Ticker

6/recent/ticker-posts

Shin Akwai Bambanci Tsakanin Sallar Namiji Da Ta Mace?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Salamu Alaikum akaramakallah barka da wannan lokaci don Allah a amsa min wannan tambayar; shin dole ne sai mace ta yi iƙama idan za ta yi sallah, kamar yadda maza suke yi idan za su yi sallah?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuh.

Toh shi Sallah dai babu wani banbanci a tsakanin Namiji da kuma mace a wajen yin sa. Ya tabbata a cikin Hadisin Maalik Bn Al-Huwairith (Radiyal Laahu Anhu) cewa Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

« ﻭَﺻَﻠُّﻮﺍ ﻛَﻤَﺎ ﺭَﺃَﻳْﺘُﻤُﻮﻧِﻰ ﺃُﺻَﻠِّﻰ »

Kuma ku yi sallah kamar yadda kuka ganni ina yin sallar. (Sahih Al-Bukhaariy: 631)

Wannan gamammiyar dokar ta haɗe maza da mata daga cikin musulmi, sai in an samu wurin da ya cire matan daga hakan.

Al-Imaam Al-Mujaddid Al-Albaaniy a ƙarshen littafinsa: Sifatu Salaatin Nabiy (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya baya yiana cewa: Babu wani abinda ya zo a cikin Sunnah da yake hukunta cire mata a cikin siffar Sallar Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam). Har kuma ya kawo maganar da Ibn Abi-shaibah ya riwaito da ingantaccen isnadi daga Ibraahim An-Nakhaiy (Rahimahul Laah) ya ce:

ﺗَﻔْﻌَﻞُ ﺍﻟْﻤَﺮْﺃَﺓُ ﻓِﻲ ﺍﻟﺼَّﻠَﺎﺓُ ﻛَﻤَﺎ ﻳَﻔْﻌَﻞُ ﺍﻟﺮَّﺟُﻞُ

Mace a cikin sallah tana aikata irin abinda namiji yake aikatawa ne. (Aslus-Sifah: 3/1040)

Sabida haka yadda Maza suke yi da kuma yadda Mata za su yi nasu kamar duk abu ɗaya ne kamar yadda Sunnar Manzon Allah (Sallallahu Alaihin Wasallama) Ya koyar kuma Ya ce ayi, sai dai wasu lokutan akwai dan banbanci a tsakanin Sallar Namiji da kuma Mace.

Shi Namiji an Shar'anta masa cewa idan zai yi Sallah ya yi kiran Sallah ko da a ce a dokar daji yake ko shi kaɗai ne, hakanan idan zai yi karatun Sallah ko Mace na kusa da shi, ko Maza ne a kusa da shi an Shar'anta masa cewa ya Ɗaga muryar sa a inda ake baya yiana karatun Sallah ɗin, wato ya baya yiana karatun ko da kuwa wanda suke Meter uku ko huɗu za su iya jin Sautin karatun nashi babu matsala wannan.

Amma ita Mace bahaka ba ne, matukar akwai Namiji a kusa da inda take yin Sallah, toh bai halatta a ce ta Ɗaga sautin muryar ta har na nesa ko na waje suna jin ta ba, ko da wanda suke tare ya kai Meter 1 ne, sai dai ta yi shi ta yadda na kusa da ita ba ya jin Sautin karatun ta, ita mace zatayi karatun ne a hankali domin kada ta Ɗaga muryar ta ya dawo fitana, kuma ba zatayi kiran Sallah ba. Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce Ku yi Sallah a inda ake kiran Sallah Maza ke nan, amma mata bahaka ba ne, idan an ce wannan Masallacin ba su kiran Sallah haka kawai suke shiga su yi Sallar su, toh bai kamata na bi su ba sai na tafi inda ake kiran Sallah na yi Sallata a wajen don Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ne Ya ce haka. Amma su mata A'a. Kin ga ke nan akwai banbanci a tsakanin Sallar namiji da kuma Mace.

Sa'annan a gurin wasu malaman suka ce baya Halatta Mace ta yi karatun Sallah a baya yiane kawai sai dai ta yi sa a Ɓoye kamar yadda take yi a Sallar Azahar da La'asar, an samu saɓani akan hakan suka ce ai muryar Mace Al'aura ce, waɗanda suka ce za ta iya baya yiana karatun ta, su kuma suka ce idan ma za ki baya yiana karatun, toh iya kunnen ki ne kaɗai ke jin sautin muryar naki bawai za ki ɗaga murya sosai irin yadda Maza yake yi ba, ko a aikin Hajji idan an je gurin Talbiya Mace ba ta buɗe Bakin ta da karfi irin na Maza, aka ce ta yi kasa da muryar ta. Kuma Mace idan zatayi Sallah abun da ake so shi ne za ta haɗe Jikin ta ba za ta bubbude jiki sosai kamar yadda Maza suke yi ba. kin ga ke nan akwai banbanci tsakanin Sallar namiji da na Mace, Namiji duk waɗannan ba a ce kada ya yi su ba, amma mace akwai yadda aka ce ta yi, sabida haka akwai banbanci a wasu lokutan.

Ki duba cikin Littafin (Ibnu Ƙudama a cikin Almugni) Ya ce Ijma'in Malamai sun tafi akan cewa ba dole ba ne idan Mace za ta yi Sallah sai ta yi kiran Sallah, ko sai ta yi iƙamar Sallah ba wannan Ijma'i ne na Malamai inji Ibnu Ƙudama, akan cewa ba dole ba ne idan Mace za ta yi Sallah sai ta yi iƙama, ko ta yi kiran Sallah ba. Amma Maza an shar'anta musu yin haka, sun din ma idan a Jam'i ne, toh iƙamar da Ladan ya yi ko wanin sa ta wadatarwa dukkan Mamu bawai kowa sai ya yi nashi daban ba.

Amma idan kin yi iƙamar ba tare da kin Ɗaga Muryar ki, sautin muryar ki ya fita har can-can ba ta yadda ko na Meter 2 ba zai ji ki ba wato kin yi a hankali, toh wannan Malamai sun ce babu laifi Mace ta yi iƙamar ta kamar irin su Imamul Shafi'i, da Imam Ahmad sun ce babu laifi ta yi.

Amma ki sani cewa ba wajibi ba ne ga Mace a ce sai ta yi sa, idan kuma ta yi toh ba ta yi laifi ba hakan ya yi wannan shi ne Ra'ayin Sheikh Muhammad Nasiruddeen Albani a cikin Littafin sa Tamamul Minnah. Sa'annan ki nema darasin mu na Siffatul Salatul Nabiya yii ki karanta su domin mun kawo misalan sosai tare da hujjoji. Allah muke roko har kullum Ya kara mana Imani Ameen.

WALLAHU A'ALAMU

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam  

Post a Comment

0 Comments