𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum, Mallam Khamis. Ni namiji ne mai tsoron in ma mace magana ina son ta kuma ga shi ina son na yi Aure, yaya zan yi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh.
Tsoron tunkarar mace
da soyayya abu ne na halitta kuma mafi yawan maza suna fuskantarsa, musamman
idan mutum yana da tsananin kunya. Kunya tana da kyau, amma idan ta wuce kima
har ta hana ka cimma burinka na rayuwa, to lallai kana bukatar ka canza takun
takawa.
Ka sani cewa mata ma
mutane ne kamar kowa, kuma suna da tasu kunyar, kuma mafi yawancinsu suna
mutunta namiji mai kunya da tsoron Allah. Macen da take da tarbiya yia ba za ta
taɓa wulakanta namiji da
ya nuna yana son ta da aure ba, koda ba ta ra'ayinsa.
An karɓo hadisi daga Anas
dan Malik (Allah Ya ƙara yarda da shi) cewa wani mutum yana tare da Manzon
Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) sai wani mutum ya wuce ta wajen sai ɗayan ya ce: Ya Manzon
Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam), ina son wannan mutumin. Sai Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce masa: “Shin ka gaya masa?” sai Ya ce: A’a.
Sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce: “Faɗa masa.” Don haka ya
same shi ya ce: Ina son ka don Allah. Shi kuma Ya ce: wanda ka so ni saboda shi,
shi ma ya ƙaunace ka. Abu Dawuud Ya ruwaito shi (no. 5125) da Imamul
Nawawi a cikin Riyadh Saliheen (183) kuma Albaani ya ruwaito shi a cikin Saheeh
Abi Dawud.
An karbo daga ‘Ali
ibn al-Husayn bin’ Ali dan Abi Taalib (Allah Ya yarda da shi) ya ce: Manzon
Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: “Idan dayanku ya
kasance yana son dan’uwansa Saboda Allah, to ya fada masa, domin yana da kyau
kuma yana sanya soyaya yia ta daɗe.”
Sannan Uwar Muminai, Uwar
gidan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) Nana Khadija ita ce Tace tana
son Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam). Sabida Kyawawan Halayensa. Kuma
ya Aureta, daga baya Allah ya Sanya Musu Albarka. Wanda bai Taɓa Haihuwa da wata
Mata ba, in banda Nana Khadija. Ita ce Uwar Ya'yansa, ita ce wadda ta Taimaka
Masa da Kuɗinta da Lokacin ta, tin
a Farkon Musulunci.
Sobada haka idan mace
ko namiji yana son mace to ya sanar da ita, yana sonta ko ta hanyar kira ta
waya ko ta tezt Massage ko ta hanyar social media, kamar WhatsApp ko Facebook
da sakon zai kai gare ta, ko ya nuna Mata wata Alama da za ta iya gane hakan.
Anan, za a samu saurayi ko budurwa suna son junansu, amma sai su kasa faɗawa junansu saboda kunya ko tsoron wani abu. A rashin faɗawar kuma, sai ka ga soyayya ta dakushe a hankali, ko kuma su shiga wani yana yi na tunani daban.
Manzon Allah
(Sallallahu Alaihin Wasallam) Ya ce hakika idan ɗayan ku ya ga wata mace sai ta kayatar
da shi toh ya tafi wajan iyalin sa, hakika yin hakan zai mayar da abin da ya ji
a zuciyar sa. Muslim ne ya ruwaito shi (hasanun sahihun).
Kada ka damu idan ba
za ka iya yi wa mace magana kai tsaye ba saboda tsoro ko fargaba. A al'adance
da kuma a Musulunci, ba lallai sai kai da kanka ka tunkari mace ka baya yiana
mata soyaya yia ba. Idan akwai macen da kake so, za ka iya tura magabata ko
amfani da dangi ko wani babban abokinka wanda ka yarda da shi, Su yi maka
magana. Za su iya tunkarar yarinyar ko iyayenta don baya yiana musu niya yiarka
ta gari ta son yin aure.
Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce; "Idan wanda kuka yarda da
addinsa da dabi'unsa yazo neman aure wajenku ku aura masa. Idan baku yi hakan
ba, to ɓarna mai yawa za ta kasance
a bayan kasa. Tirmizi ya ruwaito shi.
Ka yawaita yin
addu'ar neman zaɓin Allah (Istikhara)
da kuma addu'ar neman buɗe baki kamar yadda
Annabi Musa (A.S) ya yi:
رَبِّ
اشْرَحْ لِي صَدْرِي وَيَسِّرْ لِي أَمْرِي وَاحْلُلْ عُقْدَةً مِّن لِّسَانِي
يَفْقَهُوا قَوْلِي
"Ubangijina! Ka
buɗe mini ƙirjina. Ka sauƙaƙe mini al'amarina. Ka
kwance kulli daga harshena, domin su fahimci maganata."
Wannan ita ce addu'ar
da Annabi Musa (A.S) ya yi lokacin da Allah ya umarce shi da ya tafi wajen
Fir'auna. Addu'ar tana cikin Suratul Taha, aya ta 25 zuwa 28.
Wannan addu'a neman ƙarfin gwiwa ce, tana sanya natsuwa da cire fargaba a zuciya. Tana sa Allah ya
sauƙaƙe maka duk wani abu
mai tsanani. Tana taimakawa wajen yin magana mai fita daddala wadda mutane za
su fahimta da wuri. Ya dace a karanta ta kafin yin jawabi, jarabawa, ko wata
tattaunawa mai muhimmanci.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.