Ticker

6/recent/ticker-posts

Hatsarin Da Ke Tattare Da Zuwa Wajen Boka Ko Dan Duba

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamualaikum. Tambayana shi ne na kai shekara ishirin da uku mallam ina da samari amma dukka babu na aure da an yi magana sai ya watse, kuma ni kammamiya ce ban zina ban zuwa fati, ban yawan jin wakoki kawai jarraba ce daga Ubangiji, sannan mallam an kai ni gurin wani mallami ya ce wai na kai agwagwa da kaza za a min aiki wai bakin iska ne dani, shin mallam ya halakta a cikin addinina ko kuwa?

HATSARIN DA KE TATTARE DA ZUWA WAJEN BOKA KO ƊAN DUBA

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Waalaikumussalamu Baiwar Allah Baihalatta ba Kuma shi wannan mutumin ba malami bane Kuma maganganunsa sun tabbatar da cewa  boka ne /Ɗan duba ne. Saboda haka ku kauracewa zuwa gurin irin waɗannan bokayen Sannan Kuma idan bakusan cewa boka bane kukaje gurin sa, To kuyi gaggawan tuba ku nemi gafarar Allah. Amma idan kunsan cewa boka ne, amma kuka je gurinsa, to hakika kun kafircewa. Abin da Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya zo da shi kamar yadda ya tabbata a cikin ingantattun hadisai.

Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce: Duk wanda ya je gurin Ɗan duba ko boka sai ya kuma ya gasgata abinda yake cewa to

hakika ya karficewa abinda aka saukarwa Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam). A wani hadisin kuma cewa yayi; Duk Wanda ya je wajan ɗan duba sai ya tambaye shi wani abu to ba za’a

karbi sallar sa ba ta kwana arba’in ba. A wani hadisin kuma cewa yayi “Baya daga cikimmu duk wanda yake yin camfi ko a ke yimasa camfi ko yayi bokanci ko ake yi masa bokanci, ko yayi sihiri, ko ya sa ayi mishi sihirin, duk kuma

wanda yaje wajan boka sai ya gaskantashi a aduk abinda yake cewa to hakika ya kafircewa abinda aka saukarwa Annabi Muhammad (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).

'Yan uwa kunji Hatsarin dake tattare da zuwa wajen boka ko Ɗan duba kuma Yana kaiwa ga fita daga musulunci domin duk wanda yaje Yana sane ya zama kafiri kuma gara ya Dena sallah da Azumi. Domin ya kafircewa Allah da manzonsa, kuma Allah baya karbar sallah da azumin wanda ba musulmi ba.

Baiwar Allah sai ku nisanci zuwa gurin irin waɗannan bokayen kunji dai duk wanda ya je gurin su ya tambayesu wani abu ba za a karɓi sallar sa ta kwana arba’in ba idan kuwa ya gaskata su ya kafirta. Saboda haka saiki godewa Allah Abisa ni'imar da yayi miki ta samun damar tambaya dangane da wannan al'amari.

Baya halatta ga maralafiya ya je wajan bokaye da suke ikirarin sanin abubuwan da

ke ɓoye, wai don ya gano masa rashin lafiyansa, kamar yadda baya halatta ya

Gasganta su cikin abin da su ka bayar da labarinsa.

Sannan kuma yana dakyau ku sani akwai hanyoyin da shari'a ta amince na neman magani, musamman abinda ya shafi jinnu. Wani abu da mafi yawan Mata basu sani ba shi ne: Babu yanda za'ayi a cire aljani ta hanyar aljani, saidai ma a sake jajibo wasu.

Saboda haka ku nisanci dukkan gurin masu ce muku sai anzo da agwagwa ko kaza ku bakin zakara ko bakar akuya dasauransu. Waɗannan abubuwan duk aljanun ne suke umarta da akawo, kuma duk wanda ya kai ɗaya daga cikin abubuwan, hakika ya bautawa aljanu saboda ya kafirta. Saboda haka ku ziyarci cibiyoyin shari'a ta amince dasu waɗanda suke cire aljanu da ayoyin Alƙur'ani ta hanyar yin ruƙiyya da addu'o'i ba irin waɗannan bokayen ba.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Za ku iya samun shafinmu ta wannan hanyar...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments