2009) : Kano, Triumph Publishing Company, Nigeria.
Almajir, T. S. (2009).. Surkulle: Yanaye-Yanayensa da Muhimmacinsa ga
rayuwar Hausawa. Cikin Himma Journal of Contemporary Hausa Studies Vol I No. 1 Department of
Nigerian Languages, Umaru Musa ‘Yar’aduwa University, Kastina.
A’ishatu, B .M (2005). Ruƙiyya A Ƙasar
Hausa: Hanyar Warkar da CiwonAljanu.Kundin Digiri na Farko Sashen Harsunan
Nijeriya Jami’ar Bayero, Kano.
Azare, S. A (2O17). Canje-Canje
A Karin Harshen Guddiranci: Nazari A Kan Tsarin Sauti da Tasarifi. Kundin
Digiri na biyu. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.
Bagari, D.M ( 1979). Some
Aspects of Guddiranci. The Guddiri Dialects of Hausa. A paper presented at Symposium
on Chadic Languages.
Bunza, A. M. (2006).
Gadon Feɗe Al’ada
Lagos, Tiwal Nigeria ltd.
C. (1990). Hayaki Fidda na Kogo (Nazarin
Siddabaru da Sihirin Hausawa) Kundin binkice don Digiri na Biyu a Hausa Shashen
Nazarin Harsunan Nigeria, Jami’ar Bayero Kano.
Doguwa, M.S (2002). Surkulle
Karatun Mata: Gudummawarsa ga Adabin Hausa. Kundin Digiri na Biyu, Sashen
Nazarin Harsunan Nijeriya Jami’ar Usumanu Dan Fidiyo, Sokoto.
Hamma,A.S (1981). The Hausa
Spoken in Harɗawa A Compartiɓe
Study. A research project. Department of Languages and Lingujstics. University
of Maiduguri.
Shehu, B.M (2002). Surkullen
Mata Kundin Digirin Farko da aka gabatar a Sashen Nazarin Harsuna da
Kimiyyarsu, Jami’ar Maiduguri.
Shehu, B. M. (2013).
Surkulle cikin Magungunan Gargajiya na Hausawa Kundin Digiri na Biyu Shashen
Nazarin Harsuna da Kimiyyarsu, Jami’ar Maiduguri.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.