Ticker

6/recent/ticker-posts

Tambayar Kabari

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum, malam. Dan girman Allah, ina da wata tambaya: wai idan mutum ya mutu, ana yi masa tambayar kabari ko ba za a yi masa? Wai mala'iku ba sa zuwar wa mutum cikin kabarinsa; wai idan ya mutu, shikenan sai ranar da za a busa kawo.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuh.

A koyarwar Musulunci, idan mutum ya mutu aka binne shi, lallai mala'iku biyu (MUNKAR da NAKIR) za su zo wa mamaci, su zaunar da shi, su yi masa manyan tambayoyi uku Kamar haka: Wanene Ubangijinka? Menene addininka? Wanene Annabinka? Ko me kake cewa game da wannan mutumin da aka aiko a cikinku?

Allah zai tabbatar da harshen Muminai su ba da amsa daidai cikin sauƙi. Bayan sun amsa, za a buɗe musu ƙofa zuwa Aljanna kuma kabarinsu zai faɗada.

Munafukai ko kafirai ba za su iya ba da amsa ba. Za su riƙa cewa "Hah, hah, ban sani ba." Wannan zai janyo musu faruwar azabar kabari.

Daga nan ne ake nuna wa mumini ko kafiri makomarsa, kuma ake fara jin daɗi ko azabar kabari kafin tashin alkiyama. Wannan shi ne abin da aka sani da rayuwar kabari ko fitinar kabari, ba sai ranar tashin kiyama ba.

Babban ayar da malamai suka fassara da nuna tambayar kabari ita ce faɗin Allah Ta'ala:

يُثَبِّتُ اللّٰهُ الَّذِيۡنَ اٰمَنُوۡا بِالۡقَوۡلِ الثَّابِتِ فِى الۡحَيٰوةِ الدُّنۡيَا وَفِى الۡاٰخِرَةِ ۚ وَيُضِلُّ اللّٰهُ الظّٰلِمِيۡنَ ۙ وَيَفۡعَلُ اللّٰهُ مَا يَشَآءُ

"Allah Yanã tabbatar da waɗanda suka yi ĩmãni da magana tabbatacciya a cikin rãyuwar dũniya, da cikin Lãhira, Kuma Allah Yanã ɓatar da azzãlumai, kuma Allah Yanã aikata abin da Yake so" (Surah: Ibrahim, Ayat: 27).

An ruwaito daga Sahih al-Bukhari da Muslim cewa Sahabi Al-Bara' ibn 'Azib ya ce wannan ayah ta sauka ne game da azabar kabari da amsa tambayoyi (lokacin da aka ce wa mamaci: Waye Ubangijinka? Me ye addininka? Waye aike zuwa gare ka?). Lokacin da mumini ya amsa da cewa Ubangijinsa Allah ne kuma Annabinsa Muhammad ne (Sallallahu Alaihi Wasallam), sai wannan aya ta zama siffar tabbatar masa da gaskiya.

Wata ayar kuma da malamai ke amfani da ita wajen tabbatar da rayuwar kabari da abin da ke ciki ita ce ta Surah Ghafir Ayah ta 46 game da nunawa 'yan kabari wuta:

اَلنَّارُ يُعۡرَضُوۡنَ عَلَيۡهَا غُدُوًّا وَّعَشِيًّا ۚ وَيَوۡمَ تَقُوۡمُ السَّاعَةُ اَدۡخِلُوۡۤا اٰلَ فِرۡعَوۡنَ اَشَدَّ الۡعَذَابِ‏

"Wutã, anã gitta su a kanta, sãfe da maraice, kuma a rãnar da Sa'a take tsayuwa, anã cwa, "Ku shigar da mutãnen Fir'auna a mafi tsananin azãba." (Surah: Ghafir, Ayat: 46).

Wannan yana nuni da cewa ana nuna musu wuta safe da yamma a rayuwar kabari kafin a shigar da su azaba mafi tsanani a ranar kiyama.

An ruwaito daga Usman dan Affan (R.A) cewa: "Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya kasance idan ya gama rufe mamaci yakan tsaya a kan kabarin ya ce: 'Ku nemawa dan'uwanku gafara, ku roka masa tabbata, domin shi a yanzu ana tambayarsa'". Wannan ruwayar tana da tushe a cikin Sunan Abu Dawud, kuma malamai sun zayyana cewa yana nuni ne ga tabbacin amsa tambayoyin mala'iku MUNKAR da NAKIR.

Sabida Haka Ýan uwa tambayar 'kabari gaskiya ce kuma sai ta tabbata akan kowa, Kuma duk wanda kukaji yana da'awar cewa Babu tambayar 'kabari, azabar 'kabari ko babu rayuwar 'kabari to shi din munafuki ne ko kuma kafiri ne ko kuma yana shakka akan Manzoncin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) to kunga su kansu masu karyata tambayar 'kabarin koda suna kiran kansu musulmai idan suka mutu a haka da wannan a'kidar to suma basa daga cikin mutanan da zasu amsa tambayar 'kabari domin munafukai da kafirai da masu shakka da kokonto basa iya amsa tambaya kabari.

Dukkan mutanen da suka mutu za a yi masu tambayoyin kabari, amma akwai wasu rukunin mutane da aka kebe da su ba za a yi masu irin jarrabawar ko azabar da sauran suke fuskanta ba. Akwai waɗanda aka ambata a cikin ingantattun hadisan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) cewa Mala'iku MUNKAR da NAKIR ba za su yi masu tambaya ba. Allah zai tsare su daga fitina ko tambayoyin kabari, Wadannan sun haɗa da:

1. SHAHIDI: Wanda ya mutu a fagen daga yana yaki domin daukaka kalmar Allah, hadisi ya nuna cewa takobi a kan kansa ya isa jarrabawa, don haka ba za a yi masa tambayar kabari ba.

2. YARA KANANA DA MAHAUKATA: Waɗanda ba su balaga ba ko ba su da hankali a lokacin mutuwarsu, ba su da lissafin aikata saɓo, saboda haka ba a musu tambayoyin kabari.

3. WANDA YA MUTU RANAR KO DAREN JUMA'A: Akwai hadisi sahihi da ya nuna cewa duk Musulmin da Allah ya karbi ransa a ranar Juma'a ko daren ta, Allah kan tsare shi daga fitinar kabari.

4. ANNABAWA: Malamai sun ce Annabawa ba a musu irin wannan tambayar ba domin sun riga sun wuce wannan mataki na jarrabawa.

5. MAI GADIN DOKA (AL-MURABIT): Wanda yake tsaron iyakar Musulunci a kan hanyar Allah, inda a hadisi aka ce ayyukansa na cigaba da gudana har zuwa tashin Alkiyama.

Dukkan sauran halitta ban da waɗannan kebabbun mutane, kowane mutum (Musulmi ko kafiri, mai zunubi ko mai biyayya) za a yi masa tambayoyi uku a cikin kabarinsa: Waye Ubangijinka? Menene addininka? Waye a ka aiko muku manzo?

Ya Allah ka ɗauki rayuwarmu muna musulmai masu imani da Annabinka muhammad {Sallallahu Alaihi Wasallam} ka bamu sa'ar amsa tambayar kabari. Ameen Ya Hayyu Ya Ƙayyum 🤲

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Zaku iya samun shafinmu ta wannan hanyar...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments