Ticker

6/recent/ticker-posts

Hakkin Ciyarwa

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Aassalamu alaikum Allah ya kara lafiya da nisan kwana. Malam tambaya na shi ne ni Ina aikin gwamnati mijina Kuma ba yayi Kuma kasuwanci mijina ba me karfi ba ne sai ya zamana duk wani bukatu da kamata ya mana ni da yarsa bayayi sai dai ni na yi, to malam yanzu har yake idan Yana da shi bayayi sai dai ya ce min bashi da kudi ko da kuwa Yana dashi, to malam tambaya a nan shi ne idan nasiya Abu na ci ko na tufatarwa na ci ko na dafa acikin gidansa ba tare da nabashi bah na ci nikadai bawani hakkin akai na bassalamu alaikum?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuh.

A shari'ar Musulunci, ciyarwa da shayarwa da tufatarwa da bayar da makwanci da ilmantarwa, mutuntawa, da kiyaye mutuncin iyali wadannan kusan sune hakkokin da suka rataya akan kowanne namiji alokacin da aka daura masa aure da mace.

Ba wajibi ba ne a kan mace ta ciyar da mijinta ko ta ɗauki nauyin gidansa, ko da kuwa tana da kuɗi. Nauyin ciyarwa, tufatarwa, da kuma kula da iyali yana kan miji ne shi kaɗai. Idan mace ta yi amfani da dukiyarta ta ciyar da mijinta ko iyalinta saboda tausayi da taimako, tana samun babban lada a wurin Allah (SWT). Amma hakan ba wajibi ba ne a kanta, aikin sadaka ne ko taimako. Mace ba ta da laifi idan ta ki ciyar da mijinta, domin ba a ɗora mata nauyin ba. Ainihin nauyin ciyarwa da dawainiyar gida yana rataya ne a wuyan miji bisa shari'a.

Idan miji ya gaza saboda rashin lafiya ko talauci na gaske, za a yi hakuri tare da shi gwargwadon yadda hali ya yi. Idan kuma ya ki yin aikin ciyarwa alhali yana da ikon yi ba tare da wani uzuri ba, babban laifi ne kuma ya saɓawa umarnin Allah da ManzonSa.

Allah Yana cewa:

لِيُنۡفِقۡ ذُوۡ سَعَةٍ مِّنۡ سَعَتِهٖؕ وَمَنۡ قُدِرَ عَلَيۡهِ رِزۡقُهٗ فَلۡيُنۡفِقۡ مِمَّاۤ اٰتٰٮهُ اللّٰهُؕ لَا يُكَلِّفُ اللّٰهُ نَفۡسًا اِلَّا مَاۤ اٰتٰٮهَاؕ سَيَجۡعَلُ اللّٰهُ بَعۡدَ عُسۡرٍ يُّسۡرًا

"Sai mawadaci ya ciyar daga wadatarsa kuma wanda aka ƙuntata masa arzikinsa, to, sai ya ciyar daga abin da Allah Ya ba shi. Allah ba Ya kallafa wa wani rai face abin da Ya ba shi. Allah zai sanya sauƙi a bayan tsanani. (Surah: At-Talaaƙ, Ayat: 7).

اَلرِّجَالُ قَوَّامُوۡنَ عَلَى النِّسَآءِ بِمَا فَضَّلَ اللّٰهُ بَعۡضَهُمۡ عَلٰى بَعۡضٍ وَّبِمَاۤ اَنۡفَقُوۡا مِنۡ اَمۡوَالِهِمۡ...

Maza masu tsayuwa ne a kan mata, saboda abin da Allah Ya fifita sashensu da shi a kan sashe kuma saboda abin da suka ciyar daga dũkiyoyinsu... (Surah: An-Nisaa, Ayat: 34).

Wani Sahabi mai suna Saya yiiduna Mu'awiyatul Kushairi (radhiyal-Lahu anhu) ya tambayi Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) dangane da hakkokin da matan aure suke dashi akan mazajensu. Sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce masa : "Ka ciyar da ita idan kaima kaci, Kuma ka tufatar da ita idan ka rufatar da kanka. (Idan kuna fada da ita) Kada ka mari fuskarta, kada kayi mata wulakanci. Idan har za ka kaurace nata, to kada ka aikata hakan sai a dakinta (wato kada ka kaurace wa matarka sai acikin dakinta). (Abu Maajah da Abu Dawud ne suka riwaitoshi).

Saboda haka idan kin sayi abinci ko kaya da kuɗinki kika cinye ko kika sa ba tare da kin ba mijinki ba ko kin nemi izininsa ba, babu laifi a kanki kuma ba ki da wani zunubi, tunda ke ce da kuɗinki. Kuɗi ko dukiyar da kika samu da gumin ki naki ne. Ba ki da wani laifi idan kin kashe shi a kan abincinki ko suturarki.

WALLAHU A'ALAMU

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam  

Post a Comment

0 Comments