𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam khamis Fatan ka wuni lafiya Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana me Albarka. Malam khamis dan Allah ina son a ba ni shawarwari akan yadda zan zauna lafiya cikin farin ciki, biki na saura wata huɗu kuma kullum in na tuna irin matsalolin gidajen aure da muke ji yau da gobe sai nake ta jin tsoron auren gaba ɗaya.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh.
Ina taya ki murna da
samun wannan babban alheri na kusa shiga gidan aure! Abin farin ciki ne, kuma
al'ada ce ga duk wani da zai ɗaurawa kansa wannan babban nauyin ya ji fargaba ko tsoro,
musamman idan aka duba yadda labaran matsalolin aure suka cika gari a yau.
Kada ki bari tsoro ya
kashe miki gwiwa. Zama lafiya cikin farin-ciki a gidan aure yana yiwuwa idan
aka gina shi akan ingantaccen harsashi. Ki dena Tsoron Aure. Domin Shi Aure
Wata Ibada Ce Mai Zaman Kanta. Allah ne Da Kansa ya yi Umarni da Yin sa Kamar
yadda ya yi Umarni da Yin Sauran Ibadu a Cikin Alƙur'ani da Kuma
Hadisan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam).
Ki Shiga auren da niya
yiar yin biyaya yia ga Allah da kuma gina iyali na gari. ki Kasance Mai Biyaya
yia Sau da Kafa ga Mijin ki. Ki sani za ku fito daga gidaje daban-daban, don
haka dole a sami bambancin ra'ayi. Ki Karɓi mijinki da halayensa na kwarai, kuma ki yi haƙuri da kasawarsa.
Gidan aure gidan
yafiya ne. Wanda bai iya yafe laifi ba, ba zai daɗe yana farin ciki a gidan aure ba. Ki
Zama Mai Hakuri da Kawar da Kai Akan Abinda Mijinki ya yi Miki na Saɓani. Musamman ma
Wanda ya yi Miki cikin rashin sani.
Labarin cikin gidan
aurenki na daɗi ko na baƙin-ciki ya tsaya
tsakaninki da mijinki kawai. Kar ki riƙa kwatanta aurenki da
na kawayenki ko na mutanen kafofin sada zumunta (Social Media). Kowane aure da
irin nasa jarrabawar.
Ki Zama Mai Tsafta a
Gidan Mijin Ki. Domin Rashin Tsafta Yana Mugun Bayar da Matsala a Rayuwar Aure.
Kina Kula da Hamatar ki, Gabanki, Kitso Akan Kari, Wanke Kafarki, bakinki, Ki
Zama Mai Sanya Turare na Jiki da na Tufafi da na Ɗaki a Koda yaushe.
Idan Zai Yiwu Ki Kula da Wanke Kayan/Tufafin Mijinki da zarar ya Fitar da Su
daga Jikin sa ki ɗauka ki Wanke Masa.
Ki Rungumi shagwaba, kalamai
masu daɗi, da nuna kulawa ta
musamman ga bukatun mijinki. Ki Zama Mai Kokarin Wajen Sarrafa Abincin da
Mijinki Zai Ci, ya Zama Mai Daɗi da Tsafta.
Ki Kasance Mai Kiyaye
Zantattuka na Barkatai. Musamman zugar Kawaye ko Makota ko Zantattukan Gidan
Biki ko Suna. Domin Akasari Duk Wata Fitina daga nan Ake Kullo ta.
Ki kiyayi Wayar
Hannun ki. Kinga Wannan Wayar da kike gani, Nan da nan Za ta iya Kashe Miki
Aure. Mace Rauni ne da ita. Sai kiga ba tare da Kin Ankare ba, Sai Wani Namijin
ya ɗauki Hankalinki ta
hanyar waya, Akan Abinda ke kina Ganin ba Komi ba ne, nan Kuma Babbar Matsala
Ce ga Matar da take Zaman Aure. Kuma nan da nan Sai kiga kin Sami Matsala
Tsakanin ki da Mijin Ki.
Idan Zai Yiwu, ki
Sami Wata Sana'ar da zakike Taimakon Kanki da Kanki Kuma ki Taimakawa Mijin ki
Akan Abinda yafi Karfinsa. Ki yi murna da duk abin da mijinki ya kawo miki, komai
kankantarsa ki yi masa godiya. Wadatar zuciya tana kawo albarka acikin gidan
aure.
Idan za ki fita ko
nan da Makota ne. Ki tabbatar da Cewar da izinin Mijin ki. Kar ki Baiwa Wani
Namiji Damar Shiga Gidan Auren Ki, har Sai da Izinin Mijinki. Sai Wanda Kika
Tabbatar da Cewar Ɗan'uwanki ne Wanda babu Aure a Tsakanin Ki da Shi.
Ki Girmama Iyayen
Mijinki da Kuma Yan'uwansa. Domin duk Lokacin da Kika Sake kika Sami saɓani da Dangin
Mijinki. Kamar da Mijinki Kika Sami Matsala. A koda yaushe za Suke zuga Shi
Akanki, har Sai ya ji ya Tsane ki. Kinga Kuwa Idan Miji ya Tsani Mace, Sai dai
Kuma Rabuwa.
Idan Mijin Ki ya
Tashi Kara Aure. Karki tayar da Hankalinki. Ki yi Addu'ar Idan Alkairi ne, Allah
ya tabbatar, Idan Kuma ba Alkairi bace, Allah ya Chanja Muku Mafi Alkairi.
Domin Wata Matar ta Gwammace da Mijin ta ya Kawo Mata kishiya, Gwanda ya saketa
ta Fita ta bar Mata Gidan, ita Kuma ta koma Gidan su ta Kama Zawarci. Wanda
Kuma Wannan Shi Ake Cewa "SAKE RISHE KAMA GANYE".
Babu ke babu Harkar
Malaman Tsubbu da Bokaye, ko Wata za ta je Miki Kar ki yadda. Ki Riki Allah, Shi
ne Kaɗai Zai Baki Kariya, duk
Abinda zai Baki, babu Mai Hanawa, haka Duk Abinda Bai Baki ba, babu Wanda ya
Isa ya Baki.
Ki rike Addini sau da
Kafa, ki Kula da Addu'o'i da Sallolin dare, Waɗanda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi
Wasallam) ya karantar da Kula da Su. Za su Taimaka Miki Kuma za su kare ki daga
Sharrin duk Wani Shaidani na Kusa da na Nesa.
Ina yi Miki Addu'ar
dacewar duniya da Lahira, Ina Yi miki Addu'ar Allah ya sa Kin dakko Miji na
Kwarai, Mutumin Kirki Mai Addini. Domin Duk Macen da ta Dakko Namiji Mai Bakin
Hali, Akwai Babbar Matsala, Sannan Kuma Wannan ba Karamin Barazana ba ne ga
Rayuwar Matar da ta Dakko Irin Wannan Namijin da har ya Kasance a Matsayin
Mijinta ba. Sabida haka Matukar dai na Gari ne, In Sha Allahu ke Kan ki za ki
ji dadin Zama da Shi, Kuma Za a Taya Ki Murna da Farin-Ciki Akan Kasancewar ki
tare da Shi.
Zan Ɗan Takaita a nan.
Domin Gaskiya Abubuwan Suna da yawa. Wanda na sani in Sha Allahu Idan Kin Riki
Waɗannan Shawarwari da
na Baki, za ki Zauna Lafiya acikin gidan aurenki. Allah ya Sanya Albarka. Allah
ta'laa yasa mudace. Ameen
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.