Ticker

6/recent/ticker-posts

Tattaunawa Tsakanin Dan Jahamiyya Da Ahlus Sunna

Dan Jahamiyya ya ce: Ayoyi da Hadisan Siffofin Allah dukkansu "Majaz" ne ba Hakika ba.

Ahlus Sunna ya ce: Yaya za mu yi da wadannan Nassoshin Alkur'ani da Sunna da Maganganun Salaf masu yawa da suka zo suke tabbatar ma Allah wadannan Siffofi?

Dan Jahamiyya ya ce: Ai dole a yi Tawilinsu, don a tsarkake Allah daga "Tajsimi" da "Tashbihi".

Ahlus Sunna ya ce: Yanzu kana nufin Zahirin Alkur'ani da Hadisan Annabi (saw) suna nuni ga "Tajsimi" da "Tashbihi", alhali "Tajsimi" da "Tashbihi" kafirci ne, don haka kenan Allah da Manzonsa a Alkur'ani da Sunna sun bayyana mana abin da zahirinsa kafirci ne?

Dan Jahamiyya ya ce: Ai yin magana da "Majaz" Uslubi ne na Fasahar Larabci, wato a yi magana da lafazi amma ba zahirinsa ake nufi ba.

Ahlus Sunna ya ce: To amma sai dai yawan wadannan Nassoshi, da yadda dalalarsu suka zo bisa nau'uka daban-daban, yana tabbatarwa bisa yakini cewa; wadannan Siffofi tabbatattu ne ga Allah Madaukakin Sarki, kuma Annabi (saw) da ya zo da su yana nufin a kudurce zahirinsu.

Yanzu zai yiwu ya zama duka Nassoshin da suka zo, a ce kowane Nassi a cikinsu Allah ba zahirin Nassin yake nufi ba?

Zai yiwu a ce: abin da Allah yake nufi shi ne ra'ayin masu kore wadannan Siffofi ga Allah, sai tawile-tawilen da suka fada su zama su ne gaskiya, su ne abin da Allah yake nufi?

Idan kuwa haka ne to dole a samu wasu abubuwa guda uku munanana a tare da Allah wanda ya fadi Nassoshin ko Annabi (saw) da ya zo da su:

1- Suka cikin ilimin wanda ya fadi wadannan Nassoshi.

2- Suka cikin bayaninsa.

3- Suka cikin Nasiharsa.

Na farko: Wanda ya fadi wadannan Nassoshi imma ya zama ya san cewa; gaskiya shi ne tawile-tawilen masu kore Siffofin, ko kuma bai sani ba. To idan bai sani ba, wannan suka ne cikin iliminsa.

Amma idan kuma ya san cewa: gaskiya ita ce: kore Siffofin, da yin Tawilin Nassoshinsu, to imma ya zama zai iya bayanin hakan wa mutane, ya tsarkake Allah daga "Tashbihi" da "Tajsimi", ko kuma ya zama ba zai iya yin bayanin hakan ba. To idan ba zai iya yin bayani ba, to hakan suka ne a fasaharsa da bayaninsa. Sai ya zama 'Yan Falsafa da 'Yan Jahamiyya da Mu'utazila da yaransu Asha'ira sun fi shi fasaha da iya bayani. Wannan kuwa kowa ya san cewa; maganar banza ce, saboda Annabi (saw) ya fi kowa cikin mutane fasaha da iya bayanin gaskiya da shiriya.

Amma idan kuma yana da ikon yin bayani, amma sai ya ki yin bayani wa mutane, sai ya fada wa mutane sabanin hakika, wato Allah ba shi da wadannan Siffofi, amma ya zo ya ce: Allah yana da fiska, hannaye biyu, yana da ido, yana da kafa, kuma yana sama, yana saukowa sama ta Duniya… to wannan suka ne cikin Nasiharsa, bai zama mai Nasiha ga mutane ba. Alhali kowa ya san Annabi (saw) ya fi kowa cikin mutane Nasiha da son shiriyar mutane. Shi ya sa Allah ya siffanta Manzanninsa da Nasiha da bayani, Allah ya ce:

{وَمَا أَرْسَلْنَا مِنْ رَسُولٍ إِلَّا بِلِسَانِ قَوْمِهِ لِيُبَيِّنَ لَهُمْ} [إبراهيم: 4]

((Ba mu aiko wani Manzo ba face da yaren mutanensa don ya yi musu bayani)).

Kuma ya ce:

{وَأَنْزَلْنَا إِلَيْكَ الذِّكْرَ لِتُبَيِّنَ لِلنَّاسِ مَا نُزِّلَ إِلَيْهِمْ} [النحل: 44]

((Kuma mun saukar maka da "Zikr" don ka yi bayani wa mutane abin da aka saukar gare su)).

Kuma Sahabbai sun yi shaidan cewa lallai Annabi (saw) ya isar da dukkan Manzanci, ya yi musu bayanin komai na Shiriya. Sun tabbatar ya yi musu Nasiha bai ha'ince su ya boye wani abu ba. Babu wani alheri face ya yi musu bayaninsa, babu wani sharri face ya tsoratar da su game da shi.

To idan tabbatar da zahirin wadannan Nassoshin Siffofin Allah sharri ne da bata da kafirci me ya sa Annabi (saw) bai bayyana wa al'ummarsa ya tsoratar da su a kan yin hakan ba?

To in dai Annabawa da Manzanni suna da ilimi, kuma sun iya bayani, kuma su masu Nasiha ne ga mutanensu, masu so musu alheri da shiriya ne, ta yaya za su bar mutane cikin duhu da bata, su zo da Nassoshi masu nuna cewa: Allah yana da fiska, yana da hannaye biyu, yana da kafa, yana da Sura da sauransu, alhali kuma Allah ba shi da wadannan Siffofi, kuma tabbatar masa su "Tajsimi" da "Tashbihi" ne?

Kuma idan Tawile-tawilen Asha'ira su ne gaskiya, me ya sa Annabi (saw) ko Sahabbansa ba su yi mana bayani ba, su ce: ga gaskiyan abin da ake nufi da Nassoshin?

Yanzu zai yiwu su wadannan Malaman Asha'ira su zama sun fi Manzon Allah (saw) sanin Allah kenan, ko sun fi shi iya bayanin gaskiya, ko sun fi shi son tsarkake Allah, sun fi shi son shiryar da mutane, shi ya sa shi ya bai bayyana ba, su kuma suka bayyana?!

Dan Jahamiyya ya ce: Ai kai Basalafe ne Mujassimi, ba za ka fahimci gaskiya ba, saboda Ibnu Taimiyya ya bata maka tunani.

Ahlus Sunna ya ce: Ina binka bashi fa Malam, dole ka zo ka ba ni amsoshin tambayoyina.

Dan Jahamiyya ya ce: Babu wata amsa da zan ba ka, tafi ka ba ni wuri Mujassimi kawai.

Ahlus Sunna ya ce: Allah ya shirye ka, ya sa ka dawo bin Alkur'ani da Sunna da Mazhabar magabata, ka bar Mazhabar 'Yan Falsafa da Jahamiyya da yaransu; Mu'utazila da Asha'ira.

Ma'assalama..

Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)

09 September, 2022

Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

Post a Comment

0 Comments